Kenza eBookz

Damuwata complete novel - Chapter 8

Damuwata complete novel - Chapter 8

Damuwata complete novel Chapter 8: Damuwata complete novel Chapter 8. "Jiya Uncle ya kira wayarki kinyi barci."

3,349 words

"Jiya Uncle ya kira wayarki kinyi barci."

Ware idanu na yi cikin jin fad'uwar gaba.

"Na tabbata zai kuma kira."

"Dan girman Allah ki kashe wayar."

"Saboda me?"

"Bana son na yi magana da shi ta waya ne sai bayan na yi masa godiya baki da baki."

"Kinyi magana kam amma ba za'a kashe ba, kidai hanzarta zuwa yi masa godiya kafin ya kira."

"Insha Allah zanje."

"Good."

Shiru ya ratsa wurin zuwa can na katse shirun da cewa "Kince zaki sanarmin da wani sak'o daga Uncle."

"Zan sanar miki Aunty Deejah."

"Aunty kuma?"

"Eh."

"Uhm kin fiye neman zance kam."

"Muje na gaisar da Mama tare da kammala ayyukan gida idan mun gama sai muyi maganar."

"Motsa kai ta yi ta fice ni kuma na yi hanzarin kashe wayoyina gudun kiran Uncle sannan na biyo bayanta.

*TALLA.*

*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*

Sabulu (molato and black soap) Scrub Face cream Oil Body lotion Shower gel Kulachan Humra (White and black) Turaren tsugunon Turaren kaya Turaren wuta na d'aki Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)

*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.* [10/20, 12:07 AM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona) By Safiyya (Mrsjmoon)

E.W.F

*Shafin na aminai ne My Jamee, (Mom Aysar), dear Mamie waru, Mom sayyid, my sis VC, Oum Abdul A'had, My Fauxah and Dear Safiyya Abbas Gambo (Maman Mama) Allah ya bar k'aunarmu tare da albarka ga zuri'a duniya da lahira. Amin.*

Page 09.

Ko da na fito har Beebah ta shige d'akin Mama rufa mata baya zanyi Baba ya kirani da hannu na isa gabansa na durk'usa.

"Wannan wacece mara tarbiyya ce?"

Ya ambata cikin rad'a.

"Yayar K'awata ce Fanta."

"Shi ne Fanta tafita aiki da hankali?"

Shiru na yi dan bansan abinda Beebah ta aikata masa ba.

"Tana kallona ta kasa gaisar dani ta shige d'akin Hurera sabida da ita fitsararra ce, ni da gidana wata 'yar zamani ta shigo ta maidani ni da banza duk d'aya."

"Kayi hak'uri Baba taga kana lazimi ne."

"Bata dai da tarbiyya kuma zanci mutuncinta domin bata isa ta shigo muhallina ta wulak'antani ba."

"Bazata sake ba insha Allah Baba."

"Naji amma magiyanki bai isa dakatar dani daga k'udirina ba dan sai na cimata mutunci domin gaba ta kiyaye aikatawa wani irin hakan."

'Ya Salam Baba bazai tab'a sanjawa ba dai.'

"Ya kukayi da Hurera jiya?"

Da sauri na kallesa sabida hankalina ya nausa cikin zancen zucci.

"Na ce ya kukayi da Mamanki akan maganar yafemin dukiyanta?" Ya sake cillomin tambayar ganin na k'i cewa komi.

"Bata kulani ba."

"Kamar ya?"

"Ko da na yi mata magana kallona ta yi batare da ta ce komi ba."

"Hurera akwai bala'in wayau, ta gano ni na tursa-saki kenan? Shi kenan muzuba mugani shege ka fasa kud'i dai nacisa ba zan biya ba."

"Kudai sami masalaha Baba."

Harara ya cillomin na sunkuyar da kai.

"Iskancin banza, ko in na biyata uban wa zai gajesu in bani ba."

"Me kace Baba?"

A hanzarce ya kalleni sai kuma ya watsomin harara na yi saurin matsawa ya nunoni da yatsa cikin muryan gargad'i "Wallahi kika kuskura naji zancen nan a bakinta sai na lahira yafiki jin dad'i dan sai na il...

"Wallahi Baba ba maijinsa."

Na katseshi jikina na rawa.

'Dagamin hannu ya yi alamun in tashi, na mik'e nashige d'akin Mama da sauri. Beebah na hango tana gyarawa Mama zaman labule ita kuma Mama na zaune ta jingina da kujera tana karanta Hisnul Muslim. Wurin Beebah na nufa nasoma tayata ba jimawa muka kammala gyara d'akin ciki da falon sai lokacin Mama ta idar da karatun ta kirani na iso na zauna gabanta tare da gaisheta, amsawa ta yi cikin kallon Beebah.

"Sannu Habiba Allah ya baki miji nagari."

"Amin Mama."

"Baki da kunya Beebah."

"A'a Uwata barta ta amsa a fili domin addu'ar alkhairi abar amsawa kowa yaji ne."

"Mama ki rabu da ita, k'ila kowa irinta ce mai kunya har dana rashin hankali."

"Lahaula... Kinjita ko Mama? Kunya adon Mata ne kuma tana daga cikin Imani."

"Ya isa haka nan d'iyoyin albarka, ku muje ku samawa kanku abinda zakuci ni kuma nayiwa Malam abincin gargajiya."

"Me zakiyi dafa masa Mama?"

"Tuwo miyar kuka."

Matsawa kusa da kunninta na yi na ce "Wai Mama me ya kawosa gidan nan alhalin ba girkinki ba ne?"

D'an tureni ta yi Beebah ta sanya dariya b'ata rai na yi tare da ficewa suka rufamin baya suna dariya.

Kafin k'arfe Takwas ta yi mun kammala komi na shiga wanka ina fitowa Beebah ta shiga, ko mai ban shafa ba na zira doguwar rigar shadda na fito na sami Mama zaune a baranda tana cin tuwon da tayiwa Baba.

"Mama kice dama ke ce zaki ci tuwon ba wani Baba."

"Gaskiya ne ni ce na yi marmarinsa amma ganin Malam yazo sai na ce bari inyi mana sai gashi ya fice batare da yaci ba."

"Mama dama ba'a nan ya kwana ba?"

"Eh, ina fitowa bayi dan yin alwalaln subahi na tsinkayi bugan gidansa."

"Ikon Allah Baba kenan sanin halinsa sai shi kad'ai."

"Zauna ki karya dan zaki rakani gidan Baba Umaru."

"Aikam dama na kwana biyu ban kai musu ziyara ba, dik na yi kewar Hajiya Inna."

"Itama ta yi kewarki, shiyasa na ce muje tare sabida jiya ta yi ta fad'a wai ban barinki kinayin zumunci da su kodan basu suka haifeni ba."

"Kai Hajiya Inna ba ruwanta da b'oye-b'oye."

"Hakan shi ne dai-dai Uwata, a duk inda kike to ki zamo mai gaskiya da fad'ar gaskiya komin d'acinta, domin gaskiya ita ce jigon tsanin ginuwar Imani a Ruhi."

"To Mama, Allah ya kara mana Imani."

"Amin Uwata."

"Mama bamu sami damar yin Azimin ba."

"Zamuyi dama kinsan komi nufin Allah amma tunda munyi alk'awari zamu cikashi insha Allah."

"Allah ya bamu iko gobe mu wayi gari da shi."

"Amin."

"Insha Allah zan tayaku domin aikin neman lada ba'a sanyin jiki."

"Godiya muke Habibatu."

"Mama babu godiya tsakaninmu sai sanya albarka domin tamkar Deejah na ke gareki."

"Madallah to Allah ya yi muku albarka."

"Amin."

Muka amsa a tare.

Muna kammla karyawa Beebah ta koma d'akina ta kwanta ni kuma na fice zuwa yiwa Uncle godiya. Ina zuwa bakin get d'in gidan naji k'irjina ya harba wani tsoro ya jiyarceni sai na soma karanto addu'a, na koma da baya na zauna a k'asar bishiyar dake fuskantan gate d'in na tsirawa bencin da Baba maigadi ke zama ido, tunanin yarda Aunty Nafisa taza kalleni na ke yi saboda babban abinda na tsana kallon banza wanda ya zame mata tamkar ibada. Kimanin mintoci goma ina zaune cikin nazari sai kawai na tashi cikin kuzari na doshi gate d'in domin yanzu na sami natsuwa sama da d'azun. Ina tura k'amin k'ofa Mai gadi na bud'ewa Uncle gate ganina sai ya fasa fita ya kashe motar na k'araso na russuna gefen da yake zaune na gaisheshi, bai amsa ba ya bud'e motar ya fito ya jingina da jikin motar, kallonsa na yi ta gefen ido, idanunmu ya had'u da juna sai na yi sauri sa ke russunawa kafin inyi magana na tsinkayi muryansa.

"Lafiyalau Khadija mai gudun makwaftanta."

Murmushi na yi tare da cewa "Naga sak'o nagode sosai, Allah yasa kafi haka, ya jik'an mahaifa, ya yiwa zuri'a albarka ya kayi dace da gidan Aljanna mad'aukakiya."

"Amin ya rabbi tare da ke."

Motsa yatsuna na yi suka bada sauti, ya ja fasali tare da cewa "Duka sak'on sun sameki?"

"Eh."

"Har na wajen Beebah kin karb'a da hannu biyu?"

Shiru na yi bugun k'irjina ya dawo sabo.

"Da alama Beebah bata sanar miki da sak'on nan ba ko Khadijatu?"

"Eh bamuyi maganar ba amma nasan zata sanarmin."

"Ok, shigo ki rakani yiwa su Bintu tsaraba."

"Mama zata aikeni ne Uncle."

"Ok, tafi gani nan shigowa neman alfarman ta aramin ke."

"A'a Uncle muje sai na sanar mata a waya "

"Bani number wayar nata."

Karanto masa na yi, ina tsaye ya kirata sun jima suna magana sannan sukayi sallama ya kalleni na sunkuyar da kai.

"Khadijatu mai kunya ce."

Ya ambata cikin dariya, murmusawa na yi.

Da kansa ya budemin kusa da driver na zauna sannan ya shiga muka fice. Tafiya mukeyi tamkar kurame sannan tuk'in a hankali yakeyi na gane hakan ne jin yarda ake zabga mana horn amma baisa ya k'ara gudu ba, wani d'an a daidaita sahune yazo gefena ya zabgo masa zagi, na rafka salati tare da neman masa shiriya wurin Allah.

Wani ajiyar zuciya na ji ya saki tare da k'ara gudu yana kallon titi ya ce "Ke d'in Uwa ce ta gari Khadijatu mai nemawa d'iyoyinta falalar Allah tun kafin su iso duniya."

"Uhm."

Kawai na iya ambata tare da maida fuskata gefe.

"Kina da bambanci mai tazara tsakaninki da Nafisa domin da ita ce maida masa da martani zatayi harma da k'ari dan ta iya manyan zagi tamkar jikar maguzawa."

"Ai Uncle ba kowo ne ke iya mallakan hankalinsa ba ya yin da wani ya zagesa, banga laifin Aunty Nafisa ba dan ta ramawa mijin zagin da akayi masa."

"Khadijatu shi komi na duniya d'an hak'uri, zagin nan fa bai mannewa a jiki balle ace zai zama tambo, idan kabar wanda ya aikata da halinsa kansa ya zaga kamar yarda kika aikata sai zagin ya koma masa ke kuma kika sami lada yayin da kikayi masa addu'a."

"Allah ya k'ara mana hak'uri."

Na ambata ahankali domin zantukansa gaskiya ne.

"Amin."

Shiru ya ratsa zuwa can na tsinkayiaganarsa. "Ina neman alfama idan Beebah ta sanar miki da sak'ona ki amince ba dan na isa ba."

Shiru na yi gabana na fad'uwa, nidai ban k'aunar jin sak'on nan sam. Latsa horn ya yi na kalleshi da sauri ya saukemin murmushi, ya maida hankali kan titi ya cigaba da cewa "Bazan takuraki ba Khadijatu, na bar miki zab'in ranki, dik abinda kika zanta da ruhinki ki sanar mata domin lamari ne dake buk'atar amincewar ruhi da ruhi."

Still ban ce komi ba shima ganin nak'i tankawa sai ya sauya zancen da jefomin tambayoyi game da rayuwar yau da kullum, ina bashi amsa dai-dai fahimtana, kuma na fahimci yana gamsuwa da bayanen. Da k'arfi da yaji dai Uncle ya maidani masuraciya domin bai bar bakina ya huta ba har muka iso babban kanti.

*** *** Dai-dai sadda Uncle ya bud'ewa Deejah k'ofa tashige, Nafisa na isowa volcany sam bata hango Deejah ba amma ta shiga tunanin da wanda mijinta zai fita. Ta ke zuciyarta ya hasko mata da Beebah ce ko Fanta.

"Kai amma ai ba zai bud'e musu mota ba."

Jim ta yi cikin jin fad'uwar gaba, sai ta sakko zuwa wurin Baba Mai gadi, sadda ta jefo masa tambayar rud'ewa ya yi, tsawa ta daka masa tamkar yaronta alhalin ya yi jika da ita.

"Hajiya da Khadijatu ce."

"Khadijatu kuma? Wacece ita?"

"K'awar Fanta."

Wani ashar ta zabga wanda ya firgita Baba maigadi ya ja da baya ta nunosa da yatsa idanu jajur cike da tarin masifa, kafin ta zabga masa zagi ya shige d'akinsa da sauri ya kulle k'ofa domin da jimawa kallon mara hankali yakeyi mata tun sadda ta tab'a rufeshi da fad'a har da daga hannu kamar zata dukeshi dan kawai ya bar yaronta Hafiz ya fita waje wasa da yaran unguwa bisa tsautsayi mashin ya bugeshi yasami gobcewar gashi a hannu.

"Gara Alhaji ka auro mai hankali da da sanin darajar bil'adam ko wannan sokuwan ta yi hankali ta gane me duniya ke ciki. Zan cigaba da yi masa addu'a akan Allah ya bashi Khadijatu amatsayin mata, tabbas da kagama hayewa kam, yarinya mai hankali da aiki da ilimi, hak'ik'a gidan zai gyaru idan hakan ya kasance."

Haka dai maigadi ya yi ta zancensa shi kad'ai kulle da d'aki.

Nafisa kam a tsiyace ta koma cikin gida direct d'akin Fanta ta shiga ta sameta kwance tana amsa wayar saurayinsa Abul Abbas.

"Ke tashi in aikeki wurin Uwar Deejah."

Mik'ewa tsaye ta yi jikinta na rawa tare da datse wayar, tama kasheta baki d'aya ta dubi Aunty Nafisa idanu waje.

"Yes wurinta zan aikeki, ki ce mata na ce ta datse banzan alak'ar da ta k'ulla tsakanin d'iyarta da mijina tun kafin na d'auki mataki wanda ba mai dad'i ba ne dan zan iya kashe 'yarta har lahira in har ta sa ke ta auremin miji."

Lumshe ido Fanta ta yi ta koma ta zauna gefen gado ta yi tamkar ba ita Aunty Nafisa ke bawa umurni ba.

"Fanta ko dai da had'in bakin ki cikin lamarin ne?"

"To Aunty ai ban fahimci inda zantukanki suka dosa ba ne, Deejah dai kinfi kowa sanin ta kwana biyu bata shigo gidan nan ba balle su had'u da Uncle haka kinfi kowa sanin ingantaccen tarbiyyanta amma sai naji kinzomin da zancen cin mutunci, to a gaskiya bazanje ba, kina da k'afa kije mana amma kafin nan ki sani Mama bata d'aukan raini, idan kikayi mata fitsara zata ladaftar da ke kuma ki tuna kina da tambo a wurinta, kika kuskura kika taka mata gida da tijara komi zai iya faruwa wanda na rashin dad'i ne haka Uncle ya sami labari kinfi kowa sanin abinda zai faru, at end sai ince Allah kaiki lafiya ya dawo da ke da idanu lafiyayyu."

Abin mamaki duk zancen da Fanta keyi mata kasak'e Nafisa ta yi tana kallon bakinta har ta dasa aya bata motsa ba. Ganin haka sai Fanta ta fad'a toilet da gudu domin ta kwana da sanin shirunta ba alkhairi ba ne.

"Shegiya da dai kin zauna kallona wallahi dana illata miki bakin rashin kunyar."

Ta ambata ganin Fanta ta nemi mab'oya, ficewa ta yi cikin nazarin zantukan.

"Maganar Fanta da k'amshin gaskiya fa na san wacece Mama zata iya nad'amin duka in har na rattafa mata sak'on da na bawa Fanta, yanzu me ye abinyi? Bari in jira dawowar Abban Hafiz naji abinda yake nufi da fita da d'iyar makwafta unguwa alhalin gani matarsa ta sunnah bai fita da ni ba. Kai wallahi namiji munafuki ne yanzu ya rasa abinda zai sakamin da shi sai neman wannan 'yar banzan yarinyar mai siffan munafukai. Oh ni Nafisa ina ta murna ta tsorata ta daina shigomin gida a she suna manne a waje, kai wallahi ko me zai faru sai dai ya faru amma sai na yiwa uwarta da bokan ubanta kashedi akan mijina dan su rabashi da d'iyarsu."

Tana ambatar haka ta janyo dogon hijab ta jira ta sakko k'asa cikin had'a matakala bibiyu ta fice harabar gidan a tsiyace. Bawan Allah maigadi na hangota ya kuma d'iba da gudu ya shige d'akinsa ya kulle, ganin haka suma sauran ma'aikatan, masu kula da fulawa tare da mai wanki da guga suka kwasa da gudu suka nemi mab'oya dama maigadi na tsakiyan basu labarin abinda ya faru ne d'azun sai gata da fito a fusace."

Ita kanta lamarin ya bata dariya, ta murmusa ta fice tana tsine musu a zuciyarta ganin sun maida ita mahaukaciyar karfi da ya ji.

*** "Kin ga ne Khadijatu fito mu shiga ki zab'i abinda kike so kawai na maidaki gida in yaso idan sun dawo sai suzo da kansu su zab'i abinda ransu ke so."

Na tsinkayi maganar Uncle, sadda ya yi parking a harabar Babban Kantin.

"Nikam ban son komi, nagode mutafi gida kawai."

"Ko turaruka ba kya so?"

"Uncle d'awainiyar ta yi yawa, mutafi kawai."

"Na san ke d'in mai son k'amshi ce dan Fanta tasha sanarmin da na siyo mata turare duk in na yi tafiya wanda zata baki gift lokacin birthday naki dan haka ki amince na zab'o miki."

"Shi kenan Uncle zab'o d'in."

Na furta kaina sunkuye.

"Thank you Nana Khadijatu."

D'agowa na yi na zubawa bayansa ido har ya shige cikin Kantin, sauke ajiyar zuciya na yi inajin wani kalan natsuwa na ratsa ruhina.

"Uncle ya san kansa matuk'a dole matarka ta yi kishinka."

Na ambata cikin rad'a tare da bud'e kofar motar na fito na jingina ina kallon mutanen da ke kai kawo. Lumshe ido na yi ina shakar iskan bishiyoyin da suka k'awata harabar Kantin.

"Wow gaskiya na ji wani nishad'i a ruhina tunda na doso Kantin a she dai zanyi gam da takar ne wato gamo da matar A...

Da sauri da d'aga masa hannu, na hanashi k'arasawa, langab'e kai ya yi na sauke masa murmushi.

"Ina godiya da wannan kyauta Malama Khadija."

"Na me fa?"

"Na sadakan murmushi da kikayimin yanzu."

Nuno shi na yi da yatsa ya mik'o hannu tamkar zai kama yatsar na janye ya sanya dariya, na girgiza kai tare da gyara tsayuwa a jikin motar.

"Aliyu kana da ban dariya wanda a da ban lura da hakan ba sam."

"K'auna kansa ka soma lura da d'abi'un mosoyi."

"Uhm ka ganka ko da iya salon zance."

"Gaskiya ne Deejah, ni kaina ban san kina magana mai tsayi irin haka ba sai yanzu."

"Banda sharri dai Yallab'ai."

"Allah ki yarda kawai."

"To naji amma yarda bai zama do...

Bud'e k'ofar motar da Uncle ya yi da k'arfi ya katsemin abinda zan furta. Na kalli Aliyu shima ni yake kallo cike da tambayoyi sai na yi masa bye da hannu na shiga motar, ina zama Uncle ya fizga motar a guje ya bud'e Aliyu da hayak'i, waigawa na yi na hangosa yana karkad'e fuskansa sai na ji raina ya b'aci, na juyo muka had'a ido da Uncle shima fuskansa a had'e, tura kaina na yi tsakanin cinyoyina k'irjina na harbawa da sauri da sauri.

*TALLA.*

*Ina kuke Mata 'yan kwalisa masu bawa fatarsu 'yancinta musanman babban kadararku wato fuska. To ga dama ta zo muku cikin sauk'i wato samun kayan gyarar fuska da jiki mai inganci na organic wanda aka samar da su da abubuwa masu nagarta. Duk wacce K'uraje, Tabbai, Sunburn, kyafsi suka b'atawa fuska muna da maganin da fuskanta zai dawo fes, sumul, rangad'ad'au. Haka a fannin fatar jiki shima muna da kayan da zaiyi laushi, sulb'i tare da haske mai kyau. Ga kayan kamar haka:*

Sabulu (molato and black soap) Scrub Face cream Oil Body lotion Shower gel Kulachan Humra (White and black) Turaren tsugunon Turaren kaya Turaren wuta na d'aki Garin d'a'a (domin k'an-k'aro martaban aure a turaka)

*Duk za'a samesu a farashi mai rahusa, mai buk'atar d'aya ko sari a tun-tub'emu a wad'annan numbers d'in 08132166848 ko 08147491137. Sai munjiku.* [10/21, 2:16 PM] 💘: DAMUWATA (Sanin abin adona) By Mrsjmoon.

E.W.F.

*Shafin na ku ne 'yan uwa, abokai na gari, dukkan daukakin yan EXQUISITE WRITER'S FORUM. Allah ya bar k'auna mara algus. Amin ya rabbi.*

Page 10.

'Me hakan ke nufi, na jin harbawan zuciya dik in na had'a ido da Uncle? Please zuciyata kada kiyiwa first love d'ina haka, wallahi ina son Aliyu.'

"Shi ne wane?"

Maganar Uncle ya dawo dani duniyar zancen zuccin dana afka, d'agowa na yi na kalleshi kad'an sannan na amsa a ladabce.

"Classmate d'ina a tahfiz kuma abokin koyarwana duk a can."

"Only wad'annan ne alak'arku?"

"Yana s...

Sai na yi shiru na kasa k'arisawa.

Shima bai kuma cewa komi ba ya cigaba da gudu saman kwalta sai da muka sauka titi muka shigo layin unguwarmu sannan na kuma tsinkayar maganarsa.

"Yana sonki ko kina son shi?"

Idanu na tsira masa batare da na amsa ba, shima kallona ya yi ya sauke murmushin gefen baki.

"Naji dad'i da ya kasance fagen ina da d'an takara domin hakan ya alamtamin cewa mallakan Nana Khadijatu ba abu mai sauk'i bane, sai an zage dantse, sai anyi kamar anayi sannan tamkar fad'a ce a filin daga inda kowa zaiso ya sami narasa akan abokin karawarsa, dan hakan zan zamo jarimi ta ko wani fuska domin hanin na yi nasarar sunkuce Nana Khadijatu amatsayin mallakina."

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull