Batuol mamman complete novel - Chapter 22
Batuol mamman complete novel Chapter 22: Batuol mamman complete novel Chapter 22. Radhiya kasa motsi tayi sai idanu da take ta kiftawa ba kakkautawa. Awwab…
3,265 words
Radhiya kasa motsi tayi sai idanu da take ta kiftawa ba kakkautawa. Awwab yayi murmushi duk da yayi ne kawai saboda kannensa amma abin ya tsaya masa a rai dakewa kawai yayi ya dauko kofin da aka cika da juice ya miko saitin bakinta.
"Sorry na cika miki baki, hadiye ki sha wannan"
A guje Radhiya ta bar falon kafin ta kasa numfashi. Yau ta gamu da gamonta. Ita bata taba kunyar wani mahaluki ba kamar yadda taji Awwab ya gama da ita ba yau. [5/22, 10:51 PM] Sis Ruky: Bata tsaya ko ina ba sai daki ta cire hijabin da dankwali ta fada kan gado. Wani tunani ne ya shigeta haka kawai kada a sake tsautsayi ta dauki dankwalinta ta daura.
Awwab kamar bai san me yayi ba ya shiga cin abinci hankali kwance yana jin matan suna kuskus a junansu. To meye ma a ciki daga bata abinci. Da ace sun tashi tare baya jin akwai abinda zai kasa yi mata sai dai a taka masa birki tunda mace ce. Allah ne Ya hada jininsa da na iyayenta sai Ya sanya masa matukar kaunarta tun tana tsumman goyo.
Emzee yaso dauke kai amma ya kasa. Karshe ya dauko wani littafi a kusa dashi ya bude shi ya kifa akan fuskarsa yana dariyar da ba sauti. Gaskiya yaji kunya kamar shi aka bawa abincin. Ibrahim ne ya fara tsokanarsa sai kawai ya tashi da plate dinsa a hannu zai koma daki.
"Dawo ka zauna ka gama cin abincin nan" Awwab yace ko kallonsa baiyi ba.
"Na koshi"
"Kira min Alheran"
Ba musu yaje ya fadi sakon, maimakon amsa sai ta kara dukunkune kanta ta tura a karkashin filo. Murmushi yayi kawai ya fita ya dawo ya fadawa Awwab taki tashi.
Sai da yaci rabin abincin ya mika masa plate din "ka kai mata nata, sai da safen ku"
Tashi yayi zai tafi dakin Ibrahim inda aka yi masa masauki Zayyana da ta kasa hakuri ta fara shagwabe fuska "Hamma ni baka taba yi min irin haka ba, harda bata a baki"
"Ba kiji ta fada muku cewa a rashinta nake kulaki ba" ya fada da wasa.
Kukan shagwabar da ta saba ta fara "kuma sai na...."
"....fadawa Daddy" Ibrahim ya karashe mata yana kyabe fuska yadda take yi.
Awwab ya kusa kofa don idan ya biye mata karshenta a daren sai ya ga wayar Daddy. Juye juye ta soma yi Emzee ya dawo daga ajiyewa Radhiya abinci ya ganta.
"Wa kike nema?"
"Kai mana"
"Inyi miki me?"
"Ba Hamma Ibrahim bane yake tsokanata"
"In fada miki sunan Fulatancinsa ki rama?"
Cikin sauri Ibrahim yazo ya tura shi daki yana magiya da yayi shiru. Tun da Radhiya ta fassara masa ma'anar Surbajo yake gudun sunan kuma dashi Emzee yake samu ya dan kashe bakin idan ya dame su.
Da yake Mami ta fada musu cewa sammako zasuyi su baro Katsina su ma basu yi sanya ba wurin tashi da wuri. Zuwan 'yan matan ba karamin dadi ya yiwa Zainab ba. Su tayata hira ayi ta barkwanci sannan basa bari tayi komai. Zahra da Fauziyya sun jima da gogewa wurin aikin gida da girki. Saboda Mami taran safe zuwa taran dare tana gidan aikinta. Su ne suke komai. Shiyasa Zayyana ta shaku dasu sosai wani zubin bazaka ce yayyenta bane da suka girme mata da yawa.
Kowa ya shirya cikin kayan kirki Radhiya ta bude jakarta kenan bayan ta gama shafa mai Zainab ta leko tayi kiranta. Dakinta ta bar musu dama. Yanzu kuwa da ta kai Hadir falo bayan ya gama breakfast sai ta kirata dakinsa. Ledoji uku ne a gabanta manya ta tura mata daya.
"Ga naki kafin ku tashi daga bacci telan ya kawo"
Radhiya ta bude baki tana kallon kayan da Zainab din take zarowa. Atampa guda uku, material daya, shadda daya da wasu yadika combination biyu. Kwalkwal tayi ta idanu zata yi kuka. Duk wannan ita kadai.
"Bana son kuka fa kin sani ko yanzu naje na fada a hanaki yin sojan."
"Mama nagode" tace hawayen yana fitowa. Yarinya ce mai rike abu a rai shiyasa bata manta alkhairi ko sharri. Da yake dai wasa da shirme sunyi mata yawa a ka shiyasa sai ka ga kamar bata da damuwar komai.
Banda kaddara da Zayyan yana raye Zainab ta sani da yanzu sun kai wani mataki a aikinsu. Yadda yake da kwazo da himma tasan 'ya'yansa sai dai wani yaci arzikinsu. Babban dalilin kiran dama so take ta shirya Radhiya da kanta. Mama Zainab 'yar kwalliya ce ajin karshe. Idan ka ganta a yanzu da take cikin farincikin kasancewa da Hadir duk da a zahiri za'a iya cewa nauyi ne shi a gareta amma fes take kullum. Gogewarta a soyayya duba da tarihin rayuwarta yasa tun jiya ta daukarwa kanta nauyin sake hada Awwab da Alheran domin su cimma burinsu cikin sauki akan yaran.
Kallo daya zaka yi musu kasan sun dace da juna amma idan ka san kowannensu ta fannin zamantakewar rayuwa dole ka chanja shawara. Awwab dan boko ne tashin turai. Yana da ilimi, wayewa da kudi domin kuwa pilots masu aiki da kamfanin KLM suna cikin mafiya samun kudi cikin tsararrakinsu. Alheran Radhiya kuwa yarinya ce da ta tashi a rugar fulani a cikin wata karamar hukuma. Wannan kadai ya isa zama wawakeken bambamci tsakaninsu indai zaman aure zasuyi wanda babu soyayya. Abubuwan da ya sani ko yake so bata sansu ba bare ta so su. Wayewarsu ba iri daya bace. Tayi nata karatun daidai gwargwado amma baza'a taba hada shi da nasa ba tunda iyakarta secondary. Shiyasa indai ana so zaman aurensu yayi karko to a samu soyayya mai karfi da za ta zama igiyar dauresu.
Wani kaya Zainab ta ciro daga ledar ta mika mata "jeki ki saka wadannan gani nan zuwa. Ko hoda kada ki shafa sai nazo"
"To Mama" tace ta fita da murnarta taje ta nunawa su Zahra su ka tayata murna.
Yadi ne mai kala biyu. Mara adon light purple ne anyi mata skirt dogo da dankwali. Rigar kuwa yadinta duka zanen filawoyi ne manya pink da light light purple kamar skirt din. Tsayinta ya wuce gwiwa da kadan anyi mata dogon hannu mai dan fadi daga kasansa. Kadan akayi mata shape don kada ta kama jiki ba wani ado a jikinta sai maballai guda hudu na wuya amma tayi kyau musamman a jikin Radhiya. Wani juyi ta rinka yi tana jindadi su Zahra na zuga ta har Zainab ta shigo tace suyi sauri wanda basu ci abinci ba su je su ci nan da awa daya ko kasa da haka su Mami zasu iso. Duka su ukun su ka fita aka barsu su kadai.
Hoda, kwalli da janbaki pink mara duhu ta shafawa Radhiya a fuska bayan tayi mata lining da jagira pink mai duhu a leben. Simple make up ne amma fuskarta tayi kyau. Cikas din kawai kanta ne. Zainab ta daura mata dankwalin da kanta ya danyi tudu daga keya sannan ta mika mata hijab mai kyau da kananun duwatsu a kasansa pink irin kayan. Iyakarsa ya sauko kirjinta da kadan. Radhiya harda hajijiya a gaban mudubi.
"Mama nayi kyau ko?"
Murmushi tayi ta yaba sosai da 'yar tasu "kinyi kyau amma don Allah bana son baragada kinji ko. Wannan hayaniyar da saurin fushi ko fada ki ajiyesu. So nake naga kina taku daidai yadda babu wanda zai raina min ke"
"Idan nayi sanyi da yawa bazan kai labari ba a makarantar sojoji Mama. Anfi son mu da dakiya da fada saboda gudun raini"
"Allah nagode Maka. Har yanzu kina jiran zuwa sojan ne bayan miji zan samo miki"
Da murnarta tace "Likita?"
"Idan ba likita bane ba fa?"
"Gaskiya Mama ki barshi kawai. Idan ba likita ba sai dai ko soja irina. Sauran duk na rainasu, kada ayi auren su rinka kawo karata kullum"
Hannuwa Zainab ta tafa tana dariya, yanzu ta gama cewa ta dena shirme gashi ta hade fuska tana buga kayanta a ganinta kuma ba laifi bane.
"Jeki kici abinci kada azo ana jiranki"
Kallon kanta ta sake yi yadda tayi kyau abinci zai iya goge mats jambakin ta dawo tayi zamanta akan gado "bana jin yunwa"
"Ashe kuwa za'a tafi a barki" Zainab tace tana yin gaba.
Ba don taso ba ta tashi itama. Tana saka kafa a falon ta tuna abinda Awwab yayi mata sai ta juya suka kusa karo da Zainab.
"Wuce muje kici abinci" ta umarceta.
Gani tayi babu alamun Awwab din sai ta saki ranta ta fara gaishe da Hadir da yake kallon labarai sannan ta tafi gaban dinning table inda kayan tea suke za ta hada taji Zainab tana tambayar ko Awwab ya shirya.
"Da kyar idan ma ya tashi Mama, shi fa idan yana gida yafi zaman daki yayi bacci saboda yanayin aikinsa" Zahra ta bata amsa.
Radhiya ta saki murmushi "kice kamar dai mu sojoji ashe nasa aikin shima baya samun isasshen hutu". Suna mata dariya za ta fara abin nata ta mayar da hankali ga abinda take yi. Madara da milo ta zuba a cup din nata ta mika hannu za ta dauki sugar Awwab ya bude kofar dakin ya fito. Wani hadadden kamshi ke tasowa tun kafin ya iso tsakiyar falon. Yayi kyau cikin wani lallausan yadi ruwan madara. Rabonsa da manyan kaya ya kwana biyu sai jiya da Daddy ya bashi su guda biyu dinkakku da zai taho. Su Zainab ya fara gaisarwa sannan ya amsa gaisuwar kannensa da Radhiya da jikinta yayi sanyi saboda kada a sake irin ta jiya.
Tana tsaye ta kasa karasa abinda take yi balle ta ja kujera ta zauna. Jiya ke mata yawo a ka yadda ya bata abinci a baki kamar wata baby. Runtse idanu tayi tana son kawar da tunanin daga zuciyarta taji ya janye kofin daga hannunta.
"Kawo na karasa hadawa naga ba kya sauri"
Sakar masa tayi da sauri ya ture robar sugar din ya kara mata madara da milo ya fara zuba ruwan zafi.
"Hamma ya isa haka" tace da ta ga ya wuce rabi.
Bai saurareta ba sai da ya cika kofin ya ja kujerar gefenta ya zauna. Kujerar kusa dashi ya tura mata baya da kafarsa ta zauna tana waigen baya. Babu mai kallonsu Zainab da Hadir labarai suke gani a tashar Channels. Zahra da Fauziyya suna hirar angwayensu dake korafin sun makale a Kano. Zayyana kuwa ta tafi dafa indomie.
Wani irin kallo yayi mata sau daya ya dauke kansa, tayi masa kyau sosai har yana tsoron kada kallon da yake mata ya wuce gona da iri "namu ne mu biyu"
Turo baki tayi "Habaaa Hamma don Allah yunwa nake ji"
"Okay fara sha ki bani" yace yana tura mata kofin.
"Ni a'a, ka shanye na hada wani"
Lumshe idanu yayi yana mata murmushi "wannan zamu sha, jiya dama ance abincin da na rage miki dawo dashi kikayi. Ko muyi kama-kama da shima baki bari munyi ba"
"Na shiga uku" ta furta a hankali tana cike da kunya ta tura kujerarta baya za ta tashi ya bata rai.
"Ki dena tashi idan muna magana bana so"
Zama tayi tana ta zumbura masa baki ya sha rabin tea din ya mika mata ta karba ta bishi da harara.
"Baka saka suga ba ni kuma dashi nake sha" ta mika hannu zata dauko robar ya riga ta daukewa.
"Da zaki a haka, try it."
Samun kanta tayi da bin umarninsa ta sha tea din shi kuma ya tashi ya koma daki bai taba doyar da aka soya da kwai ba. Tana nan zaune ya dawo da ledoji masu kyau a hannunsa da tambarin wani babban kamfani a kasar Germany. Su Zainab ya fara mikawa ta karba da murmushi ta bude. Turaruka ne na alfarma na mace da na namiji ita da Babansu Hadir da agogo set shima na mace da namiji.
"Harda dorawa kanka wahala Awwab?"
"Ku sa mana albarka kawai Mama"
"To Allah Ya saka da alkhairi Yasa kafi haka. Allah Ya baku masu yi muku a nan gaba"
"Amin" kowa ya amsa harda Radhiya.
Leda ta biyu ya mika mata "na Ibrahim da Emzee, suna ina ne ma?"
"Leka ta window wankin mota ake mana"
Komawa yayi dinning table din ya zauna a inda ya tashi Radhiya ta kafe shi da ido.
"Ya?" Yace yana gimtse dariya don ya kula ta fara cika tana jiran nata.
"Ina nawa?"
"Me din?"
Kai tsaye tace "Abin cikin ledar"
"Kina harar tawa zan baki abin cikin leda? Wanda na siyo da sunanki ma zan je in kaiwa Ummi tayi sadaka dasu"
Kallon shirts da agoguna da Zainab ke fitarwa da sunan Emzee da Ibrahim yasa ta sake hade rai harda kwalla. Ita da tafi kowa cika baki akan Hamma Awwab amma ita ce ko tsinke bai bata ba. Abincin ma fushi tayi dashi ta ture. Sai yaji ta dan bashi tausayi ya gama dariyar abinda yake shirin kulla mata kawai don ya tsokaneta ya matso da kansa yana mata magana a hankali.
"Kin yarda daga yanzu ko me zamu ci zamu ragewa juna har na koma?" yayi dan murmushin rigimarsa da Mami a baya "da ko me naci sai na rage miki Mami tayi ta fada wai ba komai zaki iya ci ba. Ni kuma tana barin wurin sai na tura miki a baki ko yaya ne ki cinye"
Murmushin da tayi masa jinsa yayi har ransa saboda yadda take lumshe idanu batare da tayi la'akari da tasirin hakan gareshi ba "to ai kaine baka yi min bayani ba kawai kasa ni jin kunya jiya."
"Silly girl me akayi na jin kunyar? Kinsan me kike yi min kuwa da?"
Radhiya ta girgiza kai.
Yafito ta yayi da hannu ta sake duku kanta tana shakar daddadan kamshinsa "abin bakina kike cirewa ki saka a naki idan na hanaki"
Hannuwanta ta saka a gefe da gefen kumatunta ta bude baki da idanu duka a lokaci daya. Tana ta jiran Hamma Awwab ya dawo gashi ya dawo ya hadata da jin kunyar da bata taba sanin tana da ita ba. Abin bakinsa fa yace! Yanzu tana tashi kuma zai ce ta zauna ko yayi maganar yadda kowa sai yaji. Gara kawai tayi kamar bata ji komai ba ta bawa kanta shawara. Daurewa tayi kamar bata ji nauyin maganar ba tace
"Yanzu dai kasan bazan ci abin baki ba"
"Sure?" Yace yana mata kallon gefen ido.
"Na fa girma"
"If you say so" ya rausaya kansa sai kuma ya tashi tsaye "kinsan me? sai na sa kin karbi abin bakina kafin na koma Katsina"
"Idan naki fa?"
"Ki tambayeni duk abinda kike so. Amma nima idan nayi winning zan tambayeki"
"Ka shirya bani tsarabata kawai" tace tana dariya ta tashi tayi waje da sauri. Sai da ta rufe kofar falon ta dafe kirjinta da yake bugu kamar zai ballo. Kofar ta kalla ta jingina da bango tana girgiza kai
"Abin baki? Hmmuhmm, kai lallai ma Hamma Awwab dinnan idan ba bazan karba ba" kunya ta ji kamar me amma ta daure sosai tana bashi amsa saboda kada ya gane zancen na shigarta tana bashi wata ma'anar daban.
Emzee yana kallonta shi ya gama wanke motar Mamansu Zainab har ya fara taya Ibrahim da yake wankin bus din da zasu tafi Sumaila a ciki. Dauraye hannuwansa yayi Ibrahim ya bata baya bai hangota ba ya karasa gabanta.
"Ke da wa Adda?"
Dantsen hannunsa ta riko tana dariyar jindadi "Emzee yau na koyi basarwa"
Yasan Addarsa da shirirta "na tayaki murna, wa kika basar?"
"Hamma Awwab mana, wai kasan me yace min kuwa?"
Yatsunsa na nuni ya sanya a kunnuwansa ya toshesu "bana son ji don Allah"
Shan kunu tayi tana harararsa "me yasa?"
"Rike kayanki, hirarku ce" ya bata amsa yana komawa wurin Ibrahim. Haka kawai jikinsa ya bashi wani abin jin kunyar Awwab yayi don abinda zai korota waje ita kadai ba karami bane. Shi kuwa bai tashi jin ko ma meye ba a saka shi jin kunyar da za ta jima bata barshi ba su kuma su cigaba da harkokinsu.
********** [5/22, 10:51 PM] Sis Ruky: Basu dade da fita ba Daddy ya kira Mami yana tambayarta hanya da mai jiki, su ma shigarsu Sakkwato kenan. Ya bukaci gaisawa da Malamijo wanda hakan ba karamin dadi yayi masa ba. Da Mami ta sake karba ne yake bata shawarar me zai hana su kwana washegari su kama hanya da wuri. Banda dare da ya tabbatar sai sunyi a hanya yana ganin ko babu komai itama Mairama sun mutunta ta. Zata ji dadi su kwana yadda itama taje nasu gidajen ta kwana. Mami dama harda tsoron dora musu nauyi da take yi yace duka babu komai kwana daya dai ta sanar da Ummin Awwab yasan zata yi farinciki.
"Ummi yanzu Daddy yake cewa gara mu kwana saboda dare"
Murmushi Mairama tayi da ya nuna jindadinta kamar yadda Major yayi hasashe. Baza a rasa dakunan da za'a sauke su ba. Abinci kuwa bata da matsala tunda da 'yan kudadenta. Zata bayar ne a siyo abinda zata fita kunyarsu.
"Wannan murmushi Ummi to me yasa baki fada min kina so mu kwana ba? Duk daya muke fa"
"Nasan kinyi haka ne don kada ki dora min nauyi. Amma zanfi so ku kwana ko daya ne a gidan da bani da tamkarsa"
Yadikko da Hajjo ta sanarwa Malamijo na ji yasa aka taso kannenta ya bada umarnin a gyara dakuna biyu daya domin mazan dayan kuma na 'yan mata. Ita Hajjo tunda ita ke da girki 'yarta zata gyarawa Mairama da Mami nata dakin. Baki masu alheri irin wannan karramasu ya zama wajibi a wurin Malamijo ko don ya kara samun wani ihsanin kafin su tafi.
"Karami jeka ka fadawa yayanku ya nutsu yaci abincin tunda babu tafiyar"
**********
Kallon kallo suke yi daga bayan Awwab da ya juyawa kofa suka ji ana gyaran murya. Ba kowa bane illa Emzee wanda ya gama ganin musayar sweet. Shi ba abin ya juya ko yace bai gani ba. Murmushi ne ya subuce masa da suka hada ido da Awwab.
"Dama Mami tace na fada maka yanzu Daddy ya kira yace ku hakura da bin hanya yamma tayi"
"Bari naje na sameta, ko Kano muka koma mun rage wani abin"
Tafiya yayi Radhiya ta tsaya dauko kwanukan da tabarma. Emzee ya karbi tray din tana nade tabarmar yace "Allah Sarki bawan Allah"
"Wa?"
"Dr Kawu Zakari mana"
Gabadaya daburcewa tayi "me...me..ya same shi?"
Dariyar da bai fiye yi ba ya yi mata ganin duk ta rude irin na marasa gaskiya "babu komai na tuna irin son da kike yi masa ne a raina nace dan gata. Idan ku ka yi aure alawa zaki rinka bashi"
Borin kunya ya kamata ta fara fadan da babu gaira babu dalili. Dariya ta sake bawa Emzee ya sakalo hannunsa a wuyanta "kinga dai bance komai ba, idan kika tona kanki ba ruwana"
Baki ta bude tana harararsa, wai me yake nufi ne.
Aljihunsa ya rinka lalubawa ya zazzagesu yana cewa "rufe bakin mai alawar ya shiga ciki ni kuma ko kuli babu a jikina"
"Kwana biyu jikinka bai karbi sako ba shiyasa kake damuna" tace tana daga hannu za ta kai masa duka ya gudu tana jiyo dariyarsa.
Har yanzu babu wanda ya tashi daga tsakar gidan. Awwab ta nemo da ido ya dan durkusa a gaban Mami yana rokonta ko Kano ne su tafi. Mairama tana jinsa tace wato bazai iya kwanan kauye ba.
"Ba haka bane Ummi, bana so ki bawa kanki wahala ne kawai"
"Wace wahala ga kannenka ko ta ina, yanzu Karami zai gyara muku dakin da zaku kwana. Yau kowa zai dana kauyenmu"
"Ko don kada kice ina gudun kauye dole na kwana."