Damuwata complete novel - Chapter 21
Damuwata complete novel Chapter 21: Damuwata complete novel Chapter 21. Numfashi ya sauke ya kafe Salma da ido "Me Hajiya ta aikata a gidan su Khadija…
3,371 words
Numfashi ya sauke ya kafe Salma da ido "Me Hajiya ta aikata a gidan su Khadija wanda ya janyo ta sakani a black list ko na kirata bai shiga na ganta a online na yi mata magana ta yi blocking d'ina na sanja layi na kirata tana jin muryana ta kashe na tura sak'o ta wayar K'awarta Fanta ta k'i dawomin da amsa, maza sanarmin da abinda Hajiya ta aikata musu da ya janyo na fuskanci wannan lamarin.
"Kayi hak'uri Yaya ba zan iya sanar maka ba saboda nayiwa Hajiya alk'awarin kame bakina."
"Zanje gidan yau da kaina in yaso zanji komeye a bakinta."
"Kada kaje saboda Mamanta ta fusata zuwanka zai zamo zubewar mutuncin Hajiya ce domin ta ce idan ta isa da kai ta hanaka zuwa gidan, kenan zuwanka tamkar Hajiya bata isa da kai ba ne."
"Duk me ya kawo wannan zantukan daga zuwa dubiya?"
"Wanna tambayoyin Hajiya ke da amsoshinsu kuma ya kamata ta amsa maka domin ina zargin da abinda ta ke b'oye mana wanda ya shafi Khadija domin da kunnuwana na ji aunty Zainab na yi mata rantsuwa akan wani abu na so jin abin amma Hajiya ta sauya zancen tare da rufeni da fad'a dan na nemi k'arin bayani."
"Zainab zan sama naji munafuncin da ta k'ulla domin tunda ta gano Khadija ce wacce na ke so na hango tsanar lamarin a idanunta, kuma wallahi idan ta yi sanadin rabani da wacce na ke so rayukanmu zasu b'aci matuk'ar b'aci."
"Kabi komi a sannu Yaya amma ina ji a jikina Deejah ba matarka ba ce."
"B'acemin da gani ko in nad'a miki duka! Wawiya kawai wacce ba'ajin alkhairi abakinta sai sharri."
"Ni d'in Yaya?"
"Zaki fice ko sai na zubda miki da hak'ora?"
Cikin fushi Salma ta bar d'akin tamkar zata saka kuka.
"Ina cikin tsaka mai wuya ni Aliyu."
Ya furta tare da sake dialing number Fanta haka ya gama ringing ba'a d'aga ba, kwanciya ya yi na cigaba da kiran wayar amma baiyi dacen an d'auka ba balle ya rok'eta ta had'ashi da Deejah.
"Why Hajiya? Kin san yarda na ke jinta a ruhina kuwa? Wallahi ba zan auri wacce kike muradi ba domin ban tab'a kallonta a matar da zan aura ba sai k'anwa."
"Zakata tabbata ba aure kenan in har baka auri d'iyar d'an uwana ba wallahi ba zanyi kaffara ba kai da aure sai in anayi a lahira sai dai kuma in zakayi ba da sa albarkana ba wannan kam sai ince na barwa duniya kai babu ni babu kai har abada."
"Hajiya me yasa kika sanja daga mai k'aunar farin cikin 'ya'yanki zuwa kishiyarsa?"
"Son k'ulla zumunci ya sanjani kuma ba zan tab'a dawowa ba dan haka zab'i ya rage ga mai shiga rijiya, walau kayimin biyayya ka auri jininka Amira ko ka band'aremin na barwa duniya kai tare da yima tofin jeka ka gani."
"Innalillahi wa Inna ilaihin raji'un! Hajiya wai me ye haka kikeyi?"
"Idan ka gama yanke shawara ka sanarmin wallahi ba zan matsa maka sai ka so cikar burina ba amma dai ka tuna zab'i biyu na baka kuma duk wacce ka d'auka zan amsa da hannu biyu."
Tana fad'ar haka ta fice daga d'akin.
Kuka ya fashe da shi mai sauti baya ko jin kunyar k'anninsa su jiyo shi.
"Zainab!."
Ya ambata cikin kaushin murya. Wayarsa ya laliba ya doka mata kira bugu d'aya ta d'auka cikin karad'in cewa "Angon Takwara my in-law kana lafiya?"
"Abinda kikayimin Allah ya yi miki fiye da shi, Allah ya sanyo k'unci a ruhinki sama da wanda kika jagoranci dasamin, Allah ya kawo sanadin da mijinki zai gano b'oyayyen halinki na raina masa Mahaifiya, Allah ya karya k'adarinki ki gamu da gamonki ta hanyar da bakiyi zato ba."
"Me ke damunka Aliyu?"
"Allah ya isa tsakanina da ke kuma k'anwarki ba dai taji dad'in zama da ni ba, wawiya kawai bulutu mai saka khairan da sharran."
Kafin ta sake furta kalma ya datse kiran.
Sai numfashi ya ke saukewa cikin furzar da huci, key d'in mashin nasa ya d'auka ya fice tamkar zai kifa.
Zainab kam kuka ta fashe da shi cikin durawa Aliyu zagi tamkar ba yayata ba, ganin hakan baiyi mata ba ta kira Hajiya ta rattafa mata k'arya da gaskiya.
Shiru Hajiya ta yi bata da niyyar cewa komi saboda yarda ranta ya b'aci.
"Hajiya wallahi in wani abu mara kyau ya sameni bakin Aliyu ne."
"Zaizo har gida ya baki hak'uri d'iyata, ki daina kuka insha Allah ba abinda zai sameki sai alkhairi."
"To Hajiya nagode."
"Na ce ki daina kukan nan."
"Na bari."
"Da kyau, ki shafamin kan jikalleta."
Bata amsa ba Hajiya ta kashe wayar tare da neman Aliyu aka sanar mata wayar a kashe ne. Tsaki ta ja ta cije leb'en k'asa cike da takaicin rashin samunsa.
Aliyu kam na fita gidan su Deejah ya nufa sai dai ya aika yara har uku ana dawo masa da amsar bata nan alhalin duk in ya tambayi yaran sun ganta suna amsa masa da ita ce ta ce a ce masa bata nan. Garin yaji na juya masa ya samu dakali ya zauna ya tsirawa bishiyar ced'iya da ke nesa da k'ofar gidan ido tamkar mai irga rassanta nan kuwa lulawa ya yi cikin tunani.
"Kai! Me kakeyi a nan?"
Muryan Baba ya katse masa tunani.
Firgigit ya yi tare da zubewa yana gaisheshi.
"Lafiya, daga ina?"
"Abokin karatun Khadija ne."
Ya sami kansa da furta hakan.
"Oh bari aturo maka ita dan nasan kazo gaisheta sa jiki ne ko?"
"Eh, Baba."
"To jirata."
Da idanu ya raka Baba yana zabga masa albarka a cikin ransa. Yana tsaye na fito fuska a had'e. Wawan ajiyar zuciya ya sauke ya taho da hanzari tamkar zai rungumeni na koma da baya cikin zaure da sauri ya rufa min baya, ganin zan koma cikin gida sai ya rik'o hijabina na juyo idanuna na zubar hawaye na had'e hannayena alamun rok'o na ce "Dan soyayyarka da fiyayyen halitta Aliyu ka rabu da ni rabuwa ta har abada."
"A'a Khadija, kada kiyimin haka, ruhunanmu bazasu d'auka ba dan Allah ki saurareni."
"Aliyu lamarin mahaifiya dabanne da na kowa dan haka na ke baka shawara da kayi mata biyayya tamkar yarda na yiwa tawa Mahaifiyar na tabbata zamuga haske cikin rayuwarmu."
"Khadija kin amince zaki iya rabuwa da ni?"
Shiru na yi masa saboda bakina ya yi nauyin amsawa Amma ba wai dan bazan iya amsawa da a'a ba ne sai dan ina ganin cin kuska ne na amsa masa kai tsaye.
"To ni bazan iya hak'ura da ke ba ki rubuta da k'aunarki zan koma ga mahaliccinsa."
Kuka ne ya kufcemin ganin yarda ya ke furta kalamin da iya kacin gaskiyarsa.
"Koma ciki kai kuma tafi kayiwa mahaifiyarka biyayya dama Uwani ba sa'ar aurenka ba ne Allah ne ya baka ita har ta soma kulaka sai kuma somuwar Uwarka ta yi sanadin b'ata komi saboda son zuciya."
Tsit mukayi muna kallon Baba da ya shiga tsakiyarmu ya raba tsakaninmu yana mazurai.
Hannun na d'aga masa alamun bye na shige gida da gudu shi kam zubewa gaban Baba ya yi ya ce "Baba kayi wani abu akai wallahi jna sonta, itama tana sona."
Mik'a masa hannu Baba ya yi Aliyu ya zaro idanu kai Baba ya gyad'a.
"Ban fito da kud'i ba Baba kayi hak'uri zan kawo maka."
"Zaka iya tafiya kuma wannan shi ne rana ta k'arshe da zaka sake zuwamin k'ofar gida tunda matsiyaci ne kai."
"Baba kayi hak'u...
"Kaci Uban Uwarka mataccen nan na ce kaji ko?"
Baba ya gabgowa Aliyu zagi cikin nad'e hannun riga, alamun zai bugeshi.
Da gudu Aliyu ya fito zauren ya kunna mashin d'insa ya bar unguwar amma yana jin aransa ba zai iya rabuwa da Deejah ba.
*Assalamu alaikum, 'yan uwa Barkanmu da warhaka ga wata dama ta samu mai burin dogaro da kansa. Shahararren kamfanin nan na oriflame na yin registration kyau a wannan wata duk mai burin a dama da ita ko shi a harkan siye da siyarwa na kayan kamfanin a samu riba Mai yawa ko yin amfani da kayan domin jin dad'in rayuwa to wannan babban damace a gareku, maza ku garzayo ayi muku register kyauta kafin wata nan ta November ya k'are domin in ya k'are sai kun biya kusan 5k kafin ku samu damar zama 'yar kamfanin masu 'yanci dan haka ku taho dan zama masu 'yanci a kyauta. Domin k'arin bayani ku tuntub'i wannan number 08131166848.* [11/7, 2:06 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona) By Safiyya (Mrsjmoon)
E.W.F.
Page 23
"Ina uwani ta ke? To maza kizo ki bud'e kunnuwanki da kyau ki saurari kalamina akan matsiyacin yaron can."
Ina jiyo Baba daga cikin uward'akan Mama amma ban motsaba saboda wani haushin shi na ke ji duk kuwa da yarda na ke korar lamarin amma sai k'ara nitsawa ciki raina keyi. Jiyo sabon hargaginsa yasa na tashi daga kwancen da ni ke na tallabe kumatuna hawaye na cigaba da wankemin fuska tamkar an fud'e famfo.
"Narabaki da wannan matsiyacin yaron na fad'a na k'ara tabbas na rabaki da shi domin baida komi sai k'wambon banza da k'arya da ganinsa ba zai iya rik'eki ba balle har mu sami ihsani daga gare shi, d'an gidan matsiyata ne wanda ke neman cin yau babu na gobe dan haka nima ina bayan Mamanki ki fita sabgarsa ki auri mai arziki wanda zan fanshe rainonki da na yi, a yau ina bayan cikar burin Hurera wato auren mijin da ya kerewa sa'a wato d'aya tamkar da million ba dubu ba, kamar dai Alhaji Muhseen ko ma wanda ya zartashi inda darajana zai k'ara hauhawa duk inda na ratsa ayimin fad'anci tamkar basarake dan ina da suriki ishasshe wanda ya kama k'asa, gagara badau wanda arziki ya yiwa mayafi ya barranta da talauci."
"A'uzubillahi! Malam me kake ambata haka? Dama jari muke nema da ita ko me? Wani talauci garemu da zamu jira sai mijin Uwata ya bamu abin duniya? Malam dan Allah ka sanja sam wannan son abin duniyar naka bai da kyau, ba haka musulunci ya tsara mana da mu nemi duniya ba, wallahi ina jiye maka fad'awa halaka akan wannan makauniyar d'abi'a naka wanda baka bar kowa ba tamkar ba masanin illimin addini ba."
"Na fahimci bak'in cikin da kikeyimin ya wuce iyaka Hurera, bayan kina son amshe dukiyanki ki mallakawa Uwani ta yi arzikin da kikeyi mata fata shi ne ni kike son na talauce tamkar b'eran masallaci, to wallahi baki isa ba, kinyi kad'an ki zamenin inuwar giginya na nesa kasha dad'i, na rantse da Allah sai Uwani ta zamemin jari kamar yarda ta zame miki hanyar bud'ewar k'ofofin samu tun bata san kanta ba wanda kike neman maida mata da kayanta na koma a huhun ma'ahu, ba wan ba wan karatun d'an kama, na yiwa duniya zuwar zomo yarda na zo a guje na koma a guje, to da sake wai anyiwa mai dami d'aya sata, dole ne ki sanja tsari a game ta amshe dukiyanki ko kuma Uwani ta zamemin jari ko zab'i na k'arshe shi ne na tafi masallaci na yi shela ga mai son sadakar aurenta na bawa ko waye ko da kuwa Makaho ne, Kuturu ne, Gurgu ne, Bebe ne kai ko duk wanda ya had'a duka nak'asar ne indai ta zamo rabonsa zan bashi ita Sadakarta."
"Malam! Kana cikin hankalinka kuwa?."
"A'a sama na ke cizo."
"Innalillahi wa Inna ilaihin raji'un, wai shin har sai yaushe zamu sami kwnaciyar hankali daga sababinka ne Malam? Shin son kud'i hauka ne?"
"Kanki akeji Hurera abinda na sani ne indai ni Uban Uwani ne dole ki barni na yi duk yarda naso da ita tunda bak'in jininta ya ta'azzara ta zama uwar mata a gabanmu muna ta ibada da haramtacce ruwa."
"Me ka ke nufi da kalamanka Malam?"
"Abin da jahilan farko sukayi ittifa'i."
"K'alu innalillahi wa inna ilaihin raji'un! Kana nufin ka zama irinsu kenan?"
"Ke! Hurera shiru-shiru fa ba hauka ba ne, kada kiga na baki dama kina jefomin tambayoyi ki d'auka na zama mijin ta ce ne to ina nan a tsayena tamkar Nonon maza ban rankwafa ba ko na kafan allura dan haka wallahi ki shiga hankalinki da ni ko allura ta tono garma, sirrin b'oye ya fito fili a yi walk'iya kowa ya ga zahiri, idan kuma kin musanta to ki cigaba da tsayawa a gaba kina furtamin duk kalaman da suka zo bakinki ni kuma zan shayar da ke zumar mamaki ba Madara ba domin terere zanyi ma'ishi ban da abin kaico."
"Allah ya shirya ka."
"Amin, yin la'asar yafi miki ko inyi bankad'a, kuma dole ki bani wani kaso a dukiyarki domin dogaro da kaina ko in hau munbari na fed'e biri har wutsiya, in na ce har wutsiya to tundaga salsalan zan soma tareda bada damar duk wanda bai fahimta ba yazo na yi masa bayani gamsas-shiya."
"Malam me ka sha ne yau?"
"Abin da tunaninki ya baki."
Shiru Mama ta yi jikinta asake hakan da Baba ya hango ya sake bud'e mata wuta da barazana ta wani sigan mai tab'a zuciya wanda ya sanyani fitowa idanuna cike da hawaye na russuna gabansa na ce "Dan Allah Baba kayi shiru kaga makwafta na iya jiyo harshenka sannan ni ta kace tayimin duk hukunci da kaso ba mai hanaka dama kyawun mijin d'iya na farko ya zamo zab'in mahaifinta ne, na amince Baba ka yi sadaka da ni ga kowa zaka sameni mai biyayya ga zab'in ka ni dai fatana rashin jituwar da ke samuwa tsakaninka da Mama ya zo k'arshe, hankalin mahaifana ya dawo wuri d'aya yarda zasu kashe su rufe ba mai ji."
"Uwata ta shi ki koma d'akin ki bana son shirme."
"Mama kiyi hak'uri yau komi yazo k'arshe walallahi bana son wannan rayuwar da mukeyi na sababin Baba."
"Na ce ki koma d'akin ki ko ki tafi wurin Fanta."
"Da dai kin barta taji komi saboda lamarin ya shafeta kinga daga nan za...
"Malam na rantse da wanda ya haliccemu zan wulak'an...
"Mama ki bari, miji darajarsa daban ya ke nasan kin sani to dan darajar mai daraja Manzon farko da k'arshe ki daina d'aga harshenki sama da nasa domin hukuncin Allah zai sauka kanki kai tsaye batare da duban 'yancinki kike karewa ba."
"Allah ya yi miki albarka Uwata, nagode ainun da tunasarwa, maza tashi ki tafi wurin Fanta ina son samun masalaha da Malam."
Kallon Baba na yi ya zunkud'a kafad'a sai na maida kollon kan Mama ta murmusa tare da bani umurni da hannu wato na tashi. Mik'ewa na yi na koma d'akina na fito da hijab na yi waje amma ba gidan Uncle na nufa ba, titi na mik'e ina zantukan zucci ganin ina ta tafiya mutane na rakani da ido sai na tsaida mai Napep na sanar masa da inda na nufa wato gidan Baba Umaru domin kalaman Baba sun tsayamin a rai ina burin sanin fashin bak'insu a bakin Hajiya Inna domin na tabbata ta san komi.
'Fed'e biri har wutsiya, tereren bankad'a, abin b'oye ya fito fili, allura ta tono garma.'
Sune kalaman da na ke ta maimaitawa a cikin zuciyana, ina mai burin jin fashin bak'in su.
*** Deejah na fita Mama ta nuna Baba da yatsa cikin b'acin rai ta ce "Duk abin da ka shirya Malam tafi kayi amma ka sani hukuncin mai karya alk'awari zai hau kanka kuma zan kai k'ararka wurin wanda baya barci balle gyan-gyad'i wato Allah sannan ka tuna Allah na amsar addu'ar wanda aka zalunta nan ta ke, a k'arshe ina yima albishi da cewa Aurenmu guntilalle sunarsa dan na fahimci ka manta yarjejeniyarmu sanan kamar yarda ka tonamin asiri nima zan tona naka, muzuba shege ka fasa d'an halas sai yanka, zamuga wanda zaifi kunyata a idon duniya."
Baki bud'e Baba ke kallonta har ta dasa aya.
"Sharri zakiyi min ko me Hurera?"
"Au sharri ko? Tam ga fili ga mai doki ai wanda ya fasa aikata nufinsa ba d'an hakas ba ne."
"Hurera kinfi kowa sanin banda tambon abin ash-sha dan haka ki gama borin kunyarki ki dawo kan hanya domin ba mai hanani samun rabo a cikin dukiyarki."
"Sai Allah da ya haliccemu, shi ne zai hakana samun rabon nan."
Mama ta bashi amsa idanu soye cikin rashin tsoro na ban mamaki.
"Shi kenan muzuba mugani."
Ya ambata cikin buga babban rigansa.
Har ya juya zai tafi Mama ta bi bayarsa da sauri ta rik'o babban rigarsa ya juyo a fusace sai ta fad'a k'irjinsa ya ko rungumeta tsan-tsan yana sauke numfashi saboda duk tsiyarsa yana son Mama matuk'a, sun jima a haka sannan ya d'agota ta k'ara lafewa tare da yin d'age ta kai bakinta cikin kunninsa ta yi masa rad'a lamarin da ya sanya shi tureta yana gwama numfashi cikin nunota da yatsa sai dai ya kasa furta kalma saboda nauyin da harshensa ya yi.
Barin masa wurin ta yi jikinta a mugun sanyaye.
'Innalillahi wa Inna ilaihin raji'un, Malam, a she dai shi d'in ne ba wani bare ba, wayyo ni Hureratu naga takaina, wannan wacce irin rayuwa ce na ke kan fuskanta? Ba laifi na ba ne, tun daga tushe bansan ta inda aka hau balle saukan amma k'addarar bata sanja zani ba, Allah Astagafirullah.'
Sune zantukan zuccin da Mama ke ambata har ta isa d'akinta ta yi masauki a bakin dago tallabe da kumatunta duka biyun, hawaye na bin samansu.
Baba kam zama ya yi a k'asa dab'as kamar kayan wanki dafe da k'irjinsa wanda ke bugawa da k'arfi, addu'a ma ya kasa ambata haka kunnuwarsa sun kasa yarda da abinda Mama ta furta masa, ya jima zaune sannan ya tashi tsaye ya k'urawa hanyar zaure idanu zuwa can harshensa ya motsa. 'Ta ya hakan zai faru? Kai dole na san inda kaina ke ciwo, wallahi ko zan rasa rayuwata ba zan bari Hurera ta fidda bak'in labarin nan ba, Anya Hurera bata da shafan shed'anu kuwa?.'
Amsar da baibawa zuciyarsa kenan ba ya zabura ya fad'a d'akin Mama a fusace.
Tana ganinsa ta mik'e ta bi gefensa ta fice zuwa d'akin Deejah ta murza key saboda in har ta tsaya za'a iya haifar d'a mara ido dan ta tabbata yarda ta kekijin zugi a zuciyarta abin da bai tab'a faruwa da su ba shi ne zai afkuwa wato fad'a da duka.
*** Ina isa k'ofar gidan Baba Umaru kiran Mama ya shigo wayana na d'auka tare da sanar da ita inda na tafi.
"Uwata kada inji zancen komi ya fito abakinki idan har kina son zaman aurena da Malam ya yi k'arko."
Shiru na yi zuciyata na kuma d'aukan zafi.
"Idan kinsan ba wanda ya ganki to ki juyo domin kina shiga Hajiya Inna zata gano da matsala ta sanarwa da Baba shi kuma ya yi alk'awarin raba aurenmu duk in wata matsala ya kuma fillowa a tsakaninmu, na san kinfi kowa son zamammu da Malam ya d'ore."
A jiyar zuciya na sauke tare da cewa mai Napep "Juya dani inda ka d'auko ni."
"Allah ya yi miki albarka."
"Amin."
Na amsa cikin rawar murya.
A kwanar fita layin motar Kawu Habibu ya sha gabanmu, k'iris ya rage bamu fad'a masa ba salati muka ambata da k'arfi, ni da mai Napep
"Kalli wani banza dai."
"Yi hak'uri Malam Kawuna ne."
"Amma dai bai da lafiya ne ko?"
Ban amsa masa ba na hango fitowar Kawu, yana isowa ya mik'awa mai Napep dubu d'aya tare da cewa "Sauketa, Allah bada sa'a."
Godiya ya yi masa amaimakon zagi dana zata zai auna masa tamkar yarda ya soma
' Kud'i kenan, masu gidan rana.'
Na ambata cikin raina sannan na fito na shiga motar, maimakon mu nufi hayar gida sai ya juyo dani gidan Baba Umaru.
"Ka kaini gida ne Kawu."
"Hajiya Inna ta umurceni da in kawo mata ke domin Annur yaron Yaya Shafi'i ya sanar mata da zuwarki tare da komawarki batare da kin taka k'ofar gidan ba."
Lumshe ido na yi ina tunano abin da zansanar mata domin kare martaban auren Mama wanda na ke burin ganin ya inganta har zuwa mutuwa.
"Ina son Mata mai halayyaki Khadija."
Ban bud'e ido ba amma na tabbata kallona Kawu keyi.
"A yau kuma a yanzu na k'ara nutso da son k'ara aure da mai kamanninki sak ko da ta hayayyane ba sai lalai mai siffarki ba."