Kenza eBookz

Duhun dare book 1 complete novel - Chapter 3

Duhun dare book 1 complete novel - Chapter 3

Duhun dare book 1 complete novel Chapter 3: Duhun dare book 1 complete novel Chapter 3. Mutuwa ta yi! Tabbas wannan Ihun da ya ji babu makawa mutuwa tayi…

3,359 words

Mutuwa ta yi! Tabbas wannan Ihun da ya ji babu makawa mutuwa tayi tunda already Doctor Anil ya tabbatar masa da cewa kokawa take tsakanin rayuwa da mutuwa,kuma a kowane irin lokaci za ta iya mutuwar. To amma mutuwa miyasa yanzu? Miyasa za ki ɗauke ta yanzu bayan iyayenta suna kwance a cikin mawuyacin hali ga Mukarram shi ma baya nan???

✍️ OUM-AMEER ✍️ *D U H U N D A R E* *A 2026 N O V E L* *BOOK ONE*

*ADABI WRITER'S ASSOCIATION*

*AMEENA IBRAHEEM* *OUM-AMEER* Arewapen: @Oumameer2671 Wattpad: @Ummu-Amir

*PAGE 3*

Gefen su Oga Jud kuwa. Misalin ƙarfe biyar na yamma. 5:30pm, Zaune suke a bakin swimming pool na katafaren Gidan na su. Wasu laptop ce a gabansu suna aiki da ita, wasu lissafin kuɗi suke domin kassafawa kamar yanda suka saba.

Wayar Oga Jud da tayi ringing ce ya ɗaga tare da kara ta a kunnensa yace.

"Alaji ka karɓi kayan ka?"

Daga can ɓangaren mutumin ya ce.

"Na karɓa. But where is the money?"

Karan sigarin da ke hannunshi ya wani zuƙa da ƙarfi sannan ya yi wurgi da ita ya furxar yana mai jinjina kai.

"Kuɗi namu ne Alaji. Kai kasan ba sa daga cikin jadawalin aikin da ka bamu, abin da ka nema ka samu, komai an yi shi yanda ka ce babu kuskure a ciki..."

Daga can ɓangaren Alajin ya katse shi da faɗin.

"Yes! Aiki ya yi kyau. But dole ku bani nawa kason daga ciki because nasan cewa manyan kuɗi ne kuka karɓa..."

Yanzu kam ƙara gyara tsayuwar sa ya yi da kyau ya ɓata fuska tamkar yana a gabansa ya ce.

"Alaji! Listen very well...Bana tsallake iyakar mutum, haka zalika bana son nima a tsallaka iyaka ta. Ina da rules ɗina, Aikin da ka bamu ya kambala ba tare da an samu kuskure ba. Ka aiko mana da cikon kuɗinmu, ka manta da kuɗin da mu ka karɓo domin babu naka a ciki, idan kuma ka ce za ka kawo mini wasa...tabbas zan kashe ka,zan shafe tarihin ka ka zamto tamkar ba'a yi ka ba. Na rantse da Allah kasan zan aikata..."

Cikin tashin hankali Alajin ya ce.

" Kwantar da hankalinka..eh..Ahm! daman wasa nake maka. Zuwa an jima In Sha Allahu zan tura maka cikon kuɗ..."

Kashe wayar ya yi kai tsaye ba tare da ya jira ya sauke maganar tasa ba.

Waigawa ya yi ya kalli Daniel (Bado) dake ta faman lissafi ya ce.

"Daniel...ka ajiye kassafa kuɗin nan ka bari an jima idan ya ƙarasa ciko mana kuɗin aikin sai a haɗa a turawa kowa nasa. Idan kuma yace zai kawo mana wasa ku bi duhun dare ku sheƙe min shi har lahira."

Jinjina kai Daniel ya yi yace.

"OK Oga."

Wata takarda Bash (Ashu) ya fito da ita daga cikin wani file ya ce.

"Wannan shi ne aikinmu na gaba, Habib (Tiger) ka karɓa Ka shirya bayanai sannan ka turawa kowa.."

Nan suka zauna suna ci gaba da duba abubuwan da ke gaban su.

Yayin da Jak ke can kwance a ɗaki tun baccin da ya kwanta bayan sun dawo daga operation ɗin bai farka ba sai yanxu. a hankali ya shiga motsawa jin gabaɗaya yanda gaɓoɓin jikinsa suka saki yana mai jin tamkar ba za su sake moruwa ba.

Daƙyar ya iya juyawa daga position ɗinda yake tare da saka hannayensa duka biyu ya dafe kansa jin yanda yake wani irin tsananin sara masa tamkar zai tsage ya rabe gida biyu.

"Abbah!!!"

Wannan itace kalmar da ta fara zuwa a masarrafar tunaninsa yana mai jin yanda muryarta ke ratsa dodon kunnen sa cikin wani irin taratsi tamkar yanzu ne abun yake faruwa.

Wata irin zabura ya yi ya miƙe zaune yana mai jin duniyar na juyawa da shi ƙwaƙwalwarsa kuma na daɗa hautsinawa.

A hankali hotunan abubuwan da suka faru a daren jiya suka shiga dawo masa bit by bit tun daga farko har ƙarshe.

Wani irin tsalle yaji zuciyarsa ta yi wanda a lokaci ɗaya ya ji wani irin tashin hankali ya mamaye masa zuciya.

Cikin zafin nama ya diro daga kan gadon da yake kwancen direct ya fito parlour yana rarrabo idon inda zai gansu. Ganin ba kowa a nan yasa ya fita waje da sauri tamkar zai kifa domin tashin hankalin da yake ciki a yanxu yama zarta misali, tuni ya nemi gajiya da wata kasalar da yake ji ya rasa.

Yana zuwa gaban Oga Jud ya wani turasa da ƙarfi sai da ya faɗa cikin swimming pool ɗin ba tare da ya shirya ba.

Ganin hakan yasa duk su ka miƙe a tare cike da mamaki suna kallonsa.

Cikin mamakin shima Oga Jud ya fito daga ruwan yana mai ƙure fuskarsa da kallo ya ce.

"lafiyarka kuwa?"

A fusa ce ya ce.

"Miyasa kuka cutar da wannan yarinyar??"

Cike da mamaki Oga Jud ya kalle shi domin shi har ya ma manta da wannan zancen ya ce.

"Wace yarinya??"

Idonsa a buɗe ya ce.

"Kasan yarinyar da nake nufi Oga Jud, don't pretend. Wannan yarinyar ta gidan Alhaji Mas'ood Galadima."

Jinjina kai Oga Jud ya yi sannan ya ce.

"Ohh! Wai operation ɗinmu na jiya kake magana a kai? To miye abun da ya dameka da wannan? Babu abin da tayi mana kawai dai tana cikin aikin da Alaji ya bamu yace ita fyaɗa za'a yi mata..."

Cikin wani irin tsananin ɓacin rai yana mai yi masa wani mugun kallon ya ce.

"And Why me? Why me Oga Jud??"

Hannu Oga Jud ɗin ya ɗaga masa ya ce.

"Hey! Point of correction. Ba suna na Oga Jud ba, sunana OGA BADRU kamar yanda ka sani. Kafi kowa sanin cewa sunayen da muke amfani da su a lokacin da za'a fita aiki Saƙaƙƙun sunaye ne da muke ƙirƙirarsu a lokacin da zamu fita aiki, kuma daga zaran mun dawo shikenan sun zama expired domin gujewa matsala. Kada ka sake kirana da Oga Jud...Kai da duk wanda ke wurin nan ma, kowa ka kira shi da sunansa... "

Wata irin shaƙa Jak ɗin ya kaiwa kwalarsa a fusa ce yana faɗin.

" Ba ka bani amsa ta ba. Tambayarka nake Why me? Duk cikin yaranka ba ka ga wanda za ka saka ba sai ni? Miye ya haɗani da ita da har za ka sanya na aikata mata haka? Abin da ya kai ni daban kuma abin da ya kai ku daban. Why did you involve me?"

Da ƙarfi Oga Badru ya saka hannayensa ya ture Jak ɗin sannan ya ce.

" Because naga cewar kana son ɗaukar fansar mahaifin ka ne. Kada ka manta mahaifin ta shi ne ya kashe maka mahaifi, hakan yasa naga cancanta ka ƙuntata musu sosai kamar yanda kai ma ka ƙuntata...sanin irin halin ka ne yasa na saka su Bash suka haɗa maka ƙwayoyi masu saka matsananciyar sha'awa a lemu da kuma canja tunani,wanda ba don fyaɗen kaɗai nayi maka hakan ba, hatta wurin kashe mahaifin na ta nasan cewa kana iya kofsawa. Kuma sai ga shi,ban yi kuskuren hasashe ba, duk da wannan shirin da na yi maka sai da ka kofsa ɗin Azaan. And ni na yi komai ne domin ka samu cikar burin ka na ɗaukar fansa a wannan daren..."

Wani irin girgiza kai ya shiga yi yana mai jin wani iri a ransa ya ce.

" Na yi nadamar sanin ka a rayuwata Oga Badru! Na yi matuƙar baƙin cikin haɗuwa da kai....Cutar da rayuwar mace musamman irin wannan zunubi ne, idan har wannan shi ne taimakon, to Allah ya tsinewa taimakon naka...."

Hannayensa ya saka ya dafe kansa, sannan ya shafo tundaga saman goshin sa har zuwa bayan ƙeyarsa yana mai jinjina kai sai kuma ya sake ɗagowa ya kalle shi cike da hauka ya ce.

"Kana gani fa...Hatta mahaifin na ta kasa kashe sa na yi, duba da yanda iyalinshi suke kuka, suka dogara da shi. shin idan na kashe shi a gaban su how are they going to feel? Ni ɗin ba kamar shi ba ne, ni ba zan iya kisan kai ba...Na bar shi...na barshi da Allah, shi ne wanda zai yi mana sakayya a gobe ƙiyama...but! Ya zama dole na na koma wurin wannan yarinyar,... "

A tare suka waigo suka kalle shi lokaci ɗaya jin wata irin yasassar maganar da hankali ma ba zai ɗauka ba.

Wata irin damƙa Oga Badru ya kai wa hannun Jak ɗin a ruɗe ya ce.

"AZAAN...Are you out of your senses? Noo! Ina ga ka fara hauka ne Azaan."

Wani kallon ya yi wa Oga Badrun ya ce.

"And nobody will stop me!"

Cikin wasu irin kalamai masu nuna alamar gargadi Oga Badru ya ce.

"I'm warning you Azaan! A very big sound warning! Lallai ka karɓi kuɗin ka kawai ka kama gabanka. Idan ka kuskura ka amince da wannan gurguwar shawarar da tunaninka ke baka, to fa kana cikin hatsari, domin daga lokacin da ka nuna kan ka gare su, daga lokacin tarihin ka zai shafe har abada."

Jinjina kai ya yi bakin gaskiyarsa ya ce.

" ban san mi ya kamata na yi ba, amma kuma ya zama dole na je naga halin da yarinyar mutane take ciki. Idan har wani abu ya same ta, har abada ba zan yafewa kai na ba..."

A tare su ka miƙe suka sha gaban shi kowanen su da fuskar shanu tamkar za su rufe shi da duka.

Girgiza kai Oga Badru ya sake yi a karo na barkatai sannan ya kalli Azaan ɗin ya ce.

" Ba za ka aikata hakan ba Azaan! Ni ba zan taɓa bari ba..."

Shi ma da wata irin wuta a kalamansa ya ce.

"Ba bu wanda ya isa ya dakatar dani daga cikin ku."

Wani irin karyar da wuya Oga Badru ya yi tare da yi masa wani kallon yace.

"Shekaru goma sha takwas na kwashe ina wannan harakar, daidai da rana ɗaya ban taɓa kuskure wa ba. Babu kuma wanda ya taɓa kawo min matsala, a kanka kuma ba za'a fara ba Azaan. Kada kace za ka yi wasa da rayuwarka..."

Ratsa tsakaninsu Daniel da Bash ya yi kai tsaye ya wuce.

Cikin wani irin mamaki Oga Badru ya shiga kwala masa kira amma sam ko alamar juyowa bai yi ba. Abu kamar wasa sai ga shi sun gan shi ya shiga gidan ya fito ya figi mota da ƙarfi.

" Prince...Kada ka ɗaga ƙafa, just Shoot him. We have no choice."

Oga Badrun ya faɗa yana mai kallon inda Prince ɗin yake tsaye.

******

Ya Muhammad kuwa, a hankali ya shiga maida numfashi jin cewa tana raye ba ta mutu ba. Kawai dai har yanzu likitocin sun kasa shawo kan ta ne har yasa su Mubarak ruɗewa domin da ta ja wani irin numfashi sun za ta ta mutun ne kamar yanda Dr. Anil ya faɗa.

Yana nan a tsaye jingine jikin ƙofa Yaya Amina ta zo da waya a hannunta a hankali ta kara ta zuwa kunnensa wanda shi sam bai ji zuwan na ta ba, sai saukar maganar Mukarram da ya ji tana karaɗe masa dodon kunnensa.

Daga can ɓangaren Mukarram ɗin ne ya ce.

"KATEH! (Ma'ana yaya) Miyasa ba za ka yi magana da ni ba? Na fa riga na ji komai da ya faru tun ɗazu. Idan ka buɗe bakin ka, kai ko Mubarak ku ka yi mini bayanin gaskiyar abin da yake faruwa, shi ne zai sa hankalina ya kwanta. Amma gujewa magana da ni da kuke yi shi ke sa ina ƙara jin karaya. Dan Allah ka faɗa mini miye ya faru? "

Jinjina kai Yaa Muhammad ɗin ya yi tamkar yana gabansa a rauna ne ya ce.

" Abubuwa da yawa sun faru marasa daɗi Mukarram. Na rasa ta yanda zan fara yi maka bayanin ne. But duka su ukun suna cikin mawuyacin hali..."

Nan ya yi masa bayanin komai yanda ya faru sannan daga can ɓangaren Mukarram ɗin ya sauke wata irin nannauyar ajiyar zuciya sannan a hankali ya ce.

" Ba komai. Allah yana sane damu Kateh,muna roƙon ya bamu ikon cinye wannan jarabawar ya sanya mana haƙuri da dangana ga duk wani abin da zai riskemu. A tsaurara bincike sosai. Muna kan hanya zamu je Airport In Sha Allah. Sai mun iso."

Janye wayar ya yi tare da kallon Yaa Amina wacce ke ta sharɓar hawaye ya ce.

" Thank you."

A hankali ta jinjina kanta ta ce.

" I'm sorry! Shi ne ya kira da kansa yace na baka..."

"Ba komai Amina."

Muryar Mubarak ya ji a bayansa a hankali yana faɗin.

"Daddy Ridwan ya zo yana ƙasa, Baba Salisu shi ma yana ɗakin Abbah tun ɗazu."

✍️ OUM-AMEER ✍️ *D U H U N D A R E* *A 2026 N O V E L* *BOOK ONE*

*ADABI WRITER'S ASSOCIATION*

*AMEENA IBRAHEEM* *OUM-AMEER* Arewapen: @Oumameer2671 Wattpad: @Ummu-Amir

*PAGE 4*

Da sauri Oga Badru ya ɗagawa Prince ɗin hannu ganin yanda Azaan ɗin ke ta faman danna horn but gate ɗin yaƙi ya buɗe,jinjina kai ya yi tare da kallon Prince ɗin ya ce.

"Wait! Wait prince"

Dakatawa ya yi suka zuba ido suna kallon Azaan da mamakin abin da ya hana shi tafiya.

Muryar Aroun (James) suka ji yana faɗin.

"Na rufe gate ɗin ta yanda ba zai iya fita ba."

Cikin farin ciki Oga Badru ya ce.

"Thank you so much Aroun. Haƙiƙa Aikin ka yana kyau. Tamkar kar ka koma ƙasar ka haka nake ji domin kana da matuƙar basira da kaifin tunani."

Daga haka ya taka ya isa har bakin gate ɗin inda ya tarar da Azaan ɗin still yana ta danna horn ɗin ba tare da ya sare ba.

Ganin Oga Badrun a gaban motar ne yasa ya fito daga ciki yana wani irin ɓata rai ya ce.

" Ka buɗe mini ƙofa na fita!!!"

Jinjina kai ya yi yana mai kallon fuskar Azaan ɗin ya ce.

"I will, but ina da wata 'ƴar magana wacce daga ita na baka damar yin duk abin da ranka yake so.."

A hankali ya taka ya shiga zagaye shi yana taku a hankali ya ce.

"Kana ta iƙirarin cewa kai sai ka je Kaga halin da yarinyar take ciki. Shin kana da masaniyar cewa idan kaje kuka yi ido biyu da ahlinta ba za su ƙyale ka ba? Yarinyar yanxu haka duk da ban sani ba, ina da tabbacin cewa tana gadon asibiti. Saboda haka, ba za ka ganta ba. Abu na biyu kuma mai matuƙar muhimmanci shi ne...Shin idan kai ka shirya salwantar da rayuwar ka to ita mahaifiyar ka fa? Kada fa ka manta sai da ta gargaɗe ka. Yanzu kuma da ka tsallake sharaɗinta ka karya alƙawarin da ka ɗaukar mata da umarninta ya ya kenan tsakaninku zai kasance? Duk ka bi ka wani ɗaga hankalin ka wai kai ka yi fyaɗe. To me..wannan ɗin is common, domin na yi yafi dubu kuma babu abin da ya faru. Da fyaɗen da kashin kai da ka yi niyyar yi wanne ne yafi zunubi?"

Da ƙarfi ya runtse idanunsa, yana mai jin yanda kalaman mahaifiyar tasa ke dawo masa tamkar yanzu ne take yi masa gargaɗin.

" Ban amince da ka nemi wata fansa ba! Tun da har hukuncin ya zo a haka, to ina roƙon ka alfarma don Allah mu barwa Allah. Na rasa mahaifin ka, ba zan iya jure rasa ka ba, idan wani abu ya sameka tabbas zan kasance a baƙin ciki da dana sani fiye da wanda nayi a baya da kuma wanda nake ciki a yanzu. Saboda haka, Ka bar wannan maganar ta wuce har abada. Idan kuma kaje bayan idona ka aikata wani abun to lallai kaje ka nemi wata uwar ba ni ba..."

Wani irin mugun duka ne ya kaiwa glass ɗin motar wanda duk ƙarfinsa sai da ya fashe ya tarwatse. Sosai hannunsa ya shiga zubar da jini, duk da haka ba wannan ɗin ya ke ji ba. Shi wannan wace iriyar mummunar ƙaddara ce? Ta ina zai fara?

A raunane ya sake ɗago ido ya kalli Oga Badru, murya a karye ya ce.

" And duk da cewa kasan na faɗa maka wannan kuma shi ne ka yaudare ni? Kasa na aikata mummunan kuskure, kuskuren da ba zai taɓa gyaruwa ba. Zan iya faɗawa mahaifiyata cewa na kashe Alhaji Mas'ood ta yafe min, but yiwa wannan yarinyar fyaɗe..."

Cikin ɗaga murya oga Badru ya ce.

" Common Azaan ka daina yin kamar babu ruwan ka a cikin wannan lamarin! We plan everything together, yes! Da Kai muka shirya komai, and kai ne da bakinka ka faɗamin cewa kana son kashe wanda ya kashe maka mahaifin ka. But abin mamaki yanzu kuma kana ƙala mini laifin ni kaɗai kamar janyo ka nayi don dole.."

Juyawa ya yi kawai ya koma ciki tare da barin motar nan bakin gate ɗin.

Jikin ƙofar ɗakin ya jingina tare da lumshe idanunsa tsawon lokaci yana ta tunani barkatai na neman mafita.

Ya jima yana saƙawa yana warwarewa, wanda daga ƙarshe ya wuce toilet ya yi wanka sannan ya ɗoro alwala ya fito ya shiga jera salloli.

*******

Gidan Alhaji Mas'ood kuwa.

Zaune Alhaji Mas'ood ɗin yake an rataya masa bandage a wuyan sa wanda ya tallafe masa hannun sa da suka harbe shi. Jingine yake jikin kujerar sosai tare da lumshe idanunsa waɗanda suka yi masa nauyi sosai akan rashin wadataccen baccin da baya samu a 'yan kwanakin nan. Muhammad ne zaune a kusa da shi, sai kuma Mubarak, Baba Salisu da Alhaji Ridwan zaune a mabanbanta wurare, yayin da Mukarram ke tsaye kamar yanda jami'an da suka yi sallama su ka shigo kai tsaye a tsakiyar parlourn suka tsaya su ma.

Jerin jami'ai kala uku ne suka haɗa hannu wurin aikin bincike akan wannan abun da ya faru a gidan babban Attajirin ɗan kasuwa Alhaji Mas'ood Galadima, abunda ake kira Joint Task Force. Wanda investigation ne da ya haɗa da police force sashen CID unit,sai hukumar DSS, da kuma Elite Cyber Forensics Unit. Wanda National investigator Coordinator (DCP) Hadi Balarabe Shi ne wanda yake jagorantarsu.

Mukarram shi ne wanda ya fara magana da cewa.

"Wai DCP miye yake faruwa ne? Yau sati ɗaya da faruwar abun nan amma har yanzu babu wani bayani."

Jinjina kai DCP ya yi sannan ya ce

"Wannan gaskiya ne Doctor Mukarram. Ahmm! Haƙiƙa mun gudanar da cikakken bincike na tsawon sati ɗaya, wanda mun yi aiki tuƙuru ba dare ba rana. Mun duba dukkan kyamarori, bayanan Na'urar ORION-9,motsin shiga da fitar mutane, har da bayanan Wayoyi da antenna na wannan yankin...."

Ɗan wawwara ido ya yi yana kallon su kamar yanda duk suka zuba ido suna kallonsa, sannan yaci gaba da cewa.

" But unfortunately....with all the hard work, abunda muka fuskanta a wannan lamarin ba sata ce ta yau da kullum ba kamar yanda aka saba. Waɗanda suka yi wannan ta'adin masu matuƙar basira ne sosai, domin sun yi aiki da ilmi, tsari da kuma fasahar zamani. Sun yaudari tsarin tsaro ba tare da sun bar kowace irin alama da za'a iya kama su ba. Sun yi amfani da gurɓataccen tsarin lokaci, signal Masking da kuma pre recorded feeds. Sam ba su bar kowace irin alama ba, kamar sawu, zanen yatsa, fuska ko DNA da za'a iya bin diddiginsu da shi..."

DCP ɗin ya ƙarasa maganar tare da ɗora wasu takardu akan centre table ɗin da ke gabansa na shaidar bayanan da ya gama bayarwa a yanzu.

Ɗaya daga cikin jami'an Cyber Forensics Unit ne ya jinjina kansa ya ce.

" Ko a matakin binciken Digital da muka gudanar, an goge hanyoyin data, an karya hanyar bin IP, wanda sun yi amfani da na'urorin da ba sa barin alama komai ƙanƙantar ta. To a wannan gaɓar gaskiya, bamu da wata shaida da za ta kaimu koda ga mu mutum ɗaya ne a yanzu dai, sorry to say....."

Cikin zafin rai Mukarram ya ce.

"To yanzu mi kuke nufi kenan DCP? Kuna nufin kenan waɗanda suka aikata mana hakan shi kenan sun ci bulus kenan? DCP ka kuwa san halin da Anaam ɗinmu take ciki?"

Tasowa Muhammad ya yi yazo ya dafa Mukarram ɗin camly ya ce.

"Ya isa Mukarram! Ka bari abi komai a san..."

Cikin wani irin raɗaɗi da zafi ya kalli yayan nasa ya ce.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull