Batuol mamman complete novel - Chapter 46
Batuol mamman complete novel Chapter 46: Batuol mamman complete novel Chapter 46. Sunyi ta hira kamar kada su rabu don washegari karfe bakwai zai bar gida.…
3,332 words
Sunyi ta hira kamar kada su rabu don washegari karfe bakwai zai bar gida. Da safe da wuri ta tashi don suyi sallama duk da wayar da suka dade suna yi cikin dare don ma ya dage sai ta kwanta. Bayan tafiyarsa ba jimawa su Zahra su ma suka dauki hanya ita da Raji sai kuma tawagar su Ummi. Gidan sai yayiwa su Mami shiru don ma Fauziyya tana nan amma Ibrahim da Zayyana duk sun bisu. Shi Ibrahim zasu yi kwanaki kadan da Emzee a Sumaila su dawo Kano gidan nasa kakannin.
***********
Tun dare Malamijo yake ya da habaici a cikin gidansa wanda Hajiyayye bata fahimta ba.
"Gobe iwar haka watan tatse rashin mutumcin wasu zai tsaya."
Hajiyayye tana sakace hakori zazzaro masa idanu "me kenan kake nufi"
"Zancen zuci ne ya fito fili. Ko an hana magana ne ban sani ba?"
"Kayi abarka. A dai kula ne kada yawan surutun ya tasar min yara kasan halinsu. Yanzu duk naman da suka ci sai kaji suna neman kari"
Dauriya kawai yake a kai gobe amma yana cikin tashin hankalin rashin sanin ina shanunsa. Yau tun asuba yake gonar. Tsagerin yaron nata da yaje daukan wasu sai ya kasa saboda ganin idonsa da wasu bakin fuskoki dole ya tafi.
"Allah Ya hada fuskokinku da sarkin mayu dai amaryata" Malamijo yace harda hade hannuwa irin na mai addu"a.
Cikin Hajiyayye kuwa ya cure wuri guda a take kamar zata yi zawo "wannan wane irin mugun fata ne Malamijo?"
"Ban gane mugun fata ba. Yanzu kamar ni kinsan dadin da zanji duk ranar da na hadu da Mai Martaba Sarkin Kano Dan Lamido kuwa?"
Rai a bace tace "to meye hadin sarkin Kano da sarkin mayu?"
"Meye ne naga kin soma gumi? Namu sarkin shine sarkin Kano. Ke kuma naku Sarkin mayu. Yadda nake son ganin namu kuma nake kaunarki shine ne nake miki fatan haduwa da naku kema"
"To ba amin ba...kaga ni kudi nake so kamar dubu dari karshen wata yaran nan namu kowanne ana yi masa yanka shi kadai saboda rage karfin maitar"
Allah Yaso shi ba don abinda yaji da kunnuwansa ba da yanzu hankalinsa in yayi dubu ya tashi akan neman kudin. Amma yanzu sai cewa yayi tayi hakuri zai tanadar mata zuwa dare gobe.
Saboda samun wuri harda yi masa tsaki tace "to a hanzarta"
"To ranki ya dade"
Matsawa tayi akan katifar tana nuna masa wuri "taho mu kwanta ni bacci nake ji"
Hadiyar yawu yayi saboda sai yanzu da yake sansano tsira ya kara tabbatar da kazantarta da muguwar rama. Wa ya aike shi kwanciya kusa da ita karshe kasusuwan jikinta suje suyi masa sartse ko su soke shi.
Karfe takwas na safe ya soma kiran Ummi wai yana fata yaran sun taho tace masa tare zasu zo da ita harda Halifan Salame.
"In kin barni na ma manta da sunansa tunda uwarsa bata san mutumcina ba. Wannan yaro ina tsammani kamaninsa ma sun bace min. Kinga sai kun taho dai. A hanzarta do Allah"
Ta gama tabbatarwa lallai babu lafiya gidan nasu. Sun kimtsa kowa ya fito suka yi sallama dasu Mami da Mama.
Emzee da akace ya sako kayan makaranta sai ya sami irin shirt dinnan da ake yi da zane zanen khakin sojoji ya saka akan bakin wando. Radhiya kuma atampa ta saka da mayafi tayi kyau sosai. Umminta kuma wani lace ne dan ubansu mai tsada da kyau ta saka green da orange ta dora orange din mayafi da farin gilashinta tayi kyau sosai Zayyan ji yayi kamar a dage tafiyar ko na awa guda ne ya samu ya yaba mata yadda ya dace. Dadinsa ma mota guda Daddy ya bashi da dreba daga shi sai ita. Motar gidansu Halifa kuma mai wuri uku ce yaran suka duru a ciki.
Abinka da tafiyar sammako da kuma rashin tsaye tsaye a hanya karfe hudu suna cikin garin Sumaila. Shekarun baya ne suka rinka dawowa Zayyan. Zuwansa garin nan na karshe lokacin da Mairama tazo yawon arba'in din Alheran ne. Yanzu gashi Alheran dinsa aure yake shirin yi mata. Bacci ko na minti biyar bai iya yu ba sai kalle kallen chanjin da aka samu. Kafin su karasa gidan Malamijo motar da su Radhiya suke ciki ta tsaya daga bakin wata kwana. Halifa ne ya sauka ya taho wurin motar su Ummi ya leka ta taga.
"Gwaggo Mairama nace bari naje wurin Umma na fada mata kunzo tazo ku gaisa kafin ku wuce Kanon"
Zayyan bai manta da wace Salame a baya ba kuma har yanzu ba wai yana dokin ganinta bane. Ya kula Halifa yaro ne mai nutsuwa daga jiya da suka kwana gashi uwa uba da ga Alh Salisu. Jiyan da Mairama taso sanar dashi cewa sun rabu da baban Halifa saboda kada yayi masa maganarta sharewa kawai yayi.
"Ta san da zuwan naka ne?" Ummi ta tambayeshi.
"Bata da waya amma nasan zata zo ko don ta tayamu murnar dawowar Daada" ya kare da murmushi.
Suna kallo ya gangara daga baya sai ka rantse wani babban Alhaji ne. Girman jikinsa da irin shaddodi da yadikan da yake sakawa suke kara masa cika ido.
Malamijo yau ko kofar gida bai leke ba yana jiraj zuwan bakinsa. Abinci biyu akeyi yanzu a gidan nasa. Nasu Yadikko daban na amarya da iyalinta daban. Kunya tasa bai iya fadawa Yadikko zuwan bakin da bai ma san suna da yawa ba kuma. Ita ranta ya dade Hajiyayye kuma babu dalilin da zaisa ya fada mata. Dirin mota yaji yana kashingide a tsakar gida daga shi sai dogon wando da 'yar shara duk sanyin nan ba ji yake sosai ba ya tashi da sauri kai baka ce tsoho bane mai shekarunsa sam baya jin jikinsa. Silifas dinsa ya saka yana washe bakin nan Hajiyayye ta fito daga kitchen da katuwar cooler shakare da farar shinkafa 'yar gomnati ta dafawa 'ya'ya zasu zo su ci banza.
"Ina kuma zaka je kake wannan saurin? Ga abinci ka jira in dan tsakura maka ladan ganin ido ko"
Bai ma jira masu tare masan sun shigo ba ya dora hannuwa a kugu ya daure fuska "a cikin gidan nawa kike zancen tsakura min abinci? Ashe baki da mutumci ban sani ba. To ki jira in dawo ciki zaki ga yadda zanyi dake mutuniyar banza"
Ta tsorata sosai amma sai ta dake kada tayi saurin nunawa "ni Hajiyayye kake yiwa wannan magana? Ko magagin baccin da ka soma ne bai sakeka ba?"
Kallon banza yayi mata harda su juya idanu yau take sallah fa a wurinsa ya fita a gaggauce. Kiris ya rage ya saki fitsari da ya ga 'ya'yan Hajiyayye ne ashe a akori kura manyan mazan su uku katti dasu tamkar ba daga cikinta suka fito ba. Dirowa suka yi daga bayan motar suka cewa dreban yaje gidan gonar ya jirasu. Zasu ci abinci ne su zo a dauko shanu ko hudu ne idan motar zata dauka. Idanun Malamijo sai suka kawo ruwa ya fara kokawa da kwalla. Samarin suka sauko kai cikin gidan suna muzurai su a dole mayu 'ya'yan mayya. Tsabar wulakanci basu duba tsufansa ba suka ringa bangazar kafadarsa suka shige cikin gidan. Jiki a sanyaye ya juya zai koma sai ga wasu galla gallan motoci guda biyu sun doso gidan.
Ihu ne kawai baiyi ba don tsananin murna ya koma daga soron ya tsaya yana jiransu. Jin kansa yake daidai da kowane maye da yake cikin gidansa.
Emzee da Ibrahim ne suka fara shigowa ya tarbesu cikin nishadi. Sai 'yan mata Hibbah da Zayyana sannan Radhiya ta biyo bayansu.
"Malamijo nawa" tace tana murmushin da ta saba idan zata yi masa tsiya.
"Yanzu ace kin zo kasar 'Yar soja bazan ganki ba sai nayi cigiya? Ina Mairaman take? Duniya Mairama duk tafi sona kaf 'ya'yan babu mai girmama maganar Malamijo kamar ta." Yayi maganar batare da korafin Radhiya kada tayi masa wani abu ba daidai ba a cikin gidan.
"Uhmm Malamijo tare fa muke da..." Emzee ya soma fada masa saboda yana tunanin gara ya sani kada abin yazo masa a bazata.
Hannu ya yarfe gefe yana kallon Mairama da wani mutum yasha yadi na maza mai masifar kyau da tsada cikin wanda Baban Arifah yasa aka dinka masa.
"Ko ma waye su zo ku hadu ku ci uban 'yan iskan gidan nan"
"Su wa kenan?" Radhiya tace da doki sai dai Malamijo baya ma jinta ko kadan. Mutuwar tsaye yayi hannunsa a kahon zuci yana farfar da idanu bakinsa ya kasa hada kalmar Zayyan da yake son ambata.
Zayyan na karasowa da murmushinsa ya mika hannu ya riko hannun daman Malamijo. Ai hannuwansu na haduwa Malamijo yayi sharaf a sume ya fado masa a jiki.
Dama sun sani dole ya tsorata. Emzee ya rugu zai daga shi Zayyan yace ya wuce su gyara inda zai kwantar dashi ya ciccibe shi shi kadai tamkar ya dauki yaro karami. To abu ne babu body babu alamar body. Dama ya lafiyar kura...tuntuni babu jikin Hajiyayye mayya tazo ta karasa gawar da ba tata ba.
Tsakar gidan babu kowa sai gayyar su Hajiyayye rashin wadatar dakin yasa ta dawo dasu nan duk da ma dai akwai sanyi garin. Banda cooler din shinkafa a gefe ga ta miyar da ta wadatu da nama na tinkiyar da suka dauko jiya ga salad da su tumatir yau din bushasha za'ayi saboda jiya sun tarki sa'a. Shanun da suka dauka suna ajiye a gidan Talle ranar kasuwar dabbobi zasu kai a kwashi naira.
Da sauri Emzee ya shigo sabuwar tabarmar da ta shimfida yaran nata sun soma zama ya murtuke fuska duk da bai sansu ba "kai ku tashi"
"Yaro kai kuma daga ina?" Babban cikin nasu ya tambaya yana masa kallon raini. Ido kawai Emzee ya watsa masa yaja baya da sauri. Tsabar training sai budewa kwanjinsa yake yi musamman daga kirji, hannuwa suna murdewa irin na kakkarfan namiji. Rigar jikinsa ma kusan ta kama shi ita ta karasa tona asirin yanayin jikin nasa. Wanda ya rage akan tabarmar mai bin babban ya kalla yayi masa alamar ya tashi.
"In naki fa?"
Emzee bai sake tunani ba ya ja tabarmar ya kifar dashi a wurin ya koma gefen dakin Malamijo ya shimfide masa ita sannan ya shiga ya dauko masa filo. Radhiya dakin Yadikko tayi da sauri ta same shi a rufe da karamin kwado sai ta je na Hajjo. Nan ta tarar da komai ba yadda ta sani ba sai karajin Hajiyayye daga bayanta.
"Ke daga ina kuke ne kike leka min daki?"
Da mamaki tace "dakinki? Ina Hajjon kuma?"
Daidai nan Zayyan ya shigo da Malamijo a hannu ya kwantar dashi a inda Emzee ya nuna masa Ummi tana take masa baya hankali a tashe.
"Ku su waye ne?" Hajiyayye ta matso inda suke ta kalli Malamijo ta watsar.
Cikin salama Ummi tace mata "ni 'yarsa ce wadannan kuma yarana ne da babansu"
Tsaki taja duk da suturun jikinsu sunyi mata kwarjini amma bata so raini ya shiga tsakaninta dasu. Yadda uban yake tsoronta to kowa ma fa yaji tsoro kada a kawo mata wargi ba dauka zata yi ba.
"Me ya same Malamijon?" Tace a dakile wanda tuni ran kowa ya sosu.
"Tsorata yayi ya suma" Ummi ta bata amsa.
"uhmmm" ta tabe baki "bana son hayaniya kamar yadda shi uban naku ya sani a kiyaye"
Hayaniyar da take yi ce tasa mutanen cikin gidan suka fara lekowa ganin da wa take yi. Na'e ce kawai da wasu cikin yaran. Yadikko sun tafi asibiti da Atine guda cikin jariran babu lafiya ko ta kan Malamijo bata bi ba da zasu tafi. Ita yanzu burinta kawai Atine tayi arba'in yaran su kara kwari itama ta tafi. Shekaru sama da arba'in tana zaune tamkar sharar gidansa ta kula masa da yara ya bude baki ya fada mata magana son ransa.
Kannen Mairama da suke zawarci su biyu da sauran kannensu duk sunyi zuru zuru amma ganinta sai gasu sun fara sakin fuska suna yi musu barka da zuwa.
Hajiyayye ta wani daka musu tsawa saboda tsaurin ido "ba cewa nayi idan yaran nan sun zo cin abinci kowa ya zauna a daki ba? Ko shi Malamijon bai nanata muku ba kafin shigowarsu?"
Mayunwatan yaran kananun suka matso suna jira ta zuba musu ta kalli tabarmarta "ku shiga dakinsa akwai tabarma a bani tawa zan ciyar da yaranmu"
Zayyan da Mairama sun tsaya ne kawai kallon wannan mata mai zubin mahaukata tana ta bada umarni a gidan. Daurewa tayi ta tambayi wata kanwarta matsayinta a gidan.
"Amaryar Malamijo ce"
"Amarya kuma?" A iya saninta babu sauran wuri a gidan nasu to wa ya saka. Sai gashi kafin ta tambaya ma ta bata amsa da cewa Hajjo ya saki "Malamijo Hajjo?" Tace kamar tayi kuka.
Kanenta da suke karatu a Kano gidanta su Laila duka lokacin da suka zo kafin ta wuce Abuja tasa sun tafi hutu wurin iyayensu mata. Ta san da tuni ta sami labari a wurinsu.
Babu wanda yayi motsi da Hajiyayye tace su dauke Malamijo daga kan tabarmarta ta doki cinya tana sababi wai zai farfado ya sameta ne sai ya yiwa bakin nan bayanin matsayinta.
Abin takaicin ya ishi Zayyan zaiyi magana Ummi ta dakatar dashi ta nuna masa Radhiya da take bin matar da wani irin kallon raini
"Baki ga suma yayi bane kike zancen a baki tabarma ku ci abinci?"
"Yarinya kada kice zaki yiwa Hajiyayye rashin kunya wallahi sai na farfasa miki jiki yanzun nan a wuce wurin" babban yace a kule yunwa na cin hanjinsa an tsaya ana bata musu lokaci. Ko kadan daga uwar har yaran basu da da'a.
Sai da ya gama Radhiya ta tafi gaban kulolin da ta kula suna yiwa kallon mutumci ta bude da ta ga miya ce nama ya kusan cika ta.
"Wa ya baki izinin taba min abinci? Ke idan Malamijo ya farka zan iya sawa ya hanaku sake zuwa gidan nan"
Emzee da Ibrahim Radhiya ta nunawa kulolin da hannu tamkar ba da ita ake magana ba "bros ga fa abinda ya kawomu Sumaila kuzo mu fara aiki"
Tamkar masu jira suka je zasu dauki kulolin nan yaran Hajiyayye suka yi kukan kura tamkar mayun gaske. Duk abinda suke yi Malamijo ya farfado ya ma dan bude ido da ya ga abu ya soma kankama ya runtse kayansa ya cigaba da kwanciya. Ummi da Daada wuri suka samu suka zauna saboda abin kunya ne ace suna da su Emzee su rinka saka baki suna magana da yara irin na Hajiyayye. Ummi tana da yakinin indai da yaranta a wurin bata da matsala don ko da Radhiya kadai ta barsu ta ishesu.
Wurin ke neman kacamewa Radhiya ta kira Zayyana ta nuna mata kula daya tace ta zauna a kai itama ta zauna akan daya ta dora kafa daya kan daya. Tsagerun Hajiyayye suna son tashinsu amma yadda take kada kafa ga wasu maza a tsaye a gefe wato Emzee da Ibrahim kowa ya tamke fuska duk sai suka sha jinin jikinsu. Malamijo da yaji abin baiyi masa ba ya dan kyallo ido daya yace "Zayyan"
Uba da da ne suka amsa a tare. Wai shi Malamijo a tunaninsa ko dai Hajiyayye mayar gaske ce take son tsorata shi da fatalwar surukinsa zai daure ai ba'a san Fulani da tsoro ba ya dauke kai kamar bai ganshi ba ya cigaba da cewa Emzee "ina rundunar sauran sojojin da kace zaku zo tare?"
Ba yaran ba Hajiyayye ma sai da cikinta ya bada sauti "soja kuma"
Emzee ya sake mazewa sai lokacin ta kula da kayan jikinsa ma. Hankalinta yayi mummunan tashi kuwa a tsorace ta cewa manyan su fita zata san abinyi. Su ma da sauri suka fita din kada rundunar sojojin su iso. Tana kallo Radhiya ta kira yaran gidan suka debo kwanaku yau ko biki ake a gidan sai haka. Abincin nan tas ta rabe musu harda kwakkwafe kular bata bar ko kwayar shinkafa ba.
Zayyan kallonta yayi ya saki murmushi kawai tana kara burge shi. Haka yake kaifi daya kuma haka yake son 'ya'yansa. Kada su cuci kowa kuma kada su bari a cuce su. Bayan ta gama ta tura kular wurin wanke wanke ta dawo kusa da Malamijo ta zauna. Hajiyayye ta rasa me ya kamata ta yi saboda bacin ran da take ciki. Wannan wane irin mutane ne suka shigo gidan da yake karkashin mulkinta suna neman chaza mata kai. Kwafa tayi ta bar wurin ta tafi daki zugar yaranta suna biye da ita ana kukan nama.
Malamijo sai lokacin ya bude ido yana murmushi a hankali yadda babu mai ji sai na kusa dashi yace "Alakakai gayyar mayu daga nan ma sai gidan tsoho"
Radhiya tace masa "fadi da karfi mana taji Malamijo a haka bazata san kana yi ba"
"Barni da ita a hakan ma kun more min su. Bana so taji ne ta dawo"
"Barka da yamma Malamijo" Zayyan yace bayan yaran sun gama dariyar kalaman Malamijo.
Jikinsa ne yayi wani mugun sanyi kamar an sare masa gwiwa ya juya ya tabbatar Zayyan din ne dai yake gani kawai sai ya koma ya kwanta ya rufe idanu.
"Mairama kirawo matar nan tazo ta tsallake ni."
"Tsallakewa kamar wata mayya"
"Yo ba mayyar bace? Aure ne na kaddara na kwasowa kaina. Yanzu don bala'i ko yaya na kalli bangaren arewa maso gabashin inda kike zaune sai in rinka gane gane"
Ibrahim da Emzee ne suka fara dariya Ummi ta hararesu. Zayyan da ya gane dashi ake dole ya rike tashi dariyar a gaban suruki.
"Kamar me da me kake gani?" Radhiya ta tambayeshi tana danne dariyarta.
Fuskarsa sai tayi kalar tausayi ya kalli Ummi yana girgiza kai "ina tsoron fada in saka babarku kuka". Kasa daurewa yayi da ya kyalla ido ya kuma ganin Zayyan a zaune " 'Yar soja mai kamar mahaifinku matar nan tana son yi min cune. Dadin abin ma dai tsakanina dashi sai alheri har muka rabu muna mutunta juna"
Dariyar kowa a take ta fito fili Zayyan ya matso ya sake kama hannuwan.Malamijo da yake shirin sandare masa saboda tsoro "nine dai Zayyan ban mutu ba"
"Minal hubsi wal haba isi....tuf, tuf" ya mike tsaye jiki na tsuma amma a dole dauriya zaiyi yana tofe tofe "kakana malami ne har ya mutu kuma sunansa naci har wata fatal..."
Ummi gani tayi abin ya soma yawa baban nata yasa yara suna dariya ta tashi ta riko hannunsa suka zauna kusa da Zayyan.
"Malamijo Allah Yayi da ransa ashe rufe shi akayi a kurkuku a can kasar da suka je yaki."
"Ki bari dan Manzo"
"Taba shi kaji wallahi shine"
Ali gadanga Malamijo ikon Allah sai kuka yana shasshafa jikin Zayyan.
"Allah Qadiran Ala Mayyasha'u. Zayyanu kana nan dama?"
Zaman jajantawa akayi ya kira Na'e da bata sanshi ba a wurinta yake jin Yadikko ta fita. Sun dan taba hira aka tafi yin sallah Mairama ta fada masa Kano zasu wuce a bar masa yaran. Bai fada mata komai game da Hajiyayye ba sai iya wanda idonta ya gani. Dan sauran mutumcinsa yaji yana son karewa a idanunta. Idan sun tafi zai fadawa su Radhiya ko da ja a kasa su fitar masa da ita da yaranta. Kuma a nemo masa shanunsa kafin jininsa ya karasa hawa.
**********
Kyakyawar matashiya ce irin wadda ake kira black beauty durkushe a gaban Salame tana sauraron fadan da take yi mata tana share kwalla da kasan hijabinta.
Salame ta zama tamkar wata almajira a yankwane duk ta tsufa fiye da shekarunta hakora sun soma yin wani layin kore kore daga sama ta kankance idanu tana surfa mata masifa har wani yawu ne yake kumfa kumfa daga gefen bakin.
"Banza jinin matsiyata. Dangin ubanki kaf basu da farcen susa sai kwala kwalan idanu kamar mujiya. Yanzu Rahima banda baki daukeni a bakin komai ba in aika miki cewa bani da lafiya amma kizo min gida hannu na dukan cinya"
Muryarta har ta dashe saboda kuka a tsakar dakin da ko arzikin leda babu ga kannenta 'ya'yan Alh Indararo sai murguda mata baki suke yi da masu gwalo tace "Umma wall..."