Kenza eBookz

Batuol mamman complete novel - Chapter 31

Batuol mamman complete novel - Chapter 31

Batuol mamman complete novel Chapter 31: Batuol mamman complete novel Chapter 31. Zantukan Fauziyya sun daure mata kai matuka ta kasa fahimtar me yake…

3,304 words

Zantukan Fauziyya sun daure mata kai matuka ta kasa fahimtar me yake faruwa kamar yadda itama Fauziyyan bata gama ganewa ba. Kwantar mata da hankali tayi tace mata gobe zasu taho in sha Allahu da Awwab.

Da ta koma su Mammee suka ce zasu tafi Kano su kwana biyu sannan su koma Nijar. Ummi bata ji dadi ba. Niyarsu matan su kwana a wurinta tun farko amma sun fuskanci hakan wahalarwa ne gareta saboda yanayin biki da ake yi a gidan babu masaka tsinke.

"Yara muka zo gani dake kuma Alhamdulillah mun gani duka kuna lafiya. Sai dai muna son muji yaushe ne zaiyi muku daidai mu turo ku taho Niger domin ku hadu da sauran 'yan uwa"

"Ba don bikin da zamuyi a Katsina na yara har biyu ba da tun yanzu zaku tafi dasu" Ummi tace tana kokarin boye damuwar da ta shiga tun bayan wayarsu da Fauziyya.

"Kema sai kinje Mairama ba yaran kadai ne namu ba" Mammee tace sauran suna dariya.

"In sha Allahu muna gama bikin zan sanar daku Mammee"

Sallamar Malamijo ce ta katse zancen nasu. Bai yarda ya zo wurinsu ba sai da ya shiga cikin gidan yaje ya chanja kaya. Kayan da zaisa gobe na daurin aure ya sako saboda motocin da ya gani sun tayar masa da hankali. Ya saka babbar riga yana ta baza hannuwa. Saboda karfin hali ya sami irin farin abin nan da akan gani malamai sun ninka sun daure hularsu dashi na ustazai shima haka yayi ya fito ko karya babbar rigar baiyi ba don ya kara cika ido.

Wurin bakin yaje ganinsu ya sake tayar da hankalinsa yasan lallai ba bakin rainawa bane. [5/22, 11:03 PM] Sis Ruky: Gagarumin taro aka hada na 'ya'yan marigariyi Alh Ghousman da jikokinsa manya. Hankulansu duka a tashe sai maganganu ake yi cikin harshen tamasheq.

Alh Ghoumar da Alh Sidi sune manya a iyaye maza. Hamshakan 'yan kasuwa ne wadanda noma da kiwon da suka gada a wurin mahaifinsu ya zama tushen arzikinsu. Har ila yau a cikin taron akwai Ministan yada labarai Alh Issa Bouba miji ga Gwaggon Zayyan Aghaisha. Tana zaune a kusa da 'yan uwanta tana ta zubar da hawaye.

"Abinda ban gane ba shine a wane dalili wannan yaro Maikudi zai ce mana sun rasu gabadaya?" Alh Sidi yayi maganar cikin kunar rai. Duk tsayin shekarun nan iyalin Zayyan suna raye babu wanda ya sani cikinsu. A tunaninsu tsatson Alheran 'yar uwarsu ya riga ya kare basu da wani ko wata da zasu kalla su dangantata dasu.

"Ba wannan ba ma, ina suka zauna? Me yasa matarsa bata neme mu ba?"

Cikin kuka Gwaggo Aghaisha wadda suke kira Mamme tace da Alh Ghoumar "ka manta yanzu fa mutumin nan da yace tare suke da Zayyan a filin yaki yace har makancewa tayi. Kuma yaushe zaka ga laifinta ma. Mune muka san inda take ita bata taba zuwa Agadez ba."

"Haka ne kuma" yace jiki a sanyaye.

"Duk shekarun nan kila ta yisu ne cikin jin haushinmu. Tana ganin kamar mun rabu da ita saboda babu idon mijinta a duniya" Mamme ta sake fashewa da kuka.

Ko cikakken rabin awa basuyi ba da yin waya da Major Mustapha wanda yayi musu bayanin da zai yiwu ta waya. Bayan ya tura a binciko masa inda suke da takaitaccen bayanin cewa Mairama da 'ya'yanta suna da rai shine suka hadu cikin tashin hankali da mamakin wannan labari suka kira nambar da ya bayar. Sun dade suna waya inda ya fada musu abubuwan da suka sami wannan iyali. Basu da dalilin karyata shi tunda harda hoto ya tura musu domin shaida a lokacin da yace a nemo su.

Sai da hankula suka dan natsa sannan Alh Sidi yace "ina ganin ya kamata mu shirya muje mu gansu. Yaran mu kawosu su ga 'yan uwa don kada irin haka ta sake faruwa"

Kowa yayi na'am da wannan shawara. To sai kuma batun su waye zasu je. Babu wanda yake so a barshi a baya. Jirgi suka fara tunanin bi daga baya aka soke saboda zasu bukaci motocin hawa idan sun je.

"Babu wani abin damuwa tunda zamu daukosu. A sanar da sauran dangi idan yayi muku nan da kwanaki kadan sai mu shirya duk abinda ya kamata mu tafi"

Sati dayan ma suna ganin tsayinsa to amma tafiyar basu dauketa ta garaje ba. Danginsu, jininsu da kaddara ta rabasu. Ya zama wajibi a garesu su yiwa wannan tafiya shiri na musamman.

**********

Bayan sallar magariba Awwab sunyi da Ghazalatu zai je wurinta. Yana shiryawa suna waya da Radhiya tana masa shagwaba yana biye mata. Kwankwasa masa kofa akayi tare da sallama yana makale da wayar a kafada ya budewa Fauziyya kofar.

"Daddy yana kiranka"

Da ka ya amsa ya koma ya gama fesa turare sannan ya yiwa Radhiya sallama da sakon gaisuwa ga Umminsa.

A dakin Daddy din ya samesu tare da Mami. Yana shiga Daddy yace mata tayi hakuri ta basu wuri.

"Ba sai kun koreni ba na dade da sanin kuna wareni. To dadin abin ina da 'yan mata na"

"Zahra da Fauziyya ko? Kinsan dai ko da kudi bazaki saye min Zayyanatu ba" Daddy yace da murmushin dole saboda kwata kwata baya cikin nutsuwarsa tun jiya. Mami ta kula kuma ta tambayeshi sau daya yace babu komai sai taja bakinta tayi shiru. Ita ma din tana da danuwar da take dannewa bata so ta fada masa game da Zahra.

Murmushin ta mayar masa "ka manta jiya baka bata kudin kanwar amarya day ba mun ganku a rana? Yanzu zanje na sayeta"

Bayan fitarta Daddy ya maida kallonsa ga Awwab da yake zaune a kasa daga gefen wata duguwar kujera.

"MUHAMMAD"

Dago kai yayi da sauri saboda yadda kiran ya ratsa ko ina a jikinsa. Baya tunanin idan ba a makaranta ba ko za'a fadawa wani sunansa Daddy yana kiransa da Muhammad balle da irin wannan yanayi da yake nuni da babu wasa cikin maganar da zasu yi.

"Na'am Daddy"

"Meye tsakaninka da kanwarka Ghazalatu?"

Dama yayi tunanin wannan maganar ce tunda Ghazalatu tace tana tunanin Daddy Haroun ya sani ko ma yayi zancen da Alh Baba.

"Daddy maganar aure ce"

"Awwab meyasa baka sanar dani ko mahaifiyarka ba?"

Sunkuyar da kansa yayi yana mai takaicin biye mata da yayi tun a lokacin suka boye. Da an sani a gida zasu iya rokar alfarmar ta gama karatun kafin ayi aure tunda shine babbar damuwarta. Haka nan dai ya sanar da Daddy dalilin boyewar tasu.

"Rashin sanin kana nemanta ya sanya nayi maka karambani. Zuwanmu Rugar Barkindo na yiwa kakannin Radhiya alkawarin za ka aureta saboda sharadin da suka gindaya min kenan na bani ita na dawo da ita cikinku tayi karatu."

Murmushi sosai ya ga Awwab yayi ya sake dukar da kai. Wannan ya tabbatar masa da zancen Mami da tace tana ganin kamar yana sonta.

"Daddy nagode kuma na karba"

"Yaya zaka yi da kanwarka kuma?"

Babu kwauron baki ya fadawa mahaifinsa cewa dama ya dawo ne domin neman shawararsa akan yadda ya kamata ya bullowa lamarin.

"Bazan wulakanta Ghazalatu saboda Alheran ba, itama kuma ko ba ni na nemeta da kaina ba Daddy bazan bari kaji kunyar iyayenta ba"

Hakika tunani da hangen nesa irin na Awwab suna daga cikin dalilin da suka sa Major yake matukar son yaron. Sai aka samu kyakkyawar shakuwa a tsakaninsu wadda tasa suke shawartar juna akan abubuwa daban daban. Yaji dadin amsar dan nasa sosai amma kuma ba abinda nasa iyayen suke so ba ne.

"Ina zaka kai mata biyu a lokaci guda?"

Cikin yanayi na damuwa yace "Daddy nima ban sani ba amma don Allah kada kace na hakura da kowacce bazan iya ba. Dukkansu ni na kai kaina garesu kuma suka amince min"

"Muhammad kayi hakuri da Radhiya, su Alh Baba sun ce na bawa iyayenta hakuri Ghazalatu kadai zaka aura"

A firgici ya dago kai yana mikewa tsaye baki daya "Daddy?"

"Bana son jan zancen nan har Maminku taji. Alhaji yace a bari su gama biki to zan jira a gama din naji hukuncin da zasu yanke. Na sanar da kai ne saboda idan da gaske ka fara neman Radhiya ka janye. Bana son ka cigaba da sa mata rai har sai na gama iya kokarina akan neman amincewarsu ka hada biyun"

Gumi ne sosai ya soma wankewa Awwab fuska. Idan zai iya hakura da Alheran dinsa tabbas zai iya hakura da aure baki daya. Gurfana yayi a gaban Major kamar mai rokon gafara.

"Don Allah Daddy kasa baki wallahi zan iya aurensu su duka."

"Tashi kaje dama yace yana nemanka idan ka dawo. Ka yawaita addu'ar zabin Allah"

Jikinsa sam babu kwari haka ya fita kamar mara lafiya. Mami tana kallon fitarsa Zahra na yi masa magana bai ma san tana yi ba. Jikinta itama sai yayi sanyi. Tabbas akwai abinda yake faruwa wanda Daddy baya son ta sani. To ko ya gane abinda take boyewa na Zahra ne? Kai da wahala tace a ranta tana girgiza kai. Zahra bazata taba fada ba ta sani. Kallon yarinyar tayi a zaune bayan fitar Awwab bai kulata ba tayi shiru. Zuciyarta ce tayi mata nauyi ta rasa da wa zata yi maganar nan ta saukewa kanta nauyi. Fitarta kuma ba karamar illa zai iya janyowa zumunci ba. Shirun dai da ta yi kuma ta roki Zahra da tayi itama shine take ganin kamar zai zame musu maslaha.

Kafin ya isa gidan Alh Baba missed calls din Ghazalatu sun kai goma. Kiransa take tun yana wurin Daddy tana masa tuni akan shiru da ta ji. Ransa gabadaya a cunkushe ya shiga ya gaishe da Mummy kafin ya fito da niyar gaisawa da kakaninsu mata.

"Yayana ka bari sai zaka tafi kaje. Yanzu cinye mana lokacin hira zasuyi"

"Kinfi so dare yayi sosai lokacin na shiga sunyi bacci? Ba dadewa zanyi ba"

"Daddy yace in fada maka kaje wurin Alh Baba shima yana son ganinka. Ni duk za'a cinye min lokacina"

Murmushi yayi duk don ya nuna mata komai lafiya "My G baki da dama, yanzu su Alhajin ne masu cinye miki lokaci?"

Tana ta tura baki suka shiga wajen matan Alhajin daga nan ta bishi falonsa. Sun gaisa yayi masa barka da dawowa shi kuma Alhajin ya bashi karamar robar zamzam da dabino ya karba da godiya. Ganinsu da yayi da jikar tasa ya faranta masa rai sosai. A son ransa zuri'arsu suyi ta auren junansu yadda za'a sami hadin kai mai dorewa har jikoki.

"Dan bamu wuri zanyi magana da yayanki Ghazalatu"

Shikenan za'a sake ci mata lokaci ta ayyana a ranta. Zaman da tayi don ta sami damar fita dashi ne kada Alh Baba ya dauko doguwar hira a tsakaninsu. Iyakarta bakin kofa ta makale daga gefe da zummar idan taji hirar zata yi tsayi ta koma tace ana kiransa. Abinda taji Alh Baba yana cewa ne yasa ta sake matsowa sosai don taji da kyau.

"Munyi magana da iyayenku jiya. Naji dadi kwarai da kuka hada kai da kanwarka. Kuma na yanke cewa ayi auren nan da wata uku. Ina fata zaka iya shiryawa kafin nan."

Wani tsalle Ghazalatu ta daka daga inda take. Awwab godiya yayi masa sosai yana murmushi.

"Sai dai Mustapha ya kawo wani hanzari na cewa ya nema maka auren yarinyar abokinsa batare da sanin kana neman Ghazalatu ba"

Gabanta taji ya fadi don ta sani babu wadda ake nufi ko da ba'a ambaci suna ba sai Radhiya yarinyar nan mai kwalkwalin kai.

Kansa a kasa cike da ladabi Awwab yace "hakane Alhaji"

Tsohon ya gyara zamansa yana kallon jikan nasa "tun a jiyan na fada masa sai a basu hakuri tunda kana da wadda kake so bai kyautu ace sai ka aureta ba. Ni a tsarina ma Allah Ya gani nafi son ku rinka auren junanku. Ita idan aurenta ya tashi sai yayi mata duk abinda uba yake yiwa 'yarsa"

Wannan shine son kai. Babu yadda za'ayi Awwab yayi shiru da wannan magana ya karbi hukuncin Alh Baba batare da ya gabatar masa da nasa uzurin ba.

"Alhaji kayi min izini na auresu su biyu. Ina iya fara auren Ghazalatu sai na aureta daga baya"

Rai a bace ya soma fada "abinda uban naka ya turoka ka fada min kenan. Wato saboda jiya nace ban yarda ba shine kai ka shafawa idonka toka zaka yi min rashin kunya?"

"Alhaji kayi hakuri ba haka bane"

"To nace na soke bazaka aureta ba. Banda son dorawa kai wahala ina zaka kai mata biyu Muhammad? Idan kana son yiwa mahaifinka biyayya ne kaje abinka shima ai karkashina yake"

Ran Awwab sai kuna yake ya kasa daurewa "Alhaji wallahi ina sonta"

Kallon da Alh Baba ya watsa masa a lokacin kallo ne na tsananin bacin rai.

Ghazalatu da ta gama jin komai hankalinta bai tashi sosai ba sai da taji furucin Awwab. Kuka ta fashe dashi ga bakinciki ga kishi ta bar wurin a guje. Daga Alhajin har Awwab sun jiyo muryarta.

"Ka tashi kabi sawun kanwarka ku daidaita. Na gama magana Muhammad bana son sake jin wata magana"

"Alhaji...."

"Ka tashi ka tafi nace"

Yana fita daga falon waje ya nufa ya shiga mota ya kifa kai akan sitiyari.

"Ya Allah" ya furta a hankali ko ina na jikinsa yana cikin tashin hankali. Bazai taba iya hakura ko rabuwa da Alheran ba. Ya barta a kira shi da me? Butulu ko mayaudari? A cikin abinda bai gaza sati biyu ba ya fada matsananciyar soyayyarta kuma itama ya koya mata sonsa. Akwai kunya da nauyi sosai tsakanin iyayensu wanda bai cancanci a sanadiyarsa ya kawo wata baraka a tsakani ba kamar yadda baya fatan kawo baraka ga danginsa. Shi da Ghazalatu sunyi dumu dumu a cikin dangi. Idan baka dubesu ta nan ba zaka dubesu ta can. Hadi ne tun daga kakanni an cakude da juna.

Dakin mahaifiyarta Mummy Gambo ta wuce kai tsaye tana kuka kamar ranta zai fita. Babu abinda yake mata yawo a ka sai jin da tayi Awwab da bakinsa yace yana son wannan yarinyar.

Mummy ta taso ta tarbeta da sauri "me ya sameki?"

"Mummy Yaya ne...Yaya Awwab baya sona"

"Ban gane ba, idan wani shirmen fadanku ne dama kada ki soma gaya min. Kije can ku sasanta"

"Mummy wata yake so. Yaci amanata wallahi 'yar wannan makauniyar da ta zauna gidansu yake so"

Nata hankalin sai yafi na Ghazalatu tashi "dena kuka bari na kira Hassana naji daga bakinta."

Mami tana daki da Zahra wadda take ta kuka tana bata hakuri Mummy ta kira. Shawara ta yanke gara ta sanar da ita ko Hussaina su tayata bawa Zahra baki.

Sai da ta saita muryarta don ita din ma zuciyarta a karye take "Mummyn yara yanzu kuwa nake shirin nemanki."

"Kina shirin nemana ki fada min kun yiwa Awwab mata ko" tace cikin gatse.

Mami da bata san wainar da ake toyawa ba tayi dariya "hala yazo ya fada miki. 'Yar wajen Mairama ce. Kin ganeta ai wadda tazo ta kwana mana biyu matar ....."

Kit taji shiru Mummy ta kashe wayar. Kallon wayar hannunta tayi da mamaki sai kuma ta soma kiranta missed calls biyar bata dauka. Abin ya dameta ta lallaba Zahra ta fita ta tafi dakin Daddy.

Mummy Gambo ta cika tayi fam. Ita Mami zata wulakantawa 'ya har tana fada mata wadda suka zabawa Awwab. Kenan basu aminta da ya auri Ghazalatu ba. A tunaninta tafi karfin haka a wurin 'yar uwarta ta. Kallon Ghazakatu tayi da take ta kuka tana rarrashinta ta kira Daddy Haroun a waya don ya fita unguwa. Cewa tayi kawai ya dawo gida babu lafiya yace to.

Mami tana zuwa dakin Daddy shi kuma ta same shi yana waya da Alh Baba yana ta ban hakuri. Alh Baba yace ya fadawa Awwab lallai aurensa da Ghazalatu babu fashi. Wurgi ta ga yayi da wayarsa ta karaso kusa dashi da sauri.

"Daddy lafiya?"

"Ki bari muyi maganar nan bayan bikin su Fauziyya kamar yadda Alh Baba yace"

"Wallahi hankalina ya tashi. Tun jiya ka chanja min gabaki daya. Yanzu Gambo ta kirani tana cewa munyiwa Awwab mata nace mata eh kawai ta kashe wayar kamar wadda na yiwa wani abu"

Ran Major tuni ya soma baci kuwa. Yasan Gambo da masifa amma baya son duk abinda zai sosa ran Mami. Ga dadin haushin akan 'yarta ne ake son kirikiri a gwada son kai. Meye matsalar ya auri mata biyu da za'a ce dole sai an janye maganar Radhiya. Radhiya diyar Zayyanunsa.

Sallamar Awwab din suka rinka ji kana jinsa kasan baya cikin nutsuwa. Izinin shigowa Daddy yayi masa yana zuwa ya zube masa.

"Daddy Alh Baba yace bazan auri Alheran ba. To wallahi idan bai amince ba itama Ghazalatun na rantse da Allah ko an daura sai na saketa"

"Kai Awwab, kana cikin hankalinka kuwa? Daddy me yake faruwa ne kun kara sakani cikin duhu"

"Fita ka tafi dakinka" Daddy yace ransa shima a baci. Dakin gabadaya ya juye walwalar ma'abotansa ta fi kamar an kadata da iska.

Tattaro nutsuwarsa ya daure yayi ya fadawa Mami halin da ake ciki. Boyewar bata da amfani tunda Gambo ta sani.

"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun. Yanzu sai Gambo ta ga kamar da gangan nayi"

"Gambo kike ji ko kuwa halin da Awwab zai shiga da yaran nan"

"Daddy ni fa ban ga wata gagarumar matsala a cikin wannan abu ba. Awwab namiji ne saboda haka zai iya aurensu duka. Ciki mu mun isa muce ga wadda zai zaba ya bar dayar? Babu wadda mahaifinta baiyi mana halacci ba saboda haka ka kwantar da hankalinka in sha Allahu komai zai zo da sauki"

A sanyaye yace "Alh Baba yace bazai auri mata biyu ba kuma su Baba sun amince"

Kanta ta dora akan kafadarsa ta kwantar da murya domin kwantar masa da hankali "mu bi komai a sannu saboda kuskure daya zai iya janyo mana rikici a dangi ko tare da iyayen Mairama wanda bana fata. Gobe muje mu roki arzikin suyi hakuri su amince ya auresu su biyun"

Kalamai masu kwantar da hankali ta rinka amfani dasu wurin sanyayawa mijinta rai suka dauki dogon lokaci suna shawara akan wannan matsala.

Tunda Awwab ya shiga daki bai fito ba sai asuba. Kallo daya Major yayi masa ya san cewa da wahala idan ya runtsa. Soyayyar Awwab da Alheran daga Allah ce. Ya tabbatar duk wannan tashin hankalin saboda an hanashi aurenta ne.

**********

Da wuri aka gama komai na sallamar Ummi daga asibiti. Abin da mamaki matuka ta shafe shekaru kusan goma da makanta yau ita ce take da idanun kallon Radhiya da Karami. Bayan an bata gilashinta tana kallonsu ta fashe da kuka. Karami bai baro mahaifinsa da komai ba sai fari da ya dan dara shi wanda ta alakanta shi da kuruciyarsa sai kuma tsaho da shi Zayyan din yafi dan nasa. Radhiya kuwa tafi dauko kamanni da ita sai dai ta rasa inda ta samo wannan kirar jiki. Mairama doguwa ce siririya mai kyaun sura da daukar ido yayin da Radhiya take a murje babu rama amma baza'a a kirata mai kiba ba. Jikinta a cike yake ko ta ina. Yanayin hancinta sam baiyi kama da na Umminta ko mahaifinta ba. Idan tayi murmushi sai kaji kamar ka dauketa saboda yadda fuskar take nuna zallan yarinta idan kumatunta ya lotsa ciki.

Lokacin da suka hada ido da Zainab sai sabon kuka.

"Haka kika koma wata 'yar gayu Zainab dina"

Yaran suna dariya iyayensu suka rungume juna.

"Muje gida kafin ki bar garin nan sai kin zama 'yar gayu kema. Ba biki zakuyi ba....hmmm Allah Mairama sai nasa idanu sun koma kanki a wurin bikin nan" suka yi dariya.

A gaban mota Ummi ta zauna Radhiya da Nene Marka suna baya. 'Yan samari kuwa adaidaita sahu tace su shiga su biyo bayansu.

Sunje gida Ummi ido ya bude ta ga halin da Baba Hadir yake ciki. Tana kuka Zainab tace mata kada ta jangwalo idanun tayi hakuri haka.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull