Kenza eBookz

Duhun dare book 1 complete novel - Chapter 42

Duhun dare book 1 complete novel - Chapter 42

Duhun dare book 1 complete novel Chapter 42: Duhun dare book 1 complete novel Chapter 42. Hakan yasa ya fito a hankali ya ɗan matsa kusa da ita yana kallon…

3,339 words

Hakan yasa ya fito a hankali ya ɗan matsa kusa da ita yana kallon fuskar ta murya a ƙasa sosai ya ce.

" Barka..."

Jinjina kai ta yi alamar ta masa ba tare da ta buɗe bakinta tayi magana ba.

Lumshe idanunsa ya yi ya buɗesu a hankali still idanun shi a kanta ya ce.

"Ahmmm! Daman Excuse ɗinda na ɗauka is only for today...so, I think Idan kinga Baby za mu iya komawa zuwa 7 to 8pm haka..."

Girgiza kanta ta yi ba tare da ta kalle shi ba ta ce.

"Ni dai zan zauna a nan yanzu,and if you are interested too...akwai ɗaki a ta can ɓangaren sai a baka.."

"Maryam na yi alƙawari zan dawo dake kafin Naming ceremony day ɗin..."

"Ai ni ba yarinya ba ce ƙarama da za ka ce sai ka tsare ni gudun kada na ɓata, daman kaga ka saba tafiyanka ka barni sai sanda ka ga dama kake dawowa saboda haka kada ka ce za ka min doka."

Jinjina kai ya yi yana mai jin ciwon kalaman ta murya a can ƙasan maƙoshin sa ya ce.

" Okay....ni zan koma yanzu. Please take care!"

Jinjina kai ta yi ta ce.

"In sha Allah, thank you. Allah ya tsare."

Kallonta yake yanda take tafiyan cike da nutsuwa har sai da ta shige sannan ya juyo da nufin bude mota sai kawai suka yi ido biyu da Rabi'a wacce itama shigowanta gidan kenan.

Saurin kawar da kansa ya yi tare da buɗe mota ya shige a hankali ya ja ya tafi.

Ita kuwa sai wani kallon shi take har sai da ya shige motar sannan ta nufi cikin gidan kai tsaye ta shige.

Duk wanda ya haɗu da ita sai ya yi mamaki musamman Yaa Mubarak wanda yasan cewa ya baro ta a gida ta ya kuma za'a ce ta zo nan gidan?

"Yaa Mubarak Ina wuni."

"Lafiya lau..."

Daga haka ya sa kai ya wuce yana mamakin abinda ya sake dawowa Da ita gidan nan kuma.

Tunda ta shigo gidan babu wanda ya koma sabganta domin ko Na'ima tana shiga ɗaki ta duba ta ita da baby ta fito ta dawo ɗakin Ammie ta yi kwance a parlour kan kujera har sai da Abbah ya dawo bayan sallan Isha ya ce a kira ta yana nemanta.

Koda ta shigo parlourn cikin rashin sa'a suka yi ido biyu da Mukarram wanda ya wani maka mata harara a kaikaice itama kuma sai ta hutar da Kanta ta janye idanunta daga kallonai domin bai da mutunci ko kaɗan.

Wuri ta samu kusa da ƙafar Abban ta zauna tare da gaishe da shi tana mai ƙara soke kanta.

"Rabi'a..."

Abbah ya ambata yana mai kallon inda take zaune.

Ɗagowa ta yi a hankali ta amsa ma sa sannan ya ce.

"Waɗannan da kike gani duk en uwanki ne kamar ko yaushe..so nike in ji gaskiyar zance daga bakin ki dangane da bayanin da Alhaji Salisu ya yi mini a kanki..ke yanzu Kina ganin dacewarki da Auren Faris Rabi'a?"

Cikin tsabar mamaki da al'ajabi kowa ya zubo ido yana kallonta, daman Mukarram, mubarak, Anaam da kuma Ammie su ne a ɗakin sai Yaa Naseer da ya zo da ita wanda Abbah shi ne da kansa wanda ya bada umarni tare da rarrashin zuciyar Alhaji Salisu ya ce ya turo mishi ita.

Cike da rashin haƙuri Mukarram ya miƙe tsaye yana wani kallonta sai kuma ya Kalli Abbah ya ce.

"Alaji wane Faris ɗin ne take cewa za ta aura?"

"Faris na gidan Alhaji Gimba."

Kamar wani abun arziki ya matsa yana ƙare mata kallon mamaki sai kuma kwatsam suka ji ya fasga mata wani marin da sai da ta dafe kuncen ba shiri. Yana batun ƙara mata wani marin Mubarak ya yi saurin riƙo hannunsa ya ce.

"Ya Mukarram ka barta please..."

Duk da cewa an janye shi hakan bai hana shi saka ƙafa ya sake yi mata wani irin harbi ba wanda sai da ta matsa baya ba shiri tare da fashewa da wani irin kuka.

Wata irin tsawa ce Abbah ya daka masa wacce ta yi sanadiyyar sanya shi ja baya yana mai ci gaba da ɓata fuska ya ce.

"Alhaji wannan yarinyar ba 'ƴar mutunci ba ce ka barni da ita na yi mata shegen suka ko za ta dawo hayyacinta..."

Da sauri Abbahn ya ɗaga masa hannu tare da girgiza kansa ya ce.

"Ka barta kawai Mukarram..."

Daga haka ya sake kallonta yana mai matsowa gaba kaɗan kan kujerar ya ce.

"Rabi'a Faris kike so ki aura?"

Jinjina kanta ta yi tana mai share hawayen ta da gefen veil ɗinta ta ce.

"Eh Abbah, ni shi nake so kuma ya amince zai turo iyayen sa..."

"Kin tabbata kina son sa Rabi'a?"

"Eh, Abbah..."

Ajiyar zuciya ya sauke yana mai ƙara jinjina al'amarin Rabi'a da uwarta a zuciyarsa sannan ya ce.

"Shi kenan...ta shi ki tafi. Allah ya tabbatar da alheri yasa mu dace..."

Shima Naseer ɗin cike da mamaki ya ce.

"Alhaj..."

Saurin ɗaga masa hannu ya yi tare da faɗin.

"please ina so kowa ya tafi ya bani wuri magana ta ƙare.."

Miƙewa Mukarram ya yi cike da jin wani irin ƙullutun baƙin ciki ya ce.

"Gaskiya Alhaji magana ta gaskiya idan har kace za ka biye zancen wannan yarinyar har ka mara mata baya to baka yi mana adalci ba. Alhaji kasan waye Alhaji Gimba, don Allah kada ka sake janyo mana rigima da shi."

Daga haka ya fice wanda suka fita ne gabaɗaya sannan Ammie ta kalle shi ta ce.

" Alhaji nima na yi mamaki da har ka Iya tsayawa ka saurare ta. Alhaji ina amfanin haɗa Zuriya da Alhaji Gimba? Ni na san ba zai taɓa amincewa ba kuma ba zai taɓa goyon bayan wannan abun ba...bana so aje a ƙara maimaita abun da faru baya wanda bamu san ma wannan ɗin dame zai zo ba..."

Duk maganganun da take shiru ya yi kawai bai ce mata ba tamkar ma baya ɗakin haka ya yi mata, hakan yasa ta miƙe tayi tafiyanta zuwa wasu sabgogin.

******

Sati Ɗaya har da kwana biyu Anaam ta share a gidan inda suka ci bukin su suka yi hidima mai daɗi inda yaro yaci suna Mas'ood (Khalipah). Haisam shi ne wanda ya saka sunan da kan shi wanda hakan ba ƙaramin girma ya ƙara masa a idon su Anaam da sauran dangi ba.

Tana nan da Yamma around 6pm ita da Na'ima da kuma Na'ima Hassan suna zaune suna cin Chicken Pepper soup ɗinda aka kawo wa Na'ima suna ta nishaɗin duniya sai ga Yaa Amina ta shigo tana faɗin.

"An ji daɗin gida an manta da miji ko? To sai ki tashi ki tattara naki da naki ki wuce ga shi can yana jira a waye.."

Wani irin faɗuwar gaba ta ji wanda har ba ta san lokacin da ta wani ɓata rai ba ta ce.

"Yaa Amina yanzu za'a ce na tashi na haɗa kaya zuwa Lagos?"

Wani kallon Yaa Aminar ta yi mata sannan ta ce.

"iyyeh! Mu za ki faɗawa haka? Ai na san kin san da zancen tafiya ki daina ma wani wayance mana ki daina jin kunya, saboda haka ki tashi ki tafi kawai Allah ya tsare..."

"Yaa Amina.."

"Abbah fa tun ɗazu na ji yana faɗan cewa miyasa ma ya barki har tsawon sati ɗaya. Ki rufawa kan ki asiri ki tashi ki tafi."

Ta shi ta yi ba tare da ta sake furta komai ba ta shige ɗakin Ammie ta ce Nene ta haɗa mata kayanta wanda sai da ta gama son ran ta sannan ta yi musu sallama cike da kewa ta zo ta shige motar ba tare da ta yi magana ba.

Lumshe idanunsa ya yi a hankali wanda tunda ta fito yake kallonta ita da su Aunty Aysha har suka yi mata sallama suka koma.

Hannun ta ya riƙo a hankali muryar nan tasa a natse yana ɗan murmushi ya ce.

"Fushin ne har yanxu Maryam? Har yanxu baki huce ba?..."

Ƙara ɗago hannunta ya yi sama ya sumbata a hankali wanda hakan yasa ta janye ba shiri tana mai jin wani iri a ranta ta ƙara haɗe fuska ta ce.

"Bana so..."

"Please I'm sorry...ya kamata ace kin tausayeni hakanan...ba zan iya jurar wannan yanayin da muke ciki ba dani dake...i know that I have wrong you in so many ways, but na yi miki alƙawarin gyara kuskure na. Tunda na koma na kasa yin wani cikakken aiki, kullum duniya ta da tunanina a kanki suke ƙarewa, idan na kira bakya picking, Idan na miki message bakya replying, please forgive me.. "

Ƙara turo cute lips ɗin nan nata ta yi zuwa gaba waɗanda suke matuƙar burgeshi cikin shagwaɓewa ta ce.

"Ni fa ba jimawa zan yi resuming lectures..."

"We will add only one week in sha Allah sai na dawo dake."

Shiru ta yi tana mai ƙara nazarin maganan na tsawon lokaci. Abubuwa ne da yawa a ranta, tana da tambayo yi da maganganu zuwa gare shi waɗanda take tunanin idan ta samu amsar su to wataƙila ta iya samun nutsuwa da shi.

Ganin ta yi shiru tsawon lokaci yasa ya tayar da motar a hankali yaja suka wuce zuwa Airport.

******

Alhaji Mas'ood na zaune bayan ya dawo daga masallacin Isha yana cin abincin dare sai ga kiran Alhaji Gimba kaman a mafarki.

Ɗagawa ya yi tare da yi masa sallama domin a tunaninsa wataƙila wannan karon abun arziki ne.

Sai dai cike da hargagi ya fara faɗin.

"Mas'ood Galadima wato kun kasa yin nasara a kai na shi ne ku ka koma wurin ɗana ko? To wallahy tallahy ba zan yarda ba, kuma ko mata sun ƙare babu abinda Faris zai yi da jinin ku, ni daga kai har Alhaji Ridwan wallahy na ƙare da labarinku har abada. Sannan kada ku manta cewa an yi mana iyaka a kotu., sai da ku ka sa hannu sannan na sa, saboda haka idan ba ku fita har iyalina ba wallahy ko yanzu ita ce za ta rabamu a karo na biyu..... " ✍️ *OUM-AMEER* ✍️ *D U H U N D A R E* *A 2026 N O V E L* *BOOK ONE*

*ADABI WRITER'S ASSOCIATION*

*AMEENA IBRAHEEM* *OUM-AMEER* Arewapen: @Oumameer2671 Wattpad: @Ummu-Amir

*BOOK ONE* *PAGE 50*

Numfashinsa na wani fita a rikice ya ƙarasa maganar cikin tsananin fushi, ba tare da ya bari Alhaji Mas’ood ɗin ya ce uffan ba kawai ya katse kiran.

Shiru ne ya mamaye wurin na ɗan lokaci yayin da Hannunsa ke ɗauke da wayar har yanzu yana mai kallon screen ɗin tsabar mamaki.

Hajiya Nasmah da ke zaune gefensa ta ɗan matso kusa da shi cikin damuwa ta ce.

"Alhaji lafiya kuwa? Waye yake maka magana haka kamar zai cinye ka?"

Ɗago kai ya yi a hankali ya kalleta, idanunsa cike da wani irin ƙuna ya ce.

"Gimba ne..."

Ji ta yi zuciyarta ta yi wani irin bugawa da ƙarfi, sai kuma ta zaro ido a ɗan razane ta ce.

"Subhanallah... me yake faɗamaka haka Alhaji? Ni fa wallahy ina tsoron sharrin mutumin nan, tun abinda ya aikatawa Mukarram har yau wannan shock ɗin bai bar ni ba Alhaji..Mutim ba kyau Alhaji..."

Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi yana mai ture plate ɗinda ke gabansa ya ce.

"Abinda nake ta gudu shi ne ya faru Hajiya Nasmah..maganar nan ta Faris da Rabi'a ta kai kunnen sa. Wata ƙila Faris ɗin ne ya faɗa masa."

"Faris ɗin ma ai nasan zai iya tunkararsa tunda shima ba baya bane indai gidan zuciya ne."

Wayar da ya ajiye a gefe ita ya sake ɗauka ya kira numbern Alhaji Ridwan, bayan sun gaisa ya ce.

"Ka yi wata magana da Gimba ne?"

Jinjina kai Alhaji Ridwan ɗin ya yi daga can nasa ɓangaren tamkar suna ganin juna ya ce.

"Eh, Faris ne ya kira ni akan zancen yana son auren Rabi'a kuma Mahaifinsa ya hana, yasan cewa mu kaɗai ne ke iya taka masa burki domin ko 'yan uwansa baya saurara, shi ne na kashe wayan na kira shi domin mu samu mu fahimci juna amma kasan halinsa kawai ya hau zage-zage kawai ya katse kiran."

Girgiza kai Alhaji Mas'ood ya yi ya ce.

" Uh uhm! Yara ne dai ka haifesu baka haifi halin su ba...."

" Alhaji Mas'ood... "

Alhaji Ridwan ya kira sunan Alhaji Mas'ood ɗin sannan ya ce.

" Kun shirya aurawa Faris ɗin Rabi'a?"

Cike da shakku Alhaji Mas'ood ya ce.

"Anya? Kafa san inda muka fito...."

"Alhaji Mas'ood kada ka biye ta kansa kafi kowa sanin cewa Gimba mahaukaci ne. In banda rashin hankali taya za ka kama ɗanka daga zancen aure kawai ka hau sukan sa kaman wani ka samu jaki."

"Duka??"

Alhaji Mas'ood ɗin ya ambata cike da zallar mamaki.

"Wallahy wai dukansa ya yi saboda kawai Alhaji Gimba yana da motsin ƙwaƙwalwa. Saboda haka kada ka biye shi ai shi namiji ne ba mace ba, kuma tunda har suke son juna matuƙar dai kun amince ni ne nan wanda zai tsaya masa a matsayin wakili har ayi komai a gama. In yaso ya kai mu kotun lahira ma idan zai iya.. "

" Subhanallah! Alhaji Ridwan ka yi istigfari domin wannan kalma bata kama ce ka ba a matsayinka na musulmi... "

" To Astagfirullah! Ya kai mu duk kotun da ya ji zai iya amma wannan aure an yi shi an gama. Wallahy ni yaron ma ya bani tausayi musamman yanda yake magana, yace ya nemi Anaam an hana shi yanzu kuma ace za'a hana shi wannan ɗin..."

"To ni ma ai shi nake dubawa, tabbas ni ne da kaina na hana shi Maryam domin itama ta ce ba ta yi, to amma ita wannan ɗin ta kafe ita da Uwar ta cewa shi suke so..."

"Duk wanda ya ce zai haɗiye gatari sakar masa ɓota Alhaji Mas'ood. In sha Allah zan yi ƙoƙari in dawo next week, idan na dawo zan je mu samu 'yan uwansa a can Bunguɗu sai mu tattauna, daga nan sai mu zo idan Allah ya yarda sai a saka rana da komai da komai..."

"Okay,Allah ubangiji ya yi mana jagora yasa mu wanye wannan abu lafiya."

"Amin Ya Allah."

Yana katse kiran ya kalli Hajiya Nasmah ya ce.

"Ɗauko min waccan wayan Hajiya in kira Alhaji Salisu da Madu Muji yanda za'a yi. Na san mukarram ko mai zan yi ba zai shiga maganar nan ba."

"Hmm! Mukarram! Mukarram ba zai taɓa daina halin shi na zafin rai ba."

*******

A ɓangaren Faris kuwa.... Tunda ya fice daga gidan bai koma ba har yau, ji yake gabaɗaya ina ma ace wani mahaifi ne ya haife shi! Mutum kullum faɗa kullum tashin hankali? Babu abinda ake shiryashi da shi a kwashe lafiya sai an yi rigima.

Ba zai iya ci gaba da zama a wannan gidan ba, tunda har baya girmama muradinsa to shi kuma bai ga amfanin ci gaba da zama a gidan ba.

Hakan yasa yau ya yanke shawarar wucewa wani gidansu dake Kaduna domin ya huta ko zai huce wannan baƙin cikin da mahaifin nasa ya ƙunsa masa. Mamaki yake har yanzu wai ta yanda har Daddy ya iya saka ƙarfinsa yana dukansa tamkar wani bawa da uban gidan sa.

Tafiya yake akan titi yana ta sharara uban gudu tamkar zai tashi sama amma kuma daga ƙarshe ya samu gefen hanya ya yi parking, idanun sa sun cika da wani irin ɓacin rai sun yi masa jajir yayin da zuciyar sa ke wani irin tafarfasa ya wani daki steering motar da ƙarfi ya ce.

"Why Daddy? Why?"

Girgiza kansa ya yi da ƙarfi tare da saka hannayensa duka biyu ya dafe kansa ya ci gaba da faɗin.

"I’m not a kid anymore… I deserve to choose my life…I have every right to be with who ever I want"

Wata iska ya furzar mai ƙarfi sannan ya janyo wayarsa ya kira Rabi'a.

Ita kuma Rabi'ar tana nan kwance a kan gado wanda duk ilahirin gidan idan ka cire Ammie da Abbah babu wanda take shiga shirginshi, musamman da ya kasance ta samu yanda take so Abbahn ya goya mata baya akan auren Faris ɗin.

Cikin Farin ciki ta yi picking call ɗin, but daga yanayin muryansa sai yasa murmushinta ya dawo damuwa a sanyaye ta ce.

"My Farrab Lafiyanka kuwa?"

"Beeyh Daddy yaƙi ya amince...daga yanda actions ɗinsa ya nuna he will never accept you..."

Wasu irin hawaye ne suka zubo mata jin wani irin labarin da ke nema ya zama shamaki ga samuwar farin cikinta. Murya a karye ta ce.

"To me zai faru kenan? Haƙura za ka yi dani ko me? Farrab ni fa na jure kuma na jajirce sai da na shawo kan iyayena..."

"Shhhhh!"

Ya ambata yana mai lumshe idanunsa a hankali. Jin ta yi shiru ɗin da gaske ya sake cewa.

"Do you trust me?"

Jinjina kanta ta yi murya a ƙasa sosai ta ce.

"Eh.."

"In sha Allahu aurenmu ba jimawa zai faru. Kin san sometimes you have to fight for your happiness, Saboda haka ki fara shiri kin ji ko?"

Cike da ƙwarin gwiwa ta ce.

"Thank you my Farrab..."

"Gani zan je Kaduna, ki kula."

*******

Anaam kuwa, bayan sun sauka gida har ya gama wanka ya shirya ya yi nafila tana nan zaune a bakin window ko kayan da ta zo da su bata canja ba ballantana ya yi tunanin ya ga wani annuri a fuskanta.

Jikin windown ya zo ya tsaya a kusa da ita tare da ɗaga kansa ya kalli sararin samaniya wanda itama abinda take kallo kenan. Duk da cewa ko'ina kewaye yake da haske but da ka kalli sararin samaniyar za ka tabbatar da cewa DUHUN DARE ne wanda dukkan wani mahaluƙi ya zamto mahuta a gare shi.

Lumshe idanunsa ya yi a hankali yana mai jin wani iri a ransa tuna wasu shekaru da suka shuɗe masu makamancin dare irin wannan da suka bar tarihi marar daɗi wanda tunawa da shi ma babu abinda yake ƙarawa sai danasani wacce ta kasance marar amfani.

Ganin ya zo ya tsaya yasa ta miƙe da nufin shigewa caraf ta ji ya damƙo hannunta ya ce.

"Are you still angry?"

Girgiza kai ta yi ba tare da ta kalle shi ta ce.

"No..."

Juyata ya yi suna facing juna ya ce.

"Maryam....give me a chance..."

"Why did you marry me?"

Lokaci ɗaya tambayar ya ji ta bugi zuciyarsa kai tsaye wanda yasa ba shiri ya ɗago kansa ya kalle ta. Sosai yanayinta ya sake sanya shi cikin damuwa da wata irin fargaba domin sam bai yi expecting irin wannan question ɗin ba.

"Daman abun da na tsamma kenan daga gareka..."

Saurin girgiza kansa ya yi ya ce.

"Na yi miki kuskure na yarda...but I promise to fix it, let me prove the love I have for you Maryam..."

"Ina jin bacci please.."

Daga haka ta zame hannunta a hankali ta shige ɗakinta ta canja zuwa towel ta yi wanka sannan ta fito ta haye gado ta kwanta ba tare da ko shafa lotion a jikinta ba.

Yana shigo ɗakin bayan kusan 1 hour da shigowanta sai ya hango ta can ta ƙudundune ta yi tana ta baccin ta.

Girgiza kai ya yi tare da samun wuri akan Sofa ya kwanta har bacci ya yi nasarar sace sa.

Washegari ta riga shi farkawa ta ganshi a kwance wanda kallo ɗaya za ka yi masa ka gane cewa kwanciyar ba ta yi masa daɗi ba amma duk da haka kuma ga mamakinta har ya yi iya yin bacci haka mai nauyi.

Tsayawa ta yi tana ƙare masa kallo na tsawon lokaci sannan daga ƙarshe ta wuce ta shige toilet ta yi alwala sannan ta fito amma koda ta fito ta tarar baya nan har ya fice.

Tana kambala sallah ta fito ta nufi kitchen domin sama masa abincin da zai taɓa kafin ya fita wanda bata sani ba ko sammako zai yi kaman yanda ya yi a ranar da za su tafi Abuja.

Tana shiga ta ga komai an zube shi na amfani wato ya ma shirya kenan akan za ta dawo.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull