Kenza eBookz

Kurkukun ‘kaddara (the prisoners) book 2 - Chapter 37

Kurkukun ‘kaddara (the prisoners) book 2 - Chapter 37

Kurkukun ‘kaddara (the prisoners) book 2 Chapter 37: Kurkukun ‘kaddara (the prisoners) book 2 Chapter 37. Yawu commender Ya haɗiya Kutt throat dinsa Ya…

3,374 words

Yawu commender Ya haɗiya Kutt throat dinsa Ya bada sauti, shi kanshi daurewa yake yi, surar ummin America na neman kwance mashi masarrafinsa.

"Ina so ki natsu ki fahimce ni kafin ki bani amsa" amsa mashi tayi da toh Bayani ya soma yi mata dalla dalla tun daga farkon tsintarsu Angel da su ka yi a Daji, har izuwa kawosu asibiti, da kuma abun da su ke buƙata daga gare ta, tunda commender ya fara labarta mata, ta natsu tana sauraronshi.

"Muna so ki bamu haɗin kai wurin Kula da yaran ki ruƙe su tamkar ƴa'ƴanki, munsan zaki Iyane shiyasa muka za6e ki, tun da ba yau kika fara yi mana aiki ba, mun yarda dake ummi, burinmu ki tarairayesu ta yadda yaran zasu yarda dake har su Iya faɗamaki ainihin abun da ya faru arayuwarsu' ya ƙarasa maganar idonshi akan fuskarta. Lumshe ido ta ɗanyi kafin ta waresu akan fuskarshi

"ta ya ya zaku yi tunanin damƙa amanar yara har goma sha ɗaya a hannuna? Bayan kunsan wacece ni, Ban ta6a haihuwa ba, kuma ni banason Rainon ƴa'ƴa, ban ta6a sha'awar haihuwarsu ba, balle har in iya kula da yaran wasu, Ina mai baka haƙurin Cewa Ni bazan Iya wannan aikin ba! zaifi ku samu macen da tasan zafin haihuwa mai kamun kai ku bata rainon su" tana magana jikinta na jijjiga, major duk yabi ya susuce ya rasa natsuwarshi, ba dan commender na akusa ba da ba abun da zai hana ya damƙeta ko da zai sha mari ne.

"Ummi, Ki sassauta kalamanki, Kina yi min magana da tsiwa, Ko kin manta a ina kike ne? Ki duba da kyau ki gani, nan ba club ba ne, ba kuma gidan karuwai bane, sannan ba ga6ar taku bane, Head quarter din sojoji ce" Ya yi maganar tare da zaro bindiga daga cikin drawer chest na desk din gabanshi Ya daurata saman desk din.

Tuntsirewa Tayi da dariyar rainin wayau

"Kai ma ka sani, Ummin america bata tsoron bingida, ni da ni ke yin mu'amala da masu ruƙeta, yanzu haka da nake yi maka magana shigowa ta head quarter din nan gaba ɗaya na tada masu jarabarsu, suna can waje, wandunan su sunyi masu nauyi' cike da shaƙiyanci tayi maganar, ta riga ta gama raina su bata jin tsoron su ko kaɗan.

Cikin kwantar da murya commender yace"is ok, kibar yi min wasa, Muyi magana ta hankali, ki taimaka ki kar6i buƙatarmu, kome kikeso zamuyi maki, sannan ɗawainiyar yaran da komai nasu mune zamu bada tallafin da za'a cigaba da kula da rayuwarsu, tun daga cinsu shansu, suturarsu, da karatunsu, Iya taimakon da muke so kiyi mana kija su a jiki ki zama tamkar mahafiyarsu" yamutsa fuska tayi tana faman wurwurga eye balls dinta tace"Kana nufin wai a gidana zasu zauna? Ka san gidana gidan mazane, a koda wani lokaci Ina busy wurin biya masu buƙatarsu, how ka ke tunanin zasu Iya samun kulawar data dace? Kuma naji kace yaran suna fama da depression hada me ciwon ciwo, gaskiga ba ƙaramar ɗawainiya bace kula da su, bazan Iya ba commender, kada ka tursasamin, kasan ina girmamaka saboda halaccinka agareni"

Kallon major commender yayi, hakan ya bashi damar Yi mata magana

"Ba zamu takura maki ba, amma kafin ki tafi Inaso zan nuna maki hotunan Yaran Ki gansu"

Miƙewa Major yai daga saman kujerar da yake a zaune Ya zagaya ta 6angaren Commender Ya juyo mata da laptop din saitin fuskarta.

Operating ɗinta Ya soma Yi, hotunansu Angel Ya buɗo, daga kan hotonta Ya fara Nuna ma Ummin america "Sunanta Angel" Ya ambaci hakan yana kallonta, da alamun mamaki akan fuskarta ta furta "wow she's beautiful sai dai daga ganin bakinta za ta yi tsiwa, ni kuma bana sha'awar Yara masu masifa" ta faɗa haɗi da yamutsa fuska, still murmushi ne akan fuskar major da commender.

Hoton Batul ya nuna mata, sai da ta ta6e la66anta kafin tace "tana da kyau, sai dai daga ganin fuskarta bata da masifa, wannan ko yatsa aka sanya mata abaki bazata Iya cizon shi ba" ta kare maganar tana hura hanci.

Hoto na gaba fuskar Hanna ce, Ummin america tace"har ƙwara Yarinyar daka wuce akan wannan, taci ka sanyi daga gani babu kuzari a jikinta" yadda take fayyace ɗabi'unsu kamar ta ta6a ganinsu.

Ko da akazo kan Hoton Parveen Ya cika screen din laptop din.

Da buɗar bakin Ummi sai cewa tayi"yarinyar nan daga ganin kumatuntu mayyar abinci ce, zai yi wuya idan ba asame ta da shegen ci ba, Ni bana so mutun mai ciye ciye" murmushin fuskar Major da commender sai ƙara faɗada yake yi, don ba ƙaramin nishaɗi take basu ba.

Hoton Jamimah Ya nuno mata, waro ido waje tayi hada sanya Hannu ta dafe saman ƙirjinta.

"Major, ruƙon wannan Yarinyar ai sai likitan mahauka, shi kaɗai ne zai Iya sarrafa ta, ba dai ni ba, Ni ina zan Iya kula da ita, daga ganin bakinta zatayi tsiwa" Major yayi dariya tare da nuno hoton Azeeza, shiru tayi tana ƙare mata kallo, kafin ta ɗago da ido ta kalli Major"sai naga kamar ƴan biyu ne ita da Yarinyar da ka nuna min kafin ita, sunyi kama" Major yace"haka muke tsammani, sai dai muna hasashen azeeza tafi Jemimah shekaru kamar yadda ɗan uwansu ya faɗa mana"

Yamutsa fuska Ummin america tayi"tana da kyau sai dai daga ganinta matsoraciya ce, wannan ko tsawa na daka mata zata Iya sakin fitsari a wando, gani da tsiwa bansan ya zamu ƙare da ita ba" ta fada tana ta6a baki tace"wai Iya matane Yaran"? Ta yi tambayar tana kallon Fuskar Major

"akwai maza" ya bata amsa, a dai dai kan hoton Haris Ya buɗe mata shi.

"Sunan shi Haris, shine yaron da commender Ya faɗa maki cewa Yana fama da ciwon zuciya"

Ta6e baki tayi"nifa banason namiji mai raunin zuciya, daga gani baya da hayaniya ba laifi yana da kyan fata" ta faɗi hakanne saboda kasancewarta baƙar fata, tana son mutun me duhun fata.

Wuce hoton Haris yai adai dai kan hoton Javed ya dakata Yana dubanta

"Amma dai wannan Yaron ɗan south korea ne ko?

Major yace"bamu da tabbacin ɗan Ina ne, duka yaran bamu san wani jinsi bane, sai dai sun faɗa mana cewa Ƴan Nigeria ne" da sauri ummin america ta girga kai tana fadin"Impossible, babu kalan waɗannan a nigeria, may be sun yi loosing memory ɗin su ne shiyasa su ka faɗi hakan"

Hoton Naufal Ya budo mata, lumshe ido ta ɗanyi tare da waresu akan kyakkyawan fuskarshi "Wow, kaga Namiji, sumar kanshi ta burge ni, Yayi min kyau" ta yi maganar tana hura mashi kiss.

"Yaro ne" Commender ne yace haka, Ummi tace"Ai shi namiji baya kaɗan, especially idan abunsa ya ruƙa, a wurina wannan ba yaro bane Namiji ne" murmushi suka saki, basu damu da abun da tace ba saboda sun san halinta, bata mu'amala da matasan samari, Sai mazan da su ke da aure waɗanda tasan idan ta bibiyesu za'ayi bala'i idan matansu suka kamata.

Bayan Ya wuce hoton Naufal Ya buɗe mata hoton Gabriel, tunda ta kafe shi da ido bata ƙyaftaba sai faman jinjina kanta take Yi alamar mamaki

Can dai ta numfasa tare da cewa"Allah Ya yayi halitta, gaskiya idan aka bani rainon yaran nan tamkar kun ba kura ajiyar nama ne, major idan akwai wani hoton nuna mini na ƙosa na ƙarasa ganinsu"

Lokacin da Major Ya hasko mata hoton Danish daga zaune ta zabura ta miƙe tsaye tana duban fuskarsa data cika screen na laptop din, duk suna akwance akayi masu hotunan idanuwansu arufe.

Muryarta tamkar tame Yin raɗa ta furta "Speechless! Major Ina kuka samun Kyakkyawar matashin nan mai kama da ɗan sarkin aljanu? Anya Cikakken mutunne? Ko dai A cikin Dajin da kuka tsintosu Aljana ta haife shi Ta yada" dariya kowan nan su ya saki jin sambatun ummi dama sai da ransu ya basu zata ruɗe idan taga hoton shi.

Major yace"sai ma kin ganshi a zahiri, ba ƙaramin kyaune da shi ba"

Ko da ta koma ta zauna, sam takasa ɗauke idonta daga kan fuskar Danish, Yayi matuƙar tafiya da imaninta, aranta har ta fara Ayyana koya surar shi zata kasance a zarihi?

Muryar Commender ce ta fargar da ita ga dubanshi"dukansu ne muka nuna maki, shin kin canza ra'ayinka akan kula da su ko kuwa har yanzu kina akan bakanki"

Shiru ta ɗanyi tana yanke shawara da zuciyarta, duk sun ƙagara da son jin amsarta.

"Yanzu haka case din Yaran mun miƙa shi hannun shugaban isod, shine zai cigaba da jan ragamar bincike akansu, jiya muka samu amincewarshi na kar6ar case din nasu, sai dai ya nuna baya buƙatar 6ata lokaci yanason ya tafi tare da yaran can nigeria a jet dinsa, a satin da zamu shiga"

Lokaci ɗaya ummin america ta canza fuskarta zuwa 6acin rai, da farko tayi murnar jin cewa Case din Yana a hannun chief na Isod, daga bisani daya furta komawa Nigeria ne taji komai ya fita aranta.

"Naji kin yi shiru, baki ce komai ba" Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta soma magana ranta a6ace"Idan har kuna so in ruƙe Yaran a hannuna, they should stay in America. I will not follow them to Nigeria,"

Commender yace"amma meyasa? Ke kanki fa ƴar ƙasar Nigeria ce why baki son zuwa ƙasar Ki"

Girgiza kai Tayi still fuskarta da 6acin rai ta furta"Ni ba ƴar nigeria ba ce, asalina ne acan, amma Ni black american ce, tun da nace banaso mubar maganar kawai, Ni zan koma gidan idan ka gama maganar ka"

Yanayin fuskarta Ya canza sosai, 6acin raine tsantsa, sun fahimci kamar akwai wani abu daya ta6a faruwa da ita wanda har yajawo silar barinta ƙasar, kuma batason Anayi mata maganar komawa can"

Ganin yadda ta haɗe rai babu annuri ko miskala zarratin akan fuskarta, Yasa Commender cewa"Shikenan ki kwantar da hankalin ki, ba zamu takura maki ba, Zaki Iya tafiya" ba don yaso ba ya ambaci hakan, duk basu ji daɗin canzawarta ba, muryarta a disashe ta furta"thank u" ta yunƙura ta miƙe ta nufi ƙofar fita daga office din, Har ta kusa ficewa Muryar Commender ta katse mata hanzarinta"duk da bansan abunda ya faru dake a ƙasarki ba da har yasa kika tsani jin an ambaci sunanta, da akwai wani abu da nike so in faɗa maki ummi" yayi maganar tare da miƙewa hannun shi ruƙe da mug na coffee, Ya kur6a kafin ya ɗaure da cewa"wannan dama ce agare ki, da zaki koma ƙasarki a karo na farko ki nuna ma waɗanda sukayi silar barinki ƙasar cewa Kina araye kuma kinsamu cigaba a rayuwarki ba kamar yadda sukayi tsammani ba, inaso ki basu mamaki ummi, sannan zuwanki Nigeri bana dundun bane na ɗan lokacine zaki dawo nan da zarar Mun samu nasara akan binciken Yaran, zamu dawo dake nan, saboda mu kanmu ba zamu so mu rasa nagartacciyar mace irinki ba, ke kanki kin sani muna ƙaunarki kuma muna daraja ƙimarki a idanuwan mu, ba zamu so abunda zai 6ata maki rai ba ummi, kina da damar da zaki Iya zuwa gida ki zauna ki yi tunani akan maganata kafin ki yanke shawara.

Kalaman shi sun ɗan ta6ata, tuni zuciyarta ta fara sassautowa, ita kanta zataso wannan damar ta zuwa Nigeria ko dan taba waɗanda sukayi silar barinta mamaki.

Numfasawa ta ɗanyi kafin a hankali ta juya tana kallon commender dake tsaye abayanta, kamar bata son furta maganar tace"babu buƙatar yanke shawara, Na amince Zan bi su zuwa Nigeria, Kuma nagode da karramawarku agareni, da zarar na gama aikin, zan dawo ƙasata"

Murmushi major da commender suka saki, Jin abunda tace, har yanzu bata yadda ta kira Nigeria da sunan ƙasarta ba.

Sun ji daɗin amincewarta, ba tare da 6ata lokaci ba, Commender ya dauko mata kundun dake ɗauke da bayanansu Angel, duka takardun akwai Signature dinsu a jiki, saura sanya hannunta suke buƙata, cikin ƙanƙanin lokaci su ka Ƙulla Yarjejeniya ta (guardianship agreement)atsakanin su da ita, sai da ta natsu ta karanta sharuɗɗansu dalla dalla akan irin rainon da suke so tayima yaran kafin ta sanya hannu a takardun, bayan ta kammala sun bata wasu takaddun yarjejeniyar da zata ruƙe a hannunta.

Bayan tayi masu sallama, Ta fito daga office din, tana tafiya Sojoji Na binta da kallo, Yayin da ita kuma hankalinta na akan takaddun dake a hannunta, Fatanta Allah yasa Ruƙon Yaran da za ta yi da kuma zuwan ta Nigeria Ya zama alkhairi agare ta.

Tun kafin ta ƙarasa gaban motarta da ta bari a harabar ajiye motocinsu, ta hango sojoji dadda6e sun kewaye motar suna jiranta, murmushin gefe fuska tasaki har dimple dinta Ya lotsa, ta fahimci tunda ta shiga office din commender suke ta jiran fitowarta don su yi mata magana, bata tsaya sauraron su ba, daƙyar ta samu suka ƙyaleta ta shiga mota, a tsanake ta tada motar, Ta juya sitiyarin da gudu ta fuce daga head quarter din.

*EX-PRISONERS❤*

Tun ɗazu da safe kowan nan su Ya farka daga bacci, sun wayi gari da jin kyakkyawan labarin farkawar Danish, saboda zumuɗin zuwa ganin shi babu wanda ya nemi breakfast acikinsu, gaba ɗaya sun Hallara a room dinsa, tun daga kan Haris, Javed, Naufal, Gabriel, Batul, Hannah, Jamimah, Azeeza, ƙwansu da kwarkwatarsu sun yi tsaitsaye cirko cirkon suna kallon shi, fuskokinsu ɗauke da Annurin farin Ciki, Ɗaya bayan ɗaya Danish Yabisu ya rungume su a ƙirjinshi, kamar sunyi shekara basu atare da juna, Haris hada kukanshi saboda murnar ganin Danish Ya farka.

Sun tasa shi gaba suna kallonshi kamar zasu lashe shi, Musamman Azeeza da Jemimah, daɗi suke Ji Danish ɗinsu Ya farka.

Muryar jamimah da shagwa6a tace"munyi fushi ma sai yau zaka farka, kullum sai munyi kukan rashin ka, ko bacci bamu Iya yi abincin ma ba mu ci" Harara Azeeza ta watsa mata"wlh ƙarya take yi Danish kullum sai taci abinci sau uku, kuma tana Yin bacci" Murmushi ya saki yana binsu da kallo, Haris dake zaune gefen gadon Danish ya ruƙe hannunshi a Cikin nashi ji yake kamar za a kwace mashi ɗan uwanshi.

"Meyasa Angel Jiya daya farka baki tada mu daga bacci ba? Bayan kinsan irin ƙagarar da muka Yi na son ganin shi" Hanna ce tayi maganar, Gabriel Yace"Ni dai ba abunda zance sai godiya, saboda ba zamu Iya misalta farin Cikin da muke aciki ba, Yau babbar rana ce agaremu ɗan uwanmu abun alfarinmu Ya farka da ranshi da lafiyarshi" yana daga tsaye yake yin maganar Ya goye hannayenshi saman ƙirjinshi.

"Allah sarki Rayuwa kenan, Har na tuna kokawar da Ku ka yi kaida Danish akan nace zan dire taga" gaba ɗayansu suka sanya dariya.

Batul tace"ai mu bamusan abunda ya haɗa su faɗa ba"

Parveen dake tsaye gefen Naufal hannunta ruƙe da Ayaba sai ci take Yi, Kunnuwanta akansu ta natsu tana sauraransu.

Labari Angel ta basu na abunda ya faru lokacin da zata dire taga, ba ƙaramin nishaɗi su ka yi ba.

Azeeza tace"munyi kuka lokacin sosai, Munyi tsammanin Danish ɗinmu zai rasa idonshi ɗaya, sai gashi Allah ya dawo mana dashi da ranshi da Lafiyarshi, gaskiya munji daɗi" da farin ciki akan fuskarta ta ƙare maganar, idanuwan Danish akan faces dinsu, ita da Jemamah.

Parveen tace"ni banaso muna tuna baya, nafi so inji muna magana akan abunda zai faru agaba"

Jemimah tace"Genie yaushe zamuje gidan daddyn naki? Ni na ƙosa mu koma can, waɗannan mutanan masu jan kumatun, kullum sai sun tsira mana allura a ɗuwawun mu" ta yi maganar tare da nuna ass dinta da indext finger dinta, gaba ɗaya suka tuntsire da dariya, Azeeza tace"Kai jamimah ki ji tsoron Allah, Jiya fa ba ayi mana allura ba, nurse ta faɗamin an gama yi mana ita, sai dai magani da zamu dinga sha na tsawon one month" turo mata baki Jemimah tayi Javed yace"Kufa baku gajiya da abun magana, Kun Cika ɗan uwanmu da surutu, Ko so kuke yi ya koma baccin" atare suka zaro ido haɗi da ɗan buɗe baki"A'a wlh bamu so Ya koma bacci,"

"Alhamdulillah, Tun da yanzu mun haɗu mu dukanmu, Yakamata Muyi wa Allah godiya" Angel Ce tayi maganar, Tare da Ɗaga tafin hannayenta sama, Da sauri suma suka ɗaga nasu zasu yi addu'a, Mutun ɗaya ne bai ɗaga nashi hannun ba, Hatta Gabriel da ya ke Christian sai da ya ɗaga hannunshi don su yi addu'ar atare, Don shi a yanzu baida za6in addini, yafi ƙarfi ta 6angaren musulunci saboda Angel.

Kallon fuskarshi Angel tayi"danish zamuyi addu'a, ba zaka ɗaga hannu ba" Girgiza mata kai Yayi alamar a'a, ɗaure mashi fuska tayi sai yayi tamkar baisan tana Yi ba Cikin sanyin murya Haris yace"Danish meyasa har yanzu baka goyan bayan addinin musulunci"?

Shiru danish bai yi magana ba, Kuma babu alamun zaiyi ta. Damuwace ƙarar akan fuskokinsu "Pls danish just for today ka ɗaga hannu Muyi addu'a" Muyar Angel tamkar zata fashe mashi da kuka Tayi maganar.

Marairaice mashi fuska Azeeza da jemimah sukayi"Bro pls, let pray together,"

Runtse idanuwanshi Yai, ba tare daya buɗe su ba Ya furta"I can't, ku daina yi mini magana akan Inyi, bana so"

Sai lokacin Batul ta sanya baki"tun da ya nuna bayaso mu ƙyaleshi, damu da shi duk abu ɗayane, ko da ace baiyi ba mu zamu yi mashi, hakan ma ya wadatar" Angel bata ji daɗi ƙin Yin addu'a da yai ba, addu'oi' ta soma karanto masu suna amsa mata da ameen ameen, idanuwanta sun cicciko tab da ƙwalla, bayan sun Kammala kowan nan su Ya shafa saman fuskarshi, banda Angel maimakon ta shafa addu'ar da tayi saman fuskarta, sai ta shafa ma danish saman sumar kanshi, a hankali ya ɗago da idanuwanshi yana duban fuskarta, harara ta watsa mashi tare da murguɗa mashi baki, hakan da tayi ba ƙaramin ƙayatar da shi yai ba, muryarshi ƙasa ƙasa ya furta mata"thank u" ta6e mashi baki tayi"kada ka yi tunanin na damu dakai," ƙayataccen murmushin gefen fuska yasakar mata, Su Batul sun natsu suna kallonsu.

Muryar Dr. laura ce ta katse masu hanzarinsu"Congratulation! My lovely Children Ina tayaku murnar farkawar ɗan uwan ku daga bacci, banjima da shigowa asibitin ba, dr Harry ke faɗamin cewa ɗan uwanku Danish Ya farka, wannan abun farin Ciki ne" ta ƙarasa maganar, a yayin da take ƙarasowa Gaban gadon Danish. Fararen idanuwanta dake asanye cikin farin glass ta ɗaura su kan face dinshi.

"An sanar dani cewa Baya kula kowa sai ƴan uwanshi, dagaske ne masoyiya Angel? Tayi tambayar tare da kallon Angel

Da fara'a akan fuskar Angel ta amsa mata da cewa "Jiya ne amma yau ya saki jiki, zai Iya magana da kowa"

Dr laura tace"Anya kuwa? Naga ko kallona baisan Yi, danish Ya jikin naka? Ko akwai inda ke yi maka ciwo a jikin ka"? Tayi tambayar cikin ƙagara da son jin muryarshi Cikin raɗa Angel ta furta mashi"danish pls kayi mata magana, sun taimake mu, kuma suna da mutunci" kamar wanda akayi ma dole daƙyar ya iya motsa lips dinsa ya furta"da sauƙi babu inda keyi mini ciwo,"

Dr Laura taji daɗin maganarshi"ina fata kaci abinci babu yunwa atare dakai"? Ɗaga mata kai yai alamar eh Ta furta"okey, amma meyasa jiya baka ba likitoci damar duba lafiyarka ba"? A takure yake yi mata magana"saboda lafiyata ƙalau, bana buƙatar a duba ni," Jinjina kai ta ɗanyi tayi mamakin Halinshi, basu ta6a samun patient irin shi ba.

Muryar Angel ce ta janyo hankalinta ga dubanta"Aunty, mun gode sosai da kulawarku agaremu, Allah ne kaɗai zai Iya biyanku," tayi mata maganar ne don ta mantar da ita zancen yi ma Danish maganar duba Lafiyar Jikinshi.

"kada ki damu masoyiya Angel, aikin mun e kula da lafiyarku kuma Alhamdulillah, Naga Jiki yayi kyau Allah ya ƙara Lafiya," ta ƙare maganar tare da kallon Azeeza da jemimah"My twins, Ya jikin naku" atare suka haɗa baki" da sauƙi" kafin ta ɗaura idonta kan Parveen da sauri ta 6oye Ayabar dake a hannunta, dariya dr laura ta ɗan saki"hmm ai na gani dama kin daina wahalar 6oye mini" duƙar da kai Parveen tayi fuskarta ɗauke da murmushi.

Kallonsu Gabriel Tayi"Ƴan samari, Jiki yayi kyau, badan sister dinku ta matsa akan son komawarku Nigeria ba, da a gidana zan killace ku, In cigaba da rainonku," murmushi kowan nan su ya saki.

"Zan Koma Office, Ku kula mun da kanku" har ta juya zata fuce Angel tayi saurin cewa"Aunty, har yanzu sojojin basu kira ba naji su shiru basu zo sun duba mu ba"

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull