Kenza eBookz

L u'u l u'u book 2 complete by huguma - Chapter 17

L u'u l u'u book 2 complete by huguma - Chapter 17

L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 17: L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 17. "Wannan ba muhallin wasa bane abdii,wannan din wani…

3,358 words

"Wannan ba muhallin wasa bane abdii,wannan din wani gagarumin aiki ne mafi hatsari da zakayi......faduwa ko nasarar dukka ni zatafi shafa kai tsaye......rayuwar motii rayuwar nanay rayuwar oromia gaba daya". Da wani kalan murmushin nutsuwar da bai taba gani ba saman fuskar abdii din yake kallonsa.

"Obbo......nayi maka alqawari.....zan cikashi,zan kuma baka mamaki" Abinda yace da haisam kawai kenan. Musayar kallo suka yiwa junansu na wasu daqiqu,haisam din ya dan daki kafadar abdii sannan ya ya juya a nutse yana ficewa.

Kamar a yanzun da suke gurin,ya rarraba aikin zuwa ga mutane daban daban,duk da basu da yawa,amma yana saka ran qaro wasu cikin mutanensu uku da suka rage suna rayuwa cikin agadez din tun kafin isowarsa qasar.

Beeno da salawi suna cikin hadiman,sun saje sosai dasu suna karantar reaction din kowa. Bayason bayyana fuskar dukkanin mutanensu,saboda hakan zai zama wani hadari ne na daban,kuma zai zama wata hanya ta rashin security.

Omari yana tare dashi amma ta bayan fage,yana tayashi monitoring motsin abdii da ya soma nisa cikin sassan mammina din.

Zuzzurfan muryar nan tasa dake dauke da wani irin amo ya sanya duk wani dake gurin nutsuwa da tattarar hankalinsu guri guda a kansa. Kusan ba wanda a gurin baisan sheikh muhammad haisam ba,musamman hadimai mazan dake cikin gidan,wanda dukkaninsu sun samu sanarwar nad'ashi a matsayin D'A,sanarwar da ta zauna cikin kwanyar kowanne hadimi na gidan take kuma aiki tamkar sauran dokoki cikin gidan.

Har cikin jinin tamim yakejin wani abu yana tsarga masa game da yanayin muryar haisam din,wani irin yanayi da ya saukar masa da wata mummunar kasala a dukka gabobinsa. Yana jin wani abu daban tattare dashi,yana jin wani yanayi na daban a muryarsa......kamanninsa dama tsaiwarsa gaba daya.

A nutse ya koma da baya bayan kammala jawabansa ya bawa ME WADA guri. Shine kusan dukkanin shugaban hadimai maza dake gidan,wanda haisam ya zauna dashi na mintuna goma sha biyar kafin su shigo nan din,ya kuma bashi tsarin abubuwan da zai gabatar musu.

Akwai sabbabin dokoki da tsare tsare daya shirya gabatarwa daga sanda sultane ya tashi zuwa umra. Sai a yanzu yake jin kamar wata dama ya samu da zai bude wuta akan aikinsa ba tare da tunanin sultane zai hango komai daga gareshi ba. Sabbin dokoki ne da zasu zama wajibi akan kowa dake rayuwa cikin gidan,yanaso kuma ya gabatarwa da sultane su ya sanya hannu a jimlace su zama TABBATACCIYAR DOKA da zai rarrabata tsakanin dukkan hadimai da bayi na gidan.

"Be fast abdii" Haisam ya furta qasa qasa yana duban tsakiyar tafin hannunsa da na'urar ke maqale,wanda zaka dauka tasbihi yakeja.

"Na kusa qarasawa ainihin muhallin da take kebancewa" Ya fada cikin qwarewa da takatsantsan da dukka motsinsa,duk da taswirar hannunsa da haisam ya tsarata tsaf tana nuna masa kowacce hanya daya kamata kayi.

Qofar glass din ya zuge gefe daya,ya kuma shiga a hankali. Tafkeken parlor dinta daya zama na musamman ne ya soma bayyana,wanda yake dauke da wani irin nau'in ado da yaja hankalin haisam din.

"Obbo......oromian....."

"Dakata!" Haisam ya tsaida abdii.

"Ba wani hatsari?" Abdii ya tambaya saboda tsayuwar data zama ta ba zata.

"Turn to your left side" Ya bashi umarni yanason ganin wani abu da yaga gilmawarsa. Yadda haisam din ya fadi masa hakan yayi,take tafkeken frame din dake dauke da wani nature drawing ya bayyana.

Sosai haisam ya zubawa frame din idanu,wasu abubuwa suna dawo masa akai. Wasu shekaru can baya da wasu memories da suka ja hankalinsa sosai.

"Ka dauki hoton frame din ka turamin......kafin ka shiga ciki.......kaje ka duban dining table na sassa......idan baka samu komai ba a nan ka qarasa store da yake manne da babban kitchen dinsu".

"An gama obbo" Abdii ya fadi yana ciro wayarsa yayi snapping frame din sannan ya soma laluben bangaren dining.

Ba jimawa ya sameshi,tun bai qarasa ba ya hangeshe sheqi da kwanukan abinci na alfarma da suka janye hankalinsa. A yanayinsa kamar anci abinci ba jimawa a wajen.

"Inason ganin kwanukan da kyau.....da abincin dake cikin kowanne......ka hanzarta,don kowanne lokaci hankalinta yana iya karkatowa gida" Haisam ya fada yana duban agogon dake harbawa saman device din.

"Ko da zatazo ta ritsani,ba shakka sai na yiwa obbo wannan sadaukarwar,koda wannan shine abu na qarshe da zan aiwatar cikin rayuwa ta" Abdii ya furta da wani irin confidence da ya sanya haisam sakin sassanyan murmushin da baiyi niyya ba.

"Obbo....."

"Stay silent abdii.....just be quick......you know idan ta sameka a nan you finished"

"Obbo......English dina baiyi qarfi ba ka sani...."

"Abdii" Ya kirashi da zuzzurfan muryarsan nan me kauri cikin sigar jan hankali. Ya sani sarai halin abdii,komai sai ya sanyo wasa a ciki,idan kuma baiyi da gaske ba lallai lokaci zai iya qwace musu.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 29*

Daya bayan daya abdii ke musu hotuna,bakinsa cike fal da zance d kuma mamaki. Komai na abincin kamar suna cikin yankin jimma.....komai kamar suna sassan qabilar oromo.........hatta da shayin.

Kai tsaye haisam yaci gaba da guiding nasa,yana yi yana kasa hankalinsa biyu omari yana riqa masa,har zuwa lokacin daya isa ga bedroom dinta da bincike ya nuna masa tafi zama a cikinsa,saboda gwaji da awon yawan saukar numfashi a dakin da yayi daga bayan gine gine gidan.

"Finally obbo......from where i should start?". Ya tambaya cike da jiran umarni.

*MAMMINA*

"Idan ka qarasa villah street ka tsaya a nan" Mammina ta bawa driver din nata umarni nakai tsaye bayan fitowarsu daga duba Maher da aka bata tabbacin sallamarsa a yau din. Sosai Maher ya cika da mamakin ganin zuwanta ita daya qwallin qwal,ba wani tarin motocin dake take mata baya a duk sanda zatayi fita irin wannan.....ba wani hadimi ko me tsaronta kamar yadda ta saba fita irin wannan?,wannan yabar masa ayar tambayar da tana fita ya aikewa haisam da hasashensa da kuma abinda ya gudana tsakaninsu.

Villa street din wani guri ne daya zam emata wata mahada......wata mahada me tarin sirri,zuzzurfan sirrin da ba wani hankali ko tunani a nan kusa da ya taba tsinkayoshi. Rufaffe kuma adanannen sirrin da duk tsananin kusancinka da ita bata lamuncewa kowa saninsa ba.

Wayarta ta fiddo,ta kuma soma shigar da wasu lambobi da ko da wasa bata taba ajiyarsu cikin wayar ba,iyakacin zamansu cikin kanta,da zarar kuma ta sakasu a wayar ta gama duka amfanin da zatayi dasu take sharesu.

Tana shirin danna dan maballin kira kira ya shigo wayarta,ta tsaya cak ta zubawa kiran ido tana kallonsa. Siririn tsaki taja,akhnan ce.....a irin lokaci irin wannan bata qauna ko fatan abinda zai katse mata dukka shirinta,to amma a yanzun tana buqatar yarinyar a kusa......tana buqatar nuna mata tausaya sama da yadda ta saba a baya,don haka ta yanke nata uzurin ta daga kiran.

Iya daga kiran mammina din kawai ya sanyata sakin wata nannauyar ajiyar zuciya. Ta kowanne bango ji take rayuwar ta matseta,komai kuma baya tafi mata daidai. Wani muzanci takeji har cikin jininta.......wani fusataccen yanayi takeji da dukkan abinda sultane yayi mata a gaban malamin.

"Mammina.......ina buqatarki......ina buqatarki a kusa dani" Sirrintaccen murmushi ne ya subuce mata saman labbanta. Yadda dukka rayuwarta numfashinta da kowanne kalar motsi nata ta dogara da ita yana burge mammina din.......yana mata dadi idan ta tuna yadda ta sanya dukkanin motsinta ta ta'allaqa da ita.

"Na sani akhnan.....karki wani damu......fitar gaggawa ce ta sameni,naje duba mara lafiyan daya raunata ta sanadinmu......ina kan hanyar dawowa nan da awa daya".

"Okay" Ta amsawa mammina din da wani irin yanayi. Wani boyayyen rauni ne da ita daya ita zaituna take iya ganeshi..... Murmushi ta sake saki,a hankali dai wannan taurin kan......wannan kafiyar.....wannan zafin kan yana juyewa zuwa wani irin rauni da laushi.

"Muje zuwa.....sakamako ne wannan zuwa gareku gaba daya ahalin diory hamani". Ta furta a sarari qasa qasa.

Lambobin ta sake zubawa ta kuma kira,dab da zata katse wata kakkausar murya mara dadin amo ta amsa da

"Alo"

"Ina bakin iyaka" Ta fada a taqaice,ba tare kuma da an amsa mata ba aka kashe kiran,sai itama bata damu ba,don tasan hakan wani tsari ne dadadde da suka jima akai. A nan duk wata mota data daukota take sauketa,ta kuma juya ta koma ta tsaya a duk nisan inda aka umarceta......sannan wata motar daban ta dauketa ta qarasa da ita zuwa SANSANIN SIRRINTA!.

Tana maida wayarta jakarta wani irin mummunar faduwar gaba da batasan daga inda ta yanko ba lullubeta. Har cikin kunnuwanta takejin sautin bugawar da zuciyarta tayi,saita maida idanunta ta runtse.

Tsahon sakanni talatin ta dauka tana qoqarin saita kanta da wani irin tashin hankali. Wani yanayi da ba kasafai yake alamta mata komai yana nan a daidai ba......wani yanayi da a cikin kaso dari kaso sittin idan ta jishi akwai wata matsala ko damuwa da batasan da ita ba a bayan fage.

"Juya mu koma" Ta bawa driver dinta umarni kai tsaye. Haka kawai takejin hankalinta yayi gida,haka kawai takejin kamar akwai abinda ta manta,kamar abinda ya kamata ta dauka bata dauka ba,kamar akwai abinda ta bari ba'a muhallin da ya kamata ta barshi ba.

Cikin cika umarninta ya karya kan motar yana fadawa hannun dake daura dasu yana qarawa motan sauri kamar yadda ta buqata.

Wayarta ta sake cirowa,tana tuna cewa taga tarin missed calls din yalwa. Da gaggawa ta maida kiran tana tsammanin dagawa daga bugu daya kaman yadda ta saba,saidai har ta gama ruri ba'a dauka ba. Abun ya bata mamaki qwarai,don ba wanda yake da zarrar da zata kirashi a kiran farko ba tare daya daga mata waya ba,don ba kasafai suke kiran hadimi ko bawa ba,saidai susa daya daga cikin hadimansu su kira musu duk wanda suke da muradin magana dashi,wannan shine cikakkiyar izzarsu....qasaitarsu da kuma sarautarsu.

A kira na biyar data yiwa yalwa sai taji kamar ta rufe idanunta ta bude ta ganta a gida

"To waye zata kira?" Ta tambayi kanta da kanta,kafin tunanin tafisu ya fado mata. Saida na'ura ta gaya mata ba zata iya sadata da tafisu ba sannann ta tuna,yau tunda asussuba tafisun ta wuce zuwa fataucin data saba yi duk bayan wani zango don kadar da hankalin me hankali a kanta.

"Ina buqatar nan da mintuna goma mu isa gida" Kawai ta fada cikin umarni nakai tsaye

"An gama ranki ya dade" Driver din ya amsa mata yana qarawa motar gudu kaman yadda ta umarta.

"DONE!" Shine abinda abdii ya fada da muryar nan tasa da akan komai ma saita alamta wasa a cikinta.

"Tamam" Haisam din ya furta wanda kalman ya aike da saqon zuwa kunnuwan omari beeno da salawi. Damqe komai yayi cikin tafin hannunsa,sannan a nutse ya kira sunan salawi.

"Daga hannun hagunka,ka matsa kadan a sanda aka fara bada damar fita.....da yawansu ba zasu fita ba......saidai na tabbatar akwai masu fita a cikinsu bayan fitata......ka gayawa beeno wannan aikinsa ne qidddigesu.. Akwai wayoyin dukkan wanda ke amfani da waya a ciki da aka zube......inason ka bincike min wayar da aka fi samun adadin kira......kiran daya kasance number daya ce......ina buqatar safarar dukka bayanan cikin wayar zuwa ga email dina......banason aikinka ya haura minti uku kacal"

"An gama" Ya amsa masa kamar yadda suka horu da karbar umarni kai tsaye ba tare da musu ba.

Kunnuwansa suna iya jiye masa yadda gurin ya hautsine da yabo kan horaswa da aka basu cikin awa daya kacal da basu san da ita ba......tarin ilimin daya fadakar dasu abubuwa masu tarin yawa,da tarin godiyar da bai iya bambance muryoyin dake maganan saboda sanarwar da me wada ya bayar kan tsibin envelope din da aka zube masu dauke da kudaden da yace wata qungiya ce tace a raba musu kyauta.

Kudade ne masu kauri ya sanya aka shirya masa su cikin qasa da awa daya kafin xama taron,ya fiddasu ne cikin asusunsa na rabon tallafi ga marayu da iyayen marayu da ake gudanarwa qarqashin kulawa haadeem cousin dinsa. Bai tsaya iya Ethiopia kadai ba,tallafi ne daya shafi kowacce qasa cikin qasashen africa......wannan karon ya sanya aka karkato dashi nijer din.

Yanaso ya fara iske abdii,amma kuma lokacin sallah ya riskeshi,sallar kuma tana cikin abu na farko da dukka kalar tsananin daya shiga baya wasa da lokacin ta,baya kuma bari ta kufce masa,don haka ya wuce masallaci kai tsaye kawai.

*MAMMINA*

Banda tarin izzar da takeji da babu abinda zai hanata sauka daga motar kafin isowar hadimanta,saidai duk da yadda hankalin ta ke son samun qarin bayanin sauyin data gani tun daga babbar katangar da zata sadaka da ainihin cikin ginin masarautar mamaki yake mamayarta.

"Me yake faruwa?.....ina kika ajiye wayarki?" Ta jefawa yalwa tambayar cikin dakewa ba tare data bari yalwar ta fahimci dan rudanin dake kai kawo saman fuskarta ba

"Taro muka shiga....."

"Wanne iri kenan?"

"Na wayar dakai.......sheikh haisam ya shirya shi.....zan miki bayanin komai.....muje daga ciki" Ta fada tana riqe mata handbag dinta da kyau,tabi kuma sahun hadimanta dake take mata baya a hankali har zuwa cikin sassan nata.

Dukkaninsu suna da iyakarsu,suna da iyakar da yalwa kadai ke iya qetareta,don haka suka ja tunda daga wannan iyakar,suka barta ita da yalwa suna wucewa ga parlor na gaba.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

"Banason maimaita tambaya ta....." Mammina ta fada daidai sanda take tsaiwa tsakiyar parlor din ba tare data dubi yalwa ba.

"Taro ne aka shirya na awa daya kawai" Saita soma siffanta mata yadda komai ya gudana har zuwa tashinsu.

"Ina kyautata zaton yana neman suna ne wajen sultane......yana neman matsayi ne kawai a wajensa.......yanaso ya sallama masa ne dari bisa dari!"

"Tir da kalar tunani irin naki wasu lokutan da basu da wani amfani!!!" Mammina ta dakawa yalwa tsawa tana tsaidata cikin tsananin rudani.

"Allah ya huci zuciyarki" Yalwa ta fada tana yin qasa da kanta cikin fargaba da taraddadin shiga gona ko hurumin daba nata ba,wanda tasan hakan baida alaqa da komai sai sanya kanta a uku da bala'in da batasan wanne nau'i bane.

Wani irin rudadden yanayi ke yawo cikin kwanyarta,a wannan lokacin tafisu kadai take buqata,wadda ta tabbatar ita da ita ne kawai tunaninsu zai iya zuwa daya. Yadda yalwa ta gaya mata yadda komai ya faru ta aje qatuwar ayar tambaya akan komai.....saidai batasan akan ainihin meye take tuhumar ba.....meye kuma bata yarda dashi ba?......kawai tana jin akwai wani abu shiryayye.......akwai wani abu daba daidai ba har cikin ruhi da zuciyarta. Ba kasafai tafiya gasgata abubuwa ba koda abubuwan da suka kasance na gasken ne ba jabu ba......takan dauki lokaci tana sanya idanu da jarraba komai kafin ta miqa wuya da hannu ta karbeshi a yadda kowa yake kallonsa.

"Akwai wanda bai halasci taron ba cikin masu hidima a gidannan?"

"Kowa da kowa ne" Ta amsa mata a qasqance. Ta jijjiga da qarfi,tanason qulla zaren tunanin akan wacce manufa aka shirya hakan,saidai kuma ba abinda kwanyarta ke mata kai kawo akai sai irin hasashen yalwa dai sak.

"Yana neman yabo......yana neman gurbin zama......yanason ya siya soyayyar al'ummar gidan,ta kowacce fuska takara yakeyi da matsayinki". Duk da jerin gwanon wadannan tunanikan amma sai taji yaqi dacewa da abinda ke mata zirga zirga......ta gaza aminta da kalar wannan harsashen sam.

"Dashi aka gudanar da taron?" Ta sake tambayar yalwa.

"Shi yayi dukkan jawabai".

" Kota daqiqa daya baibar gurin ba?".

"Ban gani ba Allah ya taimakeki,dashi aka fara dashi aka kammala". Shuru ya sake ratsa gurin,kafin wata ajiyar zuciya ta subuce mata.

Tana jin bai kamata ta daga hankalinta akan malamin da tasan bai mallaki komai da zai iya challenge nata ba......bashi da wata power......baida wani iko na komai,face tarin litattafan da ta sanadin,ta albarkacinsu yake samu yake sha. A yanzun akwai abubuwa da yawa daya kamata ta girmama ta fadada sanya hankalinta akai. Saidai shi dinma.....akwai dalilai da yawa da suke sanyata take gaza dauke hankalinta a kanshi. Tana iya cewa shine mutum na farko banda IBRAHEEM da taji yana mata kwarjini irin haka,mutum na farko da dukka yanayinsa yake mata kama da wani BASARAKE da IZZA ke kewayewa cikin jininsa.

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261 KO 08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 30*

A kansa ta fara ganin mutumin da tana zaune saman kujera shima yana zaune. A kansa ta fara ganin mutumin dake iya duban qwayar idanunta yayi magana da ita a tsanake. A kansa ta fara ganin mutumin da sam batayi masa wani kwarjini ba ko daya......tarin jaran gwanon wadannan abubuwa suke sanya mata wani yanayi na daban a kansa.

Bawai a kansa malamai suka saba baquntar gidan ba,amma kowa yana rayuwa ne a qarqashin ikonta,gwargwadon yadda takeso ya rayu bisa tasarrufinta.

"Ki nema tamim duk inda yake kice ina buqatar ganinsa a yanzu".

"In sha Allahu.....ki huta lafiya,da fatan za'a gafarceni" Yalwa ta fada ta yunqura ta miqe tana ficewa.

Da idanu tabi yalwa din har sanda ta bacewa ganinta. Ta sauke hannayenta data rungume qirjinta dashi tana jan siririn tsaki. Ta tsani yadda takejin wani fargaba da razani suna ratsata......ba halinta bane batason kuma dabi'ar ta soma keta jininta. Tana da tarin abubuwa da takeso ta aiwatar,wadanda suke buqatar JARUMTA da RASHIN TSORO,abubuwa masu yawan da raguwar zuciya ba zata aikatasu ba.

Tsam ta miqe ta isa ga freezer din dake ajiye tana aikinta,ta bude da kanta ta zaro ruwa me sanyi sosai. Tana neman abinda zai sanya kanta ya huce......tana neman abinda zai sanyaya mata tunaninta ko kwanyarta zata dawo aiki da kyau.

Tana dora gorar saman freezer din sanarwar isowar tamim ya marabceta.

"Zan fito yanzu......bulama ya jirayi tafiyarsa tukunna" Ta fada tana komawa mazauninta na dazu.

Alkyabbar data shigo da ita ta sake maidawa,ta kuma maida yanayinta cikin izzarnan da bata yarda ta gushe daga gareta,ta fara saukowa cikin takun isa da nutsuwar da bata jin takai mata har cikin zuciya.

Har qasa yakai gwiwoyinsa kamar yadda ya saba,bai kuma gyara ba har sai data samu guri ta zauna.

"Ya ake cikin cikin qasar can?" Ta tambayeshi a izzance. Zamansa ya gyara sosai kanshi a qasa.

"Na sanya dukkanin wasu matakai da zasu zurfafa bincike,kuma sun dauki adadin wasu kwanaki akan zasu bani cikakken bayanin dana buqata.....kwanakin ba zasu haura goma sha hudu ba......"

"Suyi qoqari kada su dara sama da haka.....ko nawa suke buqata za'a biyasu......bayanai kadai nake buqata,sautin motsin kowanne me rai.....kowanne dan adam da ya shiga cikin da'irar buqatunmu......ban dauke kowa ba,yaro ko babba,mace ko namiji.....shugaba da mabiyi!"

"Yadda kikeso hakan za'ayi Allah ya qara miki nisan kwana" Tamim ya furta da yaren oromo da yakanyi amfani dashi kadai idan suka kebe irin haka......a muhallin daya tabbatar ba wani mahaluqi da zai iya jinsu.

"Wanne sakaci ke shirin faruwa cikin gidannan qarqashin jagorancinka!" Mammina tayi magana a gaba ta biyu cike da kausasawa me yawan gaske.

Qasa yayi sosai da kansa cikin neman afuwa daya sabawa kanshi kafin yakai ga jin wanne kalar laifi gareshi?.

"Akwai dama wani me zartarwa da tsara wani abu cikin gidannan ba tare dana sani ba?.....ba kuma tare dana sahale ba?,har kuma ku mara masa baya?" Tayi tambayar tana jin wani sabon bacin ran yana motsa mata sama dan dazu.

"Tuba muke giwa.....tuba muke uwarmu maganin kuka mu......taron yazo ne a bazata......lokacin da kika fita a gidan,ba damar neman izini ko sanarmiki......sannan duban matsayinsa a gurin sultane daya sahale masa aiwatar da komai,sultane ya shaida mana umarninsa daidai yake da nashi,haka girmamashi daidai yake daka girmamashi.....shi din d'a ne a gurinsa halak malak......"

"Ya isheni haka tamim!" Ta fada tana daga masa hannu.

"Kuskure na farko da zaku fara yi kenan,ku yadda ku daidaita matsayina da nashi......saidai nan gaba kadan zan cire masa wannan girman daka zuciyar dukkan wanda yake ganinsa da girman!" Ta fadi cikin cin alwashi. Wannan alwashin nata ne,ba wani daya isa yayi mata shiga hanci da qudundune ta qyaleshi!.....ko wayeshi!.

"Kada ka yarda irin haka ta sake maimaituwa......duk qanqantar zartarwa ina buqatar ta fara wucewa ta gaba na"

"An gama"

Readers Also Read

More by Huguma