L u'u l u'u book 2 complete by huguma - Chapter 29
L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 29: L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 29. Yadda khudubar ke shiga zukatan al'umma da yadda sheikh…
3,370 words
Yadda khudubar ke shiga zukatan al'umma da yadda sheikh haisam din yayi musu wani irin kwarjini da yanayin tsakanin burgewa da samun matashi me tarin ilimi haka wanda haskensa ya bayyana,yanayin ya bayyana akan duk wani wanda ya halacci masallacin da zummar yin sallar juma'a a masallacin,gami da shaida daurin auren diyar sultane din,gudan jininsa da mutane da dama suka gama saddaqarwa cewa ba'a haifi mijinta ba a duniyarmu ta yanzu.
A cikin jikinsa yakejin hucin zazzabin yana ratsashi,abinda ya sanya hudubar zafafa sosai da wani irin husky voice data qara kaifi sanadin madaukar sauti masu kyau da masallacin yake dasu,take kuma watsa sautin har cikin gidan sultane har kuma kunnuwan mutane irin akhnan da mammina,wadanda zukatansu ke dauke da mabanbamtan burika da kuma tsammani.
A nutse ya kammala huduba ta biyu,sannan ya sauka daga saman minbarin da wata irin nutsuwa yana fuskantar alqibla sannan ya tayar da sallah.
Cikin wannan sautin.....wannan muryar wannan qira'ar dake kamaceceniya da muryar sheikh afif taj sautinsa ya fara karade masallacin,yana kuma saukar da wats irin nutsuwa a zukatan mahalarta sallar. Ba iya su kadai ba,hatta da akhnan dake kwance cikin kebantaccen dakin tana