Kenza eBookz

Damuwata complete novel - Chapter 10

Damuwata complete novel - Chapter 10

Damuwata complete novel Chapter 10: Damuwata complete novel Chapter 10. "Wai bazata auri mai mata ba saboda tana tsoron jarabar matarsa mai hali irin na…

3,373 words

"Wai bazata auri mai mata ba saboda tana tsoron jarabar matarsa mai hali irin na Aunty Nafisa sak."

Wani zabura Beebah ta yi tayo kan Fanta, ita kam ta kwasa da gudu ta fice zata rufa mata baya na rik'eta cikin tsare gira na ce "Ke kin gujewa auren tashin hankali amma ni kin dage sai na yi?"

Numfashi ta yi ta saukewa cikin alamun fushi, zuwa can ta yi gyaran murya sai lokacin na saki hannunta dana kama. Ruwa ta d'auka ta sha sosai sannan ta k'ara yin gyaran murya ta soma magana cikin natsuwa.

"Duk abinda Fanta ta sanar miki gaskiya ne illa abu d'aya shi ne da ta ce halin Mas'uda d'aya da na Aunty Nafisa, sam halinsu ya sha bamban saboda Aunty Nafisa bata tsafi haka tana shakkar Uncle Muhseen sakamakon da ita Mas'uda mijinta bai isa da ita ba hatta da mahaifiyarsa sai taso yake zuwa gaisar da ita, k'anninsa kuwa ta haramta musu zuwa gidanta, tun abin na damunsu har yanzu ya daina. Shin ta ya ina kallon wannan lamari zan amince na zama matar shige wacce bata tab'a yin daraja."

"A gaskiya Mas'uda bata da hali amma duk da haka ina ganin aurensa zai baki damar kwatosa daga halaka, domin zaki nusar da shi hakkin uwa kan d'iyoyinta, kiga kenan tamkar kinyi jihadi ne."

"Ada naji zan iya yin hakan amma tunda na had'u da burin zuciyata duk da shima tamkar son maso wani na keyi masa wanda masu iya magana kan kirasa da k'oshin wahala, naji gara in hak'ura da shi na kama na gasken a haka nan."

"Son maso wani bana gaske ba ne Sister, kidai yi hak'uri ki kama Yaya Abdallah please."

"Ko mu biyu muka rage a duniya ba zan aureshi ba."

"Me ya yi zafi?"

Banza ta yi da ni na rik'o hannunta "Beebah walalhi Abdallah ya bani tausayi yana cikin matsalar rayuwa gashi kin kasa fahimtarsa."

"Shi kuma baisan da yana cikinta ba domin duk wanda ya nusar da shi illar rayuwar da a keyi a gidansa sai ya k'ulla gaba da shi nima dan na nuna masa illar watsi da goggo da ya keyi shi ne ya soma zagina tamkar ya sami d'iyarsa har da cewa bashi bani shi ne na nuna masa nid'in 'yar halas ce na datse dik wani hanya da zai sadani da shi domin na fahimci gani yake bazan iya rabuwa da shi ba saboda kud'insa tare da kyawun da Allah ya bashi sai dai ya makaro domin ni una sonshi ne domin Allah badan wani abu nasa da Allah ya yi masa baiwar samu ba kuma kinji na rantse wallahi har ya koma ba zaiga dariyana ba, zai san ya zageni, zai san ya kirani da wawiya, banza, wofi mara tunani."

Innalillahi wa Inna ilaihin, a gaskiya Yaya Abdallah bai kyauta ba, zagi na zubda mutunci duk kuwa yarda kake d'aukan mutum."

"Ai kam ya zubar masa a idanuna, zubewa na har abada."

"Please Beebah ki sassauta hukuncin da kikayi masa, ki tarbesa in yaso da ya tafi ki watsar da shi."

"Ai na rantse kuma bazanyi kaffara ba, walalhi zai san ni 'yar hakas ce gaba da bayana."

"To Allah ya kyauta, abin ya girmama."

"Amin."

Shiru mukayi zuwa can na ce "Tashi kiyi wanka tunda kin koramin Aminiya, idan kin fito sai inyi."

"Na fasa."

"Duk saboda jin Ab...

"Deejah dan girman Allah kibar zuciyata ta sami natsuwa da kiramin sunar mara hankalin nan."

"Na shiga uku ni Nana Khadijatu."

"Ki tafi kiyi wankanki."

"Ok bari na fita na samo musu drinks saboda ba abasu Zobo da kunun Aya kawai ba tunda gasu tafe da babban bak'o."

Harara ta zabgomin na murmusa tare da ficewa.

"Walalhi sai na ciwa su Safina mutunci musanman Bintu dan nasan itace uwar kaud'in ingizashi ya zo."

"Ba ita bace sister Beebah, goggo ce da kanta ta ce ya dawo dasu kuma shi ba danke zaizo ba ni ce na ambaci hakan amma dan Allah kiyi hak'uri bansan haka ranki zai b'aci ba."

"Bakomi Fanta ya wuce."

Ta ambata cikin sakin fuska tamkar ba ita ce ta murtukesa ba.

Murmushi suka sakarwa juna. Tafi na soma daga bakin k'ofa sannan na shigo muka had'a ido da Fanta na kanne mata ido d'aya ta yomin jinjina da babban yatsarta amma a wayance gudun kada Beebah ta harbo jirgin domin plan muka had'a dan ta sakewa Abdallah fuska.

"Kin san Allah Deejah sister Beebah tana da gaskiya dan Yaya Abdallah mijin ta ce ne na gaske, hatta da unguwa in zaije idan matarsa bata gamsu ba fasawa yakeyi wai baya son barinta cikin tunanin inda ya je."

"Ikon Allah amma kam ta sami miji mai gaskiya."

"Uhm na banza da wofi ba tunda na b'atawa mahaifiyarsa raina akanta."

"Kuyi masa addu'a wata rana sai labari."

"Idan sister Beebah ta amincewa aurensa ba."

"Ba sai Beebah ce zata saitashi ba ko matarsa zata iya nusar da shi illar b'atawa iyaye rai."

"Banjin hakan zai faru ba tunda akanta komi ke faruwa, ita ce silar faruwar komi dan ance tunda ya soma neman aurenta halayyansa na kirki suka sanja zuwa na tsiya."

"To Allah ya shiryata."

"Amin, shi yasa na ke ya bawa Uncle wallahi domin shi jajirtacce ne domin duk son da ya keyiwa Aunty Nafisa tana sab'awa umurninsa zai hukuntata musanman da yanzu sister Beebah ta kuma d'orashi akan hanyar saita mata tunani wanda muke fatar halin rashin kirkinta ya zamo tarihi."

"Ku ne kuka ambata masa ya nemi aurena kenan? Shin kuna tunanin tahanyar yi mata kishiya ce zai dawo da ita hanyar gaskiya?"

"A'a shi da kansa ya ambata yana sonki wanda najima da fahimtar d'abi'unki na burgesa bai furta miki kalman k'auna ba ce sai yanzu, kinsan komi lokaci ne. Sannan Aunty Nafisa kuwa muna fatar ta dalilin zama dake ya saka ta yi koyi da halinki nagari ta dawo mai kyakkyawar mu'amala da kowa musanman mu jininta."

Shiru na yi na kasa sake cewa komi saboda yarda nake jin fad'uwar gaba.

Gyaran muryan Beebah ya sanya muka gane ta fito wanka, da sauri Fanta ta shige toilet dan gabatar da wankan itama.

"Insha Allah tsoron da ke ranki zai zamo tarihi sabida muna kanyi miki addu'ar samun rayuwa mai inganci a gidan Uncle."

"Ke da su wa?"

"Mama da Sisters d'ina."

"Shin da gaske su Bintu sun san da maganar nan?"

"Eh dan aminiyarki ta fesa musu kuma sunyi na'am da lamarin saboda zamansu da ke na kwanaki biyu sun fahimci bakya da matsala zaki iya hak'uri da halayyan 'yar uwanmu."

"Uhm har yanzu kuna kan bani mamaki wai ace kuna 'yan uwar Aunty Nafisa na jini amma kuna murnan da ayi mata kishiya."

"Ke ba kishiya ba ce Deejah, abokiyar zamace tagari mai tarin nagarta wanda muka tabbatar bazata iya bin hanyar banza ba dan ta cutar da 'yar uwanmu sabida kina aiki da iliminki kuma kin gama samun tarbiyya daga uwa ta gari wato Mama."

"Nagode da wannan yabawan, insha Allah zan nemi zab'in Allah cikin shi da Aliyu, duk wanda ya zab'amin zan amshesa da hannu biyu tare da mik'a godiya gareshi."

"Uwata neman zab'inki ya kasance na kan kowa da kowa ne ma'ana ki nemi zab'in Allah akan duk inda mijinki yake yazo gareki bisa amincinsa idan kuma yazo to ki amshesa da hannu biyun da kika ambata domin yanzu bana goyon bayan Alhaji Muhseen ko Aliyu saboda zab'in Allah shine sama da komi haka yardansa babban alkhairi ne ga rayuwar bayinsa dan haka ked'in alluran cikin ruwa ce mai rabo ka d'auka, ina fatar managarci, jajirtacce, mai tsoron Allah S.W.A da son Manzon Allah S.A.W zai d'aukeki ku rayu cikin inuwar aure na har abada."

"Amin ya rabbi Mama."

Beebah ta ambata cikin rawar murya saboda kalaman Mama sun shigeta ainun, ita dai zuwarta garin Kaduna tana ta samun natsuwar ruhi ta kalaman Mama masu cike da fikra.

Ni kam zubewa na yi gaban k'afafun Mama ina jan numfashi. Kamo ni ta yi ta rungume tana bubbuga bayana.

"Habibatu aramin ita muje unguwa, inaga sai bayan isha'i zamu dawo sai ku kula da gidan."

"Tam Mama kudawo lafiya."

"Allah ya so hakan."

"Amin."

Daga haka muka fice Mama na rungume da ni, a d'akinta na yi wanka na shirya.

"Uwata gidan Baba Umaru zamu saboda lamarin Malam yasoma bani tsoro kada wata rana ya kasheni ya maidake marainiya ya mallake dukiyar da ke zalama akan shi."

"Innalillahi wa Inna ilaihin raji'un, Mama me ya kawo wannan magan-ganun? Dan Allah kidaina ambatarsu dan suna sanyamin shakku."

"Shakkun me ne Uwata?"

Shiru na yi ganin haka sai ta ja kunnina da k'arfi na sanya k'ara ta kuma mud'ewa rik'e hannunta na yi cikin cewa "Shakkun ganin kamar ni ba d'iyar Ba...

"Nana Khadijatu!!."

Kiran sunana da Mama ta yi da k'arfi ya sanya ni yin dif da maganar ina girgiza kai.

"Wuce muje kuma kada na sake jin wannan banzan kalamin ya kuna fitowa a bakinki.'

"Kiyi hak'uri Mamana."

"Na yi, wuce muje magriba na kawo jiki."

Tafe muke a cikin Napep ina nazarin yanayin Mama, na hango tana tare da damuwa amma tana k'ok'arin b'oyemin sai na samu kaina da jin b'acin rai abinda na ke korerarsa kullum yana neman samun muhallin zama a ruhina wato tsanar Baba domin na tabbata shi ne silar faruwar b'acin ran Mama ta dalilin shigowarsa d'azun. Sadda muka isa gidan Baba Umaru suna gabatar da sallar magrib muma alwalla mukayi muka gabatar inda bamu tashi ba muka cigaba da azkar zuwa lokacin sallar isha'i domin tarbiyyan zuri'ar Baba Umaru idan anyi sallar magrib ba'a tashi sai an sallaci isha'i sai bisa babban dalili, hatta da yara k'anana 'yan shekaru Tara zuwa sama sun san da d'abi'an, 'yan k'asa da sune kawai zakaji karad'insu suma da zarar Baba Umaru ya shigo zasu natsu saboda baison hayaniya sam amma fa ya iya jan jikokinsa da sawa kamar yarda yakeyimin.

"Jikalle kuma takwarata kin b'uya ko kuma ince Hurera ta b'oyeki, sam bata bari kiyi zumunci da mu."

"Ayi hak'uri Hajiya Inna, ai gani yau nazo a gadonkima zan kwana."

"Kamar gaske."

Murmushi na saki ina kallo idanun Mama da itama ke doka murmushin.

Surikan gidan ne sukayi ta shigowa d'akin Hajiya Inna suna gaisar da Mama ni kuma ina gaisar dasu cike da kunya saboda yarda suke ta k'orafin na daina zuwa gaishesu.

"Zata rik'a zuwa duk ranar Juma'a insha Allah."

Mama ta ambata cikin 'yar dariya.

"To Allah ya nufa hakan."

Hajiya Inna ta amsa.

"Amin."

Suka amsa tare da ficewa.

"Taho muje mu gaisa da Baba naji shigowarsa."

Mama ta ambata cikin tashi tsaye.

"To."

"Hurera abi komi a hankali banda gareje kinji?"

"To Inna."

"Alhaji ya soma sanarmin da lamarin, ina ta yaki addu'ar Allah ya rayaki ku jima da Nana Khadijatu."

"Amin ya rabbi Inna."

"Sannan kiyi tunani akan zuwa wurin danginki domin shekara ashirin da d'aya ba kwanaki ashirin da d'aya ba ce."

"Insha Allah Inna zanje domin har da maganar nazo sanarwa Baba amma sai na soma zuwa Kwara naga zuri'ar Baba Abdul Ganiyu."

"Masha Allah Allah ya ida nufi."

"Amin."

Ina tsaye ina saurarensu farin ciki ya gama cikani jin zamuje wurin dangin Mamana abin da najima ina mafarkin zuwan lokacin.

"Uhm inda rai da rabo."

"Tabbas haka nr Uwata."

Kallon Mama na yi a she zancen zuccin da na yi ya fito fili.

"Idan kin gaisar da Baba ki fita in mungama zan kiraki."

Ta sanarmin daf da zamu shiga falon Baba Umaru.

"To Mama."

Da sallama muka shiga falon dattijon ya amsa mana tare da cillomin tsokana irin ta jika da Kaka.

"Matar b'oye yau ta bayyana to ki koma bana yi dan ban rasa mai neman ladar ba, gasunan buhu-buhu sai wanda naga damar ansawa gaisuwa tare da sakawa aiki."

Dariya na sanya saboda yarda yake maganar cikin zare idanu cike da barkwanci.

"Alhamdulillah yau na saka mai fuskan shanu dariya."

Nan ma wani dariya na kuma sanyawa cikin kulle bakina, hatta da Mama dariyar ta ke yi. Bayan mun gaisheshi na fito na bar Mama zaune gabansa cike da ladabi.

D'akin Hajiya Inna na dawo muka soma hira cikin maida zancen halayyan Baba wanda na fahimci na b'ata mata rai ainun. K'aran wayata ya katse mana hiran ganin Aliyu ne sai na kalleta ta sakarmin murmushi tare da mik'ewa ta fice tana cewa "Takwarata ba dai kunya ba to na bar miki d'akin, a ci soyayya lafiya."

sunkuyar da kai na yi, ina jin ta fice na gyara zama tare da d'aukan wayar wanda kiransa na biyu kenan, yi masa sallama na yi cikin laushin murya fiye da wanda Allah ya horemin.

*Affuwan 'yan uwa l ina cikin uziri ne shi yasa jiya kuka jini shiru.*

*TALLA.*

*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*

Sabulu (molato and black soap) Scrub Face cream Oil Body lotion Shower gel Kulachan Humra (White and black) Turaren tsugunon Turaren kaya Turaren wuta na d'aki Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)

*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.* [10/24, 11:20 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona)

By Safiyya (Mrsjmoon)

E.W.F.

Page 12.

"Kayi hak'uri mantawa na yi in sanar maka da mun fita tare da Mama."

Na ambata masa bayan ya amsa sallamar.

"Kada kidamu Habiba ta sanarmin yanzu suka shiga gida ai sun fansheki musanman Fanta da ta ce zatayi miki hiran tare da yin recoding idan kinzo ki saurara."

Dariya muka sanya daga nan muka cigaba da hira inda na dage ina maida masa da martani amma duk da haka wani kalman tanayimin nauyin ambata. Kimanin mintoci goma shabiyar muka d'auka sannan mukayi sallama, sosai zantukan Aliyu suka sakani cikin nishad'i. Kwanciya na yi a saman kushin ina doka murmushi.

"Hak'ik'a ina sonka Aliyu."

Na ambata a fili sai kuma na yi saurin kulle bakina tare da kife fuskata a filon kujerar saboda da yarda kunya ya ziyarce ni.

Misalin k'arfe tara da mintoci bakwai kiran Mama ya shigo wayana ban d'auka ba sai na tashi na nufi falon Baba Umaru dan nasan tafiya zamuyi. Ina shiga idanuna ya sauka kan Kawu Habib b'ata rai na yi cikin kauda kai aikam ya kyal-kyale da dariya su Mama na tayashi dan sunga abin da na yi.

"Ko kuka kika fasa ba zai hanani na kiraki da Dije ba."

"Ni ba Dije ba ce, Hajiya Inna kina jinsa na b'ata miki suna ko?"

"To Takwara ya zanyi da d'an neman zance, ai inda kara ke d'in Mama ya kamata ya kiraki."

Kallonsa na yi ya murgud'amin baki kamar mace sai na sanya dariya ya ko taho kamar zai dukeni na manne jikin Hajiya Inna.

Gaisar da shi na yi ya amsa cikin kamala tamkar bashi ba.

"Khadijatu Mamanki ta yi miki kyauta amma ta ce kada a sanar miki yanzu amma dai mune shedu dan haka ki kasance wurin yi mata addu'ar gamawa lafiya domin samun uwa kamarta sai antona."

"Nagode Mama Allah ya sa kifi haka, Allah ya baki kyautar Aljanna ranar sakamako."

"Amin ya bamu baki d'aya Uwata."

"Amin."

Habibullah tashi ka maidasu gida tunda hanyarka ce."

"To Baba."

"A'a Baba kabarshi ya tafi wurin iyalinsa sabida zan biya gidan Malam kafin mu isa gida."

"Yaya Hurera muje in kaiku inba dai kina son bambance matsayina gareki ba ne."

"Shi kenan Habibu muje, dafanta zakayi dariya ka daina cin maganin."

Ficewa ya yi cikin murmushi. Muma sallama mukayi da su Baba muka sameshi har ya kunna motar.

"Dije zaki zo taron suna gobe ko?"

"Sunar wa?"

"Kar dai ince bakijemin barka ba?"

"Ya Salam Aunty Zainab ta haihu ne?"

"Uhm ba laifinki ba ne na mamanki ce, yanzu na yarda da zancen Hajiya Inna sam baki d'aukemu a danginki ba kamar yarda muka d'aukeke."

"Habibu kayi hak'uri ni kaina banje barka ba dan namanta amma zamuje taron suna insha Allah."

"To, Allah baku iko.

Shiru ya ratsa motar zuwa can na ce "Kayi hak'uri Kawu Mama zata zo goben amma ni bayan sunar zanzo."

"Saboda me?"

"Kasan Uwata kifin rijiya ce data shiga taro sai taga kamar ita kowa ke kallo shiya bata son shiga taron jama'a sai dole."

"Da gaskiyanta tana da abin kallo musanman ga maza."

Da sauri na kalleshi ya murmusa tare da maida hankali kan titi."

"Habibu kaifa Kawun Uwata ce amma na lura kana son maida ita abokiyar wasanka."

"Yaya Hurera wallahi gaskiya na ambata Deejah na da abin kallo kamar ilimi, hankali, natsuwa da uwa uba hak'uri, shi yasa mazaje zasu so mallakanta a matsayin uwar 'ya'yansu, na tabbata duk wanda ya aureta ya yi babban dace tare da rabon na samun mace ta gari wanda Manzon Allah S.A.W ya ce dace da samunta shi ne mafi jin dad'in duniya."

"Zancenka gaskiya ne Habibu."

"Kinga kenan dole ta rik'a killace kanta ba ko wani kucaka da gara ya kamata suna kallonta arhaba."

"Kai Kawu dan Allah kadaina fasamin kai."

"Yabon gwani ya zama dole Deejah, ke dai ki godewa Allah da kika tara baiwa wanda ba kowa yake samunsa ba."

"Nagode Kawu."

"Godewa Allah 'yar Kawu."

"Habibu hoo, ba dai tsokana ba."

"Yaya haka Allah ya halicceni ya zanyi."

"Sai hamdala ga Allah."

Na ambata a hankali.

Sadda muka isa k'ofar gidan Baba k'arfe tara da rabi saura mintoci biyar.

"Ku shiga ina jiranku."

"A'a Habibu ka wuce kada mu b'ata maka lokaci."

"Bakomi ina jiranku."

Shigewa mukayi ina jan addu'a saboda nasan ba zamu fito lafiya ba batare da an b'atawa Mama rai ba.

"Mama wai me yasa ba mu bari mun zo da safe ba?"

"Yanzu Allah ya nufa muzo. Kayan auren Khamila aka kawo."

"Oh an dai-daita kenan?"

"Oho musu nidai an sanarmin an kawo kayanta bisa alamu wani ne dan wancan anmaida masa nasa tunda makashin mutane ne."

"To Allah sanya khairan."

"Amin."

Dun zancen cikin rad'a mukeyinsa har muka shigo tsakar gidan inda muka sami mutane cike ana ta kallon kayan cikin mutunci Mama ta gaisar da su suka amsa nima na gaishesu suka amsa tare da zubomin idanu abin da natsana kenan shi yasa ban son zuwa gidan sai suyi ta kallona tamkar sunga sabon halitta.

Baya na juya musu ina latsa wayata inda na ke hira da su Beebah a wani group danaga an sakani.

"D'iyar golden ko sai yaushe mijin da ake jira zai fito?"

"Lokaci dai, zab'in Allah bana mutum ba na nan tafe."

Juyowa na yi jin amsar da Mama ta bawa Uwar gidan Baba mai suna Asabe.

"Uhm wai ba, ko sai an tsufa ba zab'in Al...

"Kada ki sake kiyi sab'o Asabe domin shi zab'in Allah ba wanda ya san sadda zaizo saboda cikin rashin tsammani ke zuwa dan haka ki sanya ilimi kafin ki furta kalami."

Tsit wurin ya yi zuwa can jama'an wurin suka soma yiwa Asabe fad'ar rashin dacewar abinda ta yi tare da bawa Mama hak'uri, ganin abin na son zama rigima babba sai Mama ta yi musu sallama tare da yiwa maman Kamila fatan alkhairi muka fito Kawu Habibu ya ja muka tafi amma ina lura da yarda Mama ke ta sauke ajiyar zuciya alamun ranta ya b'aci hatta da Kawu ya fahimci bata cikin wal-wala shi yasa bai nemi maganaba har muka isa gida.

Abin mamaki Aliyu na gani zaune saman lifan nasa, yana ganinmu ya diro ya zube gaban Mama ya gaisar da ita cikin girmamawa sannan ya koma wurin Kawu ya gaisar da shi. Sunarsa Kawu ya kira ya amsa yana sunne kai.

Mama da Kawu ciki suka shiga ni kuma natsaya wurinsa.

"Dare fa ya yi Yallab'ai."

"Alk'awari na yi sai na gaisar da Mama yau tunda kuma na cika burina sai ince Allah tashemu lafiya."

"Amin, nagode da k'auna."

"Ba godiya tsakaninmu Matar Ali."

Girgiza kai na yi, ya kunna mashin d'in ya tafi cikin d'agamin hannu.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull