L u'u l u'u book 2 complete by huguma - Chapter 23
L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 23: L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 23. Cikin jikinta da jininta gaba daya takejin…
3,308 words
Cikin jikinta da jininta gaba daya takejin kunya.....kunya me lullube da wani irin tarin baqinciki na yadda ya zartar mata da hukunci cikin rayuwarta,bayan shi din ba kowan kowa bane a rayuwarta,shi din bai darajar da hannayensa ma zasu taba sadakinta ba.....amma dukka sultane ya tattara wannan damar.....wannan kimar.....wannan martabar ya damqa masa.
Shigowar birra ya sanyata daukan siririn band ta tattare gashinta me tsaho da sulbi ta daureshi,birra ta matso cikin girmamawa da zummar mata shiri na musamman,ga zatonta baqi gareta masu muhimmanci cikin daren,ko wata muhimmiyar fita.
"Kaya kawai zaki bani na canza,cikin gida zan shiga" Ta fada tana qoqarin karbar kayan da tuni birra ta cika umarninta ta ciro mata su.
"Ki tabbatar da lafiyar hanya,sannan a dubamin kowanne sashe na gidannan a gayamin inda wancan malamin yake a yanzu haka". Tayi maganan tana fara zame hannayen rigar baccinta da har tayi shirin kwanciya labarin sadakin daya fara yawo cikin gidan ya hanata kwanciyar. Dan damm kadan birra tayi,tana tuna sabuwar dokar hana zirga zirga daga wannan sassan zuwa wancan sashen da lokacinta yake dan da fara aiki kamar kowanne dare daya zama zartaccen hukunci cikin masarautar. Tana kyautata zaton jwar dakin nata ta manta?,duk da bata da tabbacin tana da masaniyar fara aikin dokar. Dole ta shaida mata,don gudun karya dokar kamar yadda akayi gargadi me zafi akan kowa.
"Allah ya taya miki sirrin farincikin sultane......akwai doka da aka sanya na hana zirga zirga daga goma na dare a masarauta gaba daya". Cak ta daga fararen idanunta dake dauke da blue din qwayar idanu daga tsakiya tana zube dubanta akan birra,kallon dayayiwa birra nauyi,kwarjinta daya cakude da tsananin bacin rai yana tasowa.
"Doka?......waye gwanin sanya doka a sanda sultane baya nan?,sa'annan har yake da qarfin ikon tilasta kowa yin biyayya ciki harda ku da kuke qarqashin umarni da kulawarmu?" Sake yin qasa da kanta birra tayi sosai sannan a ladabce tace.
"Sheikh haisam" Ta fadi a hankali. Tunani kwanyarta ta cilla,amma bata wahal da ita da dogon nema ba ta canko mata wanda birra din ke nufi,saboda shi kadaine yake amfani da laqabin sheikh a jikin sunansa.
Wani sabon bacin rai taji yana sauko mata,ta ware idanunta sosai tana duban birra da kyau.
"Birra......hala kin manta a gaban wa kike da kike iya sanar mata akwai wata doka bata sultane ba da zata bi?" Tayi maganar da maqurar bacin rai da kuma mamakin yadda komai yake sarrafuwa ta hannunsa.
"Tuba nake ranki ya dade,kiyimin rai" Idanunta kawai ta maida ta lumshe tana jin yadda adadin farashin tsanarsa ke ninkuwa a ranta,kafin daga bisani taja iska me nauyi
"Kada na bude ido na ganki a nan,ki kuma aiwatar da umarni na......doka koda ta sultane ce a yau nasa qafa na taketa,ballanta ta tsintacciyar mage". Sosai kalaman suka yiwa birra girma,bata kuma sake tsaiwa cewa komai ba ta fice da sassarfa,don ya zame mata dole cika umarnin uwargijiyarta.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261 KO 08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 40*
"Albarkar auren itace abinda mukafi buqata,ba tarin sadaki ba,iya wannan adadin sune abinda muka yanke muku" Ya fadi cike da dattako yana sake karantar yanayin kowannensu. Cikin qasa da minti daya kacal ya karanci kallon kallon da sukewa junansu. Kamar wani kallo ne na rashin tabbas......kallo ne na rashin sukuni da rashin sakewa da hukuncin daya zartar din. Bai sake basu daman magana ta biyu ba ya miqe wazeer kuma ya dafa masa baya cikin gamsuwa da abinda haisam din yayi.
