Kenza eBookz

Batuol mamman complete novel - Chapter 37

Batuol mamman complete novel - Chapter 37

Batuol mamman complete novel Chapter 37: Batuol mamman complete novel Chapter 37. Gaban Awwab sai da yayi wata rawa kamar ance masa anyi auren Radhiya ne.…

3,358 words

Gaban Awwab sai da yayi wata rawa kamar ance masa anyi auren Radhiya ne. Likita??? Alheran da shegen son likitoci shikenan Ummi ta cuce shi wallahi. Wa ya sani ma ko sun fara soyayya an barshi a nan akan su Ghazalatu. Bai ko zauna ba ya wuce gidan Ummin sai yayi sa'ar ganin Yousuf din shine ya tsiri cin abinci tare da ita.

Juice din kankana mai sanyi ta zuba a glass cup bayan sun gama ci ta kurba sau biyu ta ajiye masa a kusa da hannunsa ta mike abinta ta koma wurinsu Zahra. Daukar cup din yayi ya shanye ya yi hanyar kofa tare da kiran Zayyana wai zai bata sako.

Wani shu'umin murmushi takeyi na abinda ta gama gani wanda dole ma ta labartawa 'yan uwanta Emzee da Ibrahim amma suna hada ido da ta ga kallon da yayi mata ta gyara fuskarta.

Radhiya na jin karar rufewar kofar ta tashi da sauri tana dafe kirji.

"Kuturin bala'i...wai... kunji kirjina kuwa? Har wani zazzabi zazzabi ne ya kamani fa"

Zahra da Fauziyya suka kwashe da dariya harda kyakyatawa. Fauziyya ta karkace kai tana kallonta a tsaye hannuwa a kirji tace "shegiya Radhiya ashe kina nan baki mutu ba"

"Lallai ma Adda to wace wannan a gabanki?"

"Nufina Radhiyanmu dai mai balotelli ashe tana nan kin boyeta."

Dariya suke sosai su ukun Zahra tace "Fauziyya auren bakatsine ya koya miki zagi"

Juya idanu tayi tana dariya "Ke Radhiya auren Katsinawa akwai riba wallahi ku dena gulmar nan haka don naga take taken Hamma wata rana sai yayi hugging dinki a gaban mutane"

Kunya taji harda dora hannu a ka "haka kika koma maman Jawad?"

"Gaskiya ta fada miki ai, ni da wannan spoon exchange din da aure kuka yi kawai sai ayi wacce za'ayi ko Fauzi"

"Na shiga uku zasu bata yarinya" Radhiya tace tana dariya sosai.

"Wallahi balotelli na nan ashe kike disguising dinta da wannan hot chick din"

"Kinsan Allah Radhiya ki hana Hamma zaman lafiya...yarinya kill him with love sai ya dawo yana baki hakurin wannan fushin nasa mara dalili" cewar Fauziyya.

"Ni dai kiyi masa a hankali amma bance a sassauta ba" Zahra ta kawo tata shawarar.

"Ance muku son sa nake yi ne?" Ta basu amsa tana dage gira.

Fauziyya tace "Eh to gaskiya baki ce ba. Na fuskanci shi da Arifah kamar akwai wata a kasa don yarinyar tayi 100%. Kamar ance zata zo kuwa gobe zanyi kana confirming meye tsakaninsu"

Nan da nan fuskar Radhiya ta chanja tana jin dan mutumcin da suka fara da Arifan ta waya yazo karshe. Zahra da Fauziyya sunyi dariya son ransu bayan ta fice zuwa gidan Mama.

**********

Washegari tsabar gajiya kasa tashi sukayi da wuri gashi sun raba dare suna hira. Ummi bata sauraresu ba ta shiga kitchen tare da Tante Nasara da ta biyota itama ta tashi da wurin. Cikinsu Fauziyya ce ta fara tashi taje ta karbi aikin kusan komai ita ta karasa shi kafin Ummi ta dawo daga yiwa Daadaa wanka don Radhiya ta lakaba masa daga zuwanta tace ita bata yarda a kira mata sunan baba ba.

Goma saura kowa ya tashi banda Radhiya. Tafi sati bata baccin kirki kullum yawon tsaraba da kuma kammala shirye shiryen project din ga tafiya a gabanta. Ummi tayi magana Tante tace a kyaleta ta gaji ne.

Sai shadaya ta tashi babu kowa a dakin. Wanka tayi ta gyara gadon sannan ta shirya cikin atampa blue da baki riga da zani wrapper. Tayi missing irinsu don bata cika sakawa ba a France. Ta gama daurinta mai kyau ta tuna ba zama zata yi ba sai kawai ta tuge shi ta tafi dakin Ummi. A can ta sami bakin mayafi mara nauyi ta yafa ta sake gyara fuskarta ta fito falo. Nan ma shiru, tana son magana da Yousuf amma bashi da sim din Nigeria. Ba ya nan yana wurinsu Awwab da Raji duk sun hadu dasu Daddy da Baba Hadir ana hira a gidan Mami.

Tasan basa wuce gidan Mama shiyasa ta tafi can. Ko neman abinci bata yi ba ta gaishe da iyayen nasu itama ta zauma zaman hira. Daadaa ta dauka ta shagala da yi masa wasa sai hamma yake.

"Kawo shi na goya shi bacci yake ji tunda akayi wanka bai koma ba" Ummi ta mika hannu za ta karbe shi.

"Don Allah goya min Ummi" tace tana ajiye mayafinta a gefe ta duka baya.

Ummi ta gyara tsayuwa "me? Rufa min asiri indai goyon ne ga masu karfi nan ki dauka"

"Tante" tace tana tura baki.

"Don Allah goya mata mana Mairama"

"Nasan halinta sarai. Dama can ba wani iya raino tayi ba bare yanzu da ta dade babu wani yaro a inda take. Da dai girki ne sai na sakar mata"

Zahra tace "Ummi ni zan bada labari. Cewa take fa na zunguri Femi don kawai taji muryarsa"

Dariya suke ta yi mata Tante na tarewa. Mama ma dai sai ta goyi baya "idan bata koya ba yanzu ba sai yaushe ni da nake fatan kafin shekara ta zagayo mun rike sabon jika"

"Yauwa Mama" tace tana murmushi ta sake dukawa.

Ummi tace babu ruwanta Mami ce ta goya mata shi aka daure shi sosai don Radhiya kam bata iya goyo ba. Ana goya mata shi kuwa ta mayar da mayafinta aka bude fuskarsa. Zama tayi akan kujera ko motsi bata son yi tana tsoron kada goyon ya kwance ya fadi. Tashi su Fauziyya suka yi zasu je suyi wanka Ummi tace bayan azahar su hadu duka da yaransu Awwab ya kaisu gidan Daddy Haroun su gaishe su. Bashi da labarin fitar tace Zayyana ta turo shi don tasan a waya bazaiyi yadda take so ba.

Can ya baro sauran mazan ya shigo falon da sallamar da ta tsinka zuciyar Radhiya.

Dauke kai tayi tana wasa da wayar hannunta ya shigo yana kamshi ya tsaya a bayan kujerar da take zaune. Na shiga uku tace a ranta tana jin kusancin dake tsakaninsu yana affecting dinta. Rikicewa tayi sosai amma bata so ta nuna shiyasa taki yarda ta dago kanta.

"Ummi gani"

"So nake bayan azahar ka hada kan kannenka ku je gidan mamanku Gambo ku gaishe su. Ga Raji da Yousuf ma duk ku tafi tare"

Shiru yayi amma yasan yanzun nan sai ta fara fada idan yaki amincewa ga mutane a wurin "to Ummi"

"Radhiya kun gaisa da yayanki ne?" Mama tace saboda dazu ya shigo sauran duka sun gaishe shi.

"Ina kwana" tace a hankali ko shi da yake bayanta baiji sosai ba. Kin amsawa yayi tunda dama baiji me tace da kyau ba.

"Nasara muje ki huta ko kin tashi da wuri ga gajiyar tafiya" Ummi tace suka tashi tare sai Mami da Mama.

Mami ma sai tace zata tafi gida a turo mata Zayyana ta tayata girkin rana. Yana kallonsu duka suka fice Mama ma ciki tayi abinta dama duk hanyar barinsu tare nemanta take yi.

Dukuwa yayi da kansa gefen fuskarta taji tsigar jikinta na tashi abinda shi yaji fiye da haka "kin dena gaisuwa ne?" Taji yace muryarsa na dukan dodon kunnenta.

Muryarta ta sake ragewa tace "na gaisheka fa"

"Sai a sake tunda banji ba"

Humm'umm bai san itama taci ganye bane yanzu ko. Kin magana tayi yana nan tsaye a bayanta har lokacin har ya soma amsa wayar Arifah tana masa barka da dawowa da sanar dashi zasu shigo gari da Mamanta kafin suna.

Haushi ya kama Radhiya da ta fahimci da mace yake magana. Gara ta bashi wuri idan ma akwai wata I love you da zamanta a wurin ya hana a fada sai yaji dadin sakewa. Tashi tayi da karfinta ai kuwa goyon nata taji gabadaya yayi sako-sako yana neman kwancewa baby ya fado. Yadda gabanta ya fadi sauri tayi ta duka jikinta na rawa ta tallafo Daadaa da hannuwanta ta baya. A hankali ta saki tana kokarin gyara gaban da ya kwance duka yaron yayi motsi a gigice tace "Hamma"

Yana da kallonta amma a zatonsa goyon zata gyara. Kuma tsabar tsoro ta kasa daga murya kada yaron ya tsorata ya fado.

"Hamma ka ajiye wayar mana" tace tana daga murya.

Sai lokacin ya cire wayar daga kunnensa "me kika ce?"

Kafafu biyu Daadaa yake dan shureta dasu alamun baya jindadin yanayin da yake.

Kuka ne ya taho mata kada ta saki dan mutane "Hamma please help" tace tana rike gaban zanin sosai kuma taki dagowa.

Wayarsa ya ajiye da sauri akan kujerar da ta tashi ya zagayo yana dukawa ya ga me ya sameta "meye?"

A rikice take bata san ya zasu kwashe da Ummi ba idan ya fado "goyon ya kwance"

"To ki gyara mana" yace yana mikewa ya gyara tsayuwarsa.

"Ban iya ba fa Hamma"

"Seriuosly?" Shima ya soma rikicewar ganin tana ta saka hannu daya a gaba daya a baya.

"Zai fadi" ta sake cewa da yayi wani irin zillo yana canyara ihu ya gaji.

"Kwace zanin da sauri" yace yana saka hannu a bayan yaron ita kuma ta kwance gaban "tashi a hankali"

Tana tashi yaron ya fada a hannunsa ya kankame shi a kirjinsa "are you okay?" ya tambayeta yana kallon yadda tayi wuri wuri.

"Allah Ya soni da ya fado..."

"Da sai mu haifi wani" yace yana kallon dimple dinta.

Idanunta ta dauke daga kansa maganar tana dada shiga kwanyarta. Duk wasu matakan nuna masa yanzu ba da bane ta nemesu ta rasa sai uwar kunyar da ya hadata da ita. Ya san me yayi mata amma sai ya wayance irin yadda ta taba yi masa.

"Silly girl, me kike tunanin ina nufi?"

"Ba nufinka idan ka haifi naka nima na haifi nawa sai mu kawo mu hada mata ba?"

Kanta tsaye tayi maganar kafin ya gama gano lagonta ta tafi ta barshi da baby a hannu.

**********

"Wurin wa kazo?"

"Waye shugabanku a nan barrack din?"

Dariya ya basu suna masa kallon wanda bai san me yake yi ba. Barrack ai ba wurin da zaka zo kai tsaye bane idan baka san wanda kake nema ba.

Chibuzor ya rasa wa zaice musu. Sai da yayi sati a garinsu ana ta jajantawa iyayensa abinda ya same shi sannan da kyar ya kwaci kansa ya taho Sakkwato saboda cika alkawarin da ya daukarwa kansa da Zayyan. Bai san komai game da tsarin sojoji ba kamar chanjin mukami shiyasa kawai yace "Lieutenant Hadir nake nema" yana fata daidai ya fadi sunan.

Duk wani hargagi da zasu yi masa sunyi a ganinsu bai san me yake yi ba. Gashi dai a haka yayo fes dashi. Kin tafiya yayi tun safe har yamma ana ta abu daya yana tsaye a bakin gate. Wani ne cikinsu ya shiga ciki bangaren ofisoshinsu suna hira da wani da yake zaune a bayan wata kanta yake bashi labarin wani msi naci a waje.

"Baku saka shi tsallen kwado ba?"

"Tausayi ya bani. Ya dage wai sako ya kawowa Lt Hadir. Ban taba jin sunan ba ma. Amma an chaje shi babu komai a jikinsa"

Wani yazo wucewa suka tambaye shi ko ya taba jin mai wannan sunan. Wanda yake bayansa ne ya amsa "an taba yi mana amma shi fa yayi retire saboda rashin lafiya tun bayan dawowarsu daga Liberia an dade don tun ina non-commisioned officer"

Wanda ya kawo zancen ya mike "yayi zancen Liberia fa. Bari dai na koma naji" [5/22, 11:03 PM] Sis Ruky: Da ya fito Chibuzor yana tsaye can gefe ya gaji da magana ya koma yana sabunta tunani da nemarwa kansa mafita. Baiyi zaton haka abin zai zama ba gabadaya ya shiga cikin tashin hankali saboda tsoron kada ya kasa fitar da Zayyan.

Wancan mutumin ne ya dawo gareshi yace masa akwai mai wannan sunan da ya taba zama amma yanzu baya nan.

Wani sanyi yaji ya ratsa zuciyarsa "a ina zan same shi? Sako nake dashi mai mahimmanci"

"Kana iya fada min sai na gani sakon yana da amfani ko babu"

Da dukkan murnarsa yace "na hadu da dan uwansa ne a prison...."

"You must be crazy" Sojan ya daka masa tsawar da ta janyo hankalin sauran da suke gefe. Shi kuwa Chibuzor jikinsa rawa ya soma yi. Tun ba yau ba yaki jinin duk wani abu da zai hada shi da hukuma. Sauran suka taru a kansa ana ta daga murya ya gigice. Fada suke yi kawai akan yazo musu da zancen banza. Meye hadinsu da prison da zai ce ya hadu da dan uwan dayansu. Dadin kayan haushin ma wanda yake magana a kai baya nan. Basuyi masa uzuri yayi musu bayanin da ya dace ba suka nemi dukansa ya gudu. A gajiye ya koma hotel din da yayi masauki ya kira matarsa Emma ya fada mata yadda ta kasance.

"Ka koma gobe ka dage sai sun barka kayi magana da wani mai mukami a ciki. Banda abinsu waye yake yanke hukunci babu sauraron bayani?"

"Gaskiya bazan iya komawa ba. Akwai matsalolin tsaro a kasar nan. Nayi sa'a da basu kamani sun rufe ba. Kallon wani mara hankali ina jin suke yi min"

"Yanzu me kake tunanin yi a kai?"

"Ban sani ba" ya fada cike da damuwa.

"Darling, me zai hana kayi amfani da media? Ka tuna nima fa a TV kawata ta ganka a news lokacin da aka kamaka a airport shine ta fada min"

Ihun murna Chibuzor yayi yana gode mata. Sam baiyi wannan tunanin ba yaje zai jefa kansa ga wahala.

Karfe goma washegari a gidan talabijin na NTA reshen garin tayi masa. Filin cigiya da sanarwa ya nema saboda a ganinsa gidan TV musamman na kasa wato NTA zai fi saurin zama hanyar yada cigiyar. Idan ya gama da nan niyarsa ya nemi gidan rediyo kuma a nan Sakkwato da Kano. Wata ma'aikaciya ce tayi masa bayanin cewa zai biya bayan ya fadi na kwana nawa yake so a rinka sanya sakon. Da suka gama da wannan ya fahimci komai ta bashi form da zai cike abinda yake nema.

"Idan akwai hoton wanda kake nema ko naka idan sun san fuskarka sai ka kawo"

"Babu hoto sai sunaye"

"Rubuta min a nan..." ta saka yatsanta a inda take bukata.

Chibuzor bai rike sunayen duka ba amma ya rubuta abinda ya tuna.

(Ina neman iyalin Lt. Zayyan Muhammad Tureta na Giginya Barrack Sokoto wanda ya tafi Liberia a 1993. Sunan matarsa Mariyama, yarinyarsa Al.....) duk yadda yaso ya kasa tuna sunan Radhiya da Zayyan ya fada masa wato Alheran (abokinsa Hadir da Mustafa da kuma Col. Nasiruddeen Aliyu). Sunan karshe shine wanda yafi zama sosai a kansa. Matar ya mikawa takardar zata duba domin tsara yadda sanarwar zata kasance ta karanta bayanin nasa bai wani gamsar da ita ba. Dole sai sunyi masa tambayoyi kenan yadda zai iya fadar me yake bukata kada ayi asarar kudi.

"Su wadannan baka san sunayen iyayensu ba domin saurin gano su?"

"Akwai matsala ne? Ban sani ba" ya bata amsa yana fatan kada tace bazai yiwu ba. "Amma ai wannan na rike, Col Nasiruddeen Aliyu.."

Daga bayansa wani ya taho rike da takardu ya dakata da sauri "Col Nasiruddeen Aliyu dai gwamnan Plateau? Me yayi? Ke akwai sabon news ne?"

"Ka sanshi ne? Nemansa nake" Chibuzor yace shima da sauri.

"Gwamna ne fa, waye bai sanshi ba? Me yake faruwa ne?" Ya tambayi matar.

Hannunsa Chibuzor ya rike "shi gwamnan soja ne? Yaje Liberia tsakanin 1993 da 1994?"

A dan tsorace mutumin ya zame hannunsa "tsohon soja ne yayi retire, amma ban sani ba ko yaje Liberia"

A gigice Chibuzor ya fito da wayarsa daga aljihu ya rattaba sunan Col. Nasiruddeen Aliyu a google search. Tashin farko sai ga bayanai sun bayyana game dashi. Inda yasan ana saurin samun bayani ya fara dubawa wato wikipedia. Karatu yake yana tsallaken layi kamar wani zai riga shi.

(Tsohon sojan kuma kwararren likita a wancan zamani ya tsunduma cikin siyasa ne wajajen 1996 inda tauraronsa ya rinka haskawa yayi suna cikin kankanin lokaci. Mutane suna alakanta wannan nasara tashi da cewa an sanshi a matsayin sojan da ya kwashi kimanin watanni takwas a hannun 'yan tawayen kasar Liberia kafin Allah Ya kubutar dashi wani dare da sojoji suka kai sumame a mabuyarsu. Tausayi da jarumtarsa da aka gani yasa bai taba tsayawa takara ya fadi ba)

Mahaukacin ihu Chibuzor ya saki yana dariya "thank you Jesus" sannan ya kaiwa mutumin nan wawura ya rungume shi kamkam sai da takardun hannunsa suka fadi. Bai tsaya bata lokaci ba ya dire mutumin ya fita daga ofishin a guje.

Kai tsaye hotel din ya koma ya tattaro kayansa ya tafi airport. Ba shi ya sami kansa a kofar gidan gwamnatin dake Jos ba sai yamma. Tunda ya gane wurin shawara ita ce ya nemi masauki gobe ya dawo. Haka kuwa akayi domin washegari takwas ma a bakin gate din ta riske shi. Ganin gwamna ba abin wasa bane. Masu gadi suka saka shi a gaba aka fara masa tambayoyi akan dalilin zuwansa.

"Sako ne zan bawa Col. Nasiruddeen"

Ganin wani mara da'a suke yi masa. Idan ba mara da'a ba ya za'ayi ya kira sunan gwamna a kofar gidansa kai tsaye irin haka. Shi kuwa dadewa rabonsa da Nigeria da kuma idan yazo ba yawo yake irin haka ba yasa ya manta abubuwa.

"Nasha wahala ku taimaka min"

"Ka koma ka nemi appoitment dashi ba wai kazo haka kawai gida ba. Idan kowa na iya ganinsa a gida duka garin nan zasu tare a nan kenan"

"Naji ta yaya ake neman appointment din?"

"Ka je office dinsa ka nema a can. Idan kayi sa'a ka ganshi a wata daya"

Suka kece da dariya. Wannan ko kadan baiyi kama da wanda Gwamnan nasu zai saurara nan kusa ba saboda ayyuka da suka sha kansa 'yan kwanakin nan. Sannan kuma ai ba haka nan ake ganinsa ba, akwai matakai da ake bi.

Bai hakura ba yace "yana gida yanzu ko office?"

"Yana office"

"Nagode"

Gefe ya koma abinsa ya tsaya a jikin katangar gidan. Da sauri cikin masu gadin mai kayan sojoji yazo yace ya bar wurin. Gaba ya kara amma duk inda yayi sai ace ya matsa wai ba wurin tsayuwa bane. Chibuzor baiyi zuciya ba don biyan bukata yafi dogon buri. Ainihin titin da ake yin kwanar dama a kansa a shigo titin gidan gwamnatin yaje ya sami inuwar wani gida da filawoyinsa suka hauro ta saman katanga ya tsaya. A nan ya wuni ko ruwa bai matsa ya saya ba saboda tsoron kada ya rasa abinda yake nema.

Gajiya, yunwa da shigowar sanyi wanda baya yiwa mutane da sauki a garin na Jos sune suka sarke shi amma da yake mutum ne mai juriya da amana bai gajiya ba. Tunawa kawai yake yi da shekarun Zayyan a prison dinnan yana ji a ransa da yana da hali ko sakan daya bazai bari ya sake yi ba.

Tara da rabi na dare sai ga jiniyar motocin gwamna sun taho a sukwane. Ko kallon titin da zai tsallaka baiyi ba ya bi zugar motocin nan a guje yana harin ta tsakiyar wadda yafi tsammanin ita ce gwamnan ke ciki.

"Zayyan Tureta is alive"

"Zayyan Tureta is alive"

"Lt. Zayyan Tureta"

"Liberia prison"

Wadannan kalmomin ya rinka maimaitawa yana bin motocin yaki sauraron ihun da sojoji suke yi masa.

His Excellency Nasiruddeen yana bayam mota tsabar gajiya har soma gyangyadi yaji kalmar TURETA da LIBERIA. Firgigit ya bude idanu ya soma cewa "stop da car" cikin gaggawa. Dreban sai da ya tsorata amma shi da PA sun kula kamar ba a hayyacinsa yake ba duk ya rude shiyasa ya danna trafikato zuwa barin dama sauran motocin bayan suka tsattsaya suma. Yau babu batun jiran a bude masa kofa da kansa ya bude don sauri ya kusa faduwa saboda babbar rigarsa da ta harde shi. Wurin da sojoji masu tsaronsa suka danne Chibuzor a kasa ya isa yana yi musu tsawar su daga shi. Kowa darewa yayi gefe da suka ga ya durkusa ya tayar da Chibuzor zaune. Cikin harshen turanci yace masa

"Me kace?"

Jikinsa babu kwari sosai ya dago kai yana kallonsa "kaine Col. Nasiruddeen Aliyu?"

"Nine, nine" ya rinka nanatawa yana gyada kai.

Yana jin wata kakkarfar ajiyar zuciya da yaron ya saki don bazai fi sa'an Awwab ba.

"Sir, Lieutenant ZAYYAN MUHAMMAD TURETA..."

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull