Kenza eBookz

L u'u l u'u book 2 complete by huguma - Chapter 21

L u'u l u'u book 2 complete by huguma - Chapter 21

L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 21: L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 21. "Subhanallah". Budesu yayi a hankali hoton yana dawowa…

3,346 words

"Subhanallah". Budesu yayi a hankali hoton yana dawowa cikin idanunsa. Baby face dinnan nata dake cike da wani irin yanayi dake nuna zallar gajiyarta rauninta da kasawarta,saidai alamu na tsananin taurin kai kafiya da kuma qi fadi irin nata yasa takejin ita din tsayya ce da ba rauni ko gajiya a tattare da ita,wanda kai tsaye a kuma kallon farko yake iya hangen dukka wadannan abubuwan a tattare da ita. Abu guda daya da yayi masa tsaye a qirji......yadda take kewaye tsakiyar wata da'ira me fadin gaske.......yadda ake wasa da rayuwarta ake juya wannan kafaffen ra'ayin nata daga hagu zuwa dama ba tare da ita tasan hakan ba.......ba tare data fuskanci hakan ba. A nasa idanun wani abune me sassauqan fahimta da ganewa......to amma ya sani a karan kansa,shi dabanne.....shi kuma na dabanne da yake iya hangen komai daga nesa tarwai kamar yayewar hijabi.

Bayaso ya shiga wasan daba nashi ba......amma tabbas wasan zai bada ma'ana inda ace shine abinda ya shigo dashi agadez.......an taki bahaguwar sa'ar da baya kallon kowanne aiki sai nasa aikin.....wannan ya sanya wasan zai zame masa abun kallo yana daga zaune a inda yake. Yana raina izzarta......yana raina tsaiwarta da kafiyarta.....yana kuma raina mulki da sarautar da takeji tana yawo a jikinta. Ya sake raina jaririyar kwanyarta......data bari ake gara rayuwarta tamkar ball a hannun qananun yara tsakiyar fillin qwallo. Baizi agadez don kowa ba sai don MAI LAIFIN DA SUKE FARAUTA......BAIZO AGADEZ BA SAI DON QASARSA ETHIOPIA......BAIZO AGADEZ BA SAI DON MOTII DA NANAY DA AL'UMMARSA......baiga dalilin da zai sauka daga wadannan matakai da tsanin nasa ba.

Saidai duk da haka,duk da tarin wannan raunin......duk da tarin wannan siffofin,yana hangen wani YAQINI da JAJIRCEWA ta cikin dukka motsi da yanayinta. Da gaske ne ita din bata karbar FADUWA da gaske ne TSAYAYYA CE akan dukka quduri da burinta,saidai yanaji a jikinsa da sannu komai zai canza.....da sannu qilan za'a cimmata a rushe komai.....wataqila a sannan ya jima a jimma Ethiopia,har ma ya mance da wata qasa daya taba wanzuwa wato niger.

Kai tsaye suka dinga buda masa hanyoyi har zuwa inda zai riskar mammina. A kowanne taku akwai hadimi guda daya da zai masa jagora zuwa inda take mataki mataki. Tsarin sashenta daban yake,banbamcin da ya bayyana qarara da kowanne sashe na gidan. A zahiri karon farko kenan da ya taba bayyana cikin sassan,saidai a badini kuwa sashen ba baqonsa bane,saidai ya wawantar da kansa yadda ya kamata don yayi kama da mutumin da karon farko daya taba tsintar kansa a gurin.

A kowanne motsi da kuma kowanne taku yana hankalce da yadda ba wata doka data soma aiki a sassan mammina din. Kowanne shiyya na gidan ya samu cikakken rahoton fara wanzuwar dokar da fara aiki da ita,ciki kuwa harda shiyyar sultane duk da bayanan,da sashen morsa safiyya.

Yayi marking hakan da alama ta biyu da zaiyi nazari a kanta,yana sake maida hankalinsa da inda hadimar ke masa iso tana janyewa baya,da alamu iya tata iyakar kenan.

Tun daga nesa kafin ya qaraso ta tattara dukka nutsuwarta,ta kuma bude dukkan basirarta dake mata jagora zuwa fahimtar zurfin tunanin dan adam a sanda taso karantarsa.

"Wa'alaikumussalam......bismillah" Abinda tace da haisam kenan a sanda ya qaraso farfajiyar da take zaune.

A nutse ya taka yana isa gaban wata kujera qwaya daya data fita daban da sauran,yayi bismillah a hankali yana zama,saita daga kanta tana duban yalwa.

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261 KO 08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 37*

"A marabceshi kamar kowa.....a kuma wadatashi da dukkan abun ci da abun sha" Ta furta da cikakkiyar izzar dake nuna girma da nisan inda ta dauki kanta da kuma kalar matsayin data bashi.

Idanunta ta daga a hankali,tana iya karantar zallar nutsuwar dake kwance saman fuskarsa,ba wani tsoro ko fargabar kasancewarsa a gabanta,duk da yadda takewa tarin mutane kwarjinin da ko cikakken zama a gabanta ba kowa ke iya yinsa. Wani adanannen kwarjini da tasa aka mata tattalinsa daga kowanne jini dake harbawa a jikinta.

"Sheikh haisam.....tuntuni na aika a kiramin kai......ba'a sanar maka bane?" Tayi tambayar da manufa tayin titsiye da kuma son ganin adadin girma da kwarjinin data yiwa idanunsa da zuciyarsa.

Kai ya gyada a nutse bayan ta ajiye tambayarta harma ta huta ta hanyar shaqar sabon numfashi,yana jin kamar nashi jinin OROMIA din yana shirin motsa masa,jinin ABA JIFAR amma yasa wani abu me nauyi ya danneshi yana daidaita yanayinsa da lokacin.

"Eh an sanar dani" Ya amsa mata a taqaice. Yadda ya amsa mata kai tsaye ba wani kwana kwana ko neman boye laifinsa ya tabata sosai,abinda bata taba gani ba,bata kuma saba gani ba,sai ta jinjina kai.

"An sanar dakai.....amma ka bata wasu mintuna da suka kusa tasamma jimillar awa guda cif,na kiraka ka wofantar da kiran?" Ta fadi da zafi zafi wannan karon a muryarta.

Kamar dazun,sai daya shaqi nutsatstsiyar iska sannan ya sake motsa labbansa.

"Akwai banbamci tsakanin wofantarwa da zuwa a makare......ba kowanne kira bane amsashi akan lokacin da aka yishi yake nuna girmamawa ba......manufar daya ce wanda aka kira ya amsa......gani na amsa a lokacin da yafi dacewa......idan kuma ba damuwa,kamar shiga cikin maganar kai tsaye zaifi,saboda mu ceci lokaci ni dake gaba daya" Yayi maganar kansa tsaye yana zube idanunsa cikin nata.

Kafeshi takeso tayi da idanunta,amma ta rasa wannan qwarin gwiwar,saita janye dubanta a kansa,zuciyar taqi yarda da kwarjini yayi mata,saidai tafi alaqanta hakan da fushin da takeji a kansa. Bata jin zata sakar masa wanna gabar da sauri haka ba tare data saukar masa da warning ba saboda gaba

"Cikin masarautar nan.....cikarta da batsewarta.......yana zama wajibi akan dukkan wanda na kirashi ya amsa kirana a sanda na buqata". Kansa ya juya a hankali,ya fahimci maganan rashin xuwa kiranta a sanda taso ta mata zafi sosai,hakan shi kuma yayi masa.

"A tawa al'adar da yaren.....girmamawa sifface ta dattako.....ga duk wanda ya amsa kiranka ya girmama koda baizo a sanda ka buqata ba" Ya amsa mata yana sassauta harshensa. Bayaso nan da nan tayi fusatar da zata rudar da hankalin omari daga fuskantar abinda haisam din yakeso ya fuskanta. Maganar tasa ya daketa ta kuma taso da wani tsohon al'ada da wata tsohuwar karin magana daga asalin nata yaran,ta kuma motsa idanunta kamar zata waiwaya gareshi ta kalleshi don tabbatar da abinda ya fada,amma koda ta tuna da nata mission din saita kauda hakan. Saidai hakan da tayi bai hanashi daukan haske ba.

"Ka zartar da wasu sabbi kuma baqin dokoki ba tare da neman ta bakina ko ganawa dani ba.....shin waye ya baka wannan izinin?". Murmushi ne dan siriri ya qwace masa,saidai ya tsaya iya labbansa,duk da hakan kuma bai hana tsarguwar mammina ba da rayawa a ranta kamar murmushin taga yayi ba,saidai bai bata dukkan dama ta gane hakan ba.

Ya kamata tambayar ta bashi mamaki,amma kuma yadda ya tsammaci tuhume tuhumenta zasu iso haka suka sameshi.

"Ba kowa".

"Ba kowa?" Ta tambaya a mamakance,tana jin ta samu gaba da zata soke kowacce doka hankali kwance.

"Eh.....ba kowa,saidai bayan na gama rubuta dukkan dokokin,na gabatarwa da sultane,inda hankalinki a nutse yake da zaki iya ganin stamp da sanya hannun sultane qasan kowacce doka" Ya fada da wani irin calmness yana sake tattara nazarinsa a kanta.

Wani shocked taji sosai har cikin jininta,jin da sanya hannun sultane aka wanzar da komai,ba tare da kuma sultane ya kirata yaji ta bakinta ba yadda suka saba sanya kowacce sabuwar doka a tare.

"Na tabbatar daukuwa da hankalin sultane yayi ne kan wannan tafiyar ya hanashi nemana......amma hakan bawai yana nufin kana da qarfin ikon zartar da doka kai kadai ba". Kansa ya sake juyawa a hankali,cikin Tarin nutsuwa idanunsa tsakiyar nata yace.

"Sanya hannun sultane ya wadatar........dokar bata an qirqireta bane saboda ke,an qirqireta ne saboda masarauta.....shi yasa ya zamana ba wani laifi don an kafata ko an zartar da ita bada saninki ba.....dukkanin dokar an yita ne saboda tsaron masarauta"

"Tsaro ga masarauta ko kuma neman ikon sarrafa komai da kowa?" Murmushi ya sakeyi kadan,na wannan karon yafi na dazu bayyana.

"Ikon sarrafa komai wannan siffar Allah ce mahalicci shi kadai.....ni dake da sultane duk bamu da hurumi a kanta". Maganar tasa sai taji kaman yana qoqarin tube mata rawanin ikonta ne,don haka cikin qanqance idanu tace masa.

" Kasan wacece ni kuwa?".

"Kowa nasan wayeshi.....kowa kuma nasan wa yake qoqarin zamantowa ko kasancewa kamar shi". Wani irin abu taji ya sauka yana sarar gabban jikinta. Wani irin gumi taji yana qoqarin tsatstsafo mata,saidai tasan barin hakan ya faru,barinsa ya karanci hakan babban kuskure ne a tare da ita,don zuwa yanzu cikin jikinta takejin BA HAKA KAWAI YA SHIGO AGADEZ BA....BA HAKA KAWAI YA SHIGO MASARAUTA BA.....BA GAMA GARIN MALAMI BANE.

"Amma kasan cewa masarautarmu a zaune take lafiya kafin shigowarka cikinta?" Ta sake fadi yanayinta yana nuna fara daukan zafi.

"Zaman lafiya ba shine shuru ba......wani lokaci shuru yana boye abubuwa masu nauyin gaske....cikin rashin sa'a saika dauka lafiya ce ta kurmantar da komai din" Ya amsa mata da wani irin nutsuwa a tattare dashi. A karo na biyu ta sake jin kamar dutse ya dauka ya jefeta dashi cikin tsakiyar kanta.

"Waye shi?" Ta samu kanta da tambayar kanta da kanta,zuciyarta da tunaninta suna neman zamewa. Zuciyarta ke mata wani irin tsalle,tana kuma cikata da shakku a kansa,sannan tana son jefa mata rudanin da bata shirya ko tunanin fuskantarsa ba a daidai lokacin.

"Akwai wani da kake zargi?....ko akwai wani abun zargi cikin masarautar damu muka gaza hangoshi sai kai?". Tayi tambayar cikin zafi,tambayar data sanya ita da kanta wuta dauke mata,don bata tsara ta fidda masa zafinta har haka akan komai ba.

Shuru ya ratsa dakin,haisam kallonta da wani irin duba da takejin kamar yana toxartata ne ko kuma qoqarin karantar dukkan wani plan nata.

"Zai iya yiwuwa......amna zartarwa a yanzu ba na daya daga cikinmu bane....saidai ki taimaka wajen tabbatuwar amincin amanonin rayukan dake tsakanin hannunki da na sultane.....saini yanzu da aka sakani a ciki zuwa lokacin da zan miqa muku amanarku" Yakai qarshe yana miqewa a nutse,yana kuma jin yakai gejin maganganunsa,yana sake ji a ranshi tako ta ina matar ta tabbatar ABAR ZARGI TA FARKO!.

Yadda take takawa a nutse yake tabbatar mata fita zaiyi,hakan kuma yana nuna zai tafi ne koda bada izininta ba,koda batace ba,koda kuma bata gama fadin abinda ke ranta ba,wanda tana da tambayoyin da amsarsa ce kadai zata gamsar dashi.

"Kabi a hankali sheikh haisam......masarauta tana iya hadiye baqi ba tare da ganin koda burbushin da za'a bi diddiginsu ba......karka manta gidan nan nawa ne,kada kayi abinda zai sanya da kanka ka fahimci KAI DIN BA KOWAN KOWA BANE" Wani faffadan murmushi sama dana dazu ya kubce masa,ya sakeshi a nutse ba kuma tare daya waiwayo ba.

Ya yadda kalaman baki sune abu na farko dake fara fada maka WAYE WANE?. Ya aminta su din wasu maqullaine da a yanzu suka bude masa wata qatuwar qofa da zai sake zurfi a bincikensa

"Gida mallakin sultane ne.....ina tsaiwa daidai iyakokin da zasu amintar dashi ne shi kadai.......isata kuwa....." Ya fada yana waiwayowa a nutse.

"Lokaci yana tafe da zai baki amsarta......na isa? Ko akasin haka?" Ya fada yana tsaiwa daga nan gami da bata space,saidai bata iya cewa komai ba,wannan ya bashi daman juyawa yana ficewa,saidai duk da hakan bai hanashi jin furucinta na qarshe ba.

"Zan tabbatar da cewa na nunawa duniya kai din ba kowan kowa bane.....zan nunawa duniya baka isa a komai ba face zallar malami me cin takarda allo da tawwada".

A nutse ya zare Device din daga Kunennensa don ya fara jiyo karadin omari.

"Ina mamakin yadda yariman jimma yake iya dauke wadannan kalaman.....don Allah ko sau daya kayi abinda zatasan your not an ordinary man" .

Goshinsa kawai yake murzawa a hankali yana qoqarin calming kansa. Idan ya biyewa zancansu omari shirme zasuyi kawai a agadez,su kuma bata lokaci a banza cikin agadez din,su komawa Ethiopia a empty zero hands.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

____**Hannu ta miqa tana sake jawo takardar tana fidda wani huci daga bakinta zuciyarta tana jin kamar zata fasa qirjinta ta fito. A karon farko a rayuwarta ta d'an d'ani yadda dacin jayayya da qasqantar da isa take ga wanda yakejin ya isa yakai ta kowanne fanni. Idanunta ta maida saman dokokin tana sake bitarsu tun daga farko,tana so kuma ta dire kan sanya hannun sultane din da yayi iqirari akai.

_daga wannan daren,bayi da hadimai ba'a lamunce musu zirga zirga tsakanin sassa ba daga bayan sallar isha,har sai da rubutaccen izini_

_Dukkan masu ziyara zuwa cikin kowanne sashe zasu rubuta sunayensu asalinsu yare da qasarsu,da dalili na ziyarar kaman yadda tantancewa zata hau kan kowanne hadimi da bawa dake rayuwa cikin MASARAUTA daga gobe_

_an haramta kowanne ganawa da bayi a kebantattun dakuna ko gurare_

Kasa qarasa karantawa tayi,saboda tsananin bugu da qirjinta yakeyi. Tanajin kowacce doka qwaya daya tana kiran sunan ZAITUNA ne kai tsaye,saita zarce da idanunta kan sa hannun sultane. Sa hannu ne da tafi kowa sanin girma da qarfinsa. Sa hannu ne daya kasance na daban wanda muddin sultane yayi irinsa saman takarda to kowacce magana ce komai qarfinta ta zama TABBACIYAR da babu sauyi a cikinta!!!.

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261 KO 08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 38*

"Yalwa!" Ta kira sunanta kai tsaye a yau din da kanta.

"Ki nemomin tamim yanzu.....ki gaya masa kada yazomin da tsohon labari,sabuwar magana nake son ji" . Umarnin daya qara yawan rawar jikin yalwa da son cikashi,wataqila wannan ya shafe hukuncin da take zaman jiran fuskanta kan aikenta na dazun.

★ "akwai boyayyu kuma nannadun al'amura masu girma da yawa cikin masarautar nan......haisam,akwai wani abu daban dake cikinta bayan abinda muke nema.....akwai wani abu na daban dake faruwa bayan bincikenmu......girman abinda ke cikin masarautar nan yafi qarfin princess akhnan kawai....yafi qarfin rikicin cikin aurenta kadai......inaji a jikina haisam.....matar nan tana hadarin gaske,me yasa ba zaka taimaki sultane ba?." Omari dake zaune suna fuskantar juna shida haisam ya furta damuwa zaune fal saman fuskarsa. Wani irin kallo haisam yayi masa yana qoqarin daidaita kansa tsakanin idanun omari din.

"Kasan me kake fada kuwa omari?" Ya masa tambayar calmly,saidai idanunsa na nuna girman abinda yake fadi din.

"I know haisam.....na sani" Ya fadi kai tsaye yana duban idanun haisam,yanason ya fahimci da gaske yana jin interest na fadada bincikensu da bin diddigin cikin gidan.

Kallon kallo ne ya wanzu a tsakaninsu na wasu sakanni kafin haisam ya zare idanunsa. Da gaske ya karanci tunanin omari,kuma da gaske yake fadin abinda yake fada din,ba wasa sam a ciki.

"I wasn't cross boarders to save the palace" Ya furta da wani irin accent dake nuna tasirin yaren oromo cikin harshensa,yayi maganar ne kuma yana dauke dubansa daga kan omari,yana maida dubansa ga cup din gabansa da omari ya zuba masa coffee.

Idanu sosai omari ya zubawa haisam din,a karon farko yana mamakin sauyawar dabi'ar haisam din. Baida kutsa kai kan sha'anin mutane.....amma yana damuwa kan mutumin da duk yaga zai cutu muddin yana da ikon taimaka masa. Me yasa a yau a yanzu yake kauda kai daga taimakawa akhnan da mahaifinta?.

"Amma......me yaci gaba da shigo da issue dinta cikin maganamu inde haka ne?" Omari ya jefa masa tambayar. Sau daya tak ya daga ido ya kalli omar,sannan ya dauki mug din coffee dinsa ya shanye,kana ya miqe a nutse yana zube hannayensa cikin aljihun trouser din jikinsa,ya taka a hankali zuwa bakin qarfen balcony din.

"Saboda tana kanannade da wadda nake zargi....dole a wasu lokutan maganan case dinta ya dinga ratsowa cikin aikinmu" Ya amsawa omari a nutse can qasan zuciyarsa kuma yanason canko dalilin da yasa omar ya masa wannan tambayar. Ya sani dukkansu ba wanda ke magana ko tambayar da bata da fa'ida ma'ana ko dalili......ko akwai wani dabi'a ko halayya ta daban da yake nunawa kan abinda ya shafi case din?. Bai iya gano komai ba,bayaso kuma ya waiwaya ya kalli omar kada ya dauka akwai wani abu daban da yake rayawa a ransa. Kaman yasan kuwa kallonshi omar din yake,kaman kuwa yasan neman reaction qwaya daya omari yake daga gareshi.

Ya jima yana raya wani abu a ransa game da haisam din. Bai taba masa wani dogon zance daya shafi akhnan ba.....amma ya dade da sanin wata dabi'a kebantacciya daga haisam din,dabi'ar da baya jin ko haisam din yasan yana da ita,dabi'ar da yasan itace SILA SANADI da saamee da MENELIK suka kasa samun matsugunni a zuciyarsa,duk kuwa da cewa suna da kowanne irin quality da ake buqata na zahiri daga gurin d'iya mace.

"Amma kasan sultane ya amince da kai?....."

".....wannan ne ma ya bani dalili na qauracewa iyakokinsa da shiga al'amuran da suka kebanci iyalinsa.......ina da kishi me yawa da nauyi,yadda bazan bari a kusanci iyalina ba daidai da d'ani ko taku guda ba.....hakanan bazan kusanci iyalin kowa da zarafinsu ba sai akan wanda gaskiya take buqatar tayi adalcinta a kansa" Ya qarashe maganar yana waiwayowa idanunsa cikin na omari.

Wani kallon kallon suka sake yiwa juna,sai kawai omari ya jinjina kansa a hankali sannan ya sauke idanunsa yana cewa.

"Nan da kwanaki uku maleek zai kawo maka ziyara,ba kuma iya gidanka kawai ba,har cikin masarauta yake sha'awar shigowa"

"Allah ya kaimu" Ya fadi kawai cikin nutsuwar rai. Dukkanin aminan nan bashi da haufi a kansu,sunsan boyayyen aikinsa da ko cikin ahalinsa ba kowa bane ya sani,tsananin amincin dake tsananinsu ya sanya sukasan kowanne doka da strategy na aikin,don haka bai shakkan haduwa da kowannensu a kowanne lokaci a kuma kowanne irin yanayi,bare maleek da abubuwansu da yawa yazo daya,saidai ta wani fannin sukance maleek ya fishi sauqin sabo da jama'a,duk da shi dinma SARAUTA na yawo a jininsa.

*MAMMINA*

Abinda takeji a ranta a lokacin wani irin yanayi ne da tun zamanin SAFEENA bata qara jin irinsa ba. Wani irin qanqanci takeji har a cikin jininta,wani irin tozarci da ya sanya takeji wani irin zafi saman fuskarta kaman an watsa mata borkono.

Kafin tamim ya iso tafisu ta rigashi isowa,tayi dukkan me yuwuwa ta kwantar da hankalin mammina amma hakan bai samu ba.

"Wai me kike tsoro game da malamin dake rayuwa qarqashin alfarmarku?" Kai ta jijjiga sosai tana gote da hannayenta.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

"Ba malami bane gama gari......ba irin malamin da kika saba gani bane.....wannan idan na runtse idanuna ZAKI nake gani a gabana tafisu.....idan na kulle kunne na TSAWA nakeji tana fita a bakinsa maimakon magana irin ta kowanne dan adam.....shi ba irin kowa bane tafisu......tabbas akwai wani abu na daban a tare dashi". Shuru tafisun tayi,tana son gwargwaje magangun mammina cikin ma'aunin nazari da lissafinta,amma sai sallamar tamim ta yanke mata wannan hanzarin.

"Me ake ciki game da labarin Ethiopia?" Ta tambayeshi kai tsaye. Bai zauna ba,don bata bashi wannan damar ba yayi qasa da kansa ya soma magana cikin girmamawa.

"Sun gaya min,akwa alamu gwada biyu da suka gwada akwa wani shinge daya motsa daga muhallinsa.....alamu ne ba'a samu tabbaci ba"

"Su maida kai akan wannan alamun!.......su bani tabbaci a nan kusa!!" Ta furta atsawace tana jin wani abu yana motsawa daga qasan zuciyarta,tamkar an fusgi zuciyartata an kuma jijjigata.

Readers Also Read

More by Huguma