Damuwata complete novel - Chapter 13
Damuwata complete novel Chapter 13: Damuwata complete novel Chapter 13. Sallama ya yi a falon duk da yaga da duhu alamun babu kowa amma bai sanya ya shigo…
3,266 words
Sallama ya yi a falon duk da yaga da duhu alamun babu kowa amma bai sanya ya shigo kai tsaye ba. Makunnin wutar ya latsa haske ya gauraye falon zama ya yi cike da gajiya ga yunwar da ta addabesa, mik'ewa ya yi dan samawa kansa abinda zai kori yunwar. Ja baya ya yi cikin razana da ganinta domin sam bai jiyo takunta ba sai gaminta ya yi tsaye gabansa.
"Dole ka razana mana saboda ka san baka da gaskiya, wallahi Abban Hafiz wutar Allah sai ta cika in har ka ce wannan mugun halin zaka tsiro da shi na yanke zumunci tare da munafunci. Wai ina matarka baka damu da ni ba kamar yarda ka damu da d'iyar makwafta, na rantse da Allah ba zan tab'a yafewa aljanan yarinyar nan Deejah ba domin ta rabani da dangina tare da mijina to wallahi Allah sai ta biya dan bata ci banza ba, zan nuna mata ainihin kalata wanda ta ke da duhun kai akansa Dan sai na wulak'antata da duk kan gatanta, sai ta yi kukan jini bana hawaye ba, billahil azim kukan da ta sakani sai ta yi ninkin baninkin nasa indai ina numfashi, sanann kaima ban ya...
"Ke! Banson sokanci da rashin natsuwa maza b'acemin da gani tun kafin ranki yafi dare duhu."
Ganin magan-ganun Nafisa bana k'are ba ne shi yasa ya dakatar da ita cikin fushi amma hakan baisa ta tsagaita da tijarar ba saima haukacewa da ta yi cikin daga murya tana kuka tana fallasa mygayen alwashinta akan Deejah muryanta sai sark'ewa keyi tamkar zatayi amai.
Shiru ya yi yana kallonta domin yasan ya tab'ota, bai kyauta mata ba saboda tunda ya fita sadda Beebah ta sanar masa da halin da Mama ke ciki bai kuma waowayen gida ba ko kayan da ya sanja Sa'ad ya turo ya d'aukan masa kuma ya tabbata sunyi halin nasu da ita saboda basa zama inuwa d'aya dalilin kenan da baya zuwa gidan saida babban dalili.
"Kiyi hak'uri Mom Hafiz, yanzu hutu na ke buk'ata, tafi ki samomin abinda zanci wallahi yunwa ke damuna."
Ya yi furucin cikin laushin murya saboda maganganunta na daf da sanya masa ciwon kai, dole dibarar lallab'ata ya zo masa.
"Ai da ka dauko dadiron naka ta huce maka gajiyan kuma ba mai sakani shiga cikin da wannan daren salon in d'auko aljannu ka barni da wahala, ai saidai ita d'iyar Bokann tazo ta dafa maka abin da zaka ci amma ba dai Nafisatu ba jinin bare-bari."
Runtse ido ya yi yana jan addu'ar samun nutsuwar zuciya saboda kada ta tunzirashi ya aikata abinda zai damesa, musanman kalman dadiro da ta ambata
"Abban Hafiz yau fa sai ka zab'a ni ko d'iyar makwafta domin nagaji da hak'uri akan cin kashin da kakeyimin akanta, wallahi yau sai ka sanarmin da hakikanin alak'ar dake tsakaninku."
"Fine, kina son sani ko?"
Ya furta cikin wata murya mai kaushi daga ji ranta ya kai k'ololuwar b'aci.
"Eh."
"Iyali ta ce."
"Me!?"
"Ban hanya in wuce ko in aikata abinda ba zaiyi mana dad'i ba duk kanmu."
Fad'awa kujera ta yi jikinta na rawa saboda yarda ta hango komi na iya faruwa idan har bata kauce ba.
"Na shiga uku ni Nafisa d'iyar Boka ta gama min da miji, shi da ke rarrashinna idan na tubure masa irin haka yau shi ne ya komamin horror, Allah ya isa tsakanina da ke Deejah wallahi sai na koya miki hankali, saina b'ata miki fuskan nan mai kama da ta aljannu inga ta inda zaki kuma d'aukan hankalin mijina."
"Aikata hakan dai-dai ya ke da yanke alak'ar aurenmu da ke na har abada sannan ko da habaici kika tozarta min Khadijay ban yafe miki ba."
Yana ambatar haka ya haye sama ranta tamkar wuta, yunwarma da yakeji nemarta ya yi ya rasa, sai bugawa zuciyarsa keyi da k'arfi.
"Hak'ik'a Aurenki shi ne kaddarata Nafisa, ya Allah ka bani ikon cinye jarabawan nan ka kuma yimin dacen samun mace ta gari mai kwantarmin da hankali ko da ba wacce raina ke burin mallaka ba ce."
Hawaye ne masu dumi suka zubo masa burinsa ya jiyo muryan Deejah wannan dalilin ya sa ya kirata da number da bata san shi da shi ba tana d'auka ya datse kiran. Abin mamaki yana jin sallamarta cikin taushi ya sami kansa cikin nutsuwar ruhi, hamdala ya yi tare da cigaba da ambatar sunar Allah AL-GAFURU. A haka yana zaune saman kujera barci ya soma kamasa sai kawai ya gyara kwanciya.
*** Kiran sallar asalatu ya farkar da ni na sauka a hankali na ji Mama ta rik'eni da sauri na kalleta ta sakarmin murmushi a hanzarce na koma jikinta na rungumeta k'am-k'am ina dariyar murna.
"Uwata Allah ya yi miki albarka mara iyaka, Allah ya inganta rayuwarki, Allah ya rabaki da ganin tijarar rayuwa Gabas da Yamma, Kudu da Arewa."
"Amin ya rabbi Mamana."
"Tafi kiyi nafila idan kin sallaci subahi sai ki taimakamin inyi wanka."
"To Mamana."
Ina idar da sallah aka kwan-kwasa k'ofa, na bud'e cikin jin faduwar gaba, Baba ne tsaye fuskan nan kamar an aiko masa da sak'on mutuwa. Russunawa na yi na gaisar da shi ya amsa a dak'ile na maida k'ofar na kulle na koma saman sallaya na cigaba da jan carbi amma hankalina na kan su Baba wanda na fahimci Mama bata so ganinsa domin yana ta kiran sunarta tak'i amsawa, ta yi kamar mai nisan barci alhalin ganin shi yasa ta koma kwance.
"Ke! Uwani tun jiya bata farka ba ne?"
"Ta farka."
"Da yaushe?"
"Tsakiyar dare."
"Alluran hutun suka sa ke yi Mata ko me?"
"Magani dai suka bata inaga shi ne ya kuma sakata nauyin barci."
"Me suka ce na damunta?"
"Hawan jini."
"Kin gani ba, ai dama na sanar mata indai tana tare da ke sai ta gamu da ciwon zuciya bama hawan jini ba."
"A'uzubillahi! Baba ni d'in?"
"A'uzubillahi akanki shegiya mai bakin jini gayyar ta zu...
Tarin da Mama ta sark'e da shi yasa Baba dakatawa da yimin tijara. A guje na hau gadon na kamota ina kiran sunarta bata amsa ba amma ta daina tarin. Kallon Baba na yi ya zabgomin harara kwantar da ita na yi na sauka na fice zuwa kiran Likita. Tare muka dawo da Likita tare da nurses biyu, cewa sukayi mu basu wuri, muka fito ni da Baba sai zagina ya keyi zuwa can ya koma kam Uncle na antayo masa zagi tamkar ba malamin ilimi ba.
"Alla wannan munafukin Alhaji Muhseen ya ke ko wa, k'ara zan shigar da shi akan shigamin safgar iyali kai tsaye batare da neman izinina ba, duk kudinsa idan na saka masa ido wallahi sai ya koma mai gyaran talkalmi ya fisa arziki, muzuba mu gani shege ka fasa ba dai aurenki ya ke son yi ba, Uhm."
Nidai kai na juya gefe ina saurarensa hakalina na ga halin da Mamana ke ciki.
Ban aune ba na ji an zabgamin carbi a kai na kwalla ihu wasu nurses suka taho wurin a guje ganinsu Baba ya bar wurin tamkar bashi ya aita dukan ba.
"Kiyi hak'uri Mamanki zata sami lafiya kinji."
Motsa kai ba yi domin d'aukansu halin da Mama ke ciki ne ya sanyani ihu, su suka kamani na zauna saman bencin da Baba ya tashi sai bani baki sukeyi, muna a haka Likita ya fito tare da nurses ya dubeni ya ce "Ina Babanki?"
"Ya tafi ya dawo."
"Ok shiga tana son ganinki amma ki kula kada ki yarda maganar bacin rai shiga tsakaninku saboda zuciyarta na daf da samun matsala."
'Shi kenan bakin Baba zai tabbata.'
"Tana son hira mai sanya nishad'i dan haka ki lula sosai."
Maganar Likita ya dawo dani tunanina.
"To."
Na amsa cikin rawar murya.
Ina shiga Mama ta d'agomin hannu na isa da sauri na kama.
"Malam ya tafi ko?"
"Eh."
"Kin sanarwa da Baba Umaru kuwa?"
"A'a."
"Maza kiramin shi."
"To."
Na tafi in d'auko wayar inda na barta jiya babu ita ba sanmatarta, shiru na yi ina nazarin inda na jefata.
"Uwata."
Mama ta kirani cikin wata murya mai kama da ta yara masu tsamin baki. Da hanzari ya juyo wurin batare da na amsa ba sai dai abinda na yi arba da shi ya kusa sanya zuciyata bugawa.
Mama ce ke d'agomin hannu cikin son furta kalma tamkar ba yanzu ta kirani da muryan yara ba. Kallon yarda bakinta ya koma gefe na ke yi jikina na rawa, ga wani irin jijjiga da ta soma ruwan kumfa na fitowa daga bakin tamkar wacce taci guba.
"K'alu innalillahi wa Inna ilaihin!."
Kalmar da na ambata kenan da k'arfi ina mai nufar Mama da wani irin k'arfi na cukumeta ina zabga ihun kiran Likita da muryana wacce ta soma dawowa hayyacinta daga dushewa, nurses suka shigo a guje wanda na ke zaton dama suna hanyar zuwa d'akin ne saboda muna da tazara da inda suke. Cikin dibara sukayi nasarar rabani da jikin Mama. Na juya musu baya ina wani irin kuka wanda na ke jin zafin fitarsa har cikin tsokar naman zuciyata.
"Mama kada ki tafi ki barni wallahi ba zan iya rayuwa babu ke ba, in kika tafi zan biki ne a birnemu tare, wayyo Allah rayuwata!. Hasbunallahu wal ni'imal wa kil!, La'ilaha illa anta subbahanaka inni kuntu minal zalimin!."
Na zame k'asa na zauna dirsha ina cigaba da mai-maita addu'o'in cikin k'araji. Saukan hannu naji a saman kafad'ana yasa na tsaya tsak tare da kallon wanda ya dafanin, zubawa Likitan ido na yi wanda ban san sadda ya shigo ba.
"Kiyi hak'uri duk mai rai...
Ban gama jinsa ba wani sautin dim ya sauka cikin kunnuwana abinda ya haifar da toshewarsu kuma alokaci d'aya idanuwana suka daina ganin komi, duhu ya mamayesu, ji na yi tamkar ina yawo a sararin samaniya, zuwa can naji kamar ana janyoni zuwa k'asa al'amarin da ya sanyani jin ina fizgar numfashi da k'yar kenan daga haka ban kuma sanin me ke faruwa ba.
*Zaku iya soma booking kafin zuwan k'arshen free pages, send #300 only a 0468069082 Haruna Safiyya GTbank, aturo shaidan biya ta 08132166848.*
*TALLA.*
*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*
Sabulu (molato and black soap) Scrub Face cream Oil Body lotion Shower gel Kulachan Humra (White and black) Turaren tsugunon Turaren kaya Turaren wuta na d'aki Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)
*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.* [10/27, 8:16 PM] 💘: DAMUWATA BY MRSJMOON
E.W.F.
PAGE 15
K'arfe biyar da mintoci goma Sha biyar Alhaji Muhseen ya fito zuwa masallaci kamar yarda ya saba saboda shi mutum ne mai rik'o da addini in kaga jam'in sallar subahi ya kubce masa to baida lafiya ne ko ya fita k'asar. Fitowarsa ya tuna da police da ya d'auko gadin su Bintu.
Wurinsu ya nufa suka gaisa tare da tabbatar masa da babu wanda ya dawo dan yunk'urin shiga gidan, godiya ya yi musu suka jera zuwa masallaci saboda musulmai ne, bayan an idar da sallah suka fito har cikin gidan ya yi musu jagora suka ga abin da akazo sata suka kuma duba ko ina ko zasu sami shaidan da zaisa agano barawon amma basuga komi ba, sallamarsu ya yi ya dawo cikin gidan ya sami su Fanta tsai-tsaye cike da tsoro jin barawo ya shigo suna barci.
"Ku shirya ku kulle ko'ina ku dawo gida 'yan sanda zasu cigaba da saka ido a gidan daga nan har zuwa sadda masu gidan zasu dawo."
"To Uncle."
Suka amsa atare.
Ya fice cikin tako mai cike da natsuwa. Yana shiga gidansa mota ya d'auko ya nufo Asibiti cike da burin son sanya Deejah a idanunsa, yana sanyo hancin motarsa a cikin Asibitin Baba na fitowa, horn ya yi masa dan ya tsaya su gaisa amma yana kallonsa ya kauda kai gefe ya yi gaba tamkar zai kifa saboda sauri.
Raka bayan Baba da kallo ya yi cike da mamakin baudadden halinsa na rashin fahimta.
"Ikon Allah sai kallo da alama taimako na son zama matsala, ko jiya badan na kai zuciya nesa tare da tuna cewa ni ke neman had'a ziri'a da shi ba tabbas da mun raba abin kallo a bainar jama'a."
Ya ambata cikin dafe gefen kansa da ke yi masa ciwo tun daren jiya. Ya jima zaune cikin motar kafin ya fito jikinsa a sake ya nufo ciki. Nurses din da ya gani sun shige d'akin da Mama ke kwance a guje yasa shima d'iba da gudu ya rufa musu baya. Saidai kafin ya isa sun kulle k'ofar wayar Deejah ya kira tana ringing ba'a daga ba ya sake kira akaro na biyu ya ji akashe.
"Me ke faruwa?"
Fitowar Likita daga d'akin ya yi hanzarin shan gabansa.
"Dr. Jalal me ke faruwa?"
"Biyoni office Yaya, dama kai zan kira yanzu."
Saida Dr. Jalal ya b'acewa ganinsa sannan ya bi bayansa.
"Yaya Muhseen yarinyar nan tana cikin wani hali domin ta shiga coma farfad'owarta zai d'auki d'an lokaci saboda firgitan da ta yi da ganin halin da Mamanta ke ciki."
"Jikin Maman ya kuma tashi ne?"
"Eh dan har munyi zaton rai ya yi halinsa wanda ya kai Dr. Salim ambatawa Khadija rasuwarta dalilin fad'awarta doguwar suma kenan."
"Innalillahi wa Inna ilaihin raji'un."
"Relax Yaya insha Allah ba zata wuce sati d'aya ba zata farfad'o."
Dr. Jalal DAMUWATA Mahaifiyarta ce kadaiga halin da ta ke ciki shin ya zata koma idan ta sami labarin?"
"Zanyi mata bayanin yarda zata fahimta, insha Allah abin da kake gudu bazai tab'a faruwa ba."
"Allah ya so hakan."
"Amin."
"Ina ita Khadijatun?"
"Tana nan a cikin d'akin."
"A sanja mata daki please."
"Hakan dama zamuyi, mun barta ne zuwa anjima."
"Dr. A sanja mata yanzu dan Allah."
"Shi kenan bari in sanarwa Nurses su kaika private room."
"Yawwa, nagode Doctor."
"Bakomi Yaya, fatarmu dai su sami lafiya."
"Allah ya basu lafiya."
"Amin."
*** Uncle Muhseen ne zaune gaban gadon ya tsira mata ido hankalinsa ya yi nisa cikin tunani, sam baiji motsin bud'e k'ofa ba sai maganarsa ya ji.
"Yaya tunani ba shi ne mafitar lamura ba, kayi musu addu'a shi ne sukafi buk'ata."
Ajiyar zuciya ya sauke tare da mik'ewa ya rik'o hannun Sa'ad.
"Nagode da tunatarwa Brother."
"Bakomi magajin Abba."
Murmushin ya ke ya yi tare da komawa ya zauna a inda ya tashi ya dora hannunsa kan na Deejah ya kalli inda Sa'ad ya ke tsaye.
"Brother ka zamo shaidana akan k'aunar da na keyiwa Nana Khadijatu, wallahi ina sonta, so mai tsafta wanda na ke hasko kwanciyar hankali a cikinsa domin ina fatar zamanta a karkashina ya sanya gidana ya gyaru wanda dangi zasu cikamin shi ta hanyar sada zumuntar da suka yanke saboda mugun halin Nafisat."
"Allah ya cika maka wannan burin."
"Amin."
"Yaya Abokina Dr. Jalal ya sanarmin dalilin tashin ciwon Mamanta guba aka shafa mata a lips domin sunyi buncike sun gano hakan amma bai shiga bakinta ba ya k'i sanar makane saboda yarda yaga kana cikin damuwa."
"Innalillahi wa Inna ilaihin, waye ya shiga d'akin bayan Khadijatu?"
"Bansa ni ba kam."
"Zauna da ita ina zuwa."
Yana ambatar haka ya fice Sa'ad ya rakashi da ido daga bisani ya zauna ya kafe Deejah da ido cike da tausayi, siririn tsaki ya ja tare da mik'ewa ya fito ya kira Nurse ta kula da ita.
"Abokina ya kamata ku gano wanda ke son kashe matar can."
"Engineer lamarin a rikice ya ke kaga dai d'aga yarinyar sai Babanta suka kasance a cikin d'akin kaga ba wanda zamu zarga cikinsu."
"Haka ne."
"Sannan matar kamar lamarinta da junnu dan ko su zasu iya had'a wannan kaidin dan su had'a rigima domin a d'orawa wani laifin su koma gefe suna dariya."
"Eh da wannan kuma dan a yarda aka kawota alamominsu ya nuna duk da hawan jini shima na sanya fad'awa yanayin."
"Haka Engineer kuma mai shirin zama Likita."
"Be serious Malam."
"To Yallab'ai yanzu abinda zamuyi shi ne hana kowa ganinsu sai wanda aka yarda da shi kuma tare da amintattun Nurses wanda zasuyi masu rakiya har zuwa sadda zasu fito."
"Good job Abokina, Allah ya k'ara fasaha."
"Amin."
"Bari in koma gida domin daga Masjid na taho nan."
"Allah sarki, hak'ik'a Engineer kai da d'an uwanka kuna da hali mai kyau, Abba ya yi dacen samun 'ya'ya masu albarka."
"Uhm abin da Momy ta kasa ganowa kenan."
"Kai ne ka kasa fahimtarta Abokina."
"Jalal me kake son inyi wanda zata fahimceni?"
"Nuna mata ka daina aikata sab'on Allah tare da bin umurninta kuma ka amince da zab'in ta."
"Ban aikata komi Abokina, nasha sanar da kai amma ka kasa aminta."
"Wallahi na aminta abin da Momy ke zargi ba gaskiya ba ne domin Abokina tsoron mata ya keyi."
"Uhm nagode da fahimta kuma abin da na aikata ai kuskure ne sannan natuba ina da tabbacin Allah ya yafemin."
"Insha Allah Abokina."
Furzar da iska ya yi idanunsa jajur.
"Sorry Yallab'ai, abu d'aya na ke so kayi yanzu shi ne ka amince da zab'inta tunda kai ka lalata hanyar to ya zama dole ka gyara ko dan rufuwar asiri."
"Bazan amince ba."
"Abokina zab'in Momy ne fa."
"Ko zab'in Abba ne banga mai sanyani na amince ba dan haka kada ka sake yimin zancen banzan nan sannan ka sani Momy bata da wani zab'i sai takura dan haka ka kiyayeni da kalamin nan tun ranka baifi nawa b'aci ba."
"Affuwan Yallab'ai sarkin hawa tamkar garin kwaki."
"Ai saikayi, kuma kada ka sa ran sake ganina nan kusa a Asibitin nan."
"Kaga matsalata da kai kenan saurin fushi."
"Shi yasa zan d'auke kafa ka daina ganin fushin."
"Zauna Abokina muyi magana na fahimta domin bana son fushin mahaifiya ya tab'a min kai."
Wani dogon tsaki Sa'ad ya ja tare da ficewa ya bugo masa k'ofar office d'in da k'arfi wanda saida ya razana.
"Kai anya Sa'ad shi kadaine kuwa? Tabbas ruwa baya tsami banza, saurin fushin nan ya yi yawa ga rashin fahimta, hak'ik'a bai rama mutsa-mutsai saman kansa."
Dr. Jalal ya ambata cike da damuwa.
*** Gidan malamin da ya yi saukar Alqur'ani Uncle Muhseen ya nufa sun jima suna magana kan lamarin inda ya yi ta bashi labarin yarda mugayen aljannu suke had'a fitintunu tsakanin al'umma a rasa gano kan lalura, domin kai tsaye ya karyata zancen guba, ya ce siddabarun mugayen aljannu ne da akayi mata turensu suka juya lamarin da guba dan had'a fitina asoma zargin da babu makama.
Uncle kam ya gamsu da bayanan, a k'arshe suka fito tare zuwa Asibitin. Sun sami Baba da matarsa kewaye da da Mama, k'iri-kiri Baba ya hana su isa wurinta duk kuwa da suna kallonta tana magana akan ya barsu amma ya rufe ido ya yi ta fesa bala'i tare da ik'irarin samuwar alkaba'i ga Uncle wanda tashin harshensa ya janyo Likita ya shigo ya koresu tare da bawa Uncle damar ganinta shi da Malam wannan abu da Likita ya yi ya bakanta ran Baba ainun inda ya k'ara kullatan Uncle domin bai jira komi ba ya fice tare da matarsa suka bar Asibitin baki d'aya, ya tarar musu Napep suka tafi gida shi kuma ya nufi gidan Baba Umaru wanda har zuwa lokacin bai sami labarin lalurar ba.