Buzu book 1 complete - Chapter 44
Buzu book 1 complete Chapter 44: Buzu book 1 complete Chapter 44. Sai da Ummi ta aiko musu da maganin sauro, saboda akwai sauro sosai da sosai a gidan, ga…
4,378 words
Sai da Ummi ta aiko musu da maganin sauro, saboda akwai sauro sosai da sosai a gidan, ga zafi, shi kuma ga yanayin ciwonsa ba ya son zafi yana buƙatar wadatacciyar iska. Haka Nana ta yi ta aikin fifita. Da safe Ummi ta sake aiko musu da Abin karyawa. Sai dai daga shi har ita, ba wani ci suka yi ba. Nana ta shirya ta ce "Sayyid, bari na je na yi musu sallama, mu gaisa da mutanen gidan"
"To"
"Yauwwa, kai ma zaka gaisa da mazajen su dan Allah, haka ake yi idan an je gurin, da ba a san mutum ba" kallon ta ya yi, ya maze kamar bai ji me ta ce ba, amma ta san ya ji ta sarai.
Ta fita tsakar gidan, ta yi sa'a matan na tsagar gida, su na aikace-aikace. Nana ta ce "Sannu ina kwanan ku"
Suka amsa mata cikin sakin fuska.
Nana ta ce "Sunana Nana, ni ce muka tare a wannan ɗakin"
"Allah sarki, sannu, ni sunana Barira, ga kuma Sajida, mai wancan ɗakin"
Nana ta ce "Allah sarki, to ma sha Allah, Allah ya iya mana" sun so jan Nana da hira, amma ta tashi tsam ta koma ɗaki, gurin mijinta.
****
"Alhajin Allah, aka ce ka tafi umara?"
Alhaji Zailani ya ce "Ɗagawa na yi Alhaji Magaji, Madam ta tafi, saboda tafiyar ta yi karo da wani taro da za mu yi na shekara, shi yasa na ɗaga. Ashe kai ma na garin Abujan?"
"Wallahi kuwa, na ma kwana biyu, ina neman wata kwangila ne. Ya jikin amininka kuwa, Fatuhu?"
Alhaji Zailani ya yi wani irin makirin murmushi ya ce "Yana can ya kwanta dama"
"Subhanallah, rasuwa ya yi?"
"A'a na fa, yana nan a raye, amma rai ne kawai a jikinsa"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wallahi na yi mamakin yadda rayuwa ta yi wa mutumin nan tsutsun jaki lokaci guda, ga asarar dukiya, komai nasa an ƙwace an biya masa bashi. Kai Allah dai ya kyauta. Da tuni yanzu ya ja tawagar tafiyar umarar maulidin nan, da shi da 'yan uwa da abokan arziki"
Alhaji Zailani ya ce "Sosai kam, faɗuwar wani ai tashin wani, yanzu waɗanda ya tare wa ƙofar arziki tun da ya gusa su ma za su ɗago" suka tafa su na wata irin ƙyaƙyacewa da dariya.
*****
Jamila bakinta ya ƙi rufuwa, kasancewar a wannan karon a jirgi za su tafi babban birnin tarayya tare da Hajiya Sa'a. Hajiya Sa'a ta ce "Ai sai ranar da za mu je Dubai, ko Qatar ma, wannan ai ba wani abu bane ba sam. Sai kin gaji da hawa jirgi, muddin za ki ci gaba da bayar da haɗin kai"
Jamila ta ce "Kai, wa ya ganni a Qatar"
"Amm Jamila ina Nana kuwa?"
"Tana gidanta, kwanaki ma na ji an ce ta yi ɓari"
Hajiya Sa'a ta jinjina kai kawai. Daga airport aka zo da mota, aka ɗauke su aka tafi da su. Wani irin katafaren gida ne, da ko a irin finafinan Hausa da Jamila take gani, ba a taɓa hasko mai girma da kyansa ba.
"Hajiya amma nan Hotel ne ko?"
"A'a gida ne, a nan za mu yi taron shekara"
"Ikon Allah, ai ganin gidan na yi ƙato guri-guri. To gidan waye?"
"Gidan wani ne" Hajiya Sa'a ta bata amsa tana dariyar, ganin yadda gidan ya ƙayatar da Jamila.
**** Kwanakin su Nana uku a gidan da suka koma, amma ita kanta, ba ta jin daɗin zaman gidan, duk da a gehtto area ta tashi ita ma, amma zaman gidan nan sam babu daɗi. Inda suka baro, sai ka wuni ba ka ji ƙwaƙwƙwaran sauti ba, sai na giftawar motoci. Amma gidan nan, musamman idan yamma ta yi, mata ne suke cika shi dam. A yi ta hayaniya, ana gulmace-gulmace, ga zantuttukan batsa da suke bajekolinsu a cikin gidan. A kafa dashi, a ci bashi, a yi gulmar wannan a yi ta mijin waccan. Hatta shimfiɗar aurensu ba su bar ta ba, bajekolin ta suke yi a wannan gidan.
Yanzu ma yana kwance ya lumshe idanunsa, su na ta hayaniya su na musu, a kan kuɗin cefane.
"Shugaba" ya ɗago idonsa ya kalle ta.
"Sannu ya jikin?" Ya sake lumshe idanunsa ya ce "Na warke"
Ta yi murmushi ta ce "Sayyid, na san ba ka jin daɗin zaman gidan nan, amma ka yi haƙuri in sha Allah, idan muka samu hali sai mu bar gidan nan"
Ya girgiza kai ya ce "Ba na buƙatar sauran jin daɗi, in dai ki na kusa da ni" ya yi maganar yana shafa fuskarta.
"Sayyid"
"Husnah" sai kuma ta yi shiru. "Faɗi mana"
"Ba komai fa"
"Shikenan zan shigo mafarkin ki, na ji"
Ta ɗan yi dariya ta ce "Allah ne ya san dalilin da ya sanya ya haɗa mu, gaba ɗaya rayuwarmu wata iri, daban da ta sauran mutane, mu dai gamu nan"
Ya yi murmushi ya ce "Shi yasa ba zan daina yi wa Allah godiya ba, da ya haɗa ni da ke. Rayuwa da ke wata afuwa ce a gare ni Rayuwata" ta ɗora hannunta a kan nasa tana murmushi. A hankali murmushin fuskarsa ya gushe, ya ce "Ba ni wayar nan, mu sake dubawa, ko wayar Habu za ta shiga"
Nana ta ɗaukko wayar daga gefen ta, ta miƙa masa, ya karɓa ya danna lambar Habu, amma ta ƙara maimaita masa, wayar a kashe take. Ya sauke hannunsa cike da damuwa da fargaba.
"Sayyid ka daina damuwa, in sha Allah su na cikin ƙoshin lafiya"
"Asmy, rayuwa ba za ta tafi a haka ba. Akwai ɗawainiya da yawa. Ki yi haƙuri na san juriya da rashin son damuwata ya sanya, ki ke danne wa. Da nuna mini ba komai, amma na san ɗawainiyar nan ta yi miki yawa. Wallahi zuciyata na yi mini zafi, idan na ga ki na wahala"
"Ni ba wahala nake yi ba" ta yi maganar tana tsuke baki.
"Shikenan, na daina maganar"
Jin wayar na vibrating, ya sanya suka kai hankalinsu kan wayar a tare. Amma sunan Adda Saude ne yake yawo, a kan screen ɗin wayar. Nana ta ɗaga tare da yin sallama. Adda Saude ta amsa Nana ta ce "Adda ina wuni?"
"Lafiya ƙalau Nana, ya ki ke ya mijin naki?"
"Lafiya ƙalau, ina Adda Fati?"
"Tana gidanta, ga Maijidda take son yin magana da ke" wata irin zabura Nana ta yi cikin murna ta ƙara nutsuwa.
"Assalamu alaikum"
"Mama"
"Na'am Nana ya ki ke?"
"Lafiya ƙalau, ya gida ya su Walida?"
"Su na nan lafiya ƙalau Alhamdillah, ya mai gidan na ki?"
"Lafiya kalau Mama"
Sayyid ya ƙura wa Nana ido, yana ayyana abin da take ji a zuciyarta. Saboda fara'ar da ta mamaye fuskarta.
"Ki na ji Nana, ina nan ina ƙoƙari, duk yadda zan yi zan zo Kano, na ganku in sha Allah, ki ƙara haƙuri, na san kin yi ki ƙara, ina nan tafe in sha Allah"
"Kar ki damu Mama, ni jin muryar nan ta ki ma da na yi, na ji daɗi sosai. Kuma in sha Allah kafin ki zo, za mu riga ki zuwa da yardar Allah"
"A'a ni ɗin dai zan zo na gan ku in sha Allah, ina fatan dai babu wata matsala?"
"Babu matsalar komai Mama"
"Yauwwa Nana, zan ci gaba da jaddada miki, ki riƙe Allah ki riƙe addu'a. Ki bi mijinki ku zauna lafiya. Ina fatan kin fafa sana'a Nana?"
"A'a Mama, amma zan fara in sha Allah"
"A'a Nana, kullum ki ce mini za ki fara, amma ba ki fara ba. Ina da buhun barkono, zan sayar na turo miki kuɗin, ki fara sayar da wani abin. Idan kuma barkonon ki ke so, na aiko miki Nana. Ni dai ban taɓa ganin mijin nan naki ba, amma yadda su Fati suka bani labari, da yadda nake jin muryarki, a duk lokacin da na kira waya, ina samun nutsuwa. Allah ya ƙara muku zaman lafiya. Amma ki yi sana'a, tun da mai ƙaramin ƙarfi ne, ki taimaka masa, kar ki sakar masa nauyi gaba ɗaya"
"To in sha Allah Mama, amma dan Allah ki bar barkonon ki, zan yi sana'ar nan da yardar Allah, na rasa abin da zan fara sayarwa ne. Amma zan fara"
"A'a zan sako miki buhu ɗaya a mota, ki gwada, kar ki zauna haka ba kya juya taro da sisi"
"To Mama in sha Allah, na gode sosai da sosai "
"Yauwwa, haryanzu ba ki da lambar Imrana ki turo mini"
Nana ta ce "Ba ni da ita Mama"
"To shikenan, ki gaida mijin naki" suka yi sallama, ta sauke wayar a hankali, ta yi shiru tana zancen zuci. Ta san da Mamanta su na tare da Baba, da ko ba za ta ɗauke mata ɗawainiyar da take ciki ba, za ta tausaya mata ta taya ta jajanta lamarin. Amma tun da ta je gida ta sanar da Baba halin da take ciki, ko ta waya bai kira ya tambayi ya suka ƙare ba, ya kuma mai jikin ba. Dama Mama ba a magana, mutanen da tun da ta yi aure, ba su taɓa taka gidan da take ba, yaushe za ta sanya ran su damu da halin da take ciki. Tana iya ƙoƙarinta, gurin rintse idanunta, daga aibun iyayenta, saboda kar zuciya ta ɗebe ta, ta afka cikin fushin Ubangiji, amma daga yadda Baba ya yi mata gurin aurenta, zuwa yanzu zuciyarta na ƙoƙarin bijirewa.
"Ya ne?" Ta ji muryarsa. Firgigit, ta kalle shi ta ce "Babu komai. Mama na gaishe ka"
"Ina amsawa, ina son na yi magan da ita, amma ina tsoron na karɓi wayar, maganar ta ɗauke"
Nana ta ce "Haka ne, bari na fita da gas ɗina waje, na dafa mana taliya, ga kayan miya na aika yaran Ummi, sun sayo mini, ai za ka ci ko?"
"Ke ma za ki ci ko?"
Ta yi dariya ta ce "In sha Allah" Ta ɗauki kayan girkinta, ta fita kusa da ɗakinta, ta ɗora.
Gaisawa kawai suka yi da matan gidan, ta nutsu a kan aikinta. Tana zaune mata na ta shiga suna fita, kowacce da abun da yake kawo ta. Da tana da isasshen guri, a ɗakinta, da babu abin da zai fito da ita waje yin girki, balle ta din ga kallon tumasancin da matan suke yi. Har da wadda daga ita sai hijjabi, da zani, babu riga babu brezia. Idan masu gidan suka dawo, haka suke tsallake mata su shiga ɗakunan su. Tun da Nana ta kammala girki, ta tattara komai nata ta shige ɗaki.
Ta ji daɗin ganin yadda yau yake iya cin abinci, dan haka ita ma ta zage, duk da ba wani daɗi yake yi mata ba.
Saboda rashin kamun kai na matan layin nan, sukan kai har goma da rabi, su na shiga su na fita a gidan tamkar bariki.
Nana har ta fara murnar abincin da ta ci ya zauna, lokaci ɗaya ya taso sai da ta amayar da shi baki ɗaya.
Tana fitowa daga banɗakin, ya ƙura mata ido, har ta ƙaraso ta kwanta a jikinsa, tana ɓata fuska.
Ya ƙanƙame ta yana faɗin sannu.
"Ɗan ka ya hana ni cin abinci, kuma yunwa nake ji" ta yi maganar hawaye na cika mata ido.
"Yi haƙuri, sannu, to mu je Asibiti"ya yi maganar a jere.
"A'a Sayyid, dole mu din ga tattala kuɗi yanzu. Yunwa nake ji sosai" ta yi maganar cikin shagwaɓa.
"Me zan sayo miki?"
"Ba komai" ji ta yi numfashinsa yana fita da sauri da sauri, a tsorace ta kalle shi ta ce "Sayyid jikin ne?"
"A'a" ya furta a hankali.
"Dan Allah ka yi haƙuri, da wasa nake yi maka, ai na san mata masu ciki, su na fuskantar irin haka, dan Allah ka kwantar da hankalinka. Ba na so mu zauna shiru, shi yasa na tsokane ka"
"Tom" ya amsa a hankali.
Kasancewar jikinta babu ƙwari, ya sanya ta kwanta da wuri, ganin shi ma ya samu bacci. A cikin bacci ta din ga jin wani irin rugugi, tamkar na hadari, ga shi ba lokacin damina ba ne. Ta buɗe idonta, ta ji wani irin huci, na fitowa daga gurin da yake kwance, ga wani irin nishi da kakari da yake yi, tamkar an yanka rago.
Ayshercool 08081012143 51 Fitila ta laluba, ta ɗaukko ta haska shi, wata irin jijjiga yake yi, tamkar zai zauce, yana wata irin miƙa, yana nishi.
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Sayyid me ya faru? Me ya same ka?" Ta kai hannunta jikinsa, wani irin zafi ta ji yana fitowa daga jikinsa. Cikin zafin nama, ta cire rigar jikinta ta fara ƙoƙarin rungume shi. Amma ya hankaɗe ta, yana ci gaba da kakari. Ta sanya ƙarfi, da ƙyar ta shiga jikinsa ta ƙanƙame shi .
"Zafi, ƙonewa nake yi, wuta Nana jikina ana ƙona ni" ya yi maganar haƙoransa na karo da juna, muryarsa na sarƙewa.
"Sannu Sayyid, ka yi haƙuri ka daure, na san ka na shan wahala, kar mutanen gidan nan, su fuskanci halin da muke ciki ka yi haƙuri" Ta yi maganar cikin dauriya da dakiya, saboda yadda ita kanta zafin jikin nasa, ya sanya take jin, tamkar ta yi ihun, saboda tamkar ta rungume ƙarfen da aka ciro daga cikin wuta haka take ji.
"Ahhh zafi!" Ya sake furtawa cikin mawuyacin hali.
Ta kwantar da kansa a kafaɗarta, tana karanta masa abin da ya sauwwaƙa a kunnensa. "Ki cika ni, kar cikin nan ya kuma zubewa"
"Babu abin da zai same shi"
Ta saka bakin ta a kunnensa na dama, ta fara kiran salla. Ya yi wata irin miƙa, jikinsa ya sandare a haka. Ta koma kunnensa na hagu, ta fara iƙama, sai dai ta kakare, bayan shaƙar da ya yi wa wuyanta.
Ya miƙe ya danne ta a kan katifar, ta kasa addu'a, ta fara kiciniyar ƙwacewa, cike da tsoron kar ta yi wani abu, da zai sanya mutanen gidan su ji, su zo su tarar da su a wannan yanayin. Gaba ɗaya ya rikiɗe mata, zuwa wannan tsohon cikin mummunar siffa, har dogon farin gemun sa, yana taɓa fuskarta, ga numfashinta tana jin zai bar gangar jikinta.
A kan wani tsauni ta ganta, ta yinƙura da ƙyar, ta ja jikinta saboda azabar sanyin da take ji. Wuyanta sai raɗaɗi da zafin shaƙar da ya yi mata, ne yake damunta. Babu tsammani ta ga tsohon nan, a tsaye yana kallon ta.
"A'uzubikalimatillahi tammat" ta furta tana ja da baya. Ya ɗan ja da baya, yana ci gaba da kallon ta.
"Me na yi maka ne? Laifin me na yi maka da na cancanci haka?"
"Ba ki yi mini laifin komai ba, hasali ma waɗanda suka yi mini laifin, ba sa Duniya amma ba zan taɓa hucewa ba, sai na hukunta su ta hanyar tarwatsa zuriyar su, da gadar da azaba da wahala ga duk wanda ya fito daga cikin zuriyar su. Na zaɓi na azabtar da ke fiye da kowa, saboda hakan ne zai sanya na ƙuntatawa Ƙaisar, da ya fifita bil'adam a kaina. Zan ci gaba da addabawa rayuwar ki, sai na sabauta ku a ƙarshe na sanya mijinki ya yi ajalinki. Ban taɓa alfahari da yi wa biladama wani aiki ba, kamar aikin da na yi a kan Buzun nan saboda a dalilinsa ya sake sada ni da abokan gaba na, kuma ba zan gushe ba sai na ɗauki mummunar fansar da sai na bar muku mummunan tabo a zuriyar ku"
"To idan mu zuriyarmu sun yi maka laifi, shi kuma mijina me ya yi maka?"
Ya tako ya ƙaraso gaban Nana ya durƙusa, ta din ga ƙoƙarin yin addu'a, amma ta kasa. Ya buɗe bakinsa, tana iya hango cikin bakinsa, yadda wani irin baƙin hayaƙi, ke ƙoƙarin fitowa daga bakin nasa, sai dai kan ya yi wani abu, ta ga ya ɓace.
Ta motsa a hankali ta kalli Sayyid a can gefe, ya takure yana bacci. Ta matsa ku sa da shi, ta ji jikinsa ya saki babu zazzaɓin. Sai dai wani irin bacci yake yi,rabin idonsa a buɗe, ƙwayar idanunsa baƙar ta ɗauke sai farar. Ga alamar yana numfashi. Ta ɗauki bargo ta lulluɓe shi. Ta kunna karatun Alkur'ani a waya ta ajiye a gefe.
Ta ja ta zauna ta yi shiru, abin duniya ya ishe ta, sai kuma ta koma tunani kamar yanzu ta yi rauni a ibada, shaiɗan ya yi galaba a kanta, kan cewar idan ta yi addu'a wahala ta fi tsananta a gare ta. Domin hatta addu'a kwanciya bacci, ranar da ba ta yi ba, sai ta kwanta ta tashi lafiya ƙalau, ba mafarkai babu ciwon ƙafa ko baya, ko ma jikin baki ɗaya. Azkar ma ba ko yaushe take iya yi safe da yamma ba.
Ta yinƙura ta tashi, ta je ta ɗauro alwala, ta zo ta sake haska shi, ta ga bacci yake yi, ta nemi guri ta kwanta, ta ɗora hannunta a goshinsa, tana karanto addu'oin kwanciya bacci.
*****
Jamila na miƙe a kan katafaren gadon, ga chips a gaban ta, ga kakkauran shayi, hannunta riƙe da zuƙeƙiyar wayarta.
Abba ne ɗan gidan Hajiya Sa'a, yake yi mata magana ta what's app. "Ƙanwata, shi ne tun da ku ka sauka, ba ki neme ni ba ko?"
"Ba haka ba ne, ba ni da data ne"
"Kuma ba ki gaya mini ba, bari na saka miki. Ina Mummy?"
"Ta fita"
"Wai ina ku ka je ne a Abujan?"
Jamila ta yi masa reply da "Ban san sunan gurin ba, wani gida ne dai mai kyau sosai"
"Ok, to dan Allah ki kula da kan ki sosai da sosai, Allah ya bayar da nasarar abin da aka je nema, na ji ta ce taron kasuwanci ne ko?"
"Wallahi dai ban sani ba tukuna"
"Haka ta ce mini ni, ta tafi da ke ku ka bar ni a gida, ai shikenan" har za ta rufe data ta ga 10gb na data. Sai ta washe baki ta ce "Har 10gb na gode sosai da sosai"
Abba ya ce "Babu godiya tsakanin, Yaya da ƙanwarsa, ki kwanta da wuri ki yi bacci. Ki yi addu'a kuma, sai da safe"
"To yayana na gode sosai da sosai" suka yi sallama, ta rufe laste seen ɗin ta da online, ta tafi kallon videos a tiktok.
Hajiya Amina ce ta shigo ɗakin, ta ce "Jamila ba ki yi bacci ba?"
"Eh Mummy, kin dawo?"
"Eh zan sake zuwa wani gurin ne, babu lallai na dawo da wuri, za mu yi meeting, ki yi kwanciyar ki"
"To shikenan, sai kin dawo"
"Yauwwa amma ba kya buƙatar wani abu, ko jin yunwa ko?"
Ta ce "A'a a ƙoshe nake"
"To sai na dawo" Hajiya Sa'a ta fice, ta rufe wa Jamila ƙofar.
****
Nasiru tun ranar da ya je gidan Ummi, su Nana suka tashi, ya koma gida ya ba wa Baba labari. Baba ya ce "To shikenan ma, ta kwana gidan sauƙi, tun da sun samu mafita. Ni na san babu yadda za'a yi ma a kore su haka kurum, dan mijinta ba shi da lafiya akwai dai abin da suka aikata.
"Dama wasu Buzaye abin yarda ne, kalli kayan da suka kawo mata fa, Allah ka dai ya san mugun abin da suke aikatawa, har aka kama su. Kai Nasiru to ya gidan da suka koma yake?" Cewar Mama cike da son jin ƙwaƙwaf.
Nasiru na tauna rake ya ce "Normal dai gida ne, amma da wasu a gidan, wancan gidan da suka baro ya fi. Ɗakinsu ya fi kyau da girma, banɗakin har da famfo ga wuta, wannan kuwa gaskiya bai yi kyau ba"
Ta sake cewa "Kuma da gaske mijin nata ba shi da lafiya?"
Ya ɗaga kai ya ce "Kai, sosai yana daurewa ne kawai, idan ya yi magana haki yake yi fa, wannan karon na ga ya yi magana sosai. Da an yi abu sai ya ce mata Rayuwata, ki yi a hankali ki zauna ki huta"
Sai ta sake zabura ta ce "Au rayuwata yake ce mata"
"Kai Mama dan Allah ki rabu da ni, haba wannan tambayoyin kamar a kabari"
"Kai a gidan uban wa ka san kabarin, sai ka yi saɓo tukuna" ya yi mata shiru, ya tashi ya ɗauki rakensa da yake sayarwa a ƙofar gida, da wuƙa ya fice.
***** Tun da garin Allah ya waye, Nana take tashin sa, amma ya ƙi tashi, irin wannan baccin da ta farka ta ga yana yi dai shi yake yi. Gaba ɗaya ta tsorata, ga dai numfashi yana yi, idan ta taɓa zuciyarsa tana bugawa da ƙarfi jefi-jefi. Ta saka shi a gaba, ta ma rasa abin da ya kamata ta yi. Ummi takira ta a waya, ta tambaye ta babu matsala babu wani abu da take buƙata, ta ce mata eh. Har sha biyu na rana Nana ta rasa abin yi, ta kunna karatun Alƙur'ani a wayarta, ta ajiye masa sai dai bai fi mintuna talatin ba wayar ta ɗauke. Ji ta yi ana bubbuga ƙofar ɗakin nasu. Ta yinƙura ta tashi ta saka hijjabi, ta je ta buɗe.
Sajida ta gani a tsaye, ta ɗan saki fuskarta su ka gaisa. Sajida ta ce "Mun ji shiru ne, ko ƙofa ba ku buɗe ba, shi ne na ce bari na ƙwanƙwasa ko lafiya?"
Nana ta ce "Lafiya ƙalau Alhamdillah, ba ma jin daɗi ne daga ni har shi, shi yasa ba mu fito ba, amma lafiya ƙalau muke"
"Ok Allah sarki, ko dai amarya ce ne, haryanzu ba a gama cin amarci ba?" Ta yi maganar tana kallon Nana.
Nana kawai ta yi murmushi, ta koma ɗakin, ta buɗe ƙofar ta saki labule. Dama ta gyara komai a ɗakin. Ta dafa shayi da habbatussauda, da citt, kanumfari, kimba, na'ana'a kamar yadda yake dafawa, ta zuba a flask ta rasa me za ta dafa, dan ba ta son cin komai.
Tana nan zaune, sai ga 'yar gidan Ummi ta zo, Islam. Ta kawo wa Nana faten doya da wake, ya sha alayyahu. Ƙamshin attaruhun da ya daki hancin Nana, sai da ta haɗiye yawu. Ta ba wa yarinyar wayarta, ta miƙa mata caji.
Ta ɗan zuba abincin tana ci, ta zuba masa ido, tana tunanin ko Asibiti za ta nemo mota su tafi, amma kuma sai ta tuna abin da ya yi jiya ba shi da alaƙa da ciwon Asibiti. Tana ta tunanin mene ne mafita, kuma ba ta son waɗannan maganannun matan, suk san halin da suke ciki ita da mijinta. Tana nan zaune tana bin sa da kallo, ta jiyo hirar Sajida da Barira, da wasu maƙwabta. Barira ta ce "Sajida, jiya da daddare, kin ji kamar ana nishi cikin dare?"
Sajida ta ce "Wani irin nishi kuma? Ni ban ji ba"
"Wallahi nishi, kamar ana kokowa kamar wani gurnani, ga Amiru ya yi bacci, na din ga jin tsoro na kasa bacci, na ce ko gamo na yi da aljanu"
"Ba wasu aljanu, ba wani aljani da yake razana mutum, da wani sauti ko wani abu, duk ƙaryar banza ce"
"Kai ni dai na tsorata, kuma daga nan haka na din ga jiyo sautin, wajen nan" ta yi maganar tana nuna ɗakin Nana.
Sajida ta yi magana ƙasa-ƙasa, Nana ba ta ji me su ka ce, sai ji ta yi sun tuntsure da dariya. Ta yi ajiyar zuciya, ta fara tunanin ko dai wani gidan za su kama, ta san idan suka ci gaba da zama a gidan nan, asirin su na iya tonuwa, wanda ba za ta so hakan ba.
Babu tsammani ta ga ya tashi zaune, ta tashi da sauri ta nufe shi cikin kulawa ta ce "Sannu Sayyid, ka tashi?" Shiru ya yi yana bin ta da kallo, tamkar ya ga wata baƙuwar halitta daban.
"Sannu ya jikin naka?" Yanzun ma bai yi magana ba, ya ci gaba da bin ta da ido. Ta yi ta magana ya yi shiru, tamkar kurma. Can kuma ya tashi ya shiga banɗaki ya fito ya nemi guri ya zauna.
"Sayyid, za ka yi sallolin da ba ka yi ba, Asuba da kuma Azahar, duk ba ka yi ba" ya yi mata shiru, ya kawar da kansa gefe. Ta tsiyayo ruwan shayi a kofi, ta zo gabansa da cokali ta zauna ta ce "To ɗan sha tea ɗin, sai ka ci abinci ka yi sallar" ya kawar da kansa ya yi mata shiru. Ta ƙara matsawa kusa da shi, kawai ya hamɓare kofin ruwan zafin ya kware mata, a wuyanta zuwa jikinta. Wata irin zabura ta yi, ta ja da baya tana tsuma, saboda yadda zafin ya ratsa fatarta. Ko kallon inda take bai yi ba, ya ja gefe ya ci gaba da huci.
Ranta ya yi mummunan ɓaci, amma ta kalli fuskarsa, ta tabattar da yana hayyacinsa, babu yadda za a yi ya yi mata haka, dan haka ta yi shiru ba ta ce komai ba, ta tashi ta cire kayan, ta saka wasu.
Haka suka wuni a ɗakin, bai yi salla ba, bai ci abinci ba, kuma bai yi magana ba. Ana yin sallar magariba, ya haura kan katifa ya kwanta. A jikin mudubi ta tsaya, tana haska ƙirjinta, yadda inda ruwan zafin ya zuba a ƙirjinta, ya ɗuri ruwa. Ta hasaka kan katifar, ta ga ya ci gaba da wannan baccin, mai rabin idonsa a buɗe, ta nemi guri a ƙasa lungun wardrobe ta kwanta. Sai dai yau ta kwanta cike da fargaba da kuma zullumin abin da zai faru, kar ta je ya sake shaƙe ta. Sam ta kasa bacci, da ta fara sai ta razana ta buɗe idonta, dama a kunne ta bar fitila ba ta kashe ta ba.
**** Shukura ce tare da Sagir a zaune a cikin mota, ta zuba wa ƙofar gate ɗin Asibitin ido. Ya ce "Ya dai? Ki shiga ki fito ina nan ina jiran ki"
"Wallahi haka kurum gabana yake faɗuwa, ko hanyar Asibitin nan ba na son na ni an faɗi sunan ta"
"Shukura duk saboda da ɗan ki ya rasu, ban taɓa ganin mutum mara tawakkalli kamar ke ba"
"Ba haka ba ne, wallahi yanzu ma ban da Mummy ta matsa, ba zan zo ba, bari na je na dawo"
Sagir ya ce "Tom ki yi masa sannu, ni na zo na duba shi dama" ta jinjina kai ta fice daga motar.
Tana shiga cikin Asibitin, ta din ga jin kamar a lokacin ne, za a yi mata aiki a cire ɗan cikinta, wata irin fargaba da yanayi mara daɗi ta din ga ji a jikinta.