Ya shaidawa sultane komai,wani irin farinciki ya ratsa sultane din yana aje numfashi a hankali. Gefe daya kuma yana baqincikin subucewar wani abu me daraja daga cikin ahalinsa.....wani abu da yayi tsananin sanya rai a kansa
"Komai kaga ya dace ka zartar muhammad.....wuqa da nama duka suna hannunka" Abinda ya amsashi dashi kenan a taqaice.
Ko yanzun da suke tattaki zuwa sassan nasa don maleek ya fara kewar coffee yana so yasha kafin ya wuce masaukinsa dake personal gidan haisam din tunani ne fal kansa. Fuskar mutumin da aka bashi tabbaci shine wanda aka karbawa auren ya gaza barin idanu da tunaninsa.
Bawai yana mamaki bane.....ba kuma yana raina matsayi dacewa ko cancanta ba,duk akwai abubuwa masu tarin yawa daya kamata ya tsaya tsakanin kotunan sultane ya amsasu inda yana da hurumi akan abinda ya shafi rayuwarta......saidai aah......yana jin kamar akwai wani abu da yakeso ya sani......yana jin kamar akwai wani al'amari dake da alaqa da bincikensa.
"Karon farko da omar ya zauna gidan sarauta zama me dan tsaho kamar haka......shi yasa komai yake sake burgeshi,kasan kowacce rana sai ya bani labarin agadez?.....wannna yaja ra'ayina zuwa ga agadez din" Maleek ya fada yana murmushi yana kuma jin yanayin qasar da garin duka ya masa.
Kadan haisam ya jingine tunanin dake ransa,ya danja fasali kadan sannna ya magantu.
"Kamar ba aiki ne me girma a gabanmu ba.....ka yawaita maimaita masa ko zaifi fahimtar abinda nake nufi......kowanne gidan sarauta lullube yake da tarin abubuwa da idanu basa iya ganinsa......rayuwa ko tsoma kai a cikinsa sai jajirtaccen namiji". Kai maleek ya kada,don ya fahimci maganan haisam sama ma da yadda yakeso ya fahimta din.
"Gimbiya akhnan" Maleek ya fada a hankali da qaramin murmushi,sannan ya dan juya kadan yana kallon haisam.
"Ko kasan ina da labarinta kadan kadan,bada wata masaniya me yawa can can ba tun kafin omari ya fara gayamin komai akan abinda ya shafeta?" Maleek yayi maganan yana maida dubansa gabansa.
"Akwai nazzirou dan qasar nan ne,yankin diffa,amma yana rayuwa a agadez....."
"Na karbi sadakinta dazun.....daurin aurenta rana ita yau,idan kana sha'awar zama daya daga cikin shaidun daurin aurenta kana iya kaiwa har rana ita yau a agadez" Haisam ya Fadi da yanayin daya bayyanawa hakeem sam sam baya da wani interest akan hirarta ma.
Murmushi me dan sauti maleek ya sauke.
"Wannan bayani haka da wurwuri?"
"Saboda bana buqatar dogon hira akan sha'aninta......inajin kamar shigarta cikin bincikena tana sake dagulamin shine kawai tare da shiga qofofin da bai kamata ta tsaya a nan ba".
"Dalili?" Maleek ya buqata still yana boye murmushin sa bai kuma kalli haisam ba ya bada dukkan hankalisa ne kawai a kansa.
"Wanzuwarta akan wasu hanyoyi da qofofi sune silar bata lokaci na da dadewata cikin wannan masarautar da 'ya'yan cikinta ke rayuwa cikin dimuwa da rashin sanin birnannun sirrikan dake shirin binne musu rayuwa da ransu......ciki harda tata rayuwar data dauketa da wani irin kima da tsananin girman da batasan cewa batakai can ba" Ya sauke maganan da wani irin zafi kadan cikin muryarsa,saidai can qasan ransa yana jin wani mutuwar jiki yana sauka masa.
"Kasan da haka captain......me zai hana kayi ceton daka saba?" Maleek ya tambaya kai tsaye yana duban haisam gami da rage saurin tafiyarsa kadan.
Duk da cewa dare ne amma hakan bai hana maleek ganin yadda haisam ya waiwayo yana zuba manyan fararen idanunsa ba,kafin ya janyesu a hankali. Yan miskilancin suka biyo baya,sai daga bisani daya tuna maleek ne sannan ya motsa bakinsa a nutse.
"Ban gaji da kare mutuncina da martabata ba........inda ace namiji ne.......zan iya qundunbalar aikata hakan........ta yadda koda ya qalubalanceni ina iya zage qwanjina na nuna masa munin abinda yacemin.......amma d'iya mace?......" Sai ya tsaya bai dakata ba yana girgiza kansa.
"Diya mace irinta......data yiwa kanta ado da qawa da rashin iya magana......data yiwa kanta ado da qawa da tarin rashin kunya,nakanji a raina inama ace ta fito daga jini da tsatson oromia....." Sai yayi shuru bai qarasa ba.
Duk da bai qarasa din ba maleek ya fahimci me yake nufi. Tabbas qabilarsu qabila ce da girmama manya ya zama daya daga cikin dokokinsu,ya zama wani abu da ake rainon kowanne d'a nata,tun daga haihuwa har zuwa girma.
"Akwai wasu dabi'u da qualities a tare da ita.......akwai wasu halaye da ba zaka sake samun irinsu sak ga kowacce mace ba a nan kusa.....qila sai bayan shekaru masu yawan da qila zuwa sannan furfura ta gama zama abar ado a kanka da fuskarka" Maleek yayi maganar kai tsaye tana kuma sauka saman zuciyar haisam.
A hankali ya soma maido maganan daga farkonta zuwa baya,yana qoqarin mata mazauni me kyau.......saidai isowarsu dab da gurin,da kuma hango omar da yayi tsaye a gurin da nashi cup din gahwar ya sanya ya maida maganan da yakeson maidawa malee din.
Ya tabbatar idan omar yaji maganan bazai qare ba......ba kuma zai mutu ba,amma indai ta maleek ne shi kadai zai wahala ya sake tayar da maganar,saidai ko bayan wani lokaci ba wannan ba.
Hand shaking suka bawa junansu da wani irin yanayin musabaha da Huggin da zai nuna maka tsantsar qauna dake tsakaninsu.
"Ka shiga kasha ka fito mu wuce.....akwai hira me tsaho yau kam" Omari ya fadi yana dan duban haisam kafin ya maida hankalinsa ga agogonsa. Baiko kalleshi ba haisam din,don har yanzu kwanyarsa cike take da tarin tunaninnika.
A nutse maleek ya wuce ya barsu a nan,shuru ya ratsa gurin na wasu daqiqu,omar na sipping coffee dinsa,haisam kuma yana tsaye da wannan tsaho da murjewar jikin dake nuna asalin halittarsa ta GIANT MAN.
*AKHNAN*
Batasan adadin hadimai nawa ta sanya su kula mata da shigowar haisam ba tun daga sanda adadin abinda ya karba a matsayin sadakinta ya isa kunnuwanta.
Batasan adadin sau nawa ta tsaya gaban mirror tana sake qarewa kanta da kanta kallo ba. Ta sanya hannu ta baje lallausar sumar nan tata me daukan hankali ta ainihin buzuwa kuma ba'abzina.
Wanne irin muni ko lalacewa ya hango a jikinta......wanne irin naqasu ko kasawa ke tattare da ita da zai karbi mafi qasqancin sadaki da sunan sadakinta?. Sadakin da koda manyan hadiman da suka jima cikin gidan.....manyan hadiman da sarauta takewa ALFARMA su shiga rigarta sunfi qarfin wannan sadakin ballanta ita AKHNAN MUHAMMAD HAMMUD diyar SULTANE guda.
Haifaffiyar diyar da har yanzu ba'a samu wata yarinya data kamo rabin qafarta a daraja da kuma gata ba kaf masarautun da qasar niger keda ita. Yarinyar da izzarta da cikar gatanta ya sanya take ganin bata da SA'A cikin yaran sarakuna ballanta har ta qulla aminci ko qawance da daya daga cikinsu.
Kai ta girgiza a zafafe tana jin wani sashe na qwaqwalwarta na tafasa da wani irin matsanancin bacin rai. SULTANE NE SILA......ta yaya zai hada mu'amalarsa da bagidajen da baisan komai ba face tarin litatttafai da tawwada?. Me yasa duk gatanta.....duk shahara da family din mahaifiyarta sukayi idanma bata da gefan uba ya gaza wakilta mutum daya da zai zama jagora wajen aurar da ita?. Sai wannan mutumin da takejin TSANARSA ta fita daban data sauran dukkan malaman data sani. Wannan mutumin da takejin yafi dukkan sauran malaman da suka rayua fadar baqar aniya da baqin sihiri.
Dukkan malamai na baya da suka rayu cikin masarautar girmamata suke.......mutuntata suke da tsananin mutuntata ra'ayinta.....bata da wata hujja ta tsanarsu face tsana data musu tun ta asali.....amma kuma wannan fa?.....shi kuma fa?.
Ya karbe ya kuma ture dukkan wani matsayi da take gani da kusanci tana dashi.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Tana jin wata fusata da ba zata barta ta fara magana da mammina ba......tanajin ya mata nisa ta tsaya shawara da mammina. Shi ya aikata,shi ya kamata ya fara ganin fushinta. Ya dace zuwa yanzu yasan iya matsayinsa.......ya kamata ya fahimci ya zurfafa da yawa,ya kamata ta farkar dashi idan ya soma shaqar iskar 'yanci da yawa harta bugar dashi ya manta matsayinsa......ya kamata old version na AKHNAN BIFTU ya motsa.
Cikin jikinta da jininta gaba daya takejin kunya.....kunya me lullube da wani irin tarin baqinciki na yadda ya zartar mata da hukunci cikin rayuwarta,bayan shi din ba kowan kowa bane a rayuwarta,shi din bai darajar da hannayensa ma zasu taba sadakinta ba.....amma dukka sultane ya tattara wannan damar.....wannan kimar.....wannan martabar ya damqa masa.
Shigowar birra ya sanyata daukan siririn band ta tattare gashinta me tsaho da sulbi ta daureshi,birra ta matso cikin girmamawa da zummar mata shiri na musamman,ga zatonta baqi gareta masu muhimmanci cikin daren,ko wata muhimmiyar fita.
"Kaya kawai zaki bani na canza,cikin gida zan shiga" Ta fada tana qoqarin karbar kayan da tuni birra ta cika umarninta ta ciro mata su.
"Ki tabbatar da lafiyar hanya,sannan a dubamin kowanne sashe na gidannan a gayamin inda wancan malamin yake a yanzu haka". Tayi maganan tana fara zame hannayen rigar baccinta da har tayi shirin kwanciya labarin sadakin daya fara yawo cikin gidan ya hanata kwanciyar. Dan damm kadan birra tayi,tana tuna sabuwar dokar hana zirga zirga daga wannan sassan zuwa wancan sashen da lokacinta yake dan da fara aiki kamar kowanne dare daya zama zartaccen hukunci cikin masarautar. Tana kyautata zaton jwar dakin nata ta manta?,duk da bata da tabbacin tana da masaniyar fara aikin dokar. Dole ta shaida mata,don gudun karya dokar kamar yadda akayi gargadi me zafi akan kowa.
"Allah ya taya miki sirrin farincikin sultane......akwai doka da aka sanya na hana zirga zirga daga goma na dare a masarauta gaba daya". Cak ta daga fararen idanunta dake dauke da blue din qwayar idanu daga tsakiya tana zube dubanta akan birra,kallon dayayiwa birra nauyi,kwarjinta daya cakude da tsananin bacin rai yana tasowa.
"Doka?......waye gwanin sanya doka a sanda sultane baya nan?,sa'annan har yake da qarfin ikon tilasta kowa yin biyayya ciki harda ku da kuke qarqashin umarni da kulawarmu?" Sake yin qasa da kanta birra tayi sosai sannan a ladabce tace.
"Sheikh haisam" Ta fadi a hankali. Tunani kwanyarta ta cilla,amma bata wahal da ita da dogon nema ba ta canko mata wanda birra din ke nufi,saboda shi kadaine yake amfani da laqabin sheikh a jikin sunansa.
Wani sabon bacin rai taji yana sauko mata,ta ware idanunta sosai tana duban birra da kyau.
"Birra......hala kin manta a gaban wa kike da kike iya sanar mata akwai wata doka bata sultane ba da zata bi?" Tayi maganar da maqurar bacin rai da kuma mamakin yadda komai yake sarrafuwa ta hannunsa.
"Tuba nake ranki ya dade,kiyimin rai" Idanunta kawai ta maida ta lumshe tana jin yadda adadin farashin tsanarsa ke ninkuwa a ranta,kafin daga bisani taja iska me nauyi
"Kada na bude ido na ganki a nan,ki kuma aiwatar da umarni na......doka koda ta sultane ce a yau nasa qafa na taketa,ballanta ta tsintacciyar mage". Sosai kalaman suka yiwa birra girma,bata kuma sake tsaiwa cewa komai ba ta fice da sassarfa,don ya zame mata dole cika umarnin uwargijiyarta.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261 KO 08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 41*
Sassauqar rigar buba ce data zauna mata das a jiki,duk da bada fadi ta gefe da gefe amma ta tsakiya ta zauna daidai fadin qirjinta da kuma shafaffen cikin ta. Wani irin yadine me taushi daya kasance daya daga cikin suturun da asalin buzaye kan sanya a jikinsu,sai mayafin da baida cikakken kauri data dora saman kanta da zummar suturce sumarta,ta zurawa sambala sambalan qafafunta takalmin tana jan wani irin tsaki kamar zata cire harshenta.
Da wani irin qasaita take saukowa daga stairs din,kowanne motsinta kowacce gaba ta jikinta tana fidda lallausan qamshin incense by kabodaughter,duk cewa bata qara wani turaen ba a yanzu,amma yadda qamshin ya kama suturarta haka ma jikinta ya sanya ko yaya ta motsa ko ta gifta sai wani irin sassanyan qamshin ya fitini hancinka.
Birra buhaina da bushira dukkaninsu suna tsugunne suna dakon fitowarta,don haka sai kowacce ta miqe suna saita kansu gami da fara take mata baya cikin girmamawa da bada kariya ta musamman ga amanar sultane dake hannunsu.
★Shirunne yaci gaba da gudana a gurin da wani irin yanayi na kadawar iska dake nuni da tasowar hadari da kuma yiwuwar zubar ruwa daga yanzu zuwa kowanne lokaci. Tun yammacin ranar hadarin yake qugi yake kuma hada kansa,so a yanzun ba abun mamaki bane don ya soma zubda ni'imar daya qunso a cikinsa.
"Me ka fahimta game da yanayin nanay akan wannan abun hannun?" Haisam ya tambayi omari kai tsaye,don yanason gwada nasa kaifin hasashen ba tare daya buda masa bayanan daya samu daga gurin nanay ba. Bayanan da suka tunzurashi kuma ya saka wani sabon binciken bin qwaqwaq afi da diddigin yadda akayi ZEENATU amaryar ajani tayi baton dabo. Rana ta qarshe da aka ganta a Ethiopian da gurin da aka ganta na qarshe. Tare da matsawa da kunna kowanne abu da zai tayar da qurar lullubin tsohon aiki tsohon bayani,tayar da duk wani ma'aikaci daya ajiye aiki a wancan shekarun,duk wani ma'aikaci na shige da fice daya ajiye aiki shekaru goma baya da suka wuce har zuwa yanzun.
A jikinsa yakeji da gasken gaske komai yana kan turbar bayyana da warware kansa. Zarginsa yana sake tabbatuwa da qarfafa akan mammina da kowanne irin wucewa second. Bayanai yana iya samunsu yanzu na abinda ke gudana cikin gidan,saidai ya sake tabbatarwa TSANANIN WAYO gareta,wanda hakan yake sake sanyashi damqe tasa damarar da kyau. Ta canza duk wani takunta,saidai a wannan sauyin akwai wasu qofofin data bari a bude da suke iya kai ganinsa ga wani sabon babin zargin. Sake jaddada tsaro da tsari dama qofofin dakin ajiyarta dake cikin gidan,wanda ba wani daki da aka tasamma wannan aikin sai nata. Yaga zallar rashin wayonta a nan,hakan kuma ya zama NUNA KAI da motsi dake tabbatar da tsarguwa da rashin yarda,motsinta ya haifar mata da kuskure,KUSKUREN da ya qara jan hankalin haisam zuwa ga isa ga ma'ajiyar. Ya tabbatar akwai tarin SIRRIKA ajiye a ciki,girman sirrikanne kuma ya sanya hankali da nutsuwar mammina suka kasa samun sukuni da tunanin abubuwan dake binne a ciki.
"Ina tunani gani da hasashen nanay tasan komai akan abun hannun,don reaction dinta ya nuna hakan" Omari ya fada yana tattara hankalinsa akan haisam. Shuru ya sakeyi yana jinjina kansa a hankali,sai ya ajiye nannauyan ajiyar zuciya. A hankali ya motsa bakinsa cike da tarin nutsuwar nan data zame masa jiki.
"Jikina yana gayamin......akwai wata alaqa tsakanin zaituna da zeenatu,qaqqarfar alaqa" Ya fadi can qasan yana qanqance idanunsa saboda sabon gilmawar wani motsi me qarfi da yaji,motsin daya tabbatar omar baikai ga jinsa ba,bayaso kuma yaji din don a yau yana son sake aikewa da mammina ne wani babban GARGAD'I da yakeso ya ganshi baro baro saman fuskarta da ayyukanta.
Kai omari ya gyada shima yana gamsuwa da zancan.
"Idan hakan ta kasance fa?". Shuru yayi sannan wani irin lallausar murmushi ya kubce masa lokacin da idanunsa suka sake dauko masa inuwar bulama dake qoqarin kusanto inda suke.....saidai kar yake hangen inuwar bulama da irga kowanne motsi nasa.
" Zan shayar da kowa mamaki" Ya bada amsar don isar da saqo ga bulama da motsinsa,da kuma isar da saqon amsa ga omari.
Tun daga nesa kadan dasu ta sauke idanunta a kan mutum biyun dake tsaye gaban qarfen,tana tsammanin kasa tantance malamin tsakanin mutum biyun,saidai a sanda idanunta suka sauka kan mutum na biyu daga qasan zuciyarta taji tana gaya mata SHINE.
Idanunta ta qanqance tana ci gaba da duban bayansa tana jin kamar tayi taku guda ta isa gabansa maimakon taku kusan goma sha biyar da suka rage tazarar dake tsakaninsu