Kenza eBookz

Damuwata complete novel - Chapter 14

Damuwata complete novel - Chapter 14

Damuwata complete novel Chapter 14: Damuwata complete novel Chapter 14. Saida suka tabbatar Baba ya b'ace sannan suka juya da mai Napep zuwa Asibitin suka…

3,374 words

Saida suka tabbatar Baba ya b'ace sannan suka juya da mai Napep zuwa Asibitin suka sallameshi suka shiga suka zauna suna raba ido, zuwa can suka tambayi wata Nurse d'akin da Deejah ta ke ba tare da tunanin komi ba ta yi musu jagora zuwa d'akin. Zama sukayi a kujerun roba da suka samu a cikin d'akin suka tsirawa Deejah ido, suka kalli juna sai suka kyalkyale da dariya har da yin k'aramar gud'a cike da nishad'i. Bincike suka somayi ko zasu sami abin kwalam amma basu sami komi ba cike da jin haushi Asabe ta nufi inda Deejah ke kwance ta falla mata mari wanda saida yatsunta suka fito ta kai hannu ta shak'e mata wuya da iyakacin k'arfinta duk, ita kam Deejah bata san anayi ba.

"Kul! Yaya barta kada ki k'arasa gawar da banaki ba."

Cikin huci ta juyo "Wallahi Hinde ji na ke tamkar in kashe su na wataya cikin dukiyar tumakan can wanda kullum sake tunbatsa sukeyi, hassada da kushe basayi musu komi sai ginuwa"

"Wallahi Yaya nafiki bak'in ciki da ganin albarkansu haka nafiki son Hurera da wannan shegiyar su mace muci gado a bulis."

"Ki bari kawai Hinde ai ni a duk kwanar duniya sai na yi fatar samuwar sanadin macewar tumakan nan da lalacewar duk k'addarorin Hurera amma abin takaici tamkar taki ake yayyafa musu, ni lamarin har tsoro ya ke bani."

"Ai itama a tsaye ta ke bata gidan Boka bata gidan mugayen Malamai shi yasa duk asiran da muke b'atar da kud'ad'e wurin yi mata ya kasa tasiri akanta."

"Ai yanzu gashi muna zaune tasu tazo k'arshe, insha Allah Hurera bata warkewa haka wannan shegiyar daga wannan sumar sai dai ta jita cikin k'abari, rayuwar barzhu ya tabbata garesu."

Wani shewa suka tare da tafawa suka juya suka buga duwawo cike da farin ciki.

"Ai Yaya suna mutuwa kafin a kaisu zan tura Anas ya sungumomin uwar garken in kaita k'auye wurin Kaka na yi ta cin amfaninta hankali kwance."

"Nikam buhunan waken suyar nan na ke hari dan ko daren jiya na tura Kamalu ya haura ya satomin su sai wannan banzan Alhaji Muhseen d'in ya zo ya kwafsa dan iya mugunta har da saka 'yan sanda gadi wanda har yanzu zancen da na ke miki basu bar gidan ba."

"Oh ni 'ya su kajimin dan wahalar makwafci dai, ko ina ruwansa da lamarin gidanta?"

"Oho masa, amma ai ya tab'o Malam, ina mai tabbatar miki sai yaga bayarsa, duk dukiyarsa sai ya zamo tarihi, kuma ina bayarsa ya makashi a Kotu tunda banga dalilin shiga lamarin iyalinsa da ya yi ba yana k'aton baligi."

"Uhm Yaya ina tsoron kada Malam ya janyo mana fitina muna zamanmu lafiya kinsan dai yafishi kud'i da sanin manya."

"Ke dalla can matsoraciya kawai wallahi ni burina a kulleshi tare da manna masa kazafin yana lalata da Deejah kinga tunda yana da mata jefeshi za'ayi mu kuma mu tik'i rawarmu da shewa."

Wani dariya suka kuma kwashewa da shi tamkar tab'abbu.

Turo k'ofar akayi suka juyo idanu waje, tsira musu ido ta yi duk sai suka daburce, rashin gaskiya ya baiyana karara a tare da su

"Nagode zaku iya tafiya tunda kun gama nishad'in."

Hijabansu suka sanya suka fice kansu k'asa irin na munafukai.

"Mama wad'an nan mutane basu da gaskiya, rawa da guda fa nagansu ta window sunayi tamkar suna gidan biki, dalilin da yasa kenan na kirawoku dan ku gani."

Nurse da ta rakosu ta ambata cike da takaicin.

"Bakomi sunma kansu ne ai ciwo na kan kowa."

"Allah dai ya kyauta, wallahi dana san ba mutanen kirki ba ne bazan yi musu jagorar zuwa ganinta ba."

"Kada ki damu, koma bakin aikinki sai dai gaba a kiyaye wad'anda zasu nemi ganinta."

Uncle ya ambata a hankali.

"Insha Allah, Dr. Jalal ma ya saka wanda zasu kula da wanna gefen."

"Da kyau, hakan ya makata kam."

Kujera Uncle ya matsawa Mama da shi bakin gadon ta zauna idanunta cike da hawaye.

"Kada kiyi kuka addu'ar samun waraka zakiyi mata kamar yarda ta rik'a yi miki sadda kike kwance."

"To Alhaji amma kukan ne yakeyin kansa duk yarda na koreshi yak'i tafiya."

Ta amabata cikin muryan kuka.

Sauke kai kasa Uncle ya yi yana jin wani kalan tausayinsu na kuma nashe kirjinsa.

"Komi mai zuwa da wucewa ne Hajiya, ki daure kina ambatar addu'ar dana sanar da ke d'azun insha Allah dakiya zai rab'eki."

"To Malam, hak'ik'a bani da bakin gode maka sai dai na dauwama cikin nemawa rahmar Allah har zuwa ranar da ruhina zai bar gangar jikina zuwa ga mahaliccinsa."

"Ina godiya da wannan karamci, Allah ya sa damu da Rahmar Allah baki d'aya."

"Amin."

Uncle ya amsa ahankaki idanunsa na kan Deejah.

"Na k'ara yarda da addu'a takobin mumuni ne domin a dazun idan ancemin zan iya takawa da kafafuna zuwa nan zan musanta amma da zuwar Malam bayan ya gama yimin addu'a ina shan Zam-zam d'in nan sai narika jin tamkar ana kwanceni daga mugun d'auri, cikin amincin Allah na rikajin kuzari na kuma nashe duk kan gab'b'aina, kai madalla da samamuwarka cikin rayuwarmu, ina mika dubun godiya a gareku Allah ya rubuce zuwa gaban Ma'aikin Allah."

"Amin."

Suka amsa shi da Uncle.

"Itama yanzu zan jaraba sa'ata insha Allah bazata kai kwanakin da Likitoci suka ambata ba duk da nata ba nindaren aljannu."

"Allah ya taimaka."

"Amin Mamanmu."

Kallon Uncle Mama ta yi sai taji kunyar sunar ta sauke kai k'asa, shima kunyarta ce ta kamashi ya juya baya yana sosa sajensa.

Malam ya matsa gaban gadon Deejah ya ja addu'a mai tsawo ya tofa a robar Zam-zam ya guntsa ya fesa mata a fuska, bata motsa ba ya kuna fesawa duk bata motsa ba haka ya cigaba da yin addu'a yana fesa mata ruwan Zam-zam a fuska har sau bakwai sannan ya dakata yana sauke numfashi tamkar wanda ya yi gudu zuwa 'yan sakonni sai ta d'aga hannunta na dama da k'arfi ta maida ta kuma motsa kai cikin cije leb'e daga haka bata k'ara motsi ba, ta koma yarda ta ke tamkar gawa.

Hamdala Malam ya yi, ya juyo ya fuskanci su Mama da jikinsu ya gama yin sanyi da lamarin.

"Alamun masara kenan dama k'a'idar addu'ar idan ta motsa aiki ya yi kyau idan kuwa bata motsa ba har tsawon mintoci goma to koda ta tashi zata iya gamuwa da wani lalurar daban to sai gashi ta motsa ko minti d'aya ba'a samu ba, tabbas dole mu k'ara godewa Allah, domin mun rok'esa kuma ya amsa mana nan ta ke, Allah Alhamdulillah."

"Alhamdulillah."

Mama da Uncle suka ambata a tare.

"Hajiya anjima bayan la'asar Alhaji zaiyimin jagora zan shiga gidanki in sake yin saukar Alqur'ani da yarana sai mu rufe da rokon Allah akan ya baku kariya daga duk kan sharrin jinsin mutum da aljan duk da munyi hakan to zamu karayi akaro na biyu bayan kwana biyu sai mu zauna zama na k'arshe wato na uku inda zamuyisa kafin a sallamoku. Da yardan Allah kunyi ban kwana da duk kan sihirce-sihirce da akeyi muku a gida kuma idan Khadijatu ta warke zan rubuto mata addu'o'i wanda zaku rik'ayi bayan sallar subahi da magriba domin kara samun kariya daga mugaye."

"Nagode Malam, Allah ya biyaka da khairan."

"Amin."

Rakiya Uncle ya tafi yiwa Malam abinda ya bawa Mama damar yin kuka, ta kife kuskanta a tafin hannun Deejah ta saki kuka mara sauti, ji take tamkar ta dawo da laluran kanta.

"Allah ya tashi kafadarki Uwata, ina da buri mai yawa akanki, ina son naga Aurenki tare da zuri'arki, na goyasu tare da yi musu tawai, zuri'ar da ban samu ba ina burin na samesu ta fanninki, ki haifamin na gansu suna kiriniya a gabana, ya Allah ka saukar da salama zuwa ga baiwarka Nana Khadijatu ba dan halinta ba."

"Amin ya Allah Mama."

Dagowa ta yi Fanta ta fado jikinta tare da sakin kuka mai sauti.

Isowarta kenan da abinci Uncle ke sanar da ita.

"Fanta DAMUWATA mai tarin yawa ne, idan na rasa Uwata bansan ya zanyi ba, ita ce bangon dafawana, ita na ke kallo na sami farin ciki, hak'ik'a in ta tafi ta barni nima zan bita ne domin banga amfanin rayuwa babu ita ba."

Rufe mata baki Fanta ya yi tana girgiza nata kai hawaye na kuma b'ulb'ulo mata.

"Barni in fitar da DAMUWATA Fanta ko ya taima na sami sauk'in malolon da ya tokaremin k'ahon zucci."

"Mama ki ambaci sunar Allah shi ne maganin damuwarki sannan ki kwanta ki huta domin surutun sake jefaki cikin damuwa zaiyi gashi dama ba lafiya ce ta wadaceki ba."

Hannu ta kai fuskan Fanta tana share mata hawaye cikin motsa mata kai alamun aminta da kalamanta.

"Nagode Mama."

"Hak'ik'a kunyi tarayya wurin halayya sa Uwata shi yasa k'awancenku ya yi k'arko."

"Mama dan Allah ki taho ki kwanta a nan ki huta."

Ta ambata tare da nuna mata gefen gadon Deejah, tana mai zaunar da ita a wurin cikin lallab'awa, sai lamarin ya bawa Mama dariya ta murmusa ta damk'e hannun Fanta ta d'ora a saman na Deejah, ta tsirawa hannayen idanu cikin sauke numfashi zuwa can ya ce "Ko da na rasa Uwata dan kiyimin alk'awarin zamemin tamkar ita."

"Na yi miki wannan alk'awari Mama."

"Nagode, Allah ya yi miki albarka."

"Amin."

Ta amsa cikin sakin kukan da ta ke cijewa kada ya kufce. Rungumeta Mama ta yi tana sauke ajiyar zuciya saboda sunar Allah As-saburu da ta soma ambata cikin ranta ya taima wurin sanya mata jarumtar da batayi zaton samunsa ba.

*Duk wanda ya rik'e Allah tabbas shi kuwa zai ishe masa ga duk kan damuwarsa, mu daure muna mik'a lamuranmu ga Ubangiji mabud'in taskan Alkhairori. Allah ya yayemana dukkan damuwarmu alfamann Manzon Allah S.A.W*

*TALLA.*

*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*

Sabulu (molato and black soap) Scrub Face cream Oil Body lotion Shower gel Kulachan Humra (White and black) Turaren tsugunon Turaren kaya Turaren wuta na d'aki Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)

*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.* [10/28, 1:52 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona) By Mrsjmoon

E.W.F.

https://youtu.be/v9iNYDvS8JM

Pls kiyimin subcribe a YouTube channel d'ina.🖕

PAGE 16.

"Muyi hak'uri dai Fanta kuka baya maganin damuwa sai ma k'ara wa, ki tuna abinda kika sanarmin yanzu, shin me yasa zaki maida hannun agogo baya?"

"Mama Deejah ce kwance kamar gawa? Jiya fa muna tare lafiya lau, shi ne abin da ya bijiromin na kasa daurewa."

"To ya zamuyi da k'addarar Allah? Sai hak'uri kawai tare da mik'a lamarin garesa domin samun d'aukinsa ba dan iyawarmu ba."

"Innalillahi wa Inna ilaihin raji'un."

Fanta ta ambata tare da sake k'amk'ame Mama, lamarin da yaso karyamata zuciya amma sai ta soma addu'a cikin fitar sauti a hankali.

"To zaki wuce gida kuwa in har kuka zakizo kina sanya mutane."

"Uncle na kasa daurewa ne."

"Ki cigaba da ambatar addu'ar da kika sanarwa da Mama har ta sami jarumta."

Motsa kai ta yi tare da janye jikinta ta koma gefen Deejah ta wurin kanta ta zauna bakinta na motsi alamun addu'ar ta ke yi hannunta na yawo saman sumar Deejah.

*** "Yaya ka kwatantamin gidansu sai inje na dubo maka ita."

"K'anwata kinfi kowa sanin tsaron Hajiya."

"Zance mata zani gidan Aunty Zainab ce."

"Tsakanin gidan su Deejah da gidan Zainab da tazara mai nisa kafin kije ki dawo na tabbata Hajiya zata kira taji idan kinje kuma in kika soma zuwa gidan Zainab kina fita zata kira Hajiya ta sanar mata da kin fito kinga kenan lamarin ba mai sauki ba ne."

"Yaya yanzu ya za'ayi?"

"Bari ruwan ya kare sai in lallab'a na tafi da kaina."

"Bazaka iya ba Yaya, jikinka bai warke ba, kallifa yarda kake magana kana hutawa."

"Buguwar da na yi a hakarkari na ne keyimin zafi amma banjin ciwon komi bayan shi."

"Ka dai samo wani dibaran domin kaima na tabbata Hajiya baza ta barka ka fita a haka ba."

"Bari in sake kiran K'awarta ko zanyi dacen ta d'auka tunda ita nata wayar a kashe ya ke."

"Ok jaraba mugani "

Cikin jan tsaki ya jefar da wayar gefe.

"Bata dauka ba ko?"

"Ina cikin damuwa wallahi, narasa wanda zan kira na sami labarin Khadija."

"Mijin Aunty Zainab mana tunda kace, ka ganinsu tare."

"Kuma hakan ya kamata, nagode k'anwata."

Kiran number ya yi aka d'auka bayan gaisuwa sai ya rasa abinda zaice masa.

"Ya dai Aliyu?"

"Yallab'ai dama zance ya wurin su d'iyarka?"

"Oh Khadija?"

"Eh."

"Wallahi yanzu Baba ke sanarmin Mamanta bata da lafiya tana Asibiti."

"Ya rabbi, shiya ban samun wayarta kenan?"

"Eh zaiyiwu hakan ne."

"Allah yabata lafiya."

"Amin."

"Wani Asibiti ne?"

"Ban sani ba dan nima yanzu zan tafi na d'auki Baba mu tafi amma in na isa zan kiraka."

"To nahode."

Ok bakomi."

Sauke wayar ya yi tare da lumshe ido.

"Itama bata da lafiya ne ?"

"Mamanta ne a ka kwantar."

"Ayya Allah ya sa kaffara ce."

"Amin."

"Amma Yaya kana son janyowa kanka ruwa fa."

"Kinga kada ki sake maganar sokuwar nan ya hadamu."

"To ai bance komi ba "

"Gara dai haka."

"Salma fito hakanan ki barsa ya huta."

"To Hajiya."

Gyad'a mata kai ya yi ta fice tana murmushi.

*** Habibu ya cika fam da takaicin Baba akan zagin dake da durawa Uncle duk kuwa da bai sanshi ba amma ji yake tamkar d'an uwansa ake zagi ga shi Baba Umaru na ji amma bai ce kanzil ba hasalima wani littafin addu'o'i ya bud'e yana bita. Zuwa can Habibu ya ce "Haba Malam Hadi kana Malami amma ake jin wannan ashariyar abakinka dan kawai makwafci ya nuna kulawa ga iyalinka abinda na yi imani kai bazaka iya yimusu ba."

"Kai Habibu ban son rashin ta ido kaji ko? Shin kasan muhinmancin iyali kuwa?"

"A'a sai ka koyar da ni irin yarda ka san naka."

"Akul Habibu, kada na kuma jin bakinka."

"To Baba."

"Baba wallahi mutumin nan ya rainani, dan Allah kayi masa iyaka da iyalina, kwata-kwata ban son su sake mu'amala da shi domin ina jin ana maganar arzikinsa bana halas ba ce wata kilama so ya ke ya shanyemin jininsu, ya kaini ya baro."

"A'uzubillahi! Me ya kawo wannan maganar kuma Hadi?"

"Baba wallahi lamarin ne ya kasa kwantamin dubi da yarda yake kashewa Uwani kud'i duba fa ka ga wayar dubbunnan kud'ad'e da ya mallaka mata tamkar bai san zafin nemansu ba."

Mik'a hannu Baba Umaru ya yi ya amsa wayar ya jefa a aljihu batare da ya duba ba.

Hararan gefen ido Baba ya maka masa domin yaso saida wayarce shi yasa ya d'auke amma azal ya sanyashi yin maganarta ta zamo haramiyarsa.

"Hadi duk yarda makwafci ya ce shi d'in d'an uwa ne saboda shaidansa kad'ai zai iya kaika gidan Aljanna, ina tunasar da kai abinda ka sani kake takewa shi ne ka kyautatawa makwafci zato tare da rufa masa asiri musanman ga wanda ya bada kula ga iyalinka."

"To Baba amma ai musulinci bai bashi damar shigamin gida lokacin da bana nan ba, ko dan gudun gudun zargin mutane."

"Abinda na ke tunasar da kai kenan cewa ka kyautata masa zato kuma zanyiwa tufka hanci akan irin haka bazai sake faruwa ba tunda ya wuce iyaka, shiga gida yana baligi."

"Yawwa Baba kaima dai kagani."

"Zan bincika lamarin tundaga farko kafin in yanke hukunci."

"Ai wallahi ko da ka ja masa kunni sai na makashi a kotu."

"Kotu!?"

Habibu ya amtaba batare da ya sani ba.

"Eh can zan kaishi kuma sai ya gane shayi ruwa ne, dani yake zancen."

"Wato in na fahinceka dama can kuna da jika'kkiya kenan?"

Baba Umaru ya furta cikin shakewar murya domin ya soma gajiya da rashin kangadon Baba.

"A'a kawai shiga lamarin iyalinsa da ya yi na ke son ayi masa iyaka da su."

"To ba amfanin sakani cikin lamarin da kayi kenan?"

"Da shi mana Baba, kawai rubdugu zanyi masa ya gane ba da wasa na ke yi ba."

"Hadi in kanayiwa Allah da mahaifanka ka janye maganar kai makwafcinka kotu."

"Baba ka...

"In har na isa da in sanya baki cikin lamarin to ka janye."

"Shi kenan amma wallahi sai ya fita harkan iyalina."

"Naji zai fita."

Daga haka shiru ya ziyarci motar, Habibu ya ja tsaki kad'an cikin zabgowa Baba harara ta mirror, dak'uwa Baba ya auno masa batare da ya bari Baba Umaru ya gani ba, wani hararan Habibu ta bunko masa tare da cije lips.

"Kayi koyin halin girma tamkar mahaifinka."

"Kafi kowa sanin hakinsa kaf na kafe saidai kayiwa kanka wa'azin kula da iyali."

"Baba yaushe Habibu ya koma mara kunya haka?"

"Habibu ban son na sake jin amonka."

"To Baba."

Ga masifa a bakin Baba amma Baba Umaru ya katange damar amayosu saboda bakin rijiya ba wurin wasan makaho ba ne.

Koda suka isa Asibitin Uncle ya koma gida Baba ya yi ta hura hanci Baba domin bai so hakan ba, Baba Umaru dai na kallonsa cikin nazari ya yin da Habibu ke ta zabga masa harara cike da takaicin hanashi maganar da Baba ya yi da sai ya wanke Baba tas da ruwan kalamai.

Abin mamaki ko sannu da jiki Baba baiyiwa Mama ba da ya iso ya sameta cikin k'oshin lafiya sama da d'azun da ya barta cikin godiyan Allah, balle kuma ya yiwa Deejah da ke kwance tamkar gawa. Halin ko in kulan da ya nuna ya tab'a zuciyar Mama amma ganin su Baba Umaru sai ta kauda duk bacin ranta saboda matsayin su na da banne.

Addu'a Baba Umaru ya ke ta tofawa Deejah yana rik'e da hannunta na dama cike da tarin damuwa zuwa can ya juyo ya tambayi Mama yarda lamarin ya kasance.

Abinda Likitoci suka sanar mata ta fad'a masa ya jinjina kai ya sake tambayarta yarda ita kuma ciwonta ya sameta nanma abinda ta sani da wanda Uncle ya bata labari ta fad'a masa tare da taimakon Malamin nan duk ta sanar da shi sai dai bata tona tijarar da Baba ya yi ba.

"Alhamdulillah zanje gidan Malamin na yi masa godiya domin ya taimakeni wurin bawa amanata kariya, Allah ya biyashi da gidan Aljanna."

"Amin ya rabbi."

Habibu ya amsa da sauri yana aunawa Baba wani kallo.

K'ara hade rai Baba ya yi tamkar wanda aka aikowa da sak'on mutuwa.

Kallonsa Mama ta yi ta ce "Kaima Malam ka je ka gode masa domin ya taimakemu iya taimako."

"Zanje, ko ba Malam Isuhu mai gudun duniya ba?."

"Eh, haka fa sunarsa ya ke."

"Au a shema d'ana ne, kai masha Allah, ai ya yo gadon sanin lak'anin korar shed'anu wurin mahaifinsa Malam Hassan, madallah da d'an arziki irin albarka."

"Baba ka sanshi kenan?"

"Eh na sanshi Hurera, mahaifinsa mutumina ne kafin Allah ya yi masa rasuwa."

"Allah sarki gaskiya ya zamo Malami na gari."

Da sauri Baba ya kalleta ta sauke masa murmushi ya kauda kai yana tsinewa Uncle da Malam Isuhu cikin ransa.

Ni zan koma na aiko Habibu da sak'o wanda idan ta farka shi zata soma sha, insha Allah jikinta zai dawo dai-dai batare da firgicin komi ba balle kufcewar tunani."

"To Baba, nagode."

"Ke ma ki sha idan ya kawo sannan Hajiya zata zo bayan sallar magriba ta kwana da ku saboda kema ba lafiyar ce ta wadaceki ba."

"To Baba, Allah ya k'ara girma."

"Amin, Allah yasa kaffara ce."

"Amin."

"Hadi zamu barka a nan ne?"

"Eh Baba."

"To ayi ta hak'uri kada ka tada zancen nan a Asibiti saboda jama'a, idan sun dawo gida zanzo da kaina mu zauna kuma ka tabbatar ka bawa Malam Isuhu hadin kai anyiwa gidan nan addu'o'in da ya kamata dan na fahimce akwai damuwa cikinsa."

"To, za'ayi."

"Madallah, nabarku lafiya."

Suka fice da Habibu Baba ya rakasu da mugun kallo tamkar zai cinyesu da idanu.

"Malam uban nawa kake harara?"

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull