Batuol mamman complete novel - Chapter 33
Batuol mamman complete novel Chapter 33: Batuol mamman complete novel Chapter 33. Hakura tayi bata matsa masa ba saboda tana ganin akwai abinda bai dace ta…
3,315 words
Hakura tayi bata matsa masa ba saboda tana ganin akwai abinda bai dace ta matsa sai ta sani ba musamman idan danginsu ya shafa. Fatanta bai wuce kada ya kasance matsala aka samu game da neman Radhiya da yayi ba tunda Fauziyya tace Mummy din taje sunyi fada da Mami. Wannan damuwar ita ce ta karfafa mata gwiwar son zuwa Katsinan a washegari. Daren ranar suka yi waya da Zainab suna airport zasu tashi. Ummi tayi ta jero addu'o'i suna fatan Allah Yasa ayi komai cikin nasara Baba Hadir ya dawo musu da kafafunsa.
Washegari kuwa bayan daurin aure Ummi suka shirya tafiya Katsina ba zata sami kai amaren ba. Babu irin tunanin da bata yi ba a matsayin dalilin da zaisa 'yan uwan Mami su zo gidanta suyi fada da ita da ya wuce kin amincewa ace ko auren Ghazalatu ba'ayi ba Daddy ya newa Awwab wani auren shi kuma ya karba.
Emzee ne a gaba Radhiya da Ummi a baya. Ba wata hira suke yi sosai ba. Ummi da Awwab tunanin me zasu tarar a can ke damunsu. Radhiya kuma shirun da ta ga yayi tun jiya bai sake nemanta ba shine yasa itama ta kama nata bakin.
**********
Sallah Ummi ta idar ta kasa taba komai cikin kayan abincin da aka ajiye mata. Tunda idanunta suka bude sai yau suka hadu. A waya Mami ta nuna tsananin farinciki ta tayata murna amma yau da suka hadu abu na farko da ta fara gani a fuskarta shine damuwa. A haka ma Mami tana ta kokarin boyewa ne. Taji dadin dai ganin Mamin tayi kyau haka ma su Zahra. Sai dai kaifin tunaninta yasa tasha jinin jikinta da wuri. Yaran da iyayensu duka suna tattare da wani abu na rashin jindadi a zukatansu.
"Ummin Awwab har yanzu baki tashi kinci abincin ba? Ko na zuba miki da kaina ne?" Mami ta fada lokacin da take shigowa dakin rike da katunan daurin aurensu Zahra da aka aiko daga gidan Alh Baba.
"Gajiya ce take tambayata Mami"
"Ga kuma wata da zata tarar miki ke kadai tunda Zainab bata nan"
Ummi ta mike tsaye tana ninke sallayar "dadin abin Maman Ghazalatu da Anti Hussaina suna nan sai muyi tare"
A take yanayin fuskar Mamin ya sauya wanda shi Ummin ke nema don ta tabbatar da cewa lallai akwai wata a kasa. Mami sai ta chanja akalar zancen ta dauko hirar mutanen Nijar.
A bangaren 'yan matan ma Radhiya ce kadai a daki. Zayyana tana falo tare da Emzee yana cin abinci tana zuba surutu da labarin shirin biki da take yi. Fauziyya kuma tana can wurin Awwab tana yi masa bayanin abinda taji kuma ta gani a jiya suka rutsa Zahra akan sai ta fadi waye take so tana ta kuka.
A hasale yace "shirunki bashi da wani amfani da zai mana"
"Kamar yadda fadar ma bata da amfani. Hamma na riga na hakura ba shikenan ba"
"Zahra please ki fada mana" Fauziyya tace idanunta suna taruwar kwalla.
"Let us help you Zahra" Awwab ya sassauta muryarsa yana kallon kanwar tasa.
"Raji ne" tace da muryar da kuka ya sauya ta.
"Raji Abdulwahab?" Awwab yace mamaki na bayyana a fuskarsa. Abokinsa ne duk da cewa Raji din ya dan girme masa. A zuwa masallaci sallar juma'a da suka mayar al'adar gidansu a zaman Germany suka hadu da iyalin Ayodeji Abdulwahab mahaifin Raji. Wani abin dadi shine limami a community din da suka hada nasu na musulmai a wurin 'yan kasashe daban daban. Tasu tazo daya da Raji babban dan Limamin wanda yake aiki a kamfanin Benz. Yana yawan zuwa gidansu ashe Zahra yake so babu wanda ya sani.
Kai ta gyade ta kuma fashe musu da kuka "nasan babu mai yarda na aure shi saboda bayerabe ne shiyasa na kasa fada da wuri. Daga baya Mami ta sani kuma lokacin tayi alkawarin fadawa Daddy su yiwa Alh Baba magana sai kawai muka ji zancen Fawaz. Wallahi Hamma Raji har kwanciya yayi a asibiti"
Kukanta yana taba masa zuciya fiye da zato da tsammani. Shi kam Allah bai dora masa kabilanci ba musamman ga dan uwansa musulmi a duk inda yake. Sai dai a yadda ya fuskanci akidar su Alh Baba son kansu da yasa suka dagewa auren zumunci kadai babbar matsala ce balle kuma ace wani yaren daban.
"Daddy yayi miki magana ne jiya bayan Mami ta fada?"
"Yayi min da daddare. Baiji dadi ba da bamu fada masa da wuri ba gashi lokaci ya kure. Hamma yaya zanyi? Shekaranjiya da Munirat ta kirani kuka take yi wai bashi da lafiya har yanzu"
Tana kuka ne Fauziyya ma na tayata aka bar Awwab da aikin rarrashi. Kamar ance Mami ta leka su ta gansu a wannan yanayi ta kuma ji karshen maganganun nasu. Kwalla ce ta cika mata idanu ta koma batare da ta bari sun ganta ba. Rayuwar 'ya'yanta duka ta shiga wani yanayi. Fauziyya ce kadai take tunanin kila sun hada kai ita da Bilal ta kula ya ma fi Fawaz zuwa dama. Abin dai duka kadaran kadahan babu wani karsashi ko doki a bangaren amaren da angwaye.
Wurin Ummi ta koma suna dan taba hirar Zainab taji sallamar babar Fawaz matar cousin dinta saboda ta bangaren namiji suka hadu. A harzuke ta shigo gidan ranta yayi masifar baci ita da Mummy Gambo. Zayyana da take falo da Emzee aka dakawa tsawar ina mahaifiyarta ta ruga daki ta kirawota.
Mami na ganinsu tasan ba lafiya ba ta dai daure tana cewa su zauna mana.
"Ba zama nazo yi ba Hassana" Haj Azumi tace cikin kaushin murya "ni zaki wulakanta har kike ikirarin 'yarki bata son Fawaz? To wallahi ki jika abarki ki sha indai ni na haife shi ko ana muzuru ana shaho a dangin nan naku Fawaz bazai auri Zahra ba. Ke wallahi bari kiji in fada miki ko aurena ne zai mutu sai dai ayita ta kare"
Mami ta daga kai ta kalli Gambo tana mamakin wai kanwarta da suka fito ciki daya ce take ingiza wannan rigima. Ummi bata fito daga daki ba amma tana jin komai. Haka ma su Awwab dake daki ya hana kannensa fitowa saboda a ganinsa hakan bai kamata ba. Radhiya kuwa tsurewa tayi ita kadai a daki tana jin ana wannan daga murya. Ita fadan ba shine ya dameta ba kamar cewa da matar take yi danta bazai auri Adda Zahra ba. Me yayi zafi haka za'a raba masoya?
"Haj Azumi ki zauna muyi magana don Allah. Gidan nan da baki ga yara"
"Baki? Ke suka dama bakin. Idan 'yan biki ne suka fara zuwa gara su ji su tattara su koma inda suka fito. Aure ne nace a bawa Zahra da ta tashi a kasar waje tafi karfin dana wanda take so. Shi kuwa zan baku mamaki muna nan tare daku mata biyu zan aura masa a rana daya wanda suka fi taki komai da komai"
"Gambo kinga abinda kika jawo ko?" Mami tace muryarta na fallasa yadda abin yake mata ciwo.
"Sai kiji idan da dadi, ni ba tawa 'yar kike neman hanawa nata farincikin ba. Ko bikinsu ba'ayi ba kunje kun nema masa auren wata saboda tsabar son burgewa ace kuna da zumunci. To amma banda abinki zumunci ya wuce ka fara yi da jininka. Mutanen nan 'yan kauye n....."
Wani lafiyayyen mari Mami ta saukewa Mummy Gambo idanunta jajir kamar garwashi. Gidan gabadaya shiru yayi Ummi ta kasa daurewa duk da ta soma hawaye ta fito. Awwab ma fitowar yayi bayan ya gama waya da Daddy ya sanar dashi rigimar da ake yi.
"Gambo ki kiyayeni wallahi. Ba tsoronki nake ji ba sannan baki fi karfina ba. Ki fice min daga gida kafin mu kaiga abinda rayuka zasu fi haka baci"
"Ni kika mara Hassana saboda wasu can bare da kika hadu dasu rana tsaka?" Mummy tace hawaye na neman zubo mata.
Ummi lokacin ta fito zuciyarta ta gama karaya ace saboda ita ko 'ya'yanta ake wannan rigima "Mami don Allah kuyi hakuri"
"Au dama kina ciki? Kun lallabo a cigaba da cusa masa 'ya don ya aura"
Awwab zaiyi magana aka kira shi. Zuciyarsa har suya take saboda bacin rai amma ya tabbatar idan yayi wani abu na rashin da'a ga matan da suke da matsayin iyaye a gareshi ba karamin fushi Mami zata yi ba ko da kuwa yayi haka ne domin rama mata. Sunan Alh Baba ya gani sai da yasha jinin jikinsa.
"Muhammad da kai da kannenka da iyayenka dake cikin gidan nan kuzo gabadaya yanzu ina jiranku"
Sai da ya dan rissina ya amsa masa sannan ya fada musu sakonsa. Haj Azumi da Mummy suka fita suna ta masifa. Mami ta kalli Ummi kunyar baiwar Allahn nan ta sa ko idonta ta kasa kallo. Murmushi Ummi tayi ta saki fuska.
"In sha Allahu komai zai daidaita"
"Kiyi hakuri Mairama ban so kika tarar da wannan rigimar ba"
"Haba Mami waye bai san ire iren wadannan matsalolin na dangi ba? Kuje ku dawo Allah Ya kawo mana mafita"
Daki Mami ta wuce ta sako hijabi ta fito. Fauziyya da Zahra harda Zayyana su ma kowacce da lullubinta. Ta kalli Zayyana tace mata ta zauna kiran bai shafeta ba. Dama a firgice take saboda haka bata ji komai ba sai murna da aka hanata zuwa. Suna fita Mairama ta dubi Emzee.
"Ina yayarka?"
"Tana dakinmu Ummi" Zayyana ta bata amsa.
"Turo min ita dakin Mami ku zauna a nan ke da Karami."
Hawaye ne sharbe a fuskar Radhiya lokacin da ta shiga dakin ta fada jikin Umminta tana kuka sosai. Taji komai kuma ta fahimta. Duk da bata ga fuskokinsu ba amma ta gane akwai maman Ghazalatu kuma bata so ta auri Awwab. Ita kuwa wani irin mugun sonsa ma take ji yanzu bata fatan giftawar abinda zai iya raba su. Bata ki ba ko mata uku za'a aura masa a danginsu indai itama zata sami gurbi a zuciyarsa da gidansa.
"Alheran"
Faduwar gaba taji saboda bazata iya tuna yaushe ne taji sunanta ya fito daga bakin mahaifiyarta ba.
"Na'am"
"Kina son Awwab ne?"
Da ka ta amsa sababbin hawaye na gudu akan kumatunta.
"Meye matsayina a gareki?" Mairama tace babu alamun wasa da ta bari a fuskarta duk kuwa da cewa abinda take niyar yi tamkar ana yankar zuciyarta ne. Iyalin Major Mustapha wani bangare ne na rayuwarsu da bazata taba mantawa da alkhairinsu ba. Daga dawowarsu sai fadi tashi yake a kansu musamman na hadasu da danginsu da yayi.
"Babata ce" cewar Radhiya gabanta na sake faduwa.
"Daga yau babu ke babu Awwab kina jina?" A gigice Radhiya ta dago kai Ummi ta cigaba da magana nata hawayen na zuba "bani ba ko mahaifinki bana jin akwai mutumin da zaiso bawa aurenki sama da Awwab amma daga ke har shi farincikinku yayi kadan ya haddasa husuma a tsakanin iyaye. Saboda soyayyarku Mami yau ta daga hannu ta mari kanwarta. Zaman da nayi dasu na kwanaki da kuna Kano babu ranar da Mami bazata ce Gambo ba saboda yadda take sonta ta amma yau akanki ta mareta"
Jiki na rawa Radhiya tace "Ummi kada ki rabani da Hamma don Allah. Ummi tunda na fada da bakina wallahi kinsan ina son shi....Ummi don Allah"
"Kina sha'awar aure a dangin da basa sonki? Ko an fada miki idan kika aure shi daga ke sai shi sai iyayensa? Bazaki yi mu'amala da sauran 'yan uwansa bane?"
Shiru tayi babu amsa sai kukan da take yi mai sauti tana gurfane a gaban mahaifiyarta.
"Gata nake son yi muku ke dashi. Aurenku a yanzu babu abinda zai kawo sai tashin hankali da rabuwar zumunci. Mu da muka tashi da karancin dangi ai kinga yadda abubuwa suka kasance mana kafin zuwansu Innawuro ko? Kina sha'awar ki mutu a rasa mai kula da 'ya'yanki saboda kiyayyar da ake yi miki ne?"
"A'a"
"Alheran Daddynku Major da Mami da 'ya'yansu duka suna son mu suna mutuntamu. Sakayyar da zamu yi musu kenan mu rabasu da da nasu 'yan uwan? Kina ganin zaki taba yafewa wata mace ta gida ko bare da zata yi kokarin rabaki da Karami misali? Ki tayani sakawa su Mami da alkhairi na tabbatar miki wallahi Allah bazai bari ki wulakanta ba. Ki taimaka kada ki zama sanadin datse igiyar zumunci ki gani idan Allah bai saka miki da alkhairi ba. Ana barin halal ko don kunya kinji. Kin girma ke ba wannan karamar yarinyar bace da take fita ayi dambe da ita. Kece kike da burin yin abin alkhairi domin a nuna ki ace 'yar Zayyan Tureta ce ga dama ta samu gareki."
Babu abinda Ummi ta fada mata wanda ba gaskiya ba. Baza ta taba yarda ta batawa Umminta ba bayan wahalar da tasha akansu kuma ta sani cewa rabuwarsu zata taimaka kwarai wurin daidaita lamura. Tana share hawaye saboda yadda take jin zafin zuciya har dafe kirjinta tayi tace "Ummi to yaya zanyi da son shi?" muryarta can kasa kamar ba Radhiya ba.
Tsantsar tausayi da soyayyar 'ya da uwa suka sa Mairama kuka itama. Rabuwa da masoyi akwai ciwo mai radadi. Bata taba mantawa da Zayyan ba haka nan har yanzu zuciyarta bata rabo da tasowar kunci lokaci zuwa lokaci idan ta tuna sun rabu kenan har abada. Soyayya ciwo ce da bata warkewa sai dai hakuri babu abinda ya bari.
"Kiyi hakuri a hankali zaki rinka jin sauki a zuciyarki. Da kaina zan fada musu cewa ba kya son auren. Ina ganin ma idan munje Nijar din in barki a can har komai ya lafa"
Duka zantukan da suka yi tun shigar Radhiya dakin zuwa yanzu a kunnuwan Umman su Mami ne. Ta taho gidan cikin fushi ne saboda a ganinta Mami ita ke neman raba zumunci tsakanin kannenta. Ko gaisuwar Emzee da Zayyana da suke falon bata amsa ba tace ta nuna mata dakin Mamin batare da ta saurari bayanin da take mata na cewa basa gidan ba. Juyawa tayi ta tafi batare da ta yiwa kowa magana ba. [5/22, 11:03 PM] Sis Ruky: **********
Yau falon na Alh Baba ya cika sosai sakamakon yawan wadanda aka zauna dominsu. Jikokin da abin ya shafa suna cikin gida sai an gama da iyayensu za'a nemesu.
"Wace magana nake ji haka cewa jiya Gambo taje gidan Mustapha da Husaina yau kuma da Azumi ana rigima?"
Babu wadda ta iya yin ko da tari ne saboda kwarjinin iyayen nasu. Alh Baba ya kara hade rai yace Mami ta fada masa me ya faru. Kai a kasa ta zayyane masa komai. Gabadayansu sun nuna fushi akan abinda kannen nata suka yi mata tare da Azumi.
"Naga alama a kokarina na son inganta zumuncin zuri'ata al'amura suna kara tabarbarewa. A zamaninmu dai mace ko namiji sai dai ace ga wane za'a hadaku aure kuma ayi auren a zauna lafiya. To amma na kula daku da 'ya'yanku abin ba haka yake a wurinku ba"
Baba Karami ya kalli su Mummy "Gambo baku kyauta ba ko kadan abinda kuka yiwa Hassana har gida kuma a gaban 'ya'ya. Ko bata girme ku ba ai ta ci darajar auren yayanku"
Sun hadu sun yi musu fada akan abinda ya faru sannan Alh Baba yace to tunda abu ya koma kowa kanta ta sani da 'ya'yanta zai kira yaran ya sake tambayarsu. Duk abinda suka yanke shikenan.
Kana ganin yadda yake magana kasan akwai bacin rai sosai a tattare dashi
"Zabi ya rage tsakaninku da 'ya'yanku bazan sake saka muku baki ba balle inyi bakin jini"
"Alhaji kayi hakuri don Allah. Muma kaine ka aurar damu in sha Allahu duk yadda kace akansu haka za'ayi" Daddy yace sauran 'yan uwansa suka nuna amincewarsu.
Alh Baba sai kuma yaji nauyin yadda duk da yafi kowa sanin cewa son kansa ya nuna akan komai amma gabadaya yaran da iyayensu kai hatta kannensa kowa ya amince ne domin biyayya a gareshi. A tunaninsa wannan hadin kara dankon zumunci zaiyi amma zamani ya chanja. Bai manta ba daren jiya da Baban biyu yake ce masa auren hadi yanzu a cikin goma daya akan samu ana zaman lafiya. Biyu ayi zaman hakuri sauran bakwai din kuwa duk mutuwa suke yi wani lokacin ayi rabuwar da zata shafi har jikoki. Ya bashi shawara cewa idan jikokinsu sun hada kai a junansu a barsu suyi aure haka kuma masu nema a waje su ma a basu dama.
Haka suka shigo masa Zahra, Ghazalatu da Fauziyya idanunsu a kumbure suna kan kuka ma. Awwab kuwa kallo daya yayi masa ya dauke kansa. Damuwa da bacin rai sun rufe kyakkyawar fuskar yaro mai yawan fara'a da wasa da dariya. Anya ya yiwa 'ya'yan Hassana da Mustapha adalci kuwa? Yara har uku yana neman tauye musu hakki akan abinda ba addini ba. Don dai kawai Baban Biyu yana da kawaici amma ace jikokinsa har hudu duka ya nuna shine mai ta cewa akan makomar rayuwarsu kuma nasu kakan ya nade hannu ya kyale shi.
"Matso nan Fatima" ya yafito Zahra da hannu. A tsorace take ta tashi ta koma kusa da kafarsa ta zauna. Ya kira Fawaz shima yazo ya zauna daga daya gefen nasa.
"Kana son auren kanwarka?"
Shiru Fawaz yayi na 'yan dakiku kafin ya girgiza kai yace baya so. Haj Azumi tayi gajeren murmushi. Tun a gida tayi ta nanata masa idan yana son kansa da arziki kada ya yarda a aura masa yarinyar da bata sonsa. A nasa bangaren shi dai baya kin Zahra amma kuma ba soyayya bace tsakaninsu shiyasa bai ga amfanin aurenta ba.
Alh Baba ba haka yaso ba amma dole ya karba tunda a gaban iyayensu ake yi.
"Fatima waye shi wanda kike so din?"
Kasa magana tayi ya mayar da tambayar ga Major. Shi din ma bai wani san kan zancen sosai ba shiyasa Awwab ya fada masa yadda suka yi da ita dazu.
"Yanzu zuri'ata zan hada da kabilu?" Yace cikin wani irin yanayi.
Baba Karami yayi saurin gyara murya "Alhaji kada mu koyawa yaran nan kin 'yan uwansu musulmi saboda bambancin yare da al'ada. Mun sani cewa babu haramci a tarayya dasu sai ma kara karfin alakar dake tsakanin musulmi da dan uwansa."
"Haka ne, idan mun tashi daga nan a kira shi a waya yazo da magabatansa idan yana sonta. Daga yanzu na soke maganar aurenta da Fawaz."
Mami harda hawayen dadi. Lallai mai hakuri shi yake dafa dutse yasha romonsa. Bata taba tunanin zata sauyi irin wannan game da auren Zahra ba sai gashi ya samu cikin ruwan sanyi.
"Fauziyya da Bilal fa? Akwai wani korafi makamancin haka tsakaninsu?"
Bilal yaro mai tsananin kunya yace indai bata da wanda take so yana son aurenta. Fauziyya ma bata bashi kunya ba tace ta amince. Haka ya sanya farinciki a zukatansu.
"To uban gayya da aurensa ya janyo mana wannan tone-tone. Na baka izini Muhammad ka nemi amincewar Ghazalatu da waccan yarinyar ayi aurenku rana daya babu wadda zata jira wata"
Yana dire maganarsa Ghazalatu ta dago jajayen idanunta "Alhaji ina da magana"
"Ina jinki"
"Ni dai na hakura ko wani zaka zaba min zan amince amma banda Yaya Awwab"
Tsawa Daddy Haroun ya daka mata ta fashe da kuka. Tana da kishin da bata jin zata iya zama da Radhiya da take gani kamar wata kaskantacciyar yarinya. Amma ba wannan ne ya janyo mata kin amincewa ba sai zugar mahaifiyarta wadda itama Hussaina ce ta ingizata kan cewa su hada Ghazalatu da nata dan Nura. Hussaina gani take ta sami dama da zata dandali arzikin gidan Gambo yadda ya kamata. A zahiri Gambo da Mami sun fi ta rufin asiri. Sai dai bata sani ba Mami a nata gidan kafin Major ya sami lafiya har ya fara aiki guminta ake ci. Ita kawai gani take suna da kudi ne suke son hada nasu 'ya'yan ita ko oho. Mummy Gambo an hau dokin zuciya ba bata lokaci ta amince bayan sun bar gidan Mami a jiya.
"Saboda ance ya auri wadda mahaifinsa ya nema masa?" Baban Fawaz ya tambayeta.
"Ni dai kawai bana so ne yanzu"