Kenza eBookz

Damuwata complete novel - Chapter 17

Damuwata complete novel - Chapter 17

Damuwata complete novel Chapter 17: Damuwata complete novel Chapter 17. "Allah ya biyaki da khairan Hurera da kina nan sai abinda na so ci zaki dafamin,…

3,303 words

"Allah ya biyaki da khairan Hurera da kina nan sai abinda na so ci zaki dafamin, ina ci ina tura mikin masifa amma bazaki d'aga kai ba saboda sanin darajar aure, shi yasa duk rintsi ba zan rabu da ke ba sai na binne gawarki da hannayena biyu kafin nan tuni Uwani ta dad'e da zama yar gari a barzahu domin wannan sumar batashi zatayi ba."

Shi kad'ai ya yi ta zuba surutu har ya samu ya gama soya kwai tare dadafa ruwan zafi ya had'a tea mai kauri ya tafi ya kulle k'ofar gida ya dawo ya zauna saman buzunsa ya korawa hakali kwance.

"A she ban manta rayuwar almajiranci ba inda muke satar kwan kajin Malam dana makwafta mu tafi bayan gari mu d'iba girki mai rai da lafiya. Ya Allah ka yafe mana laifukanmu domin munyi cuta iya cuta na cinyewa kaji kwai da zabbi."

Sai ya kwashe da dariya. Yana kammala shan tea ya kulle gidan ya nufo gidansa cike da tarin masifa, duk wanda ya gaisar da shi hannu kawai ya ke d'aga masa sai in anyi masa sallama ne ke amsawa saboda sanin muhimmancinta. Kafin ya isa gida Uncle ya kirasa ya sanar masa da farfad'owar Deejah wani burki ya ja ya yi dif, Uncle ganin kamar da matsalar network sakamakon jin shiru ba amsa sai ya datse kiran da nufin anjima zai sake kiransa.

"Wanna d'iya anyi mai taurin ran tsiya, bari in hanzarta zuwa Asibitin kada Hurera ta mannamin hauka ta ce ina farin ciki da ciwon ne dan na hango abin da ta ke burin ambata kenan gaban jama'a."

Ya tari mai Napep tare da sanar masa da inda zaije. Ana Napep d'in sai tsaki ya ke ja.

*** Aliyu.

"Aliyu ka natsu ka san inda kanka ke ciwo."

"To Hajiya na ce zan duba buk'tarki."

"Bana son ka duba Aliyu, burina ka tafi zance gidansu saboda ita mai sonka ne da gaskiya domin da bakinta ta furta tana son ka aureta."

"Hajiya ina da fa wanda na ke so."

"Wacece ita?"

"Khadija."

"Wacce Khadija?"

"Wacce mukayi walimar haddar Qur'ani da ita."

"Oh jikan Alhaji Umaru surikin Zainab?"

"Au Hajiya a she kin san Khadija na da alak'a da su Yaya Habibu?"

"Sosai kuwa domin lamarin aurensa da Mamanta akayi mace mai karamci."

"Shi kenan fad'uwa tazo dai-dai da zama."

"A'a bata zo ba saboda gida bai k'oshi ba'a kai dawa ba sannan ka tuna Amira k'anwar Zainab ce ta jini dan haka batun Khadija babu shi kaji dai na gaya maka."

"Hajiya dan Allah ki...

"Zancen kake so Aliyu."

Tana ambatar haka ta bar mishi wurin.

"Innalillahi wa Inna ilaihin raji'un, wallahi ina son Khadija DAMUWATA duk na mallaki Khadija ce, ya Allah ka kawomin mafita cikin sauk'i."

"Amin Yaya."

"Salma kina jinmu da Hajiya ko?"

"Eh Yaya amma ina baka shawara da ka nuna tamkar ka amince amma a wurin Amira ka sanar mata da gaskiyan zuciyarka insha Allah zata fahimta tunda nasan tasha jin labarin illar auren mijin da bai son mace."

"Nagode k'anwata."

"Bakomi damuwarka tawa ce Yaya."

"Anjima zan lek'a Asibiti."

"Zan bika."

"Islamiya zaki sarkin yawo."

"Kai Yaya ziyarar maralafiya zani ba yawo ba."

"Baza ki je ba."

"To shi kenan ranar alhamis na je."

"Yawwa na amince da wannan kam."

"Yaya Deejah na da kyau tamkar shuwa ko 'yar k'asar turawa."

"Tubarkallah Masha Allah."

Dariya Salma ta kyal-kyale da shi, ya murmusa tare da ficewa. Gyara d'akin ta soma yi tana 'yan wak'e-wak'enta cike da nishad'i.

*** Hinde wai lafiya kuwa su Kamalu shiru basu dawo ba?"

"Nima zancen da zanyi miki kenan Yaya."

"Kada fa mafarkina na jiya ya tabbata."

"Na me fa?"

"Wai gini ya fad'o ya halaka su Kamalu, aka kawo mana su cikin jini tare da rakiyar 'yan sanda."

"Innalillahi, aiko da wuya ba an kamasu ba ne domin tun daren jiya gabana ke fad'uwa, wallahi cike na ke da fargaba kada asirinmu ya tonu abin da bamu samuba ya tabbata wato amsar takardan saki.

"Haba Hinde wai me yasa duk zantukanki ba na arziki ne ciki? To wallahi mugun bakinki ya k'are a kanki."

"Yaya wallahi ina jiyowa a jikina ba nasara a wannan tafiyar nasu."

"Bazan gani ba, mai bakin baki kawai."

"To shi kenan Yaya na yi shiru."

"Shi dai yafi."

Suka cigaba da aiyukansu na safe duk jikinsu a sanyaye.

"Hinde wai in tambayeki, da wa Kamalu suka tafi?"

"Kinsan Anas bai da lafiya shi ne K'asimu ya ce zai bishi sai shima Garba ya ce zaije naso hanashi amma ya kafe sai ya je, Kamalu ya cemin zai d'auki Isyaku Jagwa tunda yana da motar d'aukan kayan sai su loda a ciki."

Wani ihu Asabe ta kwalla wanda saida Hinde ta zabura.

Wani mugun ashariya ta watsowa Hinde tare ta cukumeta, suka soka kokuwa fad'i Asabe keyi "Kin kasheni da raina Hinde, duka 'ya'yana kika tura yo sata, wallahi mai rabani da ke sai Allah."

"Usaman (k'anin Baba) da matarsa suka zo rabo. Suka saki juna suna huci tamkar zakaru.

"Me ye haka kukeyi dan Allah, haba Innar Kamalu da Innar Anas, kunfa girma, kuna da surukai amma baku daina d'abi'an yara ba, to wallahi wannan abin Yaya kuke zubdawa da mutunci ba kowa ba a matsayinsa na babban Malami a garin nan."

"Usman wallahi wani abu ya sami 'ya'yana sai naga bayan Hinde koda zan tafi tsirara ne."

"Zakuwa ki tafi tsirara domin inda kika kwana na wuce da tafiya mai nisa"

"Haka kika ce?"

"Hak'k'un domin nasan da b'acin ranar nan na turasu kinga na rama lak'awa Kabiru satan kwan kajinki da kikayi shekaru goma da ya wuce inda kika janyo Malam ya illata masa kunni d'aya ya zamo baijin magana da shi."

"Tana nan dama kika b'ullo min Hinde?"

"Eh, dan ki sani yanzu raina tangaran."

Wani duka Asabe ta kaiwa bakin Hinde ta ke leb'enta ya fashe. Cikin gigita ta rarimi murfin tukunya ta wurgo mata ya sauka a gyeyar Usman wanda ya nemi janye Asabe. Ihu ya kwalla ya zube k'asa dafe da wurin, kuru-ruwa Matar ta sanya tayo kan Hinde suka rintsab'e da dambe.

"Innarmu! Ga 'yan sanda nan cikin mota tare da K'asimu fuskanci duk ta kumbura."

Atiku yaron Hinde ya shigo a guje yana fad'a.

Tamkar walk'iya haka Usman da Matarsa Mairo suka b'ace zuwa sashinsu ya yin da Hinde ta ruga d'akinta Asabe ta biyota ganin haka ta tureta da k'arfi ta fad'i k'asa ta kulle k'ofar da sakata.

Asabe ta mik'e cikin zundumawa Hinde zagi, ta nufi kofarta sai dai tana saka k'afarta a d'akin ta tsinkayi muryan K'asimu na cewa "Ga d'aya can."

Da sauri ta waiwayo ta yi arba da macen 'yar sanda, K'asimu d'aure cikin ankwa.

Cikin zafin nama tayo kan 'yar sandan ta cukumeta da dambe bisa tsautsayi tAsabe ta ture 'yar sandan da k'arfi sai ko ta zame ta yi cikin rijiya wanda ke tsakar gidan.

Sautin ihunta tare da ba fad'awarta ya janyo hankalin 'yan sandan da ke waje suka shigo a guje, Hinde da su Usman suma suka fito suna rafka salati jin abin da K'asimu ke ambata cewa Innarshi ta jefo 'yar sanda a rijiya.

*TALLA.*

*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*

Sabulu (molato and black soap) Scrub Face cream Oil Body lotion Shower gel Kulachan Humra (White and black) Turaren tsugunon Turaren kaya Turaren wuta na d'aki Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)

*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.* [11/1, 9:32 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona) By Mrsjmoon

E.W.F.

https://youtu.be/v9iNYDvS8JM

Pls 'yan uwa ku dannamin subcribe a YouTube d'ina.

Page 19.

Sadda na farka jikina ya yi k'arfi sosai sai dai yarda na hango idanun Mama sai na saka kuka dan sun kumbura suntum, damuwa ne kwance saman fuskanta abin da ya taimaka wurin karyarmin da zuciya. Jin kukana Hajiya Inna ta somamin fad'a, tsit na yi ina sauraren sababinta mai kama da na Baba saidai ita nata akan gaskiya ne sab'anin na Baba.

"Inna kiyi hak'uri."

"Bazanyi ba Hurera, shin abin da ya kamata ta yi kenan ko godiya ga Allah?"

"Hajiya Inna to na yi shiru dama Mama ce na hango cikin damuwa sai kuka yazomin."

"Duk shiri-ritanku iri d'aya, abu ba abu ba kuyi ta b'aran baki tamkar saunoni."

Murmushi na yi ta dunguremin kai, na kama yatsar zan tura a baki ta fizge tana dariya

"Mamana."

Na kira sunar cikin rauni ta taho a hankali ta kama hannuna kafin ta yi magana aka turo k'ofar Uncle ne da su Fanta suka shiga cike da farin ciki dan ko samun damar gaisar su Mama basuyi ba suka nufoni kowa na son isa inda ni ke. Hak'ik'a farin cikin da suka nuna na ganin samuwar lafiyana yafi gaban kwatance Mama sai sanya musu albarka ta ke yi bakinta har kunne Hajiya Inna kam fatar samun mazaje na gari ta yi musu, shi kuwa Uncle addu'ar da sukeyi masa na daban ne.

Sun sakani a tsakiya sai tsokanata sukeyi kamar yarda suka saba, duk rashin son maganarta yau kam na biye musu sai doka murmushi na ke yi cikin bawa kowacce amsa a hankali saboda yanayin k'arfiin jikina, lamarin da ya sake jefa Mama cikin farin ciki kenan domin ina hango motsa kai da ta ke yi cike da nishad'i.

Uncle na tsaye gefe daga bakin k'ofa Dr. Jalal na yi masa k'arin bayani game da lafiyar Deejah. Saurarensa kawai ya keyi ba tare da yana fahimtarsa ba saboda hankalinsa na kan masoyiyarsa shima sai murmushin ya ke dokawa yana jin natsuwa na daban na kuma nashe ruhinsa.

'Ina son yariyarnan matuk'ar so, ya Allah ka mallamin ita idan har hakan alkhairi ne.'

"Yaya inaga ka taho muje office zakafi fahimtar zantukana."

Kallon Dr. Jalal ya yi sai kunya ta kamashi ya wuce gaba da sauri Dr. Jalal ya sanya dariya mara sauti ya nufi wurin Deejah ya yi k'asa da murya ya ce "Ki rik'esa amana wallahi yana sonki da gaskiya."

Juya kai gefe na yi saboda zancen ya bani kunya.

"Dan Allah kubarta ta huta haka nan aminanta."

Dr. Jalal ya furta cikin sigan wasa. Dariya suka sanya ya fice yana murmushi bayan ya saukewa Fanta kallo na daban wanda faruwar hakan yasa ta rakashi da ido baki bud'e.

"Da magana a cikin kallon nan kenan ko sister."

Da sauri ta maida dubanta kan Safina.

"Eh da magana kam domin na hango k'auna a cikinsa."

"Kinga sister bana son kwashe-kwashe."

"Likitan ne kwashe-kwashe?"

"Ban sani ba."

"Aikam dole ki sani K'awata."

Na ambata cikin dariya ganin yarda ta tsare gira.

"Deejah har da ke ko?"

"A'a fa kawai dai naga ya kamata ki sani ne duk da ni fadar Abdul Abbas na ke."

Mik'ewa ta yi Bintu ta janyo hannunta ta koma zaune.

"Kinga idan kina sonshi ki bada kai muna bayanki saboda wannan gayen samunsa sai mai sa'a."

"Ban son shi, shi kenan zaku bar kunnuwana su huta?"

"Eh amma sai na sanar da Uncle kin kamu da son k'aninsa."

"Wa kenan?"

"Sa'ad."

Kama baki ta yi cikin ambatar Innalillahi.

Aikam na fashe da dariya mai sauti, su Bintu na tayani.

"Kinga k'awata ki daina dariyar nan domin baiyi miki kyau ba, gara kiyi murmushin da kika saba."

"Alamun samun natsuwar ruhi kenan Fanta "

Beebah ta ambata hankalinta na kan wayarta domin ko murmushi batayi ba tun soma hirarmu.

"Wai ita nan zata layance ne ta kori zancen Sa'ad."

Fad'in Safina ckin dariya.

"Ai sai kiyi ta yi tunda kin sami karatun sallah."

"Kinga malama bamu san gulma, ko ba maganarsa kika ishemu da shi jiya ba, to zamuce Uncle ya had'a zumunci, hakan ya yi miki ko?"

Cewar Fiddausi.

"Wallahi zan kai k'ararku wurin Uncle in baku daina yimin sharri ba."

"Ya isa haka, kun cika mana kunne da hayaniya alhalin ance mu bar Deejah ta huta."

"K'yalesu Sister Beebah, lamarin na bani nishad'i ainun."

"To nikam sun dameni."

"Munyi shiru Babban Yaya."

Fiddausi ta ambata cikin murgud'a baki. Beebah ta kawoma bakin duka ta sunkuya, suka sanya dariya.

Shigowar Baba yasa duk suka natsu saboda sun sanshi yanzu sai ya korasu waje. Suna gaisar da shi ko kallo basu ishe shi ba, ya buga babban rigarsa ya nuna Mama da yatsa cikin tijararsa na fama ya ce "Hurera in na isa da ke ki tashi yanzu mu tafi gida tunda kun sami lafiya kuma in Allah ya so ba mai sake zuwa wannan matsiyacin asibitin ko da ciwon mutuwa ne ya kamaku gara ku mace ina kallonku da dai zuwa shegen Asubiti nan mai kama da na yahudawa."

"To ta Allah ba takaba ciwo da mutuwa na kan kowa kuma Asibitina ba matsiyaci ba ne balle ya zama na kafurci saidai kai ne matsiyacin, fitinannen mutum kawai, Malamin bai kaiba, wanda baisan darajar iyalinsa ba, zalaman kawai ya ajiye, mai fuska biyu kawai. Wallahi ba dan Yaya Muhseen ba da banga wanda ya isa yasa ka sake shigomin Asibiti ba."

"Jalal ban isa da kai ba ko? Shin ba na ce kada ka sake magana ba?"

"Kayi hak'uri Yaya amma wallahi wannan makwafcin naka ba dan arziki ba ne saboda na gano yana da sa hannun a ciwon matarsa har da 'yarsa, shi ne ke son kashesu lokacinsu baiyi ba."

"K'alu innalillahi wa Inna ilaihin raji'un! Ni Malam Hadi zakayiwa kazafi Likitan fanko? To wallahi bani yarda sai na d'au mataki ba dai tak'amarka jama'ar da sukeyima tururuwa ba to sai ka koma kare bai...

"Dan soyayyarka da Ma'aikin Allah Baba kada tayi masa baki, shi d'in mai taimakon al'umma ne."

Na furta cikin kuka. Kallona ya yi sai naga ya tako ya iso daf da ni cikin cewa "Uwani ke ce haka cikin k'oshin lafiya, murya ras?"

"Eh, Baba."

"To madallah, sannu fa, kin tsallake rijiya da baya domin irin wannan ba'a cika tashi da lafiya ras irin haka ba."

"Ita dai sumul ta tashi soi fatan samun kwarin jiki wanda shima zuwa anjima zata koma tamkar taba tab'a kwanciya ciwo ba."

"To Hurera da fatan kema kin gama warwarewa?"

"Alhamdulillah ala kulli halin."

"Da kyau."

Kowa sai kallon Baba ya keyi tamkar ba shi ne ke fesawa Doctor Jalal ruwan bala'i ba, ya koma kamar wanda junnu suka shafa yana masifa lokaci d'aya ya koma maganar arziki.

"Baba kayi hak'uri yarinta ce ke damun Dr. Jalal kuma bai san alak'arka marasa lafiyan ba sai yanzu amma da duk haka bata faru ba, dan Allah ya ci albarkacina ka mance lamarin ya zamo tamkar bai tab'a faruwa ba."

Uncle ya katse shirun da rarrashin Baba.

"Alhaji Muhseen ban sanka da k'arya ba amma sai gashi yau kana yimin ba kunya balle tsoron gamuwarka da mahaliccinka, yaron nan ne baisan alak'ata sa iyalina? Sai dai ka fad'awa yaron goye amma ba Abdul Hadi ba mai hak'ora talatin da biyu cik."

Wani kunya ne ya kama Uncle ganin yarda kallo ya dawo kansa sai kawai ya juya ya fice batare da ya sake furta kalma ba.

"Amma kai ba mutumin arziki ba ne, to ka sani hukuma ce zata rabani da kai ba dai haka ka ambata cewa kare ba zan sake gani a cikin Asibitina ba, ni kuma zan nuna maka ni d'in jinin malamai ne kuma wanzamai masu tutuniya da yardan Allah ba bokanci da buge-buge k'asa ba, ni Abdul Jalal sai na baka mamakin da duk wani bil'adam bai tab'a baka shi ba tsawon rayuwarka, mu zuba mugani shege ka fasa."

Dr. Jalal na gama ambatar haka ya fice a fusace.

D'akin ya Kuma yin tsit baka jin motsin komi sai sautin kukana saboda lamarin ya b'atamin rai ainun.

"Ka kyauta Hadi sai ka tafi tunda abinda kazoyi ka gama."

Kallon Hajiya Inna ya yi wacce ke zaune gefe d'aya a saman sallaya, sai ga Baba ya sunkuyar da kai domin sam bai lura da ita ba saida ta yi magana.

"Ayi hak'uri Hajiya wallahi rai na ne ya b'aci na ganin da girmana da komi masu gad'i sun hanani shigowa duba iyalina har saida na kira Alhaji Muhseen sannan suka barni na shigo sai ga wannan yaron ya tareni da zantukan banza har da zagi tare da mannamin k'azafin iska da wofi."

"Ko me ya yi maka kaika siyo da kudinka Hadi."

"To Hajiya ayi hak'uri dai."

"Ni bakayimin laifi ba amma dai zan baka shawara agame da wannan halin naka wallahi ka kiyayi furta kalamai marasa dad'i a duk yarda suka zo maka domin in kasan wani baka san wani ba sannan ik'irarinka na alkaba'i ka bari ko masifun da kake ambatawa mutane ya koma kanka."

"Insha Allah zan kiyaye."

"Allah yasa mudace."

"Amin."

"Takwarana daina kukan nan kada kanki ya yi ciwo, kinba ba gama samuwa kikayi ba."

Sakkowa na yi zuwa gaban Hajiya Inna na russuna kafin in furta kalma ta janyoni zuwa jikinta ta kai bakinta kunnina tana mai cewa "Kada ki furta komi ni ne maganin Babanki ki zuba ido kiyi kallo domin na fahimci shi d'in zuma ne shansa saida wuta."

Motsa kai na yi, ta d'ago fuskata ta soma sharemin hawaye wanda tana sharewa wasu na biyowa.

Uncle ne ya dawo ya sanar da ansallameni, su Beebah suka soma tattara kayanmu, Baba na tsaye yana kallosu takaicin Dr. Jalal da Hajiya Inna cike da ransa domin nasihar da Hajiya Inna ta yi masa ya d'aukeshi cin fuska ne ba komi ba, kawai ya bada kai ne saboda girmanta da ya ke gani.

Uncle na kalla na langab'e kai ya kirani da hannu batare da kowa ya lura ba, ya fice waje na rufa masa baya ina jin kaina tamkar zai rabe biyu.

"Khadija ina rokonki da kizo muje ki bawa Dr. Jalal hak'uri saboda in har ya sakawa Baba ido lamarin bazaiyi kyau ba dan nasan wayeshi akan 'yancinsa sannan yana da k'anin Baba wanda in ya kai sunar Baba wurinsa abin sai addu'a kawai zance."

"Dama abinda na ke son in aikata kenan Uncle, kaini na rok'eshi domin bana son Baba ya sami matsala ta sanadin zuwarmu Asibitin nan."

"Ok kinyi tunani mai kyau Iyalina."

Kauda fuska na yi saboda bana cikin good mood d'in da zanyi masa murmushi wanda na fahimci shi ya ke son gani.

Yana gaba ina binsa a hankali saboda jiri da na ke gani, muna shiga office d'in na jingina da bango sakamakon jin da na yi zan fad'i, ido na ke son bud'ewa amma sai naji sunyi min nauyi sai na hak'ura na sake rintsesu, na mik'o hannu naji an kama, Dr. Jalal na ambatar sunana a hankali saidai na kasa amsawa saboda nauyin da harshena ya yi tamkar yarda idanuna sukayi. Daga nan ban sake sanin ya akayi ba nadai farka ne na ganni kwance saman gado, d'akin ba haske sosai amma na hango Hajiya Inna zaune saman sallaya. Salati na soma yi da k'arfi na jiyo muryan Mama na kiran sunana sai dai a dushe ya ke muryan nata wanda ya tabbatarmin da kuka ne ya haifar da hakan.

"Sannu Uwata, Allah dai yasa kafface, sannu kinji, jarabawar rayuwa ce ta zo mana da sauyi mai firgitarwa."

"Yawwa Mamana, zansha ruwa."

Hajiya Inna ce ta kamani na tashi zaune, Mama ta bani ruwa nasha mai yawa na koma na kwanta ina ambaton sunar Allah Al-hamidu a cikin raina domin shi ne kad'ai ya can-canci a gode masa a dukkan halin da mumuni ya riski kansa ciki.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull