Kenza eBookz

Batuol mamman complete novel - Chapter 30

Batuol mamman complete novel - Chapter 30

Batuol mamman complete novel Chapter 30: Batuol mamman complete novel Chapter 30. Tsayuwa Awwab yayi ya juya zai yanka masa magana tuni Emzee ya bace yana…

3,358 words

Tsayuwa Awwab yayi ya juya zai yanka masa magana tuni Emzee ya bace yana ta dariya. Hararar sai ta koma kan Radhiya ta dan ja da baya.

"Ni kuma me nayi?"

" 'Yar karamarki dake yarinyar nan kina da crush. Allah Yasa yazo kije kina masa murmushi zan sani ne"

"Shi kuma meye crush din?"

"Ko mutum baiyi niyya ba sai kin sashi dariya" yace yana murmushi.

"Crush din wani ne?"

"Yana nufin wani ya rinka burgeki kiji inama zai zama masoyinki"

Sai da tayi dariya tace ko kishi yake yi ya amsa mata da cewa "sosai ma kuwa, Allah Schatzi kada na tafi ki fara kula likitocin asibitin nan. Gabana ya soma faduwa kada suyi min kwace"

Wata dariyar take yana kallon fuskarta yana jindadi. Komai na Radhiya abin so ne a gareshi. Da kyar ya iya jan motar ya tafi tana ta daga masa hannu har ya fita daga harabar asibitin.

Tunda ya hau hanya bai tsaya ko ina ba sai cikin gidansu. Wata irin gajiya yaji ta dirar masa ya samu yayi bacci bayan yayi wanka.

********** [5/22, 11:03 PM] Sis Ruky: Awwab yana tunanin yadda zai shiga gidan ya gabatar musu da bakin ga taron mata tun daga waje sai Allah Ya taimake shi ya hango Emzee yana tahowa tare da wasu samari sa'anninsa. Shadda ce a jikinsa light green irin wadda sai ka kula da kyau zaka gane kalarta saboda rashin turuwa da hular zanna bukar saka mai kyau. Yayi aski da gyaran fuska dan gemu da gashin bakin da ya fara tarawa an gyare su fuskarsa ta sake fitowa ga kamannin Zayyan karara. Muhammad Zayyan Tureta kenan yaro matashi da yake ganiyar kuruciya dan kimanin shekara goma sha takwas.

Kayataccen murmushi yayi da ya hango Awwab ya taho wurinsa da sauri.

"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun. Zayyan?" Mammee tace muryarta da jikinta na rawa.

"Na'am" yace lokacin da ya juya yana fuskantar mutanen. Idanu suka zuba masa suna mamakin irin wannan kamanni. To ai ko ba'a nemo su ba duk inda suka hado da yaron nan zasu rantse jininsu ne.

Babu wanda ya sani cikinsu amma yadda ya gansu yawanci dattijai ne masu kuruciyar basu da yawa yasa ya rissina da zumar gaishesu wannan mata da ta kira sunansa kanwa ga kakarsa marigayiya Alheran Ghousman ta rungume shi a bainar jama'a tana kuka tare da ambaton sunansa.

"Zayyan, Zayyannn, Zayyan kuyi hakuri"

Mutanen da suke wurin sai suka fara kallonsu. Emzee ya shiga kici kicin kwace jikinsa tana kara nanikarsa. Daga gefe Salame matsowa tayi ta kare musu kallo da kyau. Bata iya ganin fuskar Emzee shiyasa bata san ko waye ba ta kada tawagarta suka shige gidan.

Awwab ne ya riko hannunsa yana yi mata murmushi yaja shi gefe "nayi ta kokarin kiran Ummi ko Alheran bana samu. Daga Nijar suke"

"Da gaske?" Emzee yace yana zaro idanu da mamaki. Da sauri ya shige ciki Awwab yace musu zai je ya sanar da Ummi ne. Duk basu damu ba suka ce zasu jira.

A ciki mata musamman manya ne suke tsokanar Emzee wai ya shigo taron mata. Hankalinsa baya garesu yana ta wurga ido yana neman Umminsa. Radhiya ya hango ta fito daga daki da shadda kalar tasa anyi mata doguwar riga mai karamin hannu da bai kai gwiwar hannunta ba. A Kano akayi musu dinkin Mama ce ta bada. Kamar ba ita ba tayi kwalliya harda janbaki. Dauri akayi mata irin mai hawa hawan nan dayake dankwalin da girma babu mai gane yaya gashin yake. Ta sami mayafi dark green kalar zaren aikin rigar ta yafa ta bayanta iya kafada ya rufe mata hannuwa amma bata hade shi ta gaba ba. Da gudu gudu ta fito daga dakin tana mita saboda Ummi tace mata saura ta bata jikinta. Ta yaya za'ace kada ta bata jiki kamar yarinya. Ummin ta rinka dariya tace ta saba jin suna haka da Innawuro.

"Sai na zata kazama ce"

"Innawuro ai ba sona take ba. Ni da tayi min...."bata iya karasa me zata ce ba ta fito shine suka hadu da Emzee.

"Ina Ummi?"

"Tana ciki"

"Hamma Awwab yana waje" yace da ita tayi hanyar kofar da sauri.

Shiga yayi ya ganta tamkar ba Ummin da ya sani ba. Sanye take da irin kayansu dinkin da komai irin na Radhiya. Bata yi kitso ba amma ta tufke gashin ya wuce kafadarta yana ta kyalli. Mairama tayi matukar kyau babu yadda zaka ce ita ta haife su. Zamansu a ruga babu yunwa babu kishi sai dai kawai rashin wayewa wanda da karfin cin tuwo Mama Zainab take cusa musu. Tsallake matan dake zaune a dakin yayi ya karasa gefenta ya duka ya sanar da ita bakin da suka yi.

Ummi bata san lokacin da taji kwalla ta taru a idanunta ba. Da gaske Major ya nemo dangin Awwab na Nijar har sun biyosu Sumaila? Da zafin nama ta tashi tunanin me ya kamata ta farayi domin karramasu ya darsu a ranta.

"Su nawa ne?" Ta tambayi Emzee a yayin da take fita daga dakin.

"Wallahi Ummi motocin da yawa"

Tana fita dakin Yadikko tayi inda suke ta fama da baki ciki harda Innawuro da Nene Marka. Sanar musu tayi kowacce ta tashi da sauri aka shiga kiran kannenta masu kuruciya su taho za'a gyara bangaren samari inda babu kowa. Wurin akwai dakuna uku da baranda mai dan girma. A barandar suke tunanin saukesu idan an share. Hajjo, Yadikko, Innawuro da Nene Marka kowa ta bazama ana kokarin hada abinda ya dace. Allah Yasa akwai kofa ta waje da za'a iya shiga wurin ba sai sun shigo cikin turmutsin 'yan biki ba. Sai da Ummi ta ga komai ya fara daukan saiti tace da Emzee yaje yace suyi hakuri tana kokarin samun wurin da za'a saukesu ne saboda 'yan biki gidan a cike yake.

Ya juya zai tafi fadin sakon sai ga Salame da 'ya'yanta ta rasa dakin wa zata je. Yadikko da Hajjo duka ta leka basa nan. Asabe da Hanne ba saninsu tayi ba kuma ma dai ta rainasu. Bai kula da ita ba ya rabe abinsa ya wuce. Yarinyar da ta yaye ce ta shiga jan zaninta tana kuka tare da nuna wasu yaran da suke cin shinkafa dafaduka.

"Umma umfafa"

"Rufe min baki dalla can za'a zuba muku"

Na biyu a cikinsu shi kuma ya ja hannunta cikin tashin hankalin kuruciya ganin wadda yaran da suke kallo suke ci ta kusa karewa "Umma zasu wawashe bamu samu ba"

Dagewa tayi ta make bakinsa ya sa kuka kuwa da ta ga an fara kallonta ta rage murya "dan ubanka rufe min baki maye"

"Ya zaki kira shi maye? Haba kinsan yara sai hakuri ki zaunar dasu mana a zuba musu abincin"

Ummi Mairama ce tayi maganar saboda zata wuce ta hango Salamen. Wani farinciki taji a ranta duk da rashin jituwar dake tsakaninsu tana kallon yadda 'yar uwarta ta chanja. Rashin lokaci saboda shirin biki da kuma hani daga Nene Marka duk da bata san dalili ba ya hanata zuwa gidanta bayan idonta ya bude. Isowarta taji suna wannan rigima da yaran.

Batare da ta dago ba, har yanzu tana duke saboda bayanta da ya amsa garin saurin dukan yaron taji wani uban kamshi mai sanyi da ya mamaye wurin wanda ke fita daga jikin Ummi tace "barni da shegu basu da aiki sai cin abinci. Gudun kwadayi yau sukunbiya na saya musuuuuuu" bakin ya makale ta kasa shiru duk da ta kai karshen kalmar.

Ido ta tsaya gogewa da hannu babu kunya babu tsoron Allah sakamakon gamon da tayi bayan ta dago. Wata take gani kamar kanwarta cikin shiga ta kece raini ta wuce sa'a. Daga sama har takalmin kafarta sai da ta bisu da ido tana jinjina kyau da haduwa irin na suturar da mai ita.

"Mairama? Mairama kece ko dai kama ce?"

Sassanyan murmushin nan nata mai kara kawata kyakkyawar fuskarta ta saki "Adda Salame nice mana"

Tsananin mamaki bai bar Salame ta dakata haka nan ba sai da ta ciro hannu tana yawo dashi a gaban fuskar Mairama wadda farin gilashinta ya karawa kwarjini.

"Kina ganin me nake da hannuna?" Tace baki na rawa.

Ummi sai ta kama hannun ta rike. Nata yayi laushi sosai saboda gyaran da akayi musu a salon. Na Salame kuwa sai dai ayi shiru ayi kurum inji dogaran sarki. Kanta da lamba...a daiyi shirun kawai.

"Adda idanuna sun bude cikin hukuncin ubangiji. Zamuyi magana dai ina da baki" ta fada tana yin gaba da sauri.

"Banten uba, kai!!!" Salame tace a gigice gabadaya ta kasa gane me take yi. Ko dai gizo ne tayi mata ba ita din bace a zahiri? A'a Mairama dai kanwarta ita ce da wannan shigar ta chanja tayi kyau haka kuma wai TANA GANI? Zuciyarta bugu take yi kawai kamar wadda tayi tsere ga bakinciki da takaici sun taru sunyi mata rubdugu.

Zaninta karamar yarinyar ta sake ja tayi nisa a tunani taji cikin kuka tana cewa "Umma, umfafa ta kare"

Wata mahaukaciyar mangara ta kaiwa yarinyar wadda take rike da zanin leshin da dama da kyar ta hade shi a jikinta saboda ciki. Yadda yarinyar tayi gaba ta fadi haka ta tafi da zanin babarta Salame a hannu. Sai ga Salame matar Alh Indararo a tsaye da dan sket dinta na ciki ya fita hayyacinsa saboda tsabar jigata da kodewa. Dan lace din da akayi masa cin baki dashi ya barke yana reto a jikin kafafunta wurin gwiwa bari daya ne dinkin bai gama fita ba. Kuma gashi na silk mai santsi wani zare zare nan duk ya fara fita daga inda dinkin lace din ya fita. Bata ma ankara da wuri ba sai da babbar 'yar tace "Umma ina zaninki?"

Baki ya goge da ashar har ta gama hado shi zata lafta mata ta ga mutane sun zuba mata ido wasu suna ta dariya. Sai a lokacin ta hango shi a hannun mai kuka. Kafafunta ta kalla kunya matsananciya da muzanta suka dirar mata. Ga ciki ga dan lace suna neman kayar da ita haka ta tafi da uban sauri ta finciko zanin ta daura mutane suna ta dariya. Duk masifarta sai ta rasa abin cewa ta shiga neman wurin buya saboda kofar gidan babu wani wurin wucewa an cika makil.

Lokacin da Radhiya ta fita Awwab yana tsaye a gefe suna magana da daya daga cikin mutanen Nijar din amma da yake tun zuwansa hankalinsa gabadaya yana kan kofar yana fatan fitowarta shiyasa tana leko da kanta ya hangeta. Ajiyar zuciya ya saki da ganin fuskar da yake matukar so da kauna. Ita kuwa sai waige waige take tana yi tana komar da kanta saboda mutane.

Alh Sidi ne ya fara ganinta daga inda suke tsaye ya tabo dan uwansa Alh Ghoumar yana murna "kaga Alheran"

Alh Ghoumar ya juya shima yayi sa'ar ganinta "Allah mai iko, ka ga kamaninta da tamu Alheran din?"

"Dalilin da yasa na ganeta ma kenan"

Tana wannan leken taji an kamo hannunta an ja ta gaba. Zata yi magana ta ga Emzee ne. Ita fa bata san da wasu baki ba Hammanta tazo gani. Yana rike da ita bai saketa ba sai a gabansu. Kanta ne ya nemi juyewa dama ga yara sun yanyame motocin saboda kyaunsu ga kuma su kansu mutanen da yawa suna ta fitowa daga mota. Kukan Mammee da ta rungumeta har yafi na dazu domin yadda Radhiya take diban yanayi sosai da yayarta. Murmushin da Radhiya tayi ya kara karya mata zuciya saboda lotsawar kumatun sak na yayarta ne.

Emzee yana yi mata bayani su ma suna ta yarensu suna dan hadowa da Hausa saboda jikokin nasu. Fada musu yayi su dan kara hakuri suka ce babu komai sun san gida ne na taro gashi ba'a san da zuwansu ba. Radhiya dai yau harda jin kunya yadda mutanen nan dukkansu suke ta rungumarta matan. Mazan ma ita dai taji wani ya kamo hannunta babba ne kuwa abokin wasan Zayyan sai dai kafin ta motsa taji wani tattausan hannu ya janyota baya sannan ya dawo gabanta ya tsaya tsakaninta da mutumin. Babu mai fahimtar mai Awwab yayi ko dalilinsa sai wanda yasan tsakaninsa sa Radhiya. Abinda yaji ya ratsa shi kuwa shima sai da yayi nadamar taba hannun nata. Daga inda yake tsaye yana kallon wannan runguma zuciyarsa ta tsinke da yaga mata sun kare kada a fara da maza. Kishin da ya yunkuro masa ba kadan bane. Allah ne Ya taimake shi ya taho da wuri yau da sai anyi abinda zai mutu bai manta ba, wato Alheran dinsa a jikin wani. Babu ruwansa da alakar dake tsakaninsu tunda ya tabbatar babu muharraminta ciki idan aka cire kakaninta biyu Alh Ghoumar da Alh Sidi. Sauran duk wanda ya tabata ya taba masa mata ne.

Ummi da kanta ta rufo mayafi ta leko kiransu. Mutane suna darewa wadannan jama'a guda wadanda dukkansu kowa ka kalla kasan ya taka wani abu a duniya na arziki mazansu da matansu suka shige inda aka nuna musu. Tabarmi ne sababbi manya aka shimfide musu suka zazzauna babu girman kai da jin su din wasu ne. Mammee ta rike Ummi tana ta sharar hawaye. Rabon da su hadu shekara goma shatara tun ranar sunan Alheran Radhiya.

Wurin minti goma ana ta matsar kwalla Ummi an fama mata rashin gwarzon namiji masoyin kwarai Zayyan uban 'ya'yanta.

"Mairama yaya bayan saduwa? Kiyi hakuri. Don Allah ke da 'ya'yan nan kuyi hakuri" Alh Sidi yace yana duban su duka su ukun.

Salame da kunya ta korota sashen mazan gidan nasu taci karo da wannan abin al'ajabi. Wurin gabadaya wani irin kamshi yake yi. Sakato tayi tana kallon mutanen. Maza biyu cikinsu wato su Alh Ghoumar sun dora rawaninsu na al'ada a kawunansu. Sauran kuwa sai ka rantse wasu larabawa ne. Buzaye ne gaba da baya da kudi ya kara gyarawa rayuwa suka kara fitowa. Bakinta bai iya neman abin fada ba na nuna mamaki taji muryar marainiyar wayonta Mairama.

"Don Allah ku dena bamu hakuri ba laifinku bane. Kaddara ce kawai da kuma abinda Kawun yaran nan yayi mana"

Kallo ta bita dashi suna zaune tsakiyar mutanen da ita da 'ya'yanta. Zuciyarta har wani girgiza tayi da ta kalli Emzee. Itama sai ya tuna mata da nata tsohon mikin na son mijin kanwarta. Babban abin da ya daure mata kai shine sanin da tayi Mairama ta makance suna kauye ita da gayyar yaranta. To tana ina ne ta warke kuma suka yi fes dasu ba yadda take tsammanin ganinsu ba? Ga wani kyakkyawan saurayi tsaye a gefe ya tokare kafarsa daya da bango shi kuma ko waye? Tambayoyi take ta yiwa kanta tana neman amsa ido rufe.

"Matsa a wuce" taji ance daga bayanta. Matsawar tayi kuwa aka fara shigowa da tray-tray na kayan abinci da abubuwan sha. Duk abinda za'a tanada Innawuro ce ta kwance gefen zaninta ta bada kudi masu yawa har su Yadikko sai da suka yi mamaki. Bafillatana tana zaune haka cikinsu ana dariya ashe dukiya ce a jikinta. An dibar musu cikin abincin bikin sannan aka siyo tsire da balangu mai yawa da lemukan roba da ruwa masu sanyi.

"Shiga ku gaisa mana 'yan uwan Marigayi ne daga Nijar" Hajjo tayi maganar tana wucewa ciki ita da su Nene Marka suka gaisa da bakin aka gabatar musu da abinci. Kamar zata hadiyi zuciya ta juya batare da ta cewa kowa uffan ba ta bar wurin. Su dinma babu wanda ya kula da ita suna murnar ganin juna.

"Bari mu baku wuri kuci abinci don Allah. An tafi kiran babana sai ku gaisa"

"Ki bar mana yaran idan tashi zaki yi"

Wata mata mai faram faram tace cikin hausar da tafi kama da ta Kanawa. Ilai kuwa ashe aure ne ya kaita Nijar ita ce amarya cikin matan Alh Sidi amma mutuniyar Kano ce.

Ummi tana murmushi tace dama wa ya aiketa. Inda Awwab yake tsaye ta kalla "dan Ummi zo muje kaci abinci"

"Bazai ci cikinmu ba? Tare muka taho shima bako ne" saurayin da suke magana dazu dashi yace yana dariya.

"Wannan naku ne kada ka damu dani" Radhiya ya kalla ta wani nutsu kamar ba ita ba "taso ki zuba min".

Ummi na jin haka tayi gaba abinta tana murmushi suka tashi aka basu wuri domin su samu su sake musamman mazan. Emzee ne kawai bai tashi ba yana aikin amsa musu tambayoyin da suke yi masa game da rayuwarsu.

Kofar da zata fitar dashi waje Awwab ya bi ba wadda zata sada shi da ainihin tsakar gidan ba. Radhiya sai tabi bayansa suka fito yayi hanyar inda ya ajiye tasa motar. Baya ya bude mata babu musu ta zauna shima ya zauna a gaba bangaren dreba kafafunsu suna waje. Lallen kafarta ya kalla ta saka daya daga cikin takalman da ya kawo mata tayi matukar kyau.

"Shigar da kafarki ciki"

Zumbura masa baki tayi sannan ta dauke kafafun.

"Me yasa kika dena daukar wayata yau kwana biyu?" Ya tambayeta da wannan deep voice din tasa.

Shagwabe fuska tayi kafin tace "to ba kaine ka dena kirana ba saboda ka koma Katsina wurin....wurin"

Fada yaso yi mata na hora shi da tayi ta hana shi jin daddadar muryarta idan tana shagwaba ko ta hado wani shirmen nata sai ya kasa. Ganinta kawai da yadda tayi masa kyau ya kawar da komai.

"Wurin wa?"

Harara ta galla masa tana juya idanu ita anyi mata laifi sai dai gabadaya abin da tayi sauke masa kasala yayi "ai ka fini sanin wa nake nufi. Wurin My G mana ni kuma ka manta dani"

Bushewa yayi da dariya damuwarsa ta ragu sosai. Babu wani abu da yake tunani sama da mallakar wannan yarinyar da take gabansa a matsayin matar aurensa.

"Kema G dinki ce ashe"

"A'a wallahi" tace da sauri, hakan ma yana kara bashi dariya har wani kada hannuwa take yi "taka ce kai dai"

"Yanzu dai kishin dreba kike yi" ya dage mata gira "Allah sarki kanwata ta kare miki gashi dreban nan bazai barki ba sai kin amsa sunan matarsa"

Tsuke baki tayi tana dariya kunya ta rufe ta. A hankali ta daga kanta suka hada ido tayi saurin rufe fuskarta da hannuwanta. Yatsun sun sha lalle kamar ya rikosu.

"Schatzi"

"Uhummm"

"I miss you"

"Zaka sa naji kunyarka Hamma"

"Kuma I love you"

Mayafi tasa ta rufe fuskar yanzu tana so ta tashi ta gudu tana gudun kada yace ya hanata.

Langabe kai yayi yace "Baki bani amsa ba ko daya. Kenan bakiyi missing dina ba kuma ba kya sona"

Radhiya ba wayo yana fadin haka ta dago da sauri "ba fa kaji nace haka ba"

"Kina son nawa ne? Ba ni kadai nake abuna ba"

"Kai Hamma Allah bance ba" ta fada kamar tayi masa kuka.

Shi kuma ya sami na yi ya cigaba da cewa "do you love me?"

"Eh mana"

Yadda maganar ta fito a bazata haka itama ta fita daga motar harda tuntube ta kutsa ta cikin mutane tana jin kunya ta barshi da yi mata dariya.

Wayarsa ce tayi ringing sai a lokacin ya kula ashe Mami ta kira shi sau biyar. Sunyi da ita suna zuwa zai hadata da Ummi tunda sun kasa samuta ya manta shaf. Bai yi tunanin amsawa ba yana gudun fada ya rufe motar ya koma ta bangaren da bakin suke don ya bawa Emzee ya kai mata. Ko da ya shiga ma sai yayi sa'a tana wurin dasu Nene tana basu labarin makantar da tayi da warakarta kwanaki kadan da suka wuce. Wayar ce ta sake shigowa ya mika mata yana cewa Mami ce.

Karba tayi ta kara a kunne da sallamarta sai dai maimakon muryar Mami sai taji Fauziyya tana kuka sosai tana cewa "Hamma ka dawo gida ba lafiya"

Ummi na jin haka ta mike tsam ta fita ta kofar waje saboda ko ina na gidan hayaniya akeyi ta sami gefen wani gida da bishiya a jikin gidansu ta tsaya. Hankalinta a tashe yake tace "Fauziyya me yake faruwa?"

Gabanta ne ya fadi. Da farko kamar bazata ce komai ba sai da Ummin ta soma yi mata fadan cewa itama babarsu ce.

"Ummi tun dazu Mami da Zahra suke kuka. Bansan me yake faruwa ba amma har Umma Hussaina da Mummy sunzo sunyi fada da Mami"

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull