Kenza eBookz

Damuwata complete novel - Chapter 19

Damuwata complete novel - Chapter 19

Damuwata complete novel Chapter 19: Damuwata complete novel Chapter 19. "Hajiya Inna a yi hak'uri idan na k'ara samun sauk'i zanzo ganin Baby musanman…

3,320 words

"Hajiya Inna a yi hak'uri idan na k'ara samun sauk'i zanzo ganin Baby musanman tabbas na san ban kyautaba, Ina neman affuwan Matar babban mutum mai halin girma."

"Allah ya yi miki albarka Takwarata."

"Amin."

Muka amsa tare da Aliyu wanda ya koma gefe yana saurarenmu tunda ya gama gaisar da Inna.

"Bari in lek'a gida Takwara."

"To Inna sai kin dawo."

"Aha, ke kuma idan kinga dama ki zauna da ita kafin wani cikin ni da Hurera ya dawo."

"Agaskiya ba zan zauna ba saboda jego na keyi nadai zo dubata kada ya zamemin abin magana wanda duk da hakan gashinan ban tsira ba saida akayimin luguden labba."

"Matar Kawu ki iya bakinki fa, Inna ba sa'ar yinki ba ce dan haka ki tauna kalaminki kafin ki furta in har kina son gamawa lafiya."

"Idan ank'i yin hakan fa?"

Bud'e baki na yi zan bata amsa Inna ta d'agamin hannu tare da komawa ta zauna.

"Zaki iya tafiya tunda kin gaisar da itan."

"Ok na barku lafiya, Allah ya k'ara affuwa."

Banza mukayi da ita ta fice abinta ba damuwar komi.

"Hajiya dan girman Allah kiyi hak'uri, halin Zainab sai ita sam bata san ya kamata ba ko a family haka ake fama da ita bata da kunyar gayawa babba duk kalamin da ya fito bakinta."

"Kada ka damu Aliyu, wannan ba sabon abu ba ne, Allah dai ya ganar da ita."

"Amin."

Ya matso daf da gadon ya ce min "Na yi kewarki, Allah yasa kaffara ce."

"Amin."

Kud'i mai yawa ya ciro yan dari bibiyu sabbi fil ya ajimin saman cinya sannan ya fice bayan ya sake bawa Hajiya Inna hak'uri.

"Me ke tsakaninku da shi Takwarata?"

Shiru na yi tare da kulle fuska da tafukan hannayena.

"Oh na fahimta, to ba damuwa za'a kuma yayibo irin rashin d'a'a ba."

"Hajiya Inna me ya yi?"

"Jinin Zainab basu k'ara shigomin ahali da yardan Allah dan haka tun kafin ki haukace a shiriritan so dinan ki koreshi."

Idanu na zare ta zabgomin harara.

"Inna wai ya suke da matar Kawu?"

"Abokik wasanta ne domin da babanshi da Mamanta uwarsu d'aya ubansu d'aya kuma yayarshi wanda suke uba d'aya abokin Habibu ne, agidansu Habibu ya had'u da ita dan Mamanshi ita ta rik'eta har zuwa aurenta."

"Ikon Allah amma duk shekarun da muka kwashe da Aliyu ban tab'a sanin hakan ba."

"To ina kike zuwa balle ki had'u da 'yan uwansa sannan shima Aliyun bai zuwa gidan Habibu sai hab'o."

Shiru na yi ina nazarin wannan lamari, ta ke naji duk damuwar da na ke ciki ya koma ba komi ba saboda tuno mugun halin Zainab da tasha gwadamin wanda nashajin Hajiya Inna na cewa d'aukosa ta yi wurin uwar goyonta.

'Wato mahaifiyar Aliyu bata da kirki kenan? Aikam na hak'ura da kai domin ina burin aure na ke inda Zan sami kwanciyar hankali ba kishiyarta ba.'

"Ban son shiga dogon tunani saboda lalurarki."

Na tsinkayi muryan Hajiya Inna daf da ni. Kallonta na yi har lokacin bata cikin walwala.

"Kiyi hak'uri Inna."

"Ya zamamin dole Khadijatu sai dai DAMUWATA shi ne na yarda surikata gudan jinina d'aya tilo zata zamemin abokiyar gaba."

"Ban gane ba Inna? Kina nufin su Mama Indo ba surukanki ba ne?"

"Surukaina ne amma duk kan mazajensu 'ya'yan uwar gidan Alhaji ce wacce ta rasu ta barmin su duk suna k'ananu, Habibu shi ne yarona na shida kuma shi ne ya rayu har naga aurensa domin yayunsa da k'anninsa daga sun taso suke mutuwa domin babban yayarsa na daf da yin aure ya sami hatsarin mota ya mutu nasan kin tuna lokacin."

Eh na tuna da kawu Hamza, Allah ya ji kansu da Rahma "

"Amin.

"To yau kinji yarda na ke da su Balarabe."

"Allahu albar, sannu Inna, lallai ke ta daban ce, Allah ya biyaki da khairan."

"Amin ya rabbi."

"A gaskiya su Mama Indo nada ladabi sama da Zainab sam ba wanda zaice ba ke ce kika haifi mazajensu ba."

"D'iyoyin tarbiyya kenan, sannan sun samu mazaje tsayayyu masu jajircewa akan abin da suke so dole abi ba irin Habibu ba da gata ya yiwa yawo ya ke ganin matarsa ba komi ta ke yimin ba saima ganin ni ce nacika fad'a da saka ido."

"Shi Kawun ke kallonki da hakan?"

"Ya wuce kokwanto Khadijatu domin yanzu indan da gabansa hakan ya faru wallahi tsaf bayar matarsa zaibi ya yi ta k'unci na tozarta masa iyali gaban mutane."

"In haka ne kam da sake wallahi, ai lamarin uwa sama da komi ya ke, gashi wayayye da ilimi amma bai aiki da shi."

"Ki bari kawai Khadijatu, shi yasa na kance da shi halinsa d'aya da Hadi."

Kulle baki na yi idanu waje na ke girgiza mata kai murmushi ta yi kad'an ta ce "Na tabbata ko halinsu bai zo d'aya ba a wani abin zaizo domin ya yi nisa akan lamarin figaggiyar matarsa mai zubin zabbin daji da kanta kamar k'ullin maganin sanyi."

Dariya na kyale-kyale da shi tana tayani. Daga haka muka saki zancen domin nagano ta sanyo mana raha ne saboda bata son acigaba da zancen.

*** Ina cin abincin rana faten Irish ne ya ji hanta da ganyen ugun wanda su Fanta suka kawomin, sai hira mukeyi hankali kwance domin Hajiya Inna ta sami wucewa gida tunda ta ga isowarsu.

Mama ce ta shigo Uncle na biye da ita tare da Baba a bayansu. K'irjina ne ya harba ganin Baba domin na tabbata sai ya b'atamin rai kafin ya tafi.

"Kai dalla! Ku fice ku bata wuri ta sha iska, kunzo kun nanuk'eta da tik'a-tik'an jikinku ba mijin kwasa ko da ya ke duk jirgi d'aya ya kwasoku da ita ga kyau da wayewa ba mashin-shini, kai tir muku!."

Tashi su Fanta sukayi duk suka fice jikinsu a sanyaye, na kalli Uncle wanda na hango b'acin rai a idanunsa kwance sai kawai na fashe da kuka mai sauti ina kaiwa k'arfe gadon duka wanda ke nuni da takaicin da na ke ciki.

*TALLA.*

*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*

Sabulu (molato and black soap) Scrub Face cream Oil Body lotion Shower gel Kulachan Humra (White and black) Turaren tsugunon Turaren kaya Turaren wuta na d'aki Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)

*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.* [11/4, 5:42 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona) By Mrsjmoon

E.W.F.

https://youtu.be/v9iNYDvS8JM

Pls 'yan uwa ku dannamin subcribe a YouTube d'ina, nagode.

Page 21.

"Ke! Kuma me akayi miki kika b'are baki kamar faranti kina kukan iyashege, to maza ki rufe mana baki ko ingamu da ke ba ciwo ba ko mutuwa kikeyi zan iya taka gawarki na wuce ta kai ba ruwana."

Shiru na yi amma badan tsoron dukansa ba sai dan takaicin halinsa tare da tunanin yin kukana baida amfani.

"Dan an kira k'awayenki tik'a-tik'a shi ne abin yin kuka saboda Hurera ta gama sangartaki, ke yanzu dan Allah ko kunya bakiji kamarki kina kuka, inda a k'auye kike da yanzu kina da 'yay'ya bakwai zuwa goma amma dubeki zaune makar gar, to wallahi ki sani kwanaki kad'an ya rage in zar...

"Dan Allah Malam kayi shiru haka ban muji da abinda ya damemu tunda kai haka Allah ya yika baka gajiya da sababi mara ma'ana da ke janyo jin kunya."

"Hurera ni...

"Dan soyayyarka da mahaliccinmu ka daina fad'ar nan haka, haba dan Allah kai ko gajiya bakyayi da zance a gaban idanun kunya."

Tsuke baki ya yi yana aunawa Mama mugun kallo, kunya ce ta rufeni ganin yarda Uncle ya ke binsa da kallon banza, tabbas kallon ya haskomin karatun ruhinsa wato takaicin Baba mai jin tamkar a rufe rufeshi da duka.

"Uncle nagode da tarin d'awainiya Allah ya jik'an mahaifa ya kuma shirya maka zuri'a tare da gamawa lafiya cikin samuwar babban rabo ranar lahira."

Sai da ya yi gyaran murya sannan ya amsa lokacin har Mama ta amsa ya yin da Baba ya tsare giran sama da k'asa yana zabgomin harara.

"Bari inga Dr. Jalal."

Uncle ya furta batare da ya jira amsawarmu ba ya fice.

"Munafukin banza wai shi nan ya ji haushi na kori k'aninsa, to an koresun in zai iya ya rufeni da duka yaga inda tsiya ke zamaninta wallahi."

"Allah ya yi mana tsari da ganin tsiya."

"Amin."

Na amsa da sauri.

"Ya jikin naki?"

Baba ya ambata cikin taushin murya. Ban dauka da ni ta keyi ba shi yasa bance komi ba.

"Au dan kin samu na tambayi ciwon karyan da kikayi shi ne zaki maidani sokon banza?"

Kafin inyi magana Mama ta rigani da cewa "Gata nan ta warke ganin idanunka sai kuma me uban 'yan sababi."

"Hurera me yasa sam baki san darajar aure ba ne?"

"Sabon karatun sanin darajojin aure zamu koma makaranta muyo tare da kai domin kome ka kirani kaine malamina."

"Zan sab'a miki fa Hurera ba ruwana da Asibiti ne nan."

"Maza aikata abin yamad'i-d'i karo na biyu a safiyar nan a samu masu d'oraka a yanar gizo da bugawa a jaridu kaga ka zama dan wasan kwai-kwayo na zahiri kamar yarda sabon sunarka ya koma a unguwarka yanzu."

"Ni Malam Hadi kike kira da d'an drama?"

Banza Mama ta yi da shi, nikam tuni na juya baya tare da tura yatsuna cikim kunnuwana saboda na gaji da sauraren sababin Baba.

"Sai mun had'u a gida zan nuna miki nafi gaban iskancinki sannan kada kiga na d'aga darajarki a gaban abokan zamanki d'azun ki d'auka kin sameni ne a'a biyana zakiyi dan wallahi sai naci buhunar wake biyar domin na saka buri akan wanda sukayi satan sai reshe ya juye da mujiya dan haka sai ki shirya bi...

"Allah ya ganar da kai hanyar gaskiya."

Mama ta ambata tare da shigewa toilet ta barshi tsaye da baki bud'e, dariya ce ya zomin na kife fuska gudun kada ya jigoni na shiga uku

K'aran buga k'ofar ya sanarmin da Baba ya fice, numfashi na sauke ina auna lamuran Baba wanda na yanzu na ke d'orasu a mizanin rashin hankali.

"Astagafirullah."

Na ambata a hankali.

Shigowar Doctor, Uncle da su Beebah biye da su ya yi daidai da fitowar Mama daga toilet. Ya bani sallama tare da shawarwari agame da daina barin damuwa ko tunani na takuramu ni da Mama saboda su ne babban matsalolinmu.

Sosai Mama ta yi masa godiya, su Fanta suka tattara mana kaya muka fito. Ni da Mama tare da Bintu motar Uncle muka shiga ya yin da su Fiddausi suka shiga wanda suka zo a ciki Beebah ta ja, ta yi gaba Uncle ya rufa mata baya, akan hanya ya kira Hajiya Inna ya sanar mata da an sallamemu.

"Yawwa Alhaji sanar da Malam kada ya zama abin laifi duk da yasan za'ayi sallaman."

"To Mama."

Ni ya mik'owa wayar batare da ya furta kalma ba.

Sunar da naga an sanya Baban Nana na kira har ta tsinke ba'a d'auka ba, haka na yi ta kira sau ba adadi a k'arshe sai aka kashe wayar.

Mik'awa Uncle wayarsa na yi ya amsa batare da ya cemin uffan ba haka nima ban tofa ba.

"Mama dan girman Allah kiyi ta hak'uri da Baba insha Allah hakurinki babban riba ne saboda halinsa ba ke kad'ai yake yimawa ba, na fahimci haka Allah ya yo shi mafad'aci ga saurin hasala akan abin da bai kai ya kawo ba."

"To Alhaji Allah ya k'ara mana hak'urin baki d'aya."

"Amin."

Muka amsa.

Wayar Bintu na amsa na turawa Aliyu sak'o. Ina kallon Uncle na hararan hannuna ta gefen ido sai lamarin yabani dariya na murmusa har sautin na fitowa ya kalleni ido cikin ido na lumshe nawa.

"Ina wayarki?"

Ya furta cikin rad'a.

"An sace wayar."

"Inji wa?"

Wannan karan ya bud'e murya.

"To Uncle nazo da ita Asibiti ba'a ganta ba."

"Ok za'a siya wani."

"A'a kada a siya tana wurin Baba Umaru, Habibu ya sanarmin da sun dawo daga tafiya za'a kawo mata."

"To Mama."

Ya amsa cikin girmamawa.

Wayar hannuna ta yi k'ara number Aliyu ya baiyana sai na maida silent tare da maidawa gefe na ajiye, ina kallo kira ya yi ta shigowa ban d'auka ba saboda idanun Uncle wanda yanzu k'imarsa ya kuma ninkuwa a gare ni ainun.

"Ki d'auka wulak'anci bai da kyau Khadijatu."

Cikin rad'a ya ambatamin haka, kallonsa na yi ya jinjinamin kai maida kai gefe na yi batare da na bi umurninsa ba.

Muna isa gida su Beebah suka gyaramin d'akina dana Mama cikin a binda baifi awa d'aya da dawowarmu ba gidan ya koma fes har girki sun d'ora, wanka na yi muka zauna a baranda saman babban tabarma Fanta na yi min fifita sakamakon zafin da na ce yana damuna, shi yasa na sanya riga mai yankakken hannu da siket mara nauyi sai na sanya k'aramin hijab wanda ya tsayamin iya wuya.

Aunty Nafisa ce tare da yaranta suka shigo mun gaisa cikin mutunci Mama ta sake yi mata godiya akan d'awainiyar da Uncle ke kanyi mana. Muna tare da ita har dare sannan tsawon lokacin ban hango tijara a idanunta ba domin duk had'a idanun da zamuyi bata yimin mugun kallon da ta ke bina da shi a tun sanina da ita. Sai bayan isha'i ta wuce tare da su Bintu, su kabar Beebah da Fanta.

Ina sallah na jiyo shigowar Baba Umaru Ina idarwa na tafi muka gaisa sai tsokanata ya keyi da gawa tak'i rami, Kawu Habibu na taremin. Shigowar Baba yasa na bar wurin da sauri ina jin Kawu Habibu na k'orafin sababin Baba dan ganin yarda na tsorata da shigowarsa. Ba jimawa na jiyo muryan Uncle inda na fahimci masalaha akazo samu bisa jagorancin Baba Umaru.

"Aliyu ya na k'ofar gida fa."

Idanu na zubawa Beebah, ta gyadamin kai "Tun kina wanka ya zo kuma ya kamata ki fita."

"A gaban su Baba Umaru zan fita zance?"

"To me ye? Kinga ba sai Baba ya gane muna da masun-sunar da ya yi mana gorinsu ba."

Sunkuyar da kai na yi saboda yarda ta yi maganar na gano zagin da Baba ya yi musu d'azun ya b'ata ranta.

"Uhm wallahi badan mahaifinki ba ne Deejah na rantse da d'azun bansan kalan maganar da zanyi masa ba dan har zagi zai iya masa amma sai ya zamo ya haifeki 'yar albarka."

"Aunty Beebah ba Uncle ya ce maganar ta wuce ba."

"Ya wuce Fanta kawai dai har yanzu haushi lamarin ya ke bani barinma dana jiyo muryansa yanzu."

"Kiyi hak'uri nima d'iyarsa bai bari ba, kin dai gani da idanunki."

"Ya wuce yanzu tashi ki tafi wurin masoyinki."

"Dan Allah ku fita ku wakilceni domin bazan iya tsallake taron can ba."

"Fanta tafi ki sanarmasa tasha magani jiri ta ke gani ya shigo su gaisa."

"A'a kada ya shigo."

"Me kike nufi?"

"Ya tafi sai da safe ya dawo."

"To baki isa ba sai ya shigo tunda dubiya yazo ba soyayya ba."

Tab'e baki na yi jin abinda ta ce idanu ta zaro na zabga mata harara tare da hayewa saman doguwar kujera na kwanta. Fita sukayi tare da Fanta zuwa can na jiyo sallamar Aliyu da sauri na tashi na jira hijab na cure wuri d'aya. Duk Ina jin sadda ya gama gaida kowa su Beebah suka yi masa jagora zuwa d'akina na sha mamaki da banji Baba ya yi sababi ba amma tuno da Baba Umaru a wurin sai na barshi saboda ganinsa sa ne ya tsuke baki.

Tashi zaune na yi muka gaisa daga nan shiru ya biyo baya, su Beebah dai na zaune saman gado kowacce na latsa wayarta basu da niyya bamu wuri sai hakan ya yimin dad'i saboda har cikin raina banda kalman furta masa..

"Allah ya k'ara lafiya."

"Amin, nagode."

"Bakomi ke matar Ali ce insha Allah."

Da sauri na kalleshi ya dokamin murmushi sunkuyar da kai na yi.

"In Allah ya kaimu gobe Hajiyana tare da Salma zasu zo dubaki."

"Ok Allah ya kaimu."

"Amin."

Ya mik'e ya fice Fanta ta rufa masa baya.

"Ke matar Muhammad Muhseen ne ba Ali ba."

"Uhm Beebah hoo naga dai ke ce duk kikayi kid'a da rawar nan fa."

"Shi yasa na ke son goge zunubina."

Dariya ta bani sosai na dara tana tayani.

"Allah Deejah kafin in bar garin nan sai kin rabu da Aliyu."

"Saboda me?"

"Haka nan naga yanzu baku dace da juna ba, farar mace sai farin namiji kamar Uncle zubin labarawa."

"Kinyi kuskuren fad'ar karin.maganar Malama cewa akayi farar mace sai bakin namiji, farin namiji kuwa sai farar mace tamkar yarda Uncle suke da Aunty Nafisa ita chocolate shi fari, my Ali baki ni 'yar fara kad'an."

"Ko ba 'yar fara kad'an ba."

Ta furta cikin kawomin duka na gofce tare da komawa serious na ce "Bazan auri Aliyu ba saboda da wasu manyan dalilai wanda zan sanar da ke kafin ku tafi."

"Zanso jinsu yanzu saboda tafiyarmu zai iya yiwuwa gobe ne."

"Gobe kuma?"

"Eh saboda Aunty Nafisa ta had'a mana gurmi wurin tsoho mai ran k'arfe ya kira Uncle lallai mu taho gobe ko ya iso garin Kaduna da kansa ya d'aukemu musanman ni da ke aikin taimakon al'umma."

"Wayyo zansha kewa."

"Muma haka amma tafiyar banda Fanta saboda muna da biki watan gobe zasuzo da fatan zakiyi mana kara kizo?"

"Insha Allah zanzo duk da muma zamuyi tafiya amma nasan kafin bikin mundawo."

"Dan Allah kizo."

"Insha Allah."

"Ok."

"Bikin na miji ko mace?"

"Babban yayarmu baki d'aya shi ne zaiyi aure."

"Masha Allah."

"K'aton tazuru ne fa duk k'anninsa sunyi aure da 'ya'yanzu shi kuwa ya tsaya bautawa boko, da kiranye ya dawo Nigeria, baki gansa ba tamkar bature."

"Ikon Allah, lokacin auren nasa ne baiyi ba sai yanzu."

K'asa ta yi da murya sannan ta ce "Ina son shi fa insha Allah zanzo a ta biyu shi yasa na yakice Yaya Abdul da k'arfi da ya ji."

"To wata sabuwa inji 'yan ca-ca."

"Ki bari kawai dear ni kad'ai na ke kidana da rawana sannan in banda ke ba wanda ya sani."

"To ta ya za'a yi auren kenan?"

"Ta yarda akeyi."

"Zanso ganin wannan soyayya wacce ta ke ma kauniya."

"Ki bari kawai Deejah ni kaina na bata wannan sunar amma ina fatar ta sami ido bada jimawa ba domin ba zan iya bawa kowa ruhina ba sai Yaya Mubajjal."

"Wow suna mai dad'i ga tarin ma'ana."

"Duk mai sunar ya tarasu wallahi ya san kansa baruwansa kowa na sa ne, kinga tunda ya dawo duk jikokin gidan shi ke d'awainiyar karatunsu hatta da mu da muke jikokin d'iyoyi mata ya d'auki nauyi sai d'an abin da ba'arasa ba iyayenmu keyi mana, kud'i ya ke samu tamkar yana hak'osu a k'asa saboda a can turai ya ginu har kamfanoni ya ke da su tare da turawa."

"Masha Allah, matarsa ta yi dacen miji mai son zumunci."

"Wallahi fa ta yi dace kuma ta tsinci dami akala domin d'iyar kawunsa zai aura itama yar boko ce lecturer ce sai dai yafita kyau da aji nesa ba kusa ba."

"To ke Beebah ba sai ki cire kanki a lamarinsa ba ki fidda masu sonki tunda shi ya sami mata."

"Bazaki gane wani kalan so na keyi masa ba wallahi ba dan kudi da kyawunsa ba ne na kamu da k'aunarsa, tun ranar da nagansa naji fad'uwar gaba kuma tundaga ranar duk in mun had'u sai na shiga yanayin daburcewa, tun ban gano dalilin ba har nagano sonsa na ke yi."

"Ikon Allah sai ji da gani."

"Kin nan me?"

"Sai kin fad'a."

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull