Kenza eBookz

Idan kaya ya gaji part 2 - Chapter 4

Idan kaya ya gaji part 2 - Chapter 4

Idan kaya ya gaji part 2 Chapter 4: Idan kaya ya gaji part 2 Chapter 4. GIDANSU BABANGIDA KACIGARI:.

4,406 words

GIDANSU BABANGIDA KACIGARI:.

Kawu Manga yana gurfane a gaban wanshi yana yi mishi bayanin yadda suka ƙarke a tsakankaninsu da Alhaji Abubakar Baban Bola. A jiya da daddare bayan sun baro asibiti kenan. Yaso ma tun jiya yazo wajen wan nashi sai dai yace bari ya bari yau tunda Alhamis ce almajirai babu karatu sai rubutu, wanki, da wanke allo. Wawo na daga gefe yana jinsu. "Gabaki ɗayan dukkan kadarorin yaronnan da muka yi musu kuɗi basu kai kuɗin da Alhaji Abubakar Baban Bola yake binshi ba, ciki mun haɗa da motar shi, da motar Amaryarshi. Kuɗaɗen dake cikin asusun bankinshine bamu san ko zasu isa a cikita bashin da ake binshi ba, a samu a gagganɗa a biya wannan kuɗaɗe domin dai kada a shiga wannan kotu Yaya. Shi Alhajin zamu rokeshi ayi rubutu dasa hannuna da garantonshi, dasa hannun lauyan kamfani takaddun kadarorin duk su zama mallakinshi, ya ɗan ɗaga mana ƙafa kafin mu haɗa ƴan uwa ayi karo karon taimakon wannan yaro. To babbar damuwata shine Babangida bazai tsira da komai ba daidai da muhalli sai mu mun taimaka mishi da inda zai zauna tare da iyalanshi. Mata har uku ga yara. Muna nema ma wannan yaro alfarma daga cikin gidajen hayar da kake dashi a bashi koda falle_fallene yaran sa dinga bin ɗakuna" Murmusawa Baba Malam yayi daman wajen da yake son azo kenan. "Manga kenan. Lallai son Babangida ya gama rufe maka idanu. To amman ka sani ni idanuna a buɗe suke ras. Kasan Allah ko haya bazan iya barin Babangida yayi a gidajena ba, balle har ni in bashi muhalli kyauta ya zauna. Batun kuɗi da kake yi, ni fa wannan duk bata shafeni ba in kun mance tattaunawar da mukayi daku anan wajen in yana magana shima bai mance ba, dangane da dukiyar da Babangida yake ta wadaƙa da'ita, sai auren mata yake yana sakinsu, ba'a wata uku zai kuma jajiɓowa kai kuma ka ɗaura mishi auren. Yaita ma mata ɓarin dukiyar mutane, yaita saka suturun alfarma. Sai yanzu data dame mishi ne za'ace inyi wani abun? La babu abinda zance, babu abinda zanyi akai. Kuma ina mai shawartarku da ku bari aje kotu domin alƙalai suke da hakkin fitarwa da me hakki hakkinshi, tunda harkar kasuwanci suke yi, Babangida shike juya kuɗi. Iyakar shawarata kenan. Ita Shari'a saɓanin hankalice sai kuga kun tsira da wasu abun da bakui zato ba. Ai kana maganane akan gudun zubar da mutuncin gidan ko? Akwai wani abun kunya da za'ayi kuwa wanda Babangida bai riga yayi bane? Karfa ka mance Manga..." "A_a Yaya ya isa dan Allah. Mun gode da shawararka in sha Allah zamu je kotun a yi komai acan Wawo taso muje mu tattauna" Cikin gidan suke shirin shiga Baba Malam yace. "A_a Manga ba dai a cikin gidana zaku tattauna wannan maganar ba. In wajen Babba kuke son zuwa to kai Wawo shiga ka kirawota kuje can gidan Manga ku tattauna amman ba a gidana ba kuwa." Ba ƙaramin mamaki sukai ba. Amman in suka duba girman Malam da girman laifukan Babangida sai sui ma malam uzuri. Wawo ya shiga ya kira Malama Babba suka haɗu dasu sa'a a gidan Kawu Manga akaita tattauna yadda zata kaya daga karshe suka tsaya a matsaya guda ta a bari a shiga kotun ko Allah zaisa Babangida ya tsira da wani abun. "To amman matanshi kuna ganin a sanar musu halin da ake ciki ko kuwa a bari a ƙarƙare zaman kotu?" Kawu Manga ne yake tambayarsu. Wawo yace. "Gudun kada a saka su cikin damuwa kan damuwa inaga a bari aga ƙarshen shariar tukunna. Kome kika gani Sa'a Kudidi?'" Sa'a da jikinta yayi murus tace. "E Wawo hakan yayi kada ayi gaggawar sanar musu tukunna. Mu jira abi komai a hankali. Amman ya batun karar da waccan balagazar ta shigar?" Usman yace. "Akan wannan ƙarar data shigar Malama gata a zaune ko bacci bata iyayi. Duk halaccin da Baba Malam yaima yarinyarnan gada abinda zata saka mana nan" Malama Babba ta nisa tace. "Zaima saketa kowa ya huta. Yaji da ɗaya. Jira nake a sanarmun da farfaɗowarshi tukunna. Ko a wayana zan kirashi muyi maganar. Tunda ya kamata da wani namijin ai dole ma su rabu." Naja'atu tace. "Ya kamata yaranma a kaisu asibiti ayi musu gwaji domin a tabbatar da nashi ne Amman malama Babba aurenki fa?' Kawu Manga yace. "Gidanku Naja'atu. Nace hakan ki. Yara dai namu ne da gani domin basu da bambanci da yaran Wawo da yaran Sa'a mu kininmu baya ɓuya. Sannan ke Babba da kike cewa zaki saka Babangida ya saki Sabuwa hala kin mance da sharaɗin Yaya ne ko? Abi komai a hankali dai." Haka dai akaita tattaunawa daga baya suka watse. Wawo da matarshi suka tafi kai abinci asibiti.

Asibiti:. Tun sassafe Yar shuwa ta kasance a asibiti. Hamida kuma taje raka iyayenta tasha zasu ɗauki hanya. Tana zaune a doguwar kujerar dake ɗakin da Babangida yake kwance tanata tunani a ranta so take tasan menene yake faruwane taga tamkar dangin Babangida da akwai abinda suke ɓoyewa dai. "Amman koma menene in tayi wari maji" Ta faɗi hakan a zuchiyarta. A hankali Babangida ya buɗe idanunshi ya kalli sama, ya dawo da kallonshi wajen Ƴar Shuwa da Ramadan dake zaune a kujerar roba yana gyangyaɗi. "Ramadan ka kira mun Mustapha a waya inason ganinshi" Ya faɗa yana nishi irinna jiki yayi tsanani. Saida Ramadan ya garzaya ya kirawo ma'aikatan jinya kafin ya isarma da Mustapha saƙon Babangida. Mustapha yace dama suna hanya shi da matanshi gashi nan ƙarasowa " Likita na tsaye a kanshi yana aunashi, ga nurse a tsaye da kwando ɗauke da takaddu da magungunan marasa lafiya" "Malam Babangida ka daure ka rage ma kanka damuwa sabida jininka ya samu ya sakko. Kaga jinin bai sauka yadda ya kamata ba. Tunda dai kai musulmine dole ka yarda da kaddara me kyau ko akasin hakan. Ka duba iyalinka da iyayenka karka kashe kanka a banza yaranka suna buƙatarka a raye" Dr ya dinga mishi nasiha tare da bashi musalai masu yawa, har da jawo mishi hadisai da ayoyin Qur'ani mai girma. "Nagode sosai Dr. Komai zai daidaita in sha Allah." Idanunshi ya runtse zuchiyarshi ke tuka mishi. Har aka gama wanke mishi ciwon aka sake yima wajen dressing Babangida idanunshi arufe sai ajjiyar zuchiya yake saukewa. Bawai baya jin zafin ciwon bane har cikin ranshi yake jin motsin zafin. Amman zafin da zuchiyarshi take ɗauke dashi ya doke zafin ciwon zafi. "Yanzu ka samu kaci abinci kasha magangunanka, sai ka daure kayi wanka. Amman sai dai a goge maka jiki da tawul kada a kwara maka ruwa a jikinka. Magungunan ya mika ma Ramadan, yayi musu sallama ya fita. "Ramadan taimaka mun in soma watsa ruwan tukunna, ji nake kamar na shekara babu wanka. Ramadan ya taimaka mishi suka shiga bayan gida, shi ya goge mishi jiki da tawul, ya buɗe mishi sabon brush yayi. Alwala ya ɗauro mishi ta hanyar shasshafa mishi ruwa ya kuma taimaka mishi suka fito. Saida yaci abinci, yasha tea, ya haɗiyi magungunanshi kafin daga gadon ya soma rama sallolin da ake binshi. Duk wannan bidirin bakin Ƴar Shuwa bai rabu dayi mishi sannu ba. Daidai da sannunta sau ɗaya bai amsa ba, inda take ma bai kalla ba. Mustapha da iyalanshi ne suka turo ƙofar suka shigo suma niƙi_niƙi da kayan abinci a basket. Daga me ciki, sai me goyo, sai me jego a matan Mustapha. Gaggaisawa akayi kafin Mustapha yace Dukkanku ku bamu waje zamu tattauna in mun kammala kwa dawo" Matan Mustapha da Ramadan suka fice, Ƴar Shuwa kuma ta gyara zama ita a tunaninta ai duk abinda za'a tauna yana da alaƙa dasu. "Ke me kike nufi da ba zaki fice ki bama mutane waje ba?" Babangida ya faɗa da ɗaga murya yana zare idanu tamkar zai cinyeta. "Kayi haƙuri jannaty da bata maka rai da nayi natuba. Amman kaga yanzu haka daga gida aka turo mun hoton Sabuwa ita da wani a zaune" A razane ya kalleta yana son ya furta kalma harshenshi ya gaza haɗa kalmomin da za'a fahimta. "Ya haka baiwar Allah, ya ina ganinki da hankalinki zaki faɗa ma mara lafiya irin wannan maganar kuma?" Cewar Mustapha kenan. "Ka kyaleta wallahi so take zuchiyata ta buga in mutu a raba musu gadon dukiyata ki fice a ɗakinnan" Cikin fushi tayi ficewarta asibitin ma ta bari baki ɗaya dan ji take da badan Babangida jinya yake yi ba bai isa ya daka mata tsawa bata mayar mishi ba. "Mustapha yaya kuka ƙare dasu Sumy ne da Ramatu, wayata na hannunka ko?" "Tana wajena dukkansu so suke dole sai sun zo asibitinnan sun duba ka. Kasan Allah da ace dukkansu sunsan a wanne asibitin kake kwance da tuni sun ɓaro maka aiki. Amman ni ba wannan ba batun Alhaji Abubakar Baban Bola shi yafi ɗaga mun hankalina in fa bawan Allahnnan kudinshi za'a biya shi Babangida wallahi dukiyar daka tara kab sai ta ƙare kuma bata kai ka biya shi kuɗinshi ba. Nace kenan asirin rufin bakin da akayi mishi tsawon shekaru shine ya karye? Cewa nayi ko zan kuma komawa Inugun ne in samu malamin a sake rufe bakin shi Alhaji Abubakar Baban Bolan?" Kai Babangida ya shiga girgizawa tunda Mustapha ya soma magana, saida ya jefo mishi tambayar ƙarshe ya samu zarafin cewa. "Kaiya Mustapha bakin alkalami ya bushe. Ai tunda Alhaji Abubakar Baban Bola ya samu baki ya fallasa wannan maganar taje har kunnen Kawu Manga da Wawo kaima kasan tabbas Baba Malam yasan da maganar. To shi in an rufe bakinshi su iyayena da ƴan uwana yaya zanyi dasu? Asirina ya riga daya fallasu" Mustapha ya busar da iska daga bakinshi yace. "A_a Babangida kacigari karka sare. Har su Baba Malam ɗin ba sai a sa a rufe musu bakinsu ba? Talauci da tsiyane fa suke shirin tukaroka. Ka bari a sake sabgarnan kaci gaba da dama dukiya" Hannu ya ɗaga mishi hakan ya tilastama Mustapha yin shiru. "Mustapha ba zaka gane bane. Mu ajjiye wannan maganar a gefe ta riga tazo ƙarshe mu dawo maganar Sabuwa zuchiyata jinta nake tamkar zata tarwatse Mustapha. Kai a tunaninka wanne matakin ya cancanta in ɗauka wanne hukunci zata karɓa ita Lolon?" "Hmm ni a nawa muguntar duk runtsi kada ka sake ta IDAN KAYA YA GAJI... GAMMO MA YA GAJI LITTAFI NA BIYU SHAFI NA HUƊU BADIAT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI

https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA

Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??

Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available ba order ba??

Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta??

Kiyi joining wnn group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki.

Muna da kaya available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾 Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽 08093932955

"Zanso insan menene dalilinki na shigar da ƙarar mijinki ya sake ki, shin wanne hujja kika riƙa a matsayin babban dalili, sannan in ba'a kotu ba bazai iya sakin ki bane?" Kaga lauyoyi duka wannan tambayoyin lokaci guda aka watso mun. Kuma ya kafe ni da baƙaƙen idanunshi yana jiran amsa. Dalilin da yasa na shigar da ƙaran shine bana sonshi, duk kwanan duniya ƙara tsanarshi nake yi. Hujjata shine. Ya dena ciyar damu, baya shayar damu, baya mana sutura, baya biyan kuɗin makarantar yara, baya mu'amalar aure dani. Sannan tambayarka ta uku tsawon shekaru sama da goma ina faɗin ya sake ni yana cewa ni dashi mutuwace zata raba, kuma badan yana sona ba sai don mugunta kawai" Kanshi ya jinjina yace. "Yana cin zarafinki ne, ko zarafin iyayenki, sannan yana dukanki ne?" Babu wanda bayayi daga cikin abinda ka lissafo. Babangida ya wuce tunaninka, wata iriyar baƙar zuchiya gareshi." Shiru yayi yana nazari can ya jefo mun wata tambayar. "Auren dole kuka yi ko Auren soyayya kuka yi?" Bazan ce auren dole ba, ba kuma zance auren soyayya ba. Babangida yayi mun irin soyayyar da babu mahalukin da zai iya yi mun ita a duniya. Daga baya ne komai ya lalace. Amman karka tambayeni dalilin lalacewar domin bata shafi shari'ar ba" Murmusawa yayi kawai kafin yace. "Iyayenki suna bayanki ne akan shari'ar kamar yadda Baba Malam yake bayanki?" Kai na girgiza nace. A_a basa bayana kona misƙala zarratin." Mijin Labbai ne yazo ya wuce mu, Labbai tayi tsaki ta bishi da harara. Barrister Ahmad Ahmad yace. "Baba Malam menene halaƙarshi dake?" Shine mahaifin mijin nawa" Har a jikinshi saida mamaki ya bayyana ba'a iya fuskarshi ba. "Ban gane ba. Kina nufin ɗanshi kika maka a kotu kuma ya ɗaukar miki lauya, yake ta jaddadamun inji tsoron Allah in yi iyakar yina a ƙwato miki hakkinki Babangida ya sake ki?" Tabbas mahaifinshi ne" "Toh Malama Sabuwa ni zan wuce in ma akwai wata tambayar zan bugo miki waya saimu tattauna. Ki kuma zauna da shirin fuskantar Shari'a ki sani kuma saɓanin hankalice, tamkar macece da ciki, kinga sanin abinda zata haifa sai Allah. Na barku Lafiya" Ya miƙe da sauri ya tafi. Nayi shiru a zaune a dakalin Labbai tace. "Wai kinsan tunda kuka fara magana da lauyannan ƙannen Ƴar Shuwa da mahaifiyarsu suke ta faman sunturi kuwa?" Baki na taɓe nace. Ina ganinsu sunata wucewa kamar ƙawayen Amarya. Naga Malam Habu ya wuce" "Malam ko buzuzu? Dallah tashi mu tafi ni. Aurene ni dashi ya ƙare" Ashe yana tawowa duk abinda Labbai tace a kunnenshi. Yana ƙarasowa buɗar bakinshi sai cewa yayi. "Aure kam ya ƙare, domin ni ba lusari bane da zan zuba idanu ina kallonki da aurena kina bin maza kamar yadda aka kama Sabuwa ba, yanzu ma ba gashi na kama ku ba. Na sake ki saki guda, dama dai kwaɗayine irin namu na maza shi yasa na auro karuwa" Naji zafin maganganun Malam Habu sosai. Musamman karuwa daya cema Labbai. Kafin in ankara Labbai ta cukumeshi tana ihu tana kwaroroto. Wallahi kafin ƙiftawa da bismillah sai ga jama'a sun taru. Malam Habu ya dinga cauɗama Labbai carbi yana jefo manya manyan maganganu marasa daɗin saurare a kanmu. Sama da ƙasa Allah baisa na iya cewa komai ba. Cikin munafukan da suka taru na kutsa na fincike Labbai a wuyan Malam Habu na jata kiyyy har cikin gida. A lokacin ƙurar cikin gidan ta lafa, Rakiya ma wanki take yi, Hauwa na kwalima. "Wai menene dama daku ake hayaniya ne Labbai. Ni naji matan Malam Habu sunata ɗuma zagi ta katanga. Kafinma mu bada amsa muka jiyo zagin. Turmi Labbai ta hau sukaita zagi in zaga da iyalan gidan Malam Habu ta karanga Da ƙyar na fige Labbai muka shige ɗaki. Yaran gidan sukaita jifa daga gidansu zuwa namu. Dawowar Gaza yasa komai ya lalace. Yana shigowa aka jefo ƙaton dutse ya sauka a ƙafar Rakiya. A guje ya shiga gidan Malam Habu, Labbai ta bishi da gudu da wuƙa a ƙugunta. Hmmm abu dai babu arziki duk matan gidan shigewa ɗaki sukai suka kulle. Gaza ya saka ragunan Malam Habu gabas ya dinga yankasu. "Ƴan abu ta kazan uba. Ku shiga ku ɗebo kayanku mu tafi. Yasin duk matar da muka haɗu a hanya sai dai ta canja hanya in ba haka ba saina farɗeta." Haka mukaita jide kayan Labbai muna ficewa dashi. A guje Rakiya ta shigo. "Gaza matsa dale katanga ka wuce ga Malam Habu da kwalawa. Take katanga maza" Ragunannan daya yanka ya suri biyu ya yaɓa a kafaɗa suna yararin jini ya haye turmi ya dire bayan lungu. Yana direwa kwalawan na shigowa a guje. Jin muryoyin ƴan sanda yasa iyalan Malam Habu fitowa. "Kaga ta'asar da yayi mun ko? Yallaɓai ku wuce da waɗannan matan dukkansu, kuma wallahi sai an biyani ragunana raguna kusan takwas a yanka mun su sabida rashin tarbiyya Gude a mayar mun da kayan Labbai ciki" "A_a Malam ka rabu dasu kawai tunda dai mai rabawa ta raba. Wallahi ina jiye mana bala'in da zai biyo baya. Ni dai Malam ka dangana kawai. Tunda kai ka yayiɓo mana dama yaran gidan farare. Meye bamu faɗa maka ba? Kar ka bari a tafi dasu, muna da yara mata kada Gaza ya turo yaranshi sui ma yaranmu fyaɗe a banza da wofi" Tana faɗan haka sai jikin Malam Habu yayi sanyi. Take yaja ƴan sandannan waje, ya suka ƙare sai Allah. "Labbai maza kwashe kayanku ku tafi" Cewar Gude da ciki ya ɗuri ruwa. Rakiya tace. "Ai ba sai kince ba. Wallahi kinyi ma kanki Alamnashara Gude da zaman unguwarnan ya gagareku.Yanzunma sai fa mun so rigimarnan zata lafa. Labbai ku kwashe kayan mu wuce miji goma ba uba goma bane. Ku ɗakko mana ƙatuwar tinkiya in dai da Bismillah ya yanka" Dukkanmu muka haɗu muka kwashe kayannan Labbai kuwa saida ta kinkimi ƙatuwar tinkiya ta fice tana ta zage zage unguwa ashe ta cika ta batse sosai da sosai. Ohhh Allah rayuwarmu tana cikin garari. Shin haka rayuwarmu zatai ta tafiya babu sauyi ne?" Muna shiga gidan muka tarar Adama tazo tana zaune da takadda akan kujerar tsugunno tana gani munata shigo da kaya babu wanda ta kula. "Adama ke kuma fa wai?" Cewar Uzairu zuchiyata daya jingine katifa. "Hmmm kai dai muje daga ciki tukunna" Ta bashi amsa tana shigewa. Tare muka ɗunguma muka shiga ɗakin duk ƴan matan basa gidan dakin kaca_kaca babu shara, kwanukan da suka ci abincinma duk yana baje a tsakar ɗakin. Ga uban suturu a a ƙasa. "Adama wannan wai takaddar asibiti ce, ko kema dai sakin naki akayine duk kika wani yi laushi? Allah na tuba da irin wannan aure ba gara zawarci sau dubu ba? Jebakki fa fara sol wanke hannu ka taɓa" Rakiya ki dena ɗaga murya na jiyo muryar Layuza a tsakar gida " Ƙasa Rakiya tayi da muryar. "Ai Qamriyya ce yau za'a kawo sadakinta da kayan Aure, wani baƙauyen zai kwasa." Baki duk muka taɓe. "Ni ba wannan ba Rakiya sakina Baban yara yayi fa in faɗa miki har saki biyu. To kinsan a baya saki ɗaya ya taɓa yi mun. Yau kwana goma cib da sakin da na saka rigimar sai dai in zauna inyi zaman Ƴaƴana wallahi yau dai a guje da bulala ya rakoni, kun ganni sai makwabta ne suka bani takalmi da mayafi. Nazo na tarar anata rikici da mijin Labbai " Ni dai take kaina ya hautsine hawan jinina ya tashi sabida damuwa. "Hmmm ai Shikenan ke da Labbai duk auren naku dai ya tsinke. Ga dai filin tsakar ɗakinnan du ya ishemu, ga wannan mitsiyaciyar itama Auren nata take so ta kaso. Duk ku dawo kuzo mu zauna ciwon zuchiya yai ajalina ga baƙin cikin Maigogul ga naku." Tana faɗan haka ta sau kukan da nayi imani sabida aurenane da zan kashe ba dan mutuwar auren Labbai da Adama ba. "Rakiya ki dena kuka kada su Hauwa su jiyoki burinsu a kullum bai wuce su gammu a ƙasa ba" "Ke dallah su gammu a ƙasan mana ai babu da abinda Hauwa ta isa goranta mun babu iriyar ƴar iskar da bata dashi a ɗakinta. Sama ne ya leƙo ɗakin Rakiya kina ciki, Adama Sabuwa kune a gidan?" "Ahh Sama ai kai zamu tambaya kaine a gidan, wai Sama ina ka shige ne?" Cewar Adama kenan. Shigowa yayi da ƴar ledar kayanshi ya nemi waje ya zauna. Duk yabi ya lalace "Ina can kasashen inyamurai neman kuɗi Adama. In ka biye ta gidannan da rikicin gidan ina mai tabbatar miki likkafanin da inka mutu da tabarmar da za'a saka daga ƙarshe nema za'ayi a rasa in dai gidannan ne. Ya kuke ya yaran naku?" Duk muka amsa mishi da lafiya, Rakiya kuwa tagumi tayi. "Wai lafiya kuwa?" Kafin a bashi amsa saiga Hauwa ta buɗe labule. "Wai yau muryar wa nake ji kamar Sama'ila dama kana duniyarnan. Yaushe da rabon mu saka a idanunmu?" Kai ya ɗan sosa. "Wallahi Hauwa balaguro kawai nayi. Na shiga duniya neman kuɗi" Haɓa ta riƙe tace. "Kuma wacce sana'ar ka kama Sama?" Harara Rakiya ta zabga mata harda jan tsaki. "Bige_bige ne duk abinda na kama yi nake yi. Amman kamar dai lokacin kirsimeti ina zaga garuruwan inyamurai ina tallen balambalo" Sai da Hauwa tayi dariya kafin tace. "Ai yafi maka zaman banzan. Kaga ƙaninka ma mijin Layuza ya kaishi shagonshi dake kasuwa yana taya shi aiki." Sama yace" "Wai ma'aru kike nufi shine aka saka a kasuwa. Yaron da ko ɓera bai kaishi sata ba? Kai Hauwa nifa ina tsoron kada yaje ya kuntaka mishi sata azo ana raba hali" Ai nan Hauwa ta shiga zage_zage haka ta saki labule. Sama kuma ya suri ledar kayanshi yakai ɗakinsu na langa_langa yayi ficewarshi. Yana waƙe_waƙe. Shi sabida tsabar shaye_shaye bama saka shi a lissafi dan ba kullum yake da hankali ba. Wataran ma sai a wayi gari dashi yaita danna ihu shi kaɗai ƙwaƙwalwar ta riga da ta taɓu. Ga ƙazanta a cikinshi kamar me. Wayata ce tayi ruri Baba Malam ke kirana. Da sallama na ɗaga muka gaisa. Sai yake tambayata lauya yazo kuwa? Nace mishi yazo yanzu ma gida nake son in koma bana jin daɗi sai zuwa yamma ko gobe zani asibiti. Da haka mu kai sallama na ajjiye wayar. Labbai taso mu tafi ni zazzaɓi nake ji gashi ban tawo da magungunana ba." "Bari in biyo ku nima Rakiya sai mun dawo kawai" Cewar Adama data miƙe. Rakiya ma miƙewa tayi. "Nima zan fita nema banci ta zama ba hantsi yayi. Kayi nayi yanzu aka soma" Tare muka fice mu makai titi, Rakiya tayi saman layinmu sana'ar kayi nayinta. Muna isa gida na kwanta a kujera sai Labbai ce ta bani magungunana na haɗiya naji dama dama. "Yanxu bari in ɗaura abinci ki daure zuwa yamma sai mu tafi asibitin ko minti goma ne muyi sai mu dawo" Kai kawai na ɗaga ma Adama, dan idanuna a rufe suke suna fitar da hawayen ciwo ga magungunan sun soma ɗibana."

GIDANSU BABANGIDA KACIGARI:.

Kawu Manga yana gurfane a gaban wanshi yana yi mishi bayanin yadda suka ƙarke a tsakankaninsu da Alhaji Abubakar Baban Bola. A jiya da daddare bayan sun baro asibiti kenan. Yaso ma tun jiya yazo wajen wan nashi sai dai yace bari ya bari yau tunda Alhamis ce almajirai babu karatu sai rubutu, wanki, da wanke allo. Wawo na daga gefe yana jinsu. "Gabaki ɗayan dukkan kadarorin yaronnan da muka yi musu kuɗi basu kai kuɗin da Alhaji Abubakar Baban Bola yake binshi ba, ciki mun haɗa da motar shi, da motar Amaryarshi. Kuɗaɗen dake cikin asusun bankinshine bamu san ko zasu isa a cikita bashin da ake binshi ba, a samu a gagganɗa a biya wannan kuɗaɗe domin dai kada a shiga wannan kotu Yaya. Shi Alhajin zamu rokeshi ayi rubutu dasa hannuna da garantonshi, dasa hannun lauyan kamfani takaddun kadarorin duk su zama mallakinshi, ya ɗan ɗaga mana ƙafa kafin mu haɗa ƴan uwa ayi karo karon taimakon wannan yaro. To babbar damuwata shine Babangida bazai tsira da komai ba daidai da muhalli sai mu mun taimaka mishi da inda zai zauna tare da iyalanshi. Mata har uku ga yara. Muna nema ma wannan yaro alfarma daga cikin gidajen hayar da kake dashi a bashi koda falle_fallene yaran sa dinga bin ɗakuna" Murmusawa Baba Malam yayi daman wajen da yake son azo kenan. "Manga kenan. Lallai son Babangida ya gama rufe maka idanu. To amman ka sani ni idanuna a buɗe suke ras. Kasan Allah ko haya bazan iya barin Babangida yayi a gidajena ba, balle har ni in bashi muhalli kyauta ya zauna. Batun kuɗi da kake yi, ni fa wannan duk bata shafeni ba in kun mance tattaunawar da mukayi daku anan wajen in yana magana shima bai mance ba, dangane da dukiyar da Babangida yake ta wadaƙa da'ita, sai auren mata yake yana sakinsu, ba'a wata uku zai kuma jajiɓowa kai kuma ka ɗaura mishi auren. Yaita ma mata ɓarin dukiyar mutane, yaita saka suturun alfarma. Sai yanzu data dame mishi ne za'ace inyi wani abun? La babu abinda zance, babu abinda zanyi akai. Kuma ina mai shawartarku da ku bari aje kotu domin alƙalai suke da hakkin fitarwa da me hakki hakkinshi, tunda harkar kasuwanci suke yi, Babangida shike juya kuɗi. Iyakar shawarata kenan. Ita Shari'a saɓanin hankalice sai kuga kun tsira da wasu abun da bakui zato ba. Ai kana maganane akan gudun zubar da mutuncin gidan ko? Akwai wani abun kunya da za'ayi kuwa wanda Babangida bai riga yayi bane? Karfa ka mance Manga..." "A_a Yaya ya isa dan Allah. Mun gode da shawararka in sha Allah zamu je kotun a yi komai acan Wawo taso muje mu tattauna" Cikin gidan suke shirin shiga Baba Malam yace. "A_a Manga ba dai a cikin gidana zaku tattauna wannan maganar ba. In wajen Babba kuke son zuwa to kai Wawo shiga ka kirawota kuje can gidan Manga ku tattauna amman ba a gidana ba kuwa." Ba ƙaramin mamaki sukai ba. Amman in suka duba girman Malam da girman laifukan Babangida sai sui ma malam uzuri. Wawo ya shiga ya kira Malama Babba suka haɗu dasu sa'a a gidan Kawu Manga akaita tattauna yadda zata kaya daga karshe suka tsaya a matsaya guda ta a bari a shiga kotun ko Allah zaisa Babangida ya tsira da wani abun. "To amman matanshi kuna ganin a sanar musu halin da ake ciki ko kuwa a bari a ƙarƙare zaman kotu?" Kawu Manga ne yake tambayarsu. Wawo yace. "Gudun kada a saka su cikin damuwa kan damuwa inaga a bari aga ƙarshen shariar tukunna. Kome kika gani Sa'a Kudidi?'" Sa'a da jikinta yayi murus tace. "E Wawo hakan yayi kada ayi gaggawar sanar musu tukunna. Mu jira abi komai a hankali. Amman ya batun karar da waccan balagazar ta shigar?" Usman yace. "Akan wannan ƙarar data shigar Malama gata a zaune ko bacci bata iyayi. Duk halaccin da Baba Malam yaima yarinyarnan gada abinda zata saka mana nan" Malama Babba ta nisa tace. "Zaima saketa kowa ya huta. Yaji da ɗaya. Jira nake a sanarmun da farfaɗowarshi tukunna. Ko a wayana zan kirashi muyi maganar. Tunda ya kamata da wani namijin ai dole ma su rabu." Naja'atu tace. "Ya kamata yaranma a kaisu asibiti ayi musu gwaji domin a tabbatar da nashi ne Amman malama Babba aurenki fa?' Kawu Manga yace. "Gidanku Naja'atu. Nace hakan ki. Yara dai namu ne da gani domin basu da bambanci da yaran Wawo da yaran Sa'a mu kininmu baya ɓuya. Sannan ke Babba da kike cewa zaki saka Babangida ya saki Sabuwa hala kin mance da sharaɗin Yaya ne ko? Abi komai a hankali dai." Haka dai akaita tattaunawa daga baya suka watse. Wawo da matarshi suka tafi kai abinci asibiti.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull