Buzu complete by ayshacool 1 - Chapter 10
Buzu complete by ayshacool 1 Chapter 10: Buzu complete by ayshacool 1 Chapter 10. Ya zo ya wuce ya buɗe wardrobe, ya ɗebo kayansa masu datti, da ya nannaɗe…
3,363 words
Ya zo ya wuce ya buɗe wardrobe, ya ɗebo kayansa masu datti, da ya nannaɗe ya bawa Habu.
Habu ya karɓa, ya yi musu sallama, ya tafi.
Nana ta din ga kallonsa, bakinta fal magana, amma ya ƙi kallonta.
"Shi ne ka ce ina yi maka rashin kunya ko? To me na yi maka na rashin kunya? Dama ashe ka na magana ni ce ba ka kulawa ko?" Ya lumshe idanunsa yana kaɗa ƙafar sa.
"Idan ba ka yi mini magana, ba zan san na yi maka laifi ba, ko na san abin da ka ke so ba, da wanda ba ka so" ta gama surutunta, ganin ba shi da niyyar tanka mata ya sanya ta kama wani abin.
Kayan miyar da Habu ya kawo, ta zauna ta gyara tsaf, ta yi greating ɗin su. Ta ɗora a kan gas. Tana jin yadda yake tari, saboda zafin attaruhu. Ta dafa taliya da miya.
Ya din ga bin ta da ido, har ta gama.
Ta zuba masa ta ajiye masa komai, ta tashi ta je ta yi alwala, ta dawo ta tayar da sallar azahar.
Ta idar ta yi azkar, ta ninke dadduma, ta gan shi ya haɗa gumi, yana cakalar abincin, fuskarsa ta yi jawur, sai gumi ne yake tsatstsafo masa.
"Lafiya ya na ga ka na gumi, abincin babu daɗi ne?" Ya ja numfashi ya kalle ta, hannunsa riƙe da cokali mai yatsu. Babu irin tambayar da ba ta yi masa ba, amma bai ba ta amsa ba, har ta gaji ta rabu da shi. A haka ya cinye abincin.
Nana ta rasa abin da ya sanya shi haɗa wannan uban gumin. Idonta ne ya sauka a kan wayarta. A take tunanin mahaifiyarta ya ƙara faɗo mata. Jiki a sanyaye ta ƙarasa ta ɗauki wayar tana kallon screen ɗin.
Jiki a sanyaye ta buɗe wayar, ta shiga gurin kira, ta shigar da lambobin kamar yadda ta haddace su, cike da fatan Allah ya sa wayar ta shiga.
Babu zato babu tsammani, ta ji wayar ta shiga. Gyara zamanta ta yi tana fatan Allah ya sa ta ji abin da take tsammanni. Sai dai akasin haka ta ji muryar namiji, muryar mutumin da ta tsana a rayuwarta.
Cikin dakiya ta ce "Baba ina wuni?"
"Lafiya kalau wace ce?"
Cikin sanyin murya ta ce "Dan Allah me wayar nake nema"
Ya ce "To wace ce ke ɗin?"
Ta yi ajiyar zuciya ta ce "Baba Nana ce, mamana nake nema" ta yi maganar cikin rawar murya, idanunta na cika da hawaye.
"Ai dama na sani, wallahi na sani, na san ba ta fasa bibiyar tsohon mijinta ba, wallahi zan gauraya da ita"
A ruɗe Nana ta ce "Dan Allah Baba ka tsaya ka ji, wallahi ba sa waya da Babanmu, lamba ta ce, dan Allah ka haɗa ni da ita ko muryarta na ji, dan Allah.. ƙit ya kashe wayar ba tare da ta gama faɗar abin da za ta faɗa ba.
Wata irin tafasa zuciyarta ta din ga yi, cike da ɓacin rai da tashin hankali. Wasu irin hawaye masu raɗaɗi suka fara biyo fuskar ta.
Ta ɗauki wayar ta yi jifa da ita, caraf ya cafke wayar.
Ya kalli yadda hawaye yake fita daga idanunta.
Kawai ya ga ta taso za ta fita daga ɗakin, jikinta yana rawa.
Har za ta gota shi, ya danƙo hannunta ya yo baya da ita, yana ƙarewa Ƙaisar kallo da ya bayyana a gefenta yana huci!.
Ayshercool 08081012143 Ayshacool Page 31
Bai kula Ƙaisar ba, ya ja Nana zuwa kan katifa, ya zaunar da ita, idanunta a lumshe, har a lokacin kuma fitar da hawaye suke yi, babu ƙaƙƙautawa. Ya taɓa tafukan hannayenta, ya ji sanyi ƙalau kamar an ciro ta daga ƙanƙara.
Ya ƙura mata ido yana nazarin ta, a take ya tuno ranar da ta shiga ɗakinsu, tana kiran Haidar, su na haɗa ido ta ja da baya ta ƙwala ihu ta faɗi. Haka jikinta ya ƙandare, ta din ga karkarwa, ya ga wani narkeken baƙin muzuru ya bayyana a ɗakin, yana ta zagaye ta.
Ya sauke numfashi, ya sanya yatsunsa biyu, ya danna bayan kunnenta. Ya miƙe ya bar kusa da ita. A hankali jikinta ya daina rawar, ta buɗe idonta, sai dai tun da ta buɗe idon, ba ta tashi daga gurin ba balle ta ci abinci. Ya din ga satar kallonta, amma ba ta tashi daga in da take ba, balle ta ci abinci. Yana son ya yi magana amma ya rasa me zai ce mata. Ta tashi zaune da ƙyar, ta haɗa kai da gwiwa, ta yi kuka mai isar ta. Sai da aka kira la'asar sannan ta tashi ta yi alwala, ta tayar da salla.
Bayan ta idar tana zaune ta yi shiru, ya dawo ɗakin, ya duba gurin da ta gama girkin, babu alamar ta ci abinci.
"Ba za a ci abinci ba?" Ta ji maganar sa babu tsammani.
Ta ɗaga kai ta kalle shi, kamar mai jiran ƙiris, kawai ta sake fashewa da kuka. Ya yi zuru da ido yana bin ta da kallo, bai ce ta yi shiru ba, har ta yi mai isar ta yi shiru.
Duk ya damu ganin ba ta ci abinci ba, ya rasa me zai ce mata, ga shi yanayinta ya fahimci rigimammiya ce.
Jin motsi a waje ana taɓa gate, ya sanya ya tashi ya rufe fuskar sa, ya fita ya duba waye. Tsayawa ya yi yana kallon su, mata ne su uku, da ƙanan yara sai wani ɗan matashin saurayi.
"Sannu malam, ko kai ne mijin Nanan?" Ya tsaya tsuru yana kallon su.
"Gurin Nana mu ka zo tana nan?" ya nuna musu ɗakin su.
Suka wuce, Ummi tana cewa "Na yi ƙoƙari fa da na iya kawo mu gidan nan"
Bayan Jamila ya bi da kallo, jikinsa na ba shi wani abu a game da ita.
Wata irin zabura Nana ta yi ta rungume Ummi, ba ta taɓa tsammanin ganin su ba. Ta rungume Jamila cikin farin ciki ta ce "Dama za ku zo ba ku gaya mini ba?"
Ummi ta ce "Mu ki bamu guri mu zauna"
Nasiru ya ce "Hajiya Anty Nana amarya" daƙuwa ta yi masa ta ce "Gidanku"
Ya yi dariya ya ce "Na yi missing ɗin ki sosai"
Take ta manta da damuwar da take ciki, ta ware suka hau hira. Ta juye musu sauran abincin da ba ta ci ba, ta ce za ta ɗora musu wani.
Ummi ta ce "Ke a ƙoshe muke, ga shi wannan miya ce na ɗan yi miki, tun bayan kawo ki da kwana biyu, na so yi miki, bana jin daɗi ne. Ga ɗan cin-cin da dubulan na yi miki. Ga kuma turarukan wuta da wata maƙwanciyar ku, ta bayar a kawo miki ga humra ma. Sai kuma kaya da na ɗan ƙara sayo miki"
Nana ta ce "Allah sarki, na gode sosai da sosai Anty Ummi, Allah ya saka da mafificin alkhairi. Jamcy ya garin ne?"
Jamila ta ce "Uhumm mamaki nake yi, kamar ba ke ce ki ka gama uban kuka ba, an aura miki buzu, amma kalli yadda ki ka ware yanzu"
Nana ta yi murmushi ta ce "To ba dole na ware ba, lafiyayyen ɗaki, ga wardrobe, ga katifata ga banɗakina nikaɗai ba takura ga wuta 2hrs ba yankewa"
Suwaiba ta ce "Katifa ko abin da ake yi a kan katifar?"
Nana ta ce "Duka ɗan sunna ai ba zai ƙi sunna ba Jamila, tun da dan haka ake auren"
Ummi ta ce "Dan uban ku da yara a gurin ku ke yi mana batsa"
Nana ta yi murmushi ta ce "Ya Baba, ina mama su ba za su zo ba?"
Ummi ta ce "Za su zo ne, Baba babu lafiya ƙafarsa ce take ciwo"
Nana ta ce "Ciwon ƙafa kuma?"
"Wallahi kuwa, ba za ki kira mijin naki mu gaisa ba"
Nana ta ɗan kwaɓe baki ta ce "Ba kula ku zai yi ba, Nasiru ya makaranta" ta karkatar da zancen ga Nasiru. "Makaranta lafiya ƙalau Alhamdilillah"
A ƙofar ɗakin ya yi gyaran murya ya tsaya, Nana ta yinƙura ta tashi, ta ɗaga labulen. Babu hijjabi a jikinta, sai doguwar rigar atamfa.
Ya miƙo mata leda, ta saka hannu biyu ta karɓa, bai ce mata komai ba, ya juya ya koma bakin gate.
Fura da Nono ne kaya guda, abin sai da ya bawa Nana mamaki, ba ta san a ina ya samo su ba. Ta ajiye musu suka dama, suka sha. Ayshacool Jamila ta miƙa wa Nana ɗan ƙaramin flask ta ce "Nana ga mutuniyar ki na yi miki wainar fulawa" Nana ta haɗiyi yawu cikin murna ta din ga yi wa Jamila godiya. Ta ce "Wannan sai dare zan dafa shayi na ci da ita"
Suwaiba ta ce "Ashe fa buzu ki ke aure, ba za a gaya miki shayi ba yanzu"
Nana ta ce "Kamar kin sani, ni yanzu shayi ai sai dai na koya wasu, kwana muke mu wuni shan shayi babu ƙaƙƙautawa" suka yi dariya. Har magariba su na gidan, sai da suka yi sallar magariba, Nana ta fito har bakin gate ta rako su, sai dai baya nan.
Ummi ta ce "Kin ga har zamu tafi, bamu haɗu mun gaisa ba"
Nana ta ce "Ina ga yana masallaci"
Suka yi sallama, suka tafi Nana ta koma ɗaki. Har cikin ranta ta ji daɗin zuwan su.
Ta yi wanke-wanke ta gyara ɗakin fes. Ta ɗaukko flask ɗin wainar fulawar, ta saka a gaba ta fara ci. Ba ta ci da yawa ba, Haula ta yi sallama.
Nana ta amsa cikin sakin fuska, duk da ta yi mamakin ganinta a daidai wannan lokacin.
"Anty Haula ba ki yi fushi ba? Haryanzu ban fara fita ba, shi yasa ban shigo miki ba"
Haula ta ce "Allah sarki, kar ki damu wallahi, ashe baƙi ki ka yi?"
Ba tare da Nana ta yi tunanin komai ba, ta ce "Eh, 'yan gidanmu ne su ka zo, bismillah matso mu ci abinci" Aikuwa Haula ta gyara zama ta zura hannu a kwano, ta fara cin abincin. Kafin Nana ta yi loma ɗaya ta yi huɗu da rabi, kafin wani lokaci Nana sai filin kwanon ta gani, Haula na ta suɗar baki saboda yajin wainar.
Sai da ran Nana ya sosu, dan kuwa ta so cin wainar nan ta ƙoshi.
Labulen ɗakin kawai ya ɗaga ya shigo, Haula ta tashi zumbur. Ta kalli Nana ta ce "Na gode sosai sai anjima" sai da Haula ta fice sannan ya shigo ɗakin.
Ya zauna a gurin da ya saba zama, Nana ta ɗaukko ta sa furar da ta ajiye masa, da cin-cin da dubulan a plate, ta nufe shi.
"Sannu da zuwa" ya jinjina mata kai.
" 'yan gidanmu ne fa suka zo" ta yi maganar fuskarta na bayyanar da annashuwa. Ya gyaɗa mata kai.
"Na gode sosai da sosai, da karamcin da ka yi mini, ga taka furar ga kuma wannan" ta yi magana tana tura masa plate ɗin dubulan.
Ya saka hannu biyu ya karɓi kofin furar, Nana ta zauna a gefensa, a tsanake yake sha, ya ɗauki cin-cin ya saka a bakinsa, maimakon ya tauna yadda yakamata, amma ya din ga tauna shi a hankali kamar mai tsoron tauna dutse.
"Da daɗi?" Ya jinjina mata kai alamar eh.
Nana ta ɗan yi ƙasa da murya ta ce "Dan Allah ka din ga yi mini magana mana. Haryanzu ban san sunanka ba" ya kalle ta yana ci gaba da tauna cin-cin ɗin sa.
"Ka gaya mini sunan ka" ya ajiye kofin hannunsa yana hamma, ya jingina da jikin bango yana lumshe idanunsa.
Ta gaji ta ƙyale shi, ta fara shirin kwanciya, ta shiga banɗaki domin kama ruwa ta yi alwalar kwanciya bacci.
A sukwane ya miƙe, duk da bacci ya fara ɗaukarsa, kwanon da Nana ta ci wainar nan ya ɗauka, ya jujjuya kwanon ya ga babu komai a ciki.
Ya ajiye kwanon, ya koma gurin da yake kwanciya, ya zauna ya yi shiru.
Nana kuwa tana saka ƙafarta a banɗakin, ta ganta a cikin wani gida, mai dogon gini, mai ɗauke da ƙofofi daban-daban. Ɗaya daga cikin kofofin ta bi, tana neman hanyar fita, amma da ta shiga sai ta ga ta koma ainihin gurin da take da farko.
Tana cikin laluben ƙofar, kawai ta ci karo da Baba, ƙafarsa ɗaya an nannaɗe ta da sarƙa, an ɗaure ta tamau. Da sauri Nana ta nufe shi, cikin tashin hankali ta ce "Baba lafiya kuwa? Me ya same ka haka?"
"Ni ma ban sani ba Nana, dan Allah ki kwance mini sarƙar nan, ina jin ƙafata kamar za ta cire, ba na iya bacci"
Cikin damuwa ta ce "Ka kwantar da hankalinka, bari na gani idan zan iya kwance maka" Ta durƙusa ta fara ƙoƙarin kwance masa sarƙar, sai dai ta rasa ina ne ainihin gurin da aka ƙulle ƙafar.
"Idan ki ka kuskura ki ka kwance masa, ba zai sake taka ƙafarsa ba har abada" Nana ta ɗago tana kallon Ƙaisar.
"Dan me za ka ce kar na kwance masa? Ba ka ga halin da yake ciki ba, ko iya taka ƙafar baya yi ba?"
Ƙaisar ya ce "Ban gaya miki sai na hukunta shi ba? Har yanzu ba ki yadda mu na cikin mummunan haɗari daga ni har ke ba, a dalilin wannan auren. Dan haka dole shi ma ya ɗanɗana kuɗarsa" Ayshacool Cikin ɗaga murya ta ce "Ƙaisar baban nawa? Ka kwance masa ƙafarsa" kawai tana waiwayewa ta daina ganin Baba.
"Idan duniya za ta taru, babu wanda ya isa ya kwance masa ƙafar nan, idan bai yi wasa ba sai ta yi ajalinsa" yayi maganar cikin ɗaga murya.
Tamkar mai shirin haukacewa ta ce "Ba zai yiwu ba, wallahi sai ka kwance shi, wai kai wane irin halitta ne da babu ɗigon imani, a zuciyar ka?"
Ƙaisar ya ce "Ko ma dai mene ne, abu ɗaya za ki yi ki kwance masa ƙafar nan, wanda kin san mene ne, ba sai na gaya miki ba. Mu ajiye wannan a gefe tukuna, ban san iya adadin lokacin da za a ɗauka kafin ki san ciwon kanki ba, ki daina wasa da rayuwar ki ba. A wannan karon ma an baki abu kin ci, za kuwa ki ɗanɗana kuɗar ki, a nan na nuna miki an tsaface ƙanwar ki, amma ta kawo abu ta baki ki ka ci"
Nana ta ce "Idan ma ka nuna mini, da na tashi nake manta komai, kuma ba zan taɓa yarda da maganganun ka ba, yaudarata kawai ka ke so ka yi, domin na amince da mugun nufin ka, kuma har abada ba zan amince ba, ko da ba ma jituwa da su, na san ba za su cutar da ni ba"
Ya ce "Shikenan, zamu gani"
A hankali ta yi kokarin yin juyi a kan katifar, amma ta ji wani irin azababben fitsari, tamkar mararta za ta yi bindiga, ga wata irin ƙullewa da mararta ta yi har cikin bayanta da ƙafafuwanta. Da ƙyar da dabara, ta tashi ta tafi banɗaki. A zaton ta da ta yi fitsarin shikenan, za ta ji marar ta saki, amma babu abin da ya canza.
Da bin bango ta fito ,ta dawo kan katifar ta kwanta. Bacci ne a kanta, amma wani irin azababben ciwon mara ya turnuƙe ta. Yana kwance yana jin nishinta sama-sama, tun farkawar ta da shigarta Banɗaki, duk a kan idanunsa. Murƙususu ta din ga yi a kan katifar, tana numfarfashi. Rabonta da ciwon mara mai irin wannan azabar, tun farko-farkon fara period ɗin ta. Da idan ta fara sai an kai ta chemist an yi mata allurai. Daga baya abin ya ragu sosai, amma na yau kam, ba ta taɓa makamancin irin sa ba, ji take tamkar ba za ta wayi gari ba.
Ko na minti ɗaya ciwon baya lafawa, ga shi ya haɗe mata da ciwon ciki, da na ƙirji kamar za ta bar duniya. A duƙe ta sake komawa banɗaki ta saka pad.
A haka ta wayi gari, cikin mawuyacin hali, ta yi kukan ta gaji. Ta saukko daga kan katifar ta kwanta a ƙasa amma babu afuwa. Ko sau ɗaya bai ce mata sannu ba, da gari ya yi haske ma bar mata ɗakin ya yi, saboda yadda kukanta ya cika masa kunne.
Tamkar za ta haihu, haka ta fita daga hayyacinta, gaba ɗaya ta manta da batun ba itakaɗai ce a ɗakin ba, ta cire kayan jikinta, ta bar vest da underwear. Rashin tanka matan da ya yi ba ƙaramin ƙona mata rai ya yi ba.
Can amai ya din ga taso mata, ga wata irin gudawa ta azaba da fitar ta kawai, yake ƙara gigita ta saboda sai cikin ya haɗu ya ƙule da marar sannan take yin ta. Ga fitarta tamkar tana zawon wuta haka take ji, ta ga duniyar tana juya mata, ta din ga salati tana ambaton Allah. Tun tana iya zuwa banɗakin a duƙe, ta koma rarrafe.
Ta din ga wani irin amai, mai wari da ƙarni. Idanunta suka yi zuru-zuru, kamar ta yi wata da watanni tana rashin lafiya.
Ta kwanta ta yi rub da ciki, ta lumshe idonta. Ta ji an ɗagota. Sosai ya ɗago ta ya haɗa ta da ƙirjinsa. Babu rawani a kansa, ya kwance gashin kansa, ya sauka a kan kafaɗarsa. Suna haɗa ido, ta sake fashewa da kuka, saboda ta ji zafin rashin kula ta da ya yi balle ya yi mata sannu.
Ya kai dogwayen yatsunsa ya share hawayen da yake fitowa daga idonta. Ta saka hannu ta ture hannunsa, da yake share mata hawayen.
Ya kama bayan hannunta ya kai bakinsa ya sumbuta, ya ɗago ya ƙura mata ido, yana matsa hannunta a hankali. Zuba masa ido Nana ta yi, sai ta ga kamar ba shi ba. Ya sake kai bakinsa goshinta ya sumbaci goshin nata. Ta sake fashewa da kuka, ya haɗa goshinsa da nata ya ce "Shhhhh" Gabanta ya faɗi, sai da ta razana jin ya ɗora hannunsa a kan marar ta.
A hankali ta fara jin releif, daga wannan matsanancin ciwon da take ji. Bai ɗauke goshinsa daga nata ba, numfashin sa da yake shiga nata, jikinta ne ya saki ya mutu murus, ta kasa ko ƙwaƙwƙwaran motsi. A hankali ta fara jin bacci yana ɗaukar ta. Ayshacool Su Jamila kuwa bayan sun dawo daga gidan Nana, Baba ya tambaye su ya suka baro ta.
Suwaiba ta ce "Tana nan lafiya kalau, ta ce a gaishe ka"
"Ina amsawa, ya gidan nata akwai abinci kuwa?"
Nasiru ya yi farat ya ce "Baba ɗaki dai, a ɗaki ɗaya take da banɗaki, amma akwai abinci a ɗakin. Har mijinta ya kawo mana fura da Nono".
Baba ya ce "Ko ma dai a rami suke ba ɗaki ɗaya ba, ai ita ta jiyo, tun da Allah ya nufi ya rufa mata asiri, ya bata miji na gari na rufin asiri ta zaɓi ta tonawa kanta asiri, yanzu ta ƙare a tantalbatete"
Jamila dai kawai fatan ta, Allah ya sa ta yi nasara a kan Nana. Babu kunya Mama ta saka Nasiru a gaba, tana yi masa tambayar ƙawaƙwaf da son sanin halin da Nana take ciki na daɗi ko akasin haka.
**** Bangaren Shukura, duk da ta kan yi mafarkai na ban tsoro barkatai, amma bai fiye damunta ba, wasu lokutan da ta farka ma shikenan, mussaman idan tana da ciki ta fi irin wannan mafarkan. Amma a wannan karon ta kasa mantawa da wannan mafarkin da ta yi, a cikin jikinta take jin tsoro da fargaba a kan mafarkin.
Duk da ba ta iya gaya wa Sagir abin da ta gani a mafarki ba, kawai ta ce masa mummunan mafarki ne, ya yi ta kwantar mata da hankali, da tabattar mata da mafarki ba gaskiya ba ne ba.
Sai dai jin abin take yi, tamkar ma ya riga ya faru ne, ko kuma yana daf da faruwa, haka kurum sai ta ji gabanta ya faɗi ta razana.
****
Tare da su Habu ta hange shi zaune kan wani ƙaton carfet fari tas, a cikin sahara , suna ta shan shayi su na hira cikin nishaɗi, gaban su dabino kala-kala a cikin tasoshi, yana cikin su ba ya magana sai murmushi. Ƙyam ta tsaya tana ƙare masa kallo. Karaf ya ɗago kai suka yi ido huɗu.