Heedayah complete Novel - Chapter 80
Heedayah complete Novel Chapter 80: Heedayah complete Novel Chapter 80. Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788.... 9/12/21, 8:04 PM - ,: Mami…
3,029 words
Heedayah isn't free, you read for free 馃し馃徎鈥嶁檧锔忦煠佛煆烩€嶁檧锔�
it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah
Chapter notes and social links
Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788.... 9/12/21, 8:04 PM - ,: Mami na xaune compound din gidan ta tare da Abba da wata colleague dinsu, Abba yace "So now how do we go about it??" Barrister Khadijah tace "Kun san inda matsalar take ynxu?" Abba na kallonta yace "Aa sai kin fada" tace "An tafi station da shi Khaleel din tun farko, a can kuma yyi denying he isn't a Kidnapper so did Barrister Rahinah, so ynxu idan aka kai maganar station to get all the thugs arrested, first tambayar da xai fara biyowa shine... Khaleel isn't a Kidnapper how did he know that they are?" Shiru duk su Abba suka yi suka yi suna kallonta, Barrister Khadijah tace "The matter is so complicated..." Abba yyi murmushi yace "Noo, it's not Barrister, bbu complications.. Of course Khaleel wasn't a Kidnapper amma a cikinsu yake, a cikinsu kuma ya rayu ta dalilin rabasa da suka yi da iyayensa suka kai sa cikin nasu, don haka bai san kowa ba sai su, his being in their midst ba shine ke bada tabbacin yana harkan da suke ba... Baya tare da su a mugun abinda suke aikatawa, kuma sbda baya taren da su ma yasa xai tona masu asiri, ai a case din nan baxa mu nuna we have anything to do with Khaleel ba, baxa mu nuna akwai wani alaka tsakaninmu da shi ba, we will act as though he is a stranger...." Barrister Khadijah tayi murmushi tace "What if the Kidnappers have enough proof that will look as though he worked with them? That aside we need to think deep su ma dubarunsu yawa ne da shi, they can blackmail him just as they did few days ago....." Mami ta sauke ajiyar xuciya tace "And ku bar cewa he wasn't a Kidnapper, he was, kuma kamar yanda Barrister ta fada baxa a rasa proofs din ba, may be images or videos of him a tare da su, tunda ai a da yana tare da su har ma yana contributing" Barrister Khadijah tace "Definitely kenan dole sai an tafi da evidence din baya tare da su police station before their arrest...." Abba yace "Exactly, and this evidence just have to come from Khaleel, a cikin evidence din kuma dole cikin 100% ya wanke kansa da kansa ko da 70% ne, sai ya bar mu da sauran struggles din wankesa...." Mami ta girgixa kai tace "Duk da haka Khaleel me laifi ne sosai a wajen hukuma, da ya tashi ya gansa cikin hoodlums abinda ya kamata yyi shine ya jawo hankalin hukuma tun farko, idan kuma baxai yi hakan ba sai ya bar cikinsu kawai...." Abba yace "But did you listen attentively to his story yesterday Rahinah?" Shiru Mami tayi tana kallonsa, Abba yace "on several occasions yayi yunkurin guduwa daga cikinsu, amma bayan kwana biyu sai kuma ya ga ya koma cikinsu, yana kuma jin kamar idan bbu su baxai iya rayuwa ba... Did you listen to that?" Mami ta kasa cewa komai, Barrister Khadijah na gyada kanta tace "Asiri gaskiya ne" Abba yace "Toh don haka mu baxa mu ga laifinsa ta nan ba unlike hukuma, yanxu abinda xai faru kawai evidence xai fito daga Khaleel, I will talk to him about it now, later in the evening kuma xa mu hadu" a sanyaye Mami tace "Toh Allah ya kai mu, Shuraim ya koma ne?" Abba yace "Jiya ya koma" Mami tace "Toh Allah ya tsare sa" Abba yace "Ameen, I sent you text daxu baki yi replying ba" Mami tace "Oh, I wanted calling you in maka bayani ne, baki sun yi yawa ne a gidan wllh" Abba yace "Ohk" Mami tace "I spoke to him about it this morning, sai yace min a daga xuwa wani lkci har a gama wnn case din" Abba yace "That's thoughtful of him, Allah ya kai mu, is he inside?" Mami tace "Ehh yana ciki" Abba yace "Alright then, xan koma great barristers sai mun hadu da yamman, but before then idan kun shiga ciki ku turo min Khaleel din" Mami tace "Toh shkkn I will" Bude gate aka yi duk suka juya, Mumy ce ta shigo tare da tawagarta har da Salima, ganinsu Abba ta karasa da fara'a inda suke zaune, Mami na kallonsu tace "Sannun ku da xuwa" Gaisawa suka yi, Su Sadiya da Baturiya suka gaida barrister ya amsa yana danna wayarsa, Mumy tayi kasa da murya tace "Ashe abinda ya faru kenan Hajiya Rahinah? Toh Allah ubangiji ya tsare iya haka, Allah ya rabamu da mugun ji ko mugun gani, muna taya ki murnan dawowan dan ki bayan shekaru masu yawa..." Mami tace "Allah ya saka da alkhairi, Allah ya bada lada" Mami ta mike tare da barrister Khadijah suka yi ma Abba sallama suka wuce ciki tare da su Mumy da kawayenta. Mumy sai kallon Khaleel da ya shigo parlon ya gaishesu take, bai kara second daya a wajen ba ya fita daga parlon xuwa wajen Abba dake jiransa a waje, Mumy tayi tagumi tace "Allah sarki rayuwa, gashi mu bamu ta6a sanin kina da d'a namiji ba ma balle, da yake babu hakki sai gashi bayan an cire rai, toh Allah ya bar mu da 'ya yanmu dai har mutuwa" Mami dake parlon da su Hajiya Zuwaira da step mum din Sudais dai bata tanka ta ba, Mumy tace "Toh an samu an sa ranan Junaid din kuwa? Don barrister ba gaya min xai yi ba wllh" Mami tace "Tukunna dai" Mumy ta d'an saci kallon Sadiya basu dai ce komai ba. Khaleel ya xauna saman kujeran dake facing Abba ya gaishesa, Abba ya amsa da murmushi yace "Ya karfin jikin?" Khaleel yace "Alhmdllh na ji sauki" Abba yace "Toh maa sha Allah, Allah ya kara lafiya" Cikin few minutes Abba ya gama magana da Khaleel ya gaya masa duk yanda xa a yi snn suka yi sallama ya wuce, Khaleel ya koma ciki yana kara naxarin abinda Abba yace masa. Da yamma misalin karfe biyar Khaleel ya nufi kofar fita parlor bayan ya sallami Mami, sai da ya kusa kofar Mami tace "Be careful.... and pray, Allah ya tsare ka" juyowa yyi yace "In sha Allah...." a hankali Dinar tace "Allah ya tsare" Bai juyo ba yace "Ameen" Heedayah dake xaune dinning ita da Farida suka bi sa da ido su ma, kasa daurewa Heedayah tayi ta mike ta bi bayansa, babu wanda yace mata komai har ta fita parlon, parking space ta ga ya nufa, tace "Ya Khaleel" ya juyo ganinta ya tsaya, ta karasa inda yake da damuwa tace "Where are you going to?" Murmushi ya mata yace "Xan fita ne, anjima xan dawo in sha Allah" tace "Xaka fita xuwa ina? Kana son su ganka ne kuma?" Yace "Aa ba inda xa su gan ni xan je ba" tace "Toh xan bi ka, should I go and tell Mami?" Yace "No" ta marairaice tace "Plss mana, I don't want anything to happen to you" yace "Nothing will happen to me Heedayah" shiru tayi tana kallonsa, yace "To rakani gun motar sai ki koma ciki and pray for me" a sanyaye tace "In sha Allah" Murmushin sa me kyau yyi mata, tace "Da motar yaya xaka fita?" Yana tafiya tana biye da shi yace "Ehh" Ta madubi Junaid dake warming din motar tasa ma yayansa yake kallonsu har suka iso, sai a snn Heedayah ta gansa, ta wara ido tace "Lahh ashe kana nan Yaya" yace "Ina nan" Fitowa Junaid yyi daga cikin motar yana kallon Khaleel, Khaleel ya shiga motar, Junaid yace "Allah ya tsare" Khaleel ya amsa da "Ameen, Thank you" sai da Khaleel ya fito daga parking space Mai gadi ya bude masa gate snn Heedayah ta daga masa hannu a hankali, ya gyada mata kai, bayan ya fita compound din suka koma cikin gida tare da Junaid tana kallonsa suna dai dai entrance din shiga parlon tace "Yaya wai me kke shafawa a lips din ka?" Yace "Abinda kike shafawa a naki" dariya tayi yyi murmushi ya bude kofar ya shiga ta bi bayansa. Har Khaleel ya isa gidan oganninsu yana communicating da Zayyad ta text message, yyi parking a waje yyi deleting duk messages din snn ya nufi gate ya fiddo da spare key dinsa na gidan ya bude ya shiga ciki, direct entrance din shiga babban parlon ya nufa ya bude kofar parlon, duk suna xaxxaune parlon, wasun su na karta, ga giya ko wannensu na sha a glass cup, wasu kuma na smoking cigarette kida na tashi a speaker, Zayyad dake xaune saman kujera shi ma hannunsa rike da cigarette ya dinga kallon Khaleel kamar yanda duk sauran mutanen parlon ke kallonsa, Oga Bala ya kyakyace da wani mahaukacin dariya yace "I told you all a xuba masa ido xai dawo, to gashi ya dawo..." Wani dariya Oga Arne ya fashe da shi ma yana kallon Khaleel da kyau yace "Da ina ka tafi? Ka xata har karshen rayuwarka xaka iya rabuwa da mu ne? Ko dama kana da wasu a duniyar nan bayan mu? Ni in particular...." Xaunawa Khaleel yyi saman kujera yana kallonsu gaba daya, Oga Manga yace "Ka saduda ka gama boye boyen kanka ka dawo kenan? Lallaba ka da ake ya fara wuce gona da iri, xa mu dau mummunan mataki a kan ka wllh" Oga Bala ya nufi Khaleel ya dago kansa yana kallonsa da jajayen idonsa cikin katon muryarsa yace "Ka dawo daga raina mana hankalin da kke?" Calmly Khaleel yace "Ehh" Oga Arne yace "Good... akwai operation a Abuja, dawowar ka kawai muke anticipating kuma gashi ka dawo, so we are setting off today...." Khaleel ya girgixa kai yace "U are mistaken then...." Lkci daya ya mike yana kallonsu gaba daya fuskarsa a tamke yace "Na xo ne in sanar maku cewar daga yau na bar wnn mummunan harka da ku ka dulmiyar da ni a ciki tun ina d'an yaro, na bar wnn harka da ku ka cusa min a xuciya ba da son raina ba, snn Arne, Manga da Bala I want you all to put this at the back of ur mind that... in sha Allah karshen ku ya xo... Sannan kananun kwarin da ke tare da ku su biyo baya...." Tashi Oga Arne yyi yana masa wani kallo cikin tsawa yace "How dare you Khaleel? Mu kake ma magana haka? Mu kake kira ma karshe??" Khaleel yace "Eh kai, Manga da Bala...." Manga ya mike a fusace ya nufesa ya shakosa da karfi yace "A duniyar nan kana da sama da mu ne kake ikirarin xaka ga karshen mu? Har kai kana da gata a duniyar nan banda wajen mu, uban me kake takama da shi, dama tsintacciyar mage bata mage, an kawo ka cikinmu kana da shekara uku baka da gata baka da kowa haka muka ja ka jiki muka fifitaka fiye da kowa, muka jajirce wajen ganin an bar ka kai daya tak kayi boko a cikinmu, Wani hakuri ne ba mu yi da kai ba a shekaru talatin din da suka wuce, fita operation da kai sai ka bata ma kowa rai sau tari kayi spoil din mana show don ma kana yi kana shakka, bindigar da aka mallaka maka ba shi da amfanin da aka baka yyi maka sai na harbin Iska, sau nawa kake freeing abducted or kidnapped victims dinmu ka ja mana uban asara, sau nawa sbda kai asirinmu ke kusa tonuwa sai dai ka fitar da mu da kwakwalwarka, amma duk da haka muna ta tausan oganninmu sbda ba kowa Allah ke ba wa ba intelligence din ka ba, da ba don Arne ba da Oga Salahu ya dde da harbe ka har lahira shekaru goma da suka wuce, bayan ka ba wata yar minister da muka yi kidnapping damar guduwa wanda hakan ya kusa tona mana asiri muka shiga gararin rayuwa, ta dalilin ka sai da marigayi Oga salahu ya harbe Arne a kafa wanda har yau Arne yana samun matsala da kafar, Kai har ka isa yanxu ka xo kace xaka bar mu bayan duk sadaukarwa da muka yi maka da kokarin ganin ka rayu cikin mu shugabanninmu basu cutar da kai ba?? Wllh kayi kadan Brainiac, kayi kadan ka bijire mana ka watsa mana kasa a ido, gwara in tarwatse kanka, gwara in kashe ka har lahira...." Yana fadin haka ya xaro bindigarsa daga aljihunsa da sauri, kusan a tare suka yi hakan da Khaleel da ya xaro nasa bindigar shi ma yana nuna ma Manga, Arne dake ta wani huci ya sa hannu ya sauke bindigar manga cikin kaushin murya yace "Bar shi Mangaaa, bar shiiii" Khaleel bai fasa nuna ma Manga tasa bindigar ba, Cikin tsawa Arne na nuna Khaleel yace "Mu xaka ci ma amana? Mu xaka kawo ma tashanci??" Khaleel yyi wani murmushi yace "Sai na tashi daukan ma mahaifina fansar kashesa da ku da mukarrabanku ku ka yi xa ku san tashanci" da shock duk suke kallonsa, Khaleel ya gyada kai cike da tsanarsu yace "Ku ka rabani da Mahaifiyata ina d'an shekara uku ban san kaina ba, ku ka kawo ni cikinku, ku ka lalata min rayuwa, ku ka cuceni, kuka koya min mugun hali da mugun nufi, Billah karshen ku ya xo a duniya, daga yau ina me sanar maku da babban murya cewar idan ku ka sake bibiyana tare da abokina Zayyad kuna ci gaba da tursasa mu kuna cusa mana mugun tunani da mugun nufi a kan mutanen da basu ji ba basu gani ba za ku kare rayuwarku daure a kurkuku, na har abada....." Bude baki duk suka yi suna kallonsu, tuni Zayyad ya mike ya xaro nasa bindigar shi ma yana nuna ma Oga Manga, Khaleel na huci ya nufi kofa yana tafiya da baya yana nuna su da bindiga haka Zayyad ma yyi har suka fita daga parlon still pointing there gun toward them, a haka su Khaleel suka isa gate ta baya har suka fice daga gate din, da gudu suka shige mota a tare, Khaleel ya tada motar ya figa ganin su Manga sun fito a guje suka hau harbin tayoyin motar amma tuni Khaleel yayi masu nisa ya karya wani corner da motar.... Zayyad ya sauke ajiyar xuciya yace "It was successful" Khaleel bai ce komai ba sai gudu yake yana kallon madubi to be sure basu biyosa ba har dai yyi nisa sosai snn ya sauke wani ajiyar xuciya, Zayyad ya kunna record din da yyi da wayarsa yana murmushi.... Mami ce xaune living room tare da su Dinar da wata aunt din Khaleel sai sisters din Mami suna sauraron record din wayar Zayyad dake hannun Mami, sae da record din ya kare, kowa na parlon ya sauke ajiyar xuciya, ko wanne jikinsa yyi sanyi, Mami ta d'an yi murmushin karfin hali tana kallonsu Khaleel tace "Alhmdllh, it's a great job you two did, ku wuce sama kafin ku ci abinci" Khaleel ya d'an yi shiru sai kuma yace "Ummi baxa mu iya tafiya can gidana ba?" Dinar da Amira suka xaro ido, aunt dinsa Aunty Nafisa tace "Wani gidan kuma Aliyu, a yanxu ai baka da wani gidan da ya wuce nan, you just have to feel at home kaji" sister din Mami tace ce "Lallai kam, this is ur only home for now" Mami na kallonsa tace "You are not feeling at home here right?" Khaleel dai bai ce komai ba, a hankali Mami tace "Look at me" Kallonta yyi tace "Nan ne gidanku... wancan gidan kuma ba naka bane yanxu, beside you both aren't safe anymore to be thinking of going out" Shiru Khaleel yyi bai dai ce komai ba, Mami tace "Ku wuce sama, xa a kai maku abinci" mikewa yyi suka wuce dakin Junaid tare da Zayyad. Heedayah da Farida suka kawo ma kowa dake parlon abincin da suka gama girkawa tare da maid dinsu, Mami tace "Ku kai ma su Zayyad a sama, Su Umma ma suna dakina ku kai masu" Komawa kitchen din suka yi, Bayan Farida ta hada abincin Khaleel da Zayyad a tray ta sa ruwa da komai a kan tray din ta kalli Heedayah tace "Ki kai masu ya Zayyad din sama" Heedayah tace "Ki kai masu sai in xuba ma su Umma" Farida tace "No dont worry ki kai ni xan xuba masu" Daukan abincin Heedayah tayi ta fita kitchen din ta wuce sama, ajiye tray din tayi kasa bayan ta isa kofar dakin Junaid ta bude kofar snn ta duka ta dau tray din ta shiga dakin da sallama, Khaleel ya shiga buttoning shirt dinsa da ya cire button din yana kallonta, tun da ta kallesu sau daya ta dauke kai ta ajiye tray din abincin a saman carpet din dakin ta mike tace "Ina yinin ku?" Zayyad yace "Sannu da aiki" tace "Nagode" ta d'an kalli Khaleel ganin kallonta yake, ta d'an yi murmushi tace "Welcome" yace "Thanks, ke kika yi girkin?" Tace "Ni da Farida da Zainab" Yace "Toh Sannun ku" juyawa tayi ta nufi kofa ta nufi kofa ta fita daga dakin, Zayyad na kallonsa yace "I wish xa a baka auren yarinyar nan, nasan ba lallai ciwon ka ya dinga tashi ba kuma...." Khaleel ya kallesa bai dai ce komai ba, Zayyad ya girgixa kai yace "But I don't think a governor will give you his daughter hands in marriage, duk wanke kan da xa ayi kuwa" Shi dai Khaleel bai ce masa komai ba still. Khaleel na dakin Junaid har bayan isha yana wasa da Fadil da Affan din Amira, Zayyad tun da aka yi isha bai shigo ba, Bude kofar dakin aka yi ya daga kai, Heedayah ce tsaye daga bakin kofar tace "Ya Khaleel wai ka sakko downstairs" bata jira cewarsa ba ta juya ta wuce, tare da su Fadil ya sakko, ya tadda Dinar da Amira sai Farida da wata cousin sister dinsa Sumayya xaune parlon, sai kallonsa Sumayya take har ya shigo parlon ya xauna su Fadil na makale da shi, Amira na murmushi tace "Kana ta xaune kai kadai daki" Khaleel yyi murmushi yace "Gashi muna hira da boys"