Kenza eBookz

Batuol mamman complete novel - Chapter 20

Batuol mamman complete novel - Chapter 20

Batuol mamman complete novel Chapter 20: Batuol mamman complete novel Chapter 20. "Kaddai? Nooo it can't be." Ya nanatawa kansa da sauri. Girgiza kai yayi…

3,319 words

"Kaddai? Nooo it can't be." Ya nanatawa kansa da sauri. Girgiza kai yayi shi kadai gamo da Radhiya yana nema tafiya da nutsuwa da tunaninsa.

Su Fauziyya da suka taho yi masa barka da zuwa kowacce tayi shiru kamar ta hadiyi kota suna jiran su ga me Radhiya za tayi. Dankwali dai gashi nan amma rabin kai a bude yake. Hannunta ta dora a ka taji iya ina ne a bude. Tana ji ta janyo dankwalin a hankali ta tashi bata ce komai ba ta bar falon.

Karar kofa suka ji da karfi wadda ta gwara saboda bacin rai. Zainab ta girgiza kai su Zayyana jiki yayi lakwas. Awwab yana lura da yadda suka sauya su duka ya daure yace "Alheran?" Da sigar tambaya yana tsananta addu'a kada ace wannan ce da ta tashi yanzu.

Kamar jiransa suke suka bushe da dariya gabadayansu. Alheran din da yaci burin gani har ya kasa zaman Katsina ce. Babu wanda ya tsammaci zuwansa Kano a yau ana tunanin zai zauna ya huta amma doki ya hana. Ghazalatu har fushi tayi ya bata hakuri da alkawarin zai dawo washegari. Kin zama tayi a gidan yayi mata shiru da yawa ta tafi gidan Alh Baba wurin kakarta.

"Ita ce ta shige ciki yanzu" Zainab ta bashi amsa da dan murmushinta.

Da ba don da kanta ta amsa masa ba zai ce ko wani salon tsokana ne kuma suke yi masa don ansan yadda ya damu da ita kuma ya matsu ya sake haduwa da ita.

Da hannu ya nuna hanyar da ta bi ya marairaice fuska "wannan din?"

Basu dena dariyar ba kuwa Zainab tace "yau idan kuka shiga hannunta ko kafata bazaku gani ba"

Rige rigen bashi labarin Radhiya suka shiga yi kowa tana fadin nata. Awwab bai san lokacin da ya saki murmushi ba wato bata chanja ba kenan daga sanin da yayi mata. Shiru kusan minti ashirin bata dawo ba abinda bata saba ba. Hadir yana ta kallon kofa Zainab ta fahimce shi tace su dubo mata ita.

"Mama gaskiya ki tura Zayyana ita ce karama"

"Wani sabon abu ne kuka koya a aikeku ku tsaya zaben mai zuwa?" Awwab yace yana dan bata rai.

"Radhiyan ce ai Hamma"

"Come on tashi ki karawo min ita Zayyana"

Tana zumbura baki ta shiga kofar hanyar dakunan. Tun kafin ta karasa take jin shesshekar kuka. Da dan gudu tayi sauri ta bude kofar dakin. Radhiya ta gani kwance akan abin sallah tana kuka fuskarta har tayi ja.

"Uhmm Adda Radhiya kizo inji Hamma Awwab"

Zumbur ta tashi zaune Zayyana ta dan ja baya kadan ta share kamar bata gani ba, cikin yanayin damuwa tace "shi wannan na falon shine Hamma Awwab din?"

"Eh"

"Kunci amanata! babu wanda yace min zai zo kuma aka ki tashina daga falo da zai shigo" Radhiya tace tana sake fashewa da kuka. Yanzu da wane ido zata kalli mutumin da taci burin haduwa dashi saboda irin labaran da ake bata. Ance mata sun shaku da tana karama kuma yana sonta sosai. Ashe ma ya zama dan gayu irin haka kamar likita amma aka bari ya ga askinta.

Zayyana komawa tayi tana jin tausayin Radhiya. Ko ita ce da kwalkwal bazata so ace kowa ya gani ba.

"Ina take?"

"Kuka take yi Mama"

Da 'yar damuwa a fuskarta tace "Yanzu dai Awwab duk kaine ka janyo wannan rigima da ka ga kanta, yau ban san yadda zamuyi ba"

"Ni kuma me nayi daga zuwana" Su Zahra ya tsare da idanuwa "me yasa baku tasheta ta rufe kan ba?"

Kusa dashi Zayyana ta zauna "haka tace wai munci amanarta da bamu tasheta ba ma"

Samun kansa yayi da rashin jindadi, ba haka ya tsara haduwarsu ba. Garin yaya ma aka yi mata aski irin haka don Allah? Sallamar Ibrahim da Zayyan ita ta katse tunaninsa. Zaratan samari ne dake ganiyar tashinsu.

"Kunga Hammana" suka ji Zayyana ta fada tana murmushi ta nuna shi.

"Naki ko namu?" Ibrahim yace yana mika masa hannu.

"Da gani kaine Ibrahim, sau biyu Zayyana tana kawo min kararka. Baka san ba'a tsokanar autar Daddy ba?" Awwab yace cikin sakin fuska.

"To kace ta dena shagwaba ko muma mu fara ko Emzee, mu dinma duka autoci ne"

Kalmar tasa ta karshe ta sanyasu dariya. Awwab ya kalli Emzee yaron is very calm sai murmushi da yake yi kawai. Ji yayi ya burge shi, a fuska ya tuna masa da babansa Zayyan sosai amma wannan Zayyan din da gani ba mai hayaniya bane. Hannu ya mika masa suka gaisa Emzee yana dari-dari ba kamar Ibrahim mai saurin sakewa da sabo ba.

"Dama kai nake jira taimaka ka fito min da yayarka wadannan duk matsorata ne" ya nuna su Fauziyya.

"Kin fitowa tayi?" Ibrahim yace da mamaki "kullum fa zancenta idan ka dawo zata dena kula kowa a gidannan"

" 'Yan cin amana sun saka mana ido ya muka iya yau sunci amanarmu" Awwab yace yana aron kalmar da Zayyana tace tayi amfani da ita.

Ibrahim yace "Mama me suka yi mata?"

Zayyana ce ta bashi labari kafin Zainab ta soma magana.

"Anci amana gaskiya, bari na koma cikin gari na kwana don ga dukkan alamu yau mutanen gidan nan zasu kwana da balotelli"

Emzee ya daki kafadar Ibrahim suna dariya kafin ya nufi dakin. Tana nan zaune hanci ya kumbura, idanu sun kankance sunyi ja saboda kukan da tasha. An cuceta da aka aske mata kai. Da an bar mata na zaman falon da ta roka ko babu komai zai rufa mata asiri yau.

"Adda kizo inji Hamma Awwab"

"Ni fa gida zan tafi"

Daure fuska ta ga yayi "ke babu dama ranki ya baci sai kice zaki je gida? Idan Ummi taji abinda kike yi a gidannan zata ji dadi ne? Kowa na tsoron bata miki rai kina jin dadi kamar abin kirki"

Mamakinsa ta soma yi. Emzee din da babu ruwansa ko me tace ta zauna shine yake mata fada. Jan hanci tayi "to ba kaina suka bari ya gani ba"

"Ance iska kika je sha, kina da wannan kan da kike boyewa ki rasa wurin shan iska sai falo. Yanzu da Kawu Zakari ne ya zo fa?"

"Bakinka ya sari danyen kashi, wannan ai mugun fata ne." tace tana harararsa ta tuna wanda ya dan gani a gidan Baffa Gide.

"Tunda Allah Ya rufa miki asiri ba shi din bane ba sai kawai ki basar ba irin a zuwan baki ma san me ya faru ba. Da nine ke fa wallahi da magagin baccin karya zan bar falon"

Sauran hawayen ta goge da bayan hannunta tana dariya harda kyakyatawa "shege Emzee ka iya bada shawara Yasin"

"Shine zaki zageni to" ya harareta yadda take masa.

Dan ture shi tayi bayan ta daure kanta da dankwali ta saka hijab "wasa ne dalla" ita ce a gaba yana bayanta. Sai da suka zo bakin kofar ta kasa fita tana jin kunya. Emzee na zuwa ya turata ta soma turjewa amma da ta ga kowa ita yake kallo sai ta dake yadda yace mata ta basar.

Duk da kumburin fuskarta bai hana Awwab sake gano kamannin wannan Alheran din mai askakken kai da 'yar karamar kanwarsa mai rigima ba. Ta girma amma tana nan da dan jikinta don tafi karfin a kirata ramammiya sannan baza'a ce ta shiga sahun lukutaye kai tsaye ba. Radhiya a dire take ta ciko ta ko ina. Da kadan ta dara Zayyana a tsayi ita da ake yiwa kallon doguwa saboda tsayin kafa.

Yayin da Awwab ke kokarin hada ido da ita, ita kuma su Zahra ta kalla tana ta kokarin kada ta kalle shi. Tunda Emzee yace ta basar to fa basarwar zata yi.

"Shine baku tasheni nayi sallah da wuri ba Adda Zahra"

"Naga baccin naki yayi dadi ne"

Sai ta maida hankalinta ga Ibrahim "ka fadawa Umma ina gaisheta?"

"Tace kafin ku koma kije kiyi mata kwana biyu"

"Mama gobe zaki sa ya rakani?"

"Sai dai jibi Radhiya. Gobe asibiti zan kaiki ko har kin manta?" Asibiti za ta kaita saboda makeron da yaki barin gashinta yayi abin kirki.

Awwab sai binta yake da ido tana ta jan mutane da hira banda shi kamar ma baya wurin. Sai da Zainab tace "wai baki ga Awwab bane?"

Radhiya ta wani bude baki da idanu irin mamakin nan "laahhhh Mama yaushe yazo? Hamma, oyoyo"

Emzee tashi yayi ya sulale daga falon saboda tsabar kunya. Radhiya halinta sai ita. Yace ta basar kamar ba'ayi ba shine zata nuna bata ganshi ba gabadaya. Ji yayi kamar ya saka kuka da ma bai bata wannan shawarar ba.

"Baki ma ganni ba sai yanzu?" Yace yana kallon fuskarta. Dimple dinnan da yake saka yatsansa a ciki idan tana dariya yake kallo yana tuna masa rayuwar da.

Dakewa tayi abinta "ina na ganka na fito ina ta hira da 'yan uwa, yaya hanya? Ka ga Ummi?"

"Baki ganni ba da kika tashi daga bacci dazun nan?"

Radhiya an koyi basarwa da gaske ta wani langabe kai "yaushe? Ka dade da zuwa ne?"

Wai raina masa wayo zata yi ne? Kowa kallonsu yake yi ana dariya kasa-kasa. Hadir kansa murmushinsa ya kusa zama dariya da ya gane so take ta nuna bata ganshi ba.

Awwab da bai fahimta ba dama shima anyi masa tambarin wauta idan abin dan farin nasa ya tashi yace "dazu fa kin farka har muka hada ido."

Tsuke baki ta soma yi. Ya kamata idan ta basar sau daya kawai a wuce wurin amma sai neman jan zance yake yi.

"Ni din? Bacci fa nayi a kan kujerar nan sai farkawa nayi na ganni a daki su Adda Zahra sun rikeni sun kaini saboda nauyin baccina, ban san lokacin da ka shigo ba"

Zahra ta soma kifta masa ido akan ya bar zancen haka shi kuma ya dage sai ya ga abinda ya turewa buzu nadi.

"Lokacin da abin kanki ya zame haka " ya kwatanta da dan jan dankwalin Fauziyya " har na ga kan...."

Ihu ta saka ta tashi da sauri tana jin kamar taje ta toshe masa baki kada ya karasa fadin ya ga kanta. Kamar zata yi kuka take kallonsa "idan nace ban ganka ba sai kawai ka yarda haka ake yi ko Em..." shiru tayi ta shiga waige da ta ga baya wurin "ina Emzee?" Tayi tambayar tana kallon Ibrahim da dariya tasa ko magana ya kasa.

"Ya fice"

"Ku ga min shegen yaro, shi yace idan na basar kamar ba'ayi ba komai zai wuce."

Gabadaya falon ya sake kaurewa da dariya. Zainab ta tashi ta kama kujerar Hadir "bari naje na bawa babanku magani, Fauziyya ku kawowa Awwab abinci ko ruwa bai sha ba tunda ya shigo kun saka min 'ya a gaba"

Gani tayi ya dace su baiwa yaran wuri don ba ta biye musu ana tunzura Radhiya ba. So take Awwab ya so kanwar tasa da wuri, gara su fara sabawa da juna. Taimakawa Hadir tayi ya kwanta ta dauko takardun asibitin ta koma kusa dashi tana yi masa bayanin kowanne don neman shawararsa. Da ido da yanayin chanjin fuska take fahimtar abubuwa da dama da yake nufi idan tayi masa tambaya.

Sakale tayi tana kallon Awwab yana murmushi "ban san haka kike so ba, to koma ki sake fitowa. I promise zan tayaki basarwa"

Ita ma sai da abin ya bata dariya ta koma ta zauna tana jiran fitowar Emzee ko ma ina yaje ya buya. Dama idan ba ganganci ba me zaisa ta karbi shawararsa. Wautar kanta take gani na biye masa.

Yana jiyo me suke yi a inda ya tsaya ya girgiza kai. Bawa Radhiya shawara wataran kamar zuba gari ne a rariya. Kana fada yana zuba. Ibrahim da Zayyana suka tashi suka bi bayan shi zuwa waje. Ibrahim na cewa ta dena binsa ta murguda masa baki tace ita wurin Emzee zata je ba shi take bi ba.

Ya rage su hudu a falon Awwab ya watsawa su Zahra idanunsa "bazaku bani abincin bane?"

Da sauri Radhiya ta tashi don yau dai taji kunya fiye da yadda ta saba "bari na kawo maka"

"No, dawo ki zauna"

Inkiya yake musu su basu wuri sumsum suka tashi suna dariyar dramar Radhiya.

Kai ta sunkuyar karon farko da zata iya tunawa a rayuwarta ta rasa bakin magana saboda kunyar da ta bawa kanta. Dan gayu kamar wannan kyakkyawa daga ita sai shi a falo ai dole harshe yayi nauyi tace a zuciyarta.

Nazarinta Awwab yake yi ya dago kansa daga jinginar da yayi da kujera yana mamakin wannan yarinyar ta gabansa ita ce Alheran dinnan da yake dauka suyi ta yawo a barrack shekarun baya.

"Alheran" ya ambaci sunanta a hankali taji wani yarr a jikinta saboda yadda muryar ta ratsata.

"Uhmm"

"Kin dena magana ne kuma?" Ya tsokaneta da ya ga kamar ma a takure take.

Girgiza kai tayi sannan tayi kwafa da guntun tsaki "Wallahi kunya naji, ashe ba haka ake basarwa ba. Bari Emzee ya dawo zai gamu dani"

"Balotelli zaki yi masa?"

Dago kai tayi da sauri ya dage mata gira yana jin komai nata na burge shi. Ba haka yayi zaton ganinta ba. Yana ta kissima wata budurwa mai ji da kai da gayu sai ya hadu da Radhiya wadda kwatancenta sai wanda ya santa. Amma duk da haka yaji tayi masa a yadda ya sameta cikin kankanin lokaci. [5/22, 10:51 PM] Sis Ruky: Shadaya da rabi mutanen Katsina suka iso. Radhiya sai murna ta ga Umminta ta kara kyau. Mairama hadaddiyar mace ce da rayuwa ta yiwa cikas. Kwanakin da tayi a Katsina da kulawar Mami yasa jikinta ya kara kyau kamar ba ita ba.

Zahra da Fauziyya na ganin Ghazalatu suka sa ihun murna don basu san da ita za'a zo ba. Mami tace bata san lokacin da zasu girma ba irin wannan tsalle da suke yi. Ita Ghazalatu hankalinta yana kan Radhiya dake zaune a gefen Umminta ana mata tsiyar Ummin na tureta bata ma san tana yi ba. Gaisawa suka yi aka dan taba hira Mami tace gara su zo su dau hanya saboda a ranar suke son dawowa.

"Ku tsaya kuci abinci an gama tun dazu"

Mami tace "muci abinci muji bacci kenan, ni kin sanni da na koshi sai na fara neman wurin kwanciya"

"Shiyasa nake jin alamun kinyi ukun yadda na sanki ashe" Mairama tace tana murmushi.

Yaran dariya suke yi Zainab tace lokaci ne ai, shekarunsu na soma ja zasu fara ajiye kiba ko da ta girma ce.

"Mama banda ni a kibar, mu sojoji ina muka ga lokacin yin kiba muna faman guje-guje a daji"

Sai da kowa ya dara Fauziyya ta tabo Ghazalatu "kinga kanwar Hamma ko, Radhiya ake ce mata. Yini daya kika yi da ita sai cikinki ya kusa ciwo don dariya"

"Na ganta". Gabadaya ranta babu dadi tun da ta ga wacece Alheran din da Awwab yake ta rawar kafa a kai. Tayi zaton wata 'yar yarinya zata gani da bata fi Zayyana ko kasa da haka ba. Dama jiya saboda wannan budurwar mai idanu a tsatstsaye ya taho Kano ya barta.

Shigowar Awwab da Abdallah wanda ya kawo su Mami dan Hussainarta daga waje kenan daidai lokacin da Mamin take ce mata.

"Idan ke soja ce bakiyi kibar ba mijinki da ba soja ba zaiyi ne"

Tsuke baki tayi tana kada yatsa "No, no, no, no , no Mami. Ni likita zan aura fa. Kinsan shima aikinsu babu zama bazaiyi kibar ba"

"Mara kunya" Mairama tace tana daka mata duka a baya. Su Ibrahim an sami abinda ake so suna ta dariya. Zainab ta maimaita musu abinda Radhiyan tace dazu wai ta raina kowa idan ba soja da likita ba.

"Mama mu dasu aikin ceton rai muke yi shiyasa kowa bai kai mu ba"

Mairama sarkin kunya sai ta soma tsoron kada Radhiyan ta fadi wani abin da yafi wannan. Ta tuna ranar da tace mata tana abu kamar ba bafillatana ba. Ita kuwa ta ce dama ba ita bace, su Sakkwatawa ne.

"Ku barni da ita kwanannan zanyi mata miji a aurar da ita mu huta" inji Zainab.

Tun shigowarsu Awwab yake kallon yadda take ta zuba surutu. Dauke kansa yayi ya kalli Ghazalatu ya sakar mata murmushi ta maida masa.

Ibrahim ne yace "Mama ki samo mata malamin makaranta kawai"

"Tabdi, yo ni malamin makaranta ba sai dai na zane shi da dorinarsa ba. Tsorona zai rinka ji"

Fauziyya da ta saka musu ido ita da Awwab tun jiya kuma take fatan hakan tace "ina jin zaki fi dacewa da dreban jirgin sama"

Mami da Zainab har Mairama sai su ka yi murmushi. Ko dai Fauziyyan ta ga wata alama ne take hasashen abinda suke shiryawa. Awwab da yake shan ruwa cire kofin yayi yana son jin amsarta. Abinka da 'Yar soja ta hade rai "ke kadai ce bakya sona Adda Fauziyya. Me zanyi da dreba sai kace ta kare min?"

Kowa yayi shiru yana kallon Awwab da ya zuba mata idanu harda Ghazalatu da misalin na Fauziyya ya kona mata rai. Bata san suna yi ba bare ta gyara zancen.

Zahra ce ta tace "mun ganku a rana ke da Hamma Awwab tunda shima dreban jirgin ne"

Ba arziki Radhiya ta tashi yana tsaye ya harde hannuwansa a kirji. Tayi zaton zaiyi fushi sai ta ga shi ya fara dariya kafin sauran "wato mu sai ta karewa mace za ta auremu ko"

"Wayo Adda Fauziyya tayi min ba haka nake nufi ba. Maimakon tace pilot yadda zan fahimta"

"Sannu Queen Elizabeth wato sai anyi turanci zaki fahimta" Ibrahim yace.

"Ka kiyayeni Surbajo" A dolensa yayi shiru da yaji abin zai dawo kansa.

Tsokanarta suka cigaba da yi tana karewa kanta. Awwab yana kallon Ghazalatu yace da Radhiya "ki shirya zata kare miki kwanannan kuwa don sai kin auri pilot. Kafin nan kuma ki zamarwa matata 'yar aiki"

Mama da Zainab suka kalli juna suna gyada kai da murmushi. Bakin mota suka firfito Mami da Ummi zasu bi karamar motar sauran kowa yace bus din da Awwab zai tuka zasu shiga. Radhiya da jikinta yayi sanyi tana jin babu dadi akan maganar da tayi tace ita ma motarsu zata shiga sai ta zauna a gaba.

"Koma cikin 'yan uwanki Radhiya" Zainab tace tana turata bakin daya motar.

Awwab ta kalla ko zaiyi magana sai ta kula hirarsa kawai yake yi da Ghazalatu. Juyowa yayi ya kalli Radhiya duk ta zama wata salihar karfi da yaji "ina zuwa" ya cewa Ghazalatu ya taho inda take tsaye a jikin motar.

"Zo in nuna miki wani abu"

"Wai ba fushi kayi da abinda nace ba kake yi min magana"

Murmushi yayi "Silly girl, kawai sai nayi fushi bayan nasan ta kusa kare miki kwanannan...auren dreba ba fashi"

"Shine ka barni inata damuwa, kuma a gaba zan zauna inyi ta ganinka tunda yau zaku dawo"

Wurin wata katuwar fulawa inda Ghazalatu ke tsaye suka nufa. Suna jiran iyayensu su gama maganar da suke yi su dau hanya ne shiyasa basu tafi ba.

"Dama babu mai zama wurinki ne nima inyi ta kallonki"

Dariya tayi fuskar Ghazalatu ta hade tsaf da kishi. Awwab yasan me yake bata mata rai don yanzu ta gama fada masa ita bata son yadda yake yiwa Alheran dinnan bayan ba karamar yarinya bace. Domin ya kwantar mata da hankali yaje ya kira ta.

"My G, ga Alheran kanwata. Alheran ga Ghazalatu kanwata kuma matar da zan aura"

Sai yanzu hankalin Ghazalatu ya kwanta sosai. Ta kurawa Radhiya ido sai ta ga yarinyar ko a jikinta sai ma dariyar ta take yi fuskarta ta tana wani annuri.

Dage girrarta duka biyun ta rinka yi yadda ta saba idan zata yi tsokana

" Eyye eyye Hamma shine kace zanyi aiki a gidanka? Naji zan rinka tayata indai itace matar"

"Bana bukatar house girl so kiyi zamanki" Ghazalatu tace tana shan kamshi.

Fuskar Awwab kadai zaka kalla kasan kalaman basuyi masa ba.

"House girl?" Yace yana kankance idanu.

Ta fuskanci ransa ne ya baci sai ta wayance "naji kace za tayi min aiki ne dazu"

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull