Damuwata complete novel - Chapter 20
Damuwata complete novel Chapter 20: Damuwata complete novel Chapter 20. "Duk cikinmu yafi yimin magana ko yanzu mafi yawancin shirye-shiryen bikin shi…
3,319 words
"Duk cikinmu yafi yimin magana ko yanzu mafi yawancin shirye-shiryen bikin shi Momynmu zatayi wanda ni ya d'ora a kai na nemi shawararta ta ce in bar mata komi a hannunta daga nan fa ya maida gidanmu wurin zuwarsa ni kuma anan na kuma kamuwa da kaunarsa matsananci saboda yarda ya ke shigemin ko nak'i fitowa idan ya zo sai yanemi izinin momy ya biyoni d'akina shi yasa na daina gudu duk in ya zo sannan gashi ya iya tsokana irin ta abokannan wasa sai dai in yana yimin daburcewa na keyi sam ban iya maida masa da martani inda zai ta kirana da 'yar k'auye mai kunyar maza, wani zubin Momy ce zatayi ta taremin."
"To shima yana sonki kenan?"
"Ko d'aya, haka yakeyiwa dukkanmu sai dai kafin ya kirasu ne ya kirani sau ba adadi."
"Amma naga ko sau d'aya banga kunyi wayata ba."
Nunomin wayarta ta yi naga Miss call barkatai.
"Kullum sai ya kirani wani in amsa wani in share saboda haushin auren da zaiyi."
Dariya na kyale-kyale da shi ta tale baki tamkar zata fashe da kuka.
"Sorry dear in baki shawara?"
"Eh."
"Ki rik'a amsa kiransa inda hali ke ce zaki soma kiransa sannan ki b'oye kishin nan ta gaibu domin wanda kikeyi bai sani ba, ki nemi zab'in Allah ba son zuciyarki ba, in har mijinki ne da kansa zai furta miki k'auna."
"Nagode da shawara amma da kamar wuya hakan ya faru kawai ni ce zan ambatawa Kaka ina son shi na tabbata aurenmu zai k'ullu cikin ruwan sanyi "
"Ban amince kiyi haka ba saboda naji masu iya magana sunce matar shige bata daraja, gara ya furta da kansa."
"D'an boko ne da makar wuya ya zauna da mata biyu."
"To ki hak'ura da shi mana ki rik'e Yaya Abdul."
"Wannan kam ko mu biyu muka rage a duniya ba zan tab'a aurensa ba, nayiwa kaina wannan alk'awarin."
"Tsana in ya yi yawa mafi lokuta k'auna ke komawa, to dan Allah ki barwa Allah lamarin sai ya zab'a miki mari alkhairan."
"Insha Allah zan mik'a lamarin ga mai zab'awa bayi duk abinda yafi zama alkhairi a garesu."
"Da kyau tawan."
Murmushi mukayi tare da tafawa. Gyaran murya Fanta ta yi muka kalleta tsaye bakin k'ofa ta kafe Beebah da ido.
"Me ye?"
"Kin tsargu ne? To babu komi sai dai ni ce ta uku wacce ta san makauniyar soyayyar nan."
Dak'uwa ta yo mata muka fashe da dariya.
"Wallahi Aunty Beebah da a ce Yaya Mubajjal zai aureki da zance kunfi dacewa akan Aunty Hajara nan mai k'aton goshi da uban salo wai ita 'yar boko."
"To sannu 'yar son kai."
"Serious aunty Beebah, kun dace da juna kuma zan tayaki addu'ar Allah ya baki shi a matsayin miji."
"Amin 'yar uwa nagode."
"Sai dai wani hanzari ba gudu ba maganar fidda miji da Dady ya yi miki yana nan fa ba d'aga k'afa, shin ya zakiyi?."
"Ki bari kawai 'yar uwa babban DAMUWATA yanzu wannan maganar ce ga Momy ta goya masa baya shi yasa na ke jin tamkar kada in koma."
"Ga shawara ki kira Yaya Mubajjal ki sanar masa tare da neman shawararsa ko ki nuna masa ya nema miki alfarma wurin Dady da ya k'ara miki lokaci tunda kuna d'asawa ba zai juya miki baya ba."
"Good idea Aminiyata."
Na ambata cikin jinjinawa Fanta.
"Kuna ganin in aikata hakan?"
"Eh amma shawarar k'arshe na ya nema miki alfarma Dady ya k'ara miki lokaci kawai zakiyi masa. "
"Tam shi kenan, anjima zan sanar masa naji abin da zaice."
"Allah ya sa ya ce zaki aureni Habibatu."
Rungumeni ta yi cikin cewa "Da na kwana yi miki addu'ar gamawa lafiya da barin miki kyautar Umrar da Uncle ya yi min."
"Oh Aunty Beebah ba kunya."
"Amsa naki Fanta."
Ta watso mata d'ak'uwa cikin tsare gira.
Dariya muka sanya cike da nishad'i.
*** Washe gari tunda subahi kiran Uncle ya tashemu inda ya sanar da Beebah ta shirya shi zai kaisu. Ina azkar duk jikina a sanyaye na jin zasu tafi.
Sabo akace turken wawa to hakan ya faru gareni domin yinin ranar ko murmushi banjin na yi ba tun Mama da d'aukan abin da wasa har ta ga da gaske na ke sai ta koma bani baki amma duk da hakan ban dawo wal-walata ba na dai rage tsare gira. Fanta dama tunda taga ina hawaye ta fice ban sake sanyata a ido ba.
Misalin k'arfe uku na rana muna zaune saman tabarma Mama na damamin furar Tamba wanda Hajiya Inna ta aikomin da shi, muka tsinkayi sallama atare muka amsa wata Mata mai jiki tana da haske dai-dai misali ta shigo tare da matashiyar budurwa wacce kallo d'aya na yi mata na gano k'anwar Aliyu ce saboda kamarsu da juna har ya b'aci duk kuwa da tana fara shi kuwa bak'i.
Cikin girmamawa Mama ta basu wurin zama yarinyar ta zauna ta gaisar da Mama tare da yimin ya jiki na amsa cikin murmushi saboda naji dad'in ganinsu.
Matar kam tsaye ta yi k'erere tana jifana da wani kallo wanda ya saukemin kasala tare da bugun k'irji, gaisuwar da na ke nufin yi mata nakasa aiwatarwa, alokaci d'aya na nemi farin cikin ganinsu na rasa.
Mama da bata lura da kallon ba ta tafi d'auko musu abin motsa baki.
"Ina yini?"
Na furta cikin jajircewa.
"Mahaifiyar Aliyu ce dafatar ya sanar miki zuwana?"
Ta maidomin da amsar gaisuwar ta bayyanamin kanta.
"Eh, kunzo lafiya?"
"Ba damuwarki ba ne wannann."
Da sauri na kalleta ta zaromin manyan idanunta kauda kai gefe na yi ina jan addu'ar duk da yazo bakina.
"Na zo yi miki kashedi ne a kansa, ki rabumin da d'a ba zai aureki ba na zab'a masa wacce ta dace da shi domin auren zumunci zaiyi da d'iyoyin ar...
"Akul! kika nemi aibatamin d'iya akan idona Hajiya Asiya, tunda dai kin fad'i abin da ya kawoki to fice min a muhalli tun ranki baifi nawa b'aci ba."
Cikin fushi Mama ke maganar wanda na hango mamaki a idanun wacce ta kira kanta da mahaifiyar Aliyu jin kalamin Mama
"Ni kike kora a gidanki?"
"Ya wuce kokwanto, maza ficemin ko in sanya afitar da ke kuma idan kin isa da d'anki kada na sake ganinsa a k'ofar gidana balle ya shigomin muhalli."
"Haka kika ce?"
"Eh."
"Kin tabbata d'iyarki ta rabumin d'a kenan na har abada?"
"Ko a lahira bana fatar Uwata ta had'u da d'anki."
"Masha Allah, abu yazo cikin sauk'i, nabarki lafiya."
Banza Mama ta yi da ita illa nuna mata hanyar ficewa da ta yi.
"Hajiya ba haka kukayi da Yaya ba dan Allah ki ba su hak'uri dan d'anki zaifi cutuwa."
"Zaki tashi mu tafi ko sai na sab'a miki?"
Da sauri Salma ta mik'e suka fice na kalli Mama ta watsomin harara sai na tashi da sauri na shige d'akina ina jin zuciyata tamkar zata fad'o k'asa.
*Assalamu alaikum. Shahararren kamfanin nan na oriflame na yin registration kyau a wannan wata duk mai burin a dama da ita a harkan siye da siyarwa na kayan kamfanin ko yin amfani da kayan domin jin dad'inta to wannan babban damace a gareki ki garzayo ayi miki register kyauta kafin wata nan ta November ya k'are domin in ya k'are sai kin biya kusan 5k kafin ki samu damar zama 'yar kamfanin mai 'yanci dan haka ki taho ki zama .ai 'yanci a kyauta. Dan k'arin bayani ku tuntub'i wannan number 08131166848.* [11/5, 1:15 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona) By Mrsjmoon
E.W.F.
https://youtu.be/v9iNYDvS8JM
Pls 'yan uwa ku dannamin subcribe a YouTube d'ina, nagode.
Page 22.
"Dan Allah ki fito waje zuciyata na koma ga mahallicina ko na huta da wannan rayuwa mai cike da damuwa kala-kala, shin wai meye dalilin zamowata mara sa'ar rayuwa ce? Ina burin gabatar da rayuwa mai cike da kwanciyar hankali tamkar sauran mutane? Wayyo ni Nana Khadijatu ina zan saka kaina? Mahaifina bai bar ruhina ya sami natsuwa daga wasi-wasin shi d'in uba na ne ko zaman agolanci na ke yi a k'ark'ashinsa ba sannan ga saurayin da na sama bayan tsawon lokacin dana kwashe ina geben samun abokin rayuwa Mahaifiyarsa ta jagoranci rabuwarmu duk da na soma fidda shi a raina amma banso rabuwarmu ya zo ta wannan sigan ba. Ina da tulin tambayoyi a gareki Mama dan Allah ki amsamin su ko natsuwar da na ke nema ya rab'eni. Ya Salam, ya rabbi ka kawomin d'auki badan halina ba. K'alu Innalillahi wa inna ilaihin raji'un, Allahumma ajirni fi masibati wa khalifni khairan minha."
Sune kalman dana rik'a ambata cikin matsanancin kuka hannayena duka biyun dafe da k'irjina wanda na tabbatar bana rabuwa da Aliyu ba ne domin ina jin wani sabon lamari na daban zai sameni wanda zanyi kukan shi yasa na bud'e baki ina yinsa tamkar wacce aka aikowa da sak'on mutuwar Mama. A k'arshe zamewa na yi na kwanta saman sallaya ina cigaba da kuka amma mara sauti saboda yin mai sautin zai janyo hankalin Mama saidai duk da rage sautin bai hanata jiyowa ba.
Ina jin shigowarta nak'i motsawa tana d'ora hannunta a gadon bayana sabon kuka ya kubcemin na fashe da mai k'arfi sosai cikin jijjiga. Hannunta ta soma yawo da shi a bayana a hankali ba tare da ta yi magana ba, ina ji a jikina itama kukan ta keyi mara sauti, d'if na d'auke nawa tare da tashi zaune da hanzari na fad'a jikinta ina cewa "Natuba Mama dan Allah ki yafemin ba burina kenan ba na sakaki kuka lamarin ne ya dameni dole saina zubda jirwaye zan sami natsuwar jiki da ruhi, dan Allah kada kiyi fushi da ni, natuba Mamana, kiyi shiru dan girman Allah, zubar hawayenki dafi ne a gareni dan Allah kibari kada wani abu mara kyau ya sameni sanadin kukan nan."
"Banyi fushi dake ba Uwata kuma ba kuka na ke yi ba fatana ki sanya salama cikin ranki dan samuwar lafiyarki sannan kada kiyi zargin na jagoranci rabaki da mosayinki ne saboda da wata manufa tawa a'a sam ba haka ba ne ina dai burin kiyi rayuwa ce mai cike da 'yanci wanda zaki sakata ki wala a gidan aurenki ba wanda zaki dawwama cikin k'unci ba bisa takurawar uwarmiji wannan dalilin yasa na datse alak'arki da Aliyu kuma idan har na isa na fad'a ki ji to daga yau babu ke babu Aliyu har abada sunarsama bana son ki sake ambata koda a cikin zuciyarki ne, burina ki kasance tamkar baki tab'a sanin shi ba balle ki tuna kun tab'a musayan kalaman k'auna."
"Mama...
"Uwata hakan na ke buk'ata da ke, hatta da makaranta da kuke had'uwa kin daina zuwarsa kenan domin na tsani mahaifiyarsa da shi kansa tunda ta sanya Uwata zubda hawaye a kan idona sannan ta nemi aibatamin ke da kalma mafi muni da natsani jinsa."
"Mama na hak'ura da shi tun kafin zuwar wannan lokaci kuma insha Allah zan ciresa a babin rayuwata sai dai ina rok'on da ki janye kalman tsana ga Aliyu saboda baiyi komi ba ko ba komi ya so Nana Khadijatunki da zuciya d'aya, ya karya bak'in tarihin nan na tana da bak'in jini ta rasa mai furta mata kalman so."
"To Uwata na jenye harma da Mahaifiyar masa duk na yi hak'uri irin wanda Allah da Manzonsa duke son mumunai nagari sunayi wato hak'uri mai kyau."
Sunkuyar da kai na yi ganin tana kallona cikin murmushi ga hawayenan cikin kwarmin idanunta suna daf da zubowa. Ban d'agoba na mik'a hannu na share mata hawayen, ta rik'e hannuna gam na d'ago da sauri ta motsa kai, matsowa jikinta na yi ta saki hannuna na samu damar shigewa na lafe, bubbugamin baya ta soma tamkar uwa na rarrashin 'yar yaye.
"Mama tun jiya na soma cire Aliyu a ruhina saboda... Na sanar da ita duk abin da ya faru zuwar matar Kawu Habibu dubani da zantukan da mukayi da Hajiya Inna.
"Alhamdulillah, Allah ya zab'a miki mafi alkhairi."
"Amin Mama."
Na amsa a hankali cike da kunya ta shafi sumar kaina cikin cewa "Taho muje ki tayani aiki domin zama wuri d'aya na janyo tunani mara tushe da fatan ban takura Uwata ba?"
"Mama kekoh."
Na ambata a shagwab'e.
Hanncina ta ja na d'auke numfashi cikin sigan wasa ta saki da sauri na fashe da dariya tana tayani.
"Allah ya cigaba da albarkatan rayuwarki Khadijatu."
"Amin Mamana."
Fitowa mukayi Mama ta yi ta yimin hira mai sanya mantawa da duk kan damuwa.
"Uwata yau Litini insha Allah jibi laraba zamu tafi Kwara dubo jikin Babana."
"Allah ya kaimu Mama."
"Amin."
"Gobe zamuje yi masu tsaraba da fatan zaki iya shiga kasuwa?"
"Zan iya Mama."
"Madallah, anjima Habibu zaizo muje shagunana domin ina son saidaasu na had'esu ya zama babba guda d'aya kamar super market."
"Masha Allah, Allah ya taimaka."
"Amin, zan dank'a a hannunsa dan hakan zai fi akan yawo da hankalin da masu hayan keyimin ko ba komi shi nawane, da wasu su cinyemin gara shi ya ci ya more."
"Hakan ya yi Mama, Allah ya yiwa nema albarka ya taya Kawu Habibu rik'o."
"Amin."
"Jiya an sami masalaha tsakanin Alhaji Muhseen da Malam ina fatar nadamar da na hango a idanun Malam ya zamo na gaskiya ne."
"Amin ya rabbi."
Shiru ya ratsa wurin na dubeta kad'an ta motsa kai alamun tana saurarona.
"To Mama kin hak'ura da zancen dukiyanki na wurin Baba ko?"
"A'a bazan hak'ura ba dan zaman jiya har da shi aka tsaida maganar ina dawowa daga Kwara zai dank'amin kayana domin lokacin yin amfani da su ya yi dama an bashi ne ya ajiye amatsayinsa da shugabana sai ya nemi a bashi damar ya juya zuwa sadda za'a nema to lokacin neman ya yi."
"To Mama idan baya da shi fa?"
"Na sanar miki yana da gidan gona wanda da kud'ina ya mallaka haka ya siya gonaki duk da kud'in yanzu haka takardun gonakin jiya Baba Umaru ya amsa daga hannunsa gidan gonar kuma zaiyi masa kud'i Habibu zai siya sai a had'a da gonakin a lissafa in sun kai adadin kud'ina in kuma sun wuce sai abashi ragowar hakk'insa."
"Kuma duk Baba ya amince cikin ruwan sanyi?"
"Eh saboda Baba Umaru ba sa'ar wasanshi ba ne sannan komi da akayi anyisa ne a rubuce tare da shaidu. Idan komi ya kammala filin da ke kan layin su Baba Umaru za'a siya a gina babban Mall wanda zai kasance babu ce kawai ba'a siyarwa."
Dariya na sanya cike da jin dad'i na ce "Da sai in zama shuga mai bada umurni."
"Allah dai ya cika mana burinmu Uwata domin komi da kikaga inayi to dan ingantuwar rayuwarki ne, kada k'asa ya rufe idona Malam ya handame komi ya koramin."
"Godiya na ke Mamana amma dan Allah ki kyautatawa Baba zato."
"To naji amma ki sani ba godiya a tsakanin Uwa da 'ya sai addu'ar samun babban rabo ranar lahira."
"Allah ya biyaki da gidan aljannatul firdausi."
"Amin ya rabbi."
"Yawwa Mama wai ya muke da Baba Abdul Ganiyu nan?"
Shiru ta yi har na cire rai da jin amsar tambayar sai kawai na kamo hannunta na langab'e kai cikin sanyin murya na ce "Kiyi hak'uri Mama idan sanarmin zai takuraki wallahi na fasa jin nasabanmu da shi."
"Zan sanar da ke amma a takaice domin zuwa yanzu ya kamata ki soma sanin ya ni ke da duk wanda kika ganmu tare."
"To Mama Ina saurarenki."
"Kinga Baba Abdul Ganiyu abokin mahaifina ne na k'ud da k'ud amma shi bayarbene ya yin da Mahaifina Abdullahi ya zamo Hausa Fulani d'an asalin garin sokoto. Sadda Allah ya nufa zan zo garin Kaduna da zama Baba Abdul Ganiyu ne ya had'ani da Baba Umaru wanda shi kuma ya zamo abokin kasuwancinsa daga arewa zuwa kudu. Baba Umaru ya rik'e ni tamkar shi ya haifeni dan haka wad'an nan mutanen biyu bani da kamarsu in kika cire mahaifana, Abdaullahi da Hadiza da kuma ke 'ya ta."
"Allah ya kai haske k'abarinsu."
"Amin."
"To Mama ina danginmu na Sokoto?"
"Suna nan."
"Me yasa ba...
"Uwata kada ki tsananta bincike domin na yi miki alk'awarin sanar da ke komi idan lokacin ki sani ya yi."
"To Mama na kame bakina."
"Da kyau, idan zaki sha furanki tana cikin fridge."
Murmushi na yi jin ta sauya akalan zancen.
"Ko sai zuwa dare zaki sha?"
"A'a zan sha yanzu, bari in d'ibo kad'an."
"Aha, sai ki zuba zuma zaifi dad'in d'and'ano akan saka siga."
"To Mamana."
Ina shan furar na dubi Mama wacce ke gyara zogale zata dafa mana wanda Hajiya Inna ta aikomin da shi domin na ce kwad'onsa na ke son ci da dare.
"Ya dai Uwata?"
Lashe lips na yi na amsa da "Ina burin na ganni cikin danginmu duk da bana son hayaniyar jama'a amma son ganina tsakanin kakanni, iyaye da abokanan wasa maza da mata wannan babban buri ne da ya jima a ruhina sai dai idan na nutsa cikin tunani sai wani lamari da na rasa gane kansa ya zo ya shafe burin ta hanyar jefani cikin fargaba har sai na ji ban son ganina cikin dangin baki d'aya sai na rik'a jin dama banzo duniyar ba."
Banza Mama ta yi da ni domin tunda na fara maganar bata nuna zata furta kalma ba. Na matso jikinta na jingina ina sauke numfashi, still bata kulani ba sai na gyara zama a gabanta na ce "Zanso idan mun dawo Kwara mu tsaya a Sokoto inda halima ki barni a can na zaga dangi na birni da karkara dan samun ladar zumunci."
"Allah ya kaimu lokacin amma zuwa Sokoto ba yanzu ba saboda ko wani tafiya nasa daban na ke son yi."
Jinjina kai na yi ina wasa da ganyen zogalen da ta tsinke.
"Uwata da magana a bakinki ko?"
Kallonta na yi ta waremin idanu cikin jiran abinda zan fura sai na girgiza kai tare da tashi na shige d'akina ina murmushi.
"Nana Khadijatu kenan, Uwata ta kaina, nasan damuwarki bai wuce zantukan da kika gamayi na yi banza da ke, affuwan Uwata bana da jarumtar biye miki ne."
Mama ta furta tare da mik'ewa ta shige madafi.
*** *Asabe da Hinde.*
Asabe ce zaune a k'ofarta ta tsefin kai wanda da kyar ta ke kamo bindin korar saboda tsabar tsufar da ya yi gami da datti, Hinde kuwa tana nesa da ita tana gyaran gyad'an miya.
"Hinde wallahi duk tijarar da na gani gami da iziya a hannun masu babbak'un kaya ban saduda ba ko misk'ala zarratin domin sai naga bayan Hurera kafin k'asa ya rufe idanu zanji dad'in a raina."
"Yaya tamkar kin shiga zuciyata, tunanin da na keyi kenan yanzu, wallahi da abin na ke kwana na ke tashi musanman mijin da Uwani zata aura, gashi mutumin kirki sam abinsa bai rufe masa idanu ba da ganinsa ya san abinda yakeyi, hak'ik'a zataji dad'in zama da shi, Hurera zata huta fiye da zatona, zata tabbata cikin jin dad'i mu kuma 'yan maula domin ko Malam sai yarda ta yi da shi dama ya lafiyar giwa balle ta yi hauka."
"Hinde kin sosamin inda keyimin k'aik'ayi, billahil azim ji na ke tamkar in wayi gari acemin Alhaji Muhseen ya mutu na rantse da sai na yi rawa da juyi dan Hurera taga samu taga rashi kenan a lokaci d'aya."
"Ai idan zaki bani had'in kai na rantse sai dai ya auri wata amma ba Uwani ba, domin nafi jin takaicin ni'imar da zata shiga muna kallo tamkar tumakai."
"Ina tare da ke 'yar uwa, tunda mun samu ya yi mana yayyafin naira muyi jari to mu had'esa kaf mu fantsama neman sa'ar datse wannan bak'ar alak'ar domin ba zan kirashi da fari ba."
Wata dariya Hinde ta b'arke da shi wanda ya bawa Asabe tsoro ta shige d'akinta da gudu biyo bayanta Hinde ta yi tana cigaba da dariyar tamkar ta sami tab'in hankali nanko ras ta ke tsabar jin dad'in kalaman Asabe ce.
*** "Yaya Aliyu kabi umurnin Hajiya domin ta yi rantsuwa ba zaka auri kowa ba sai Amira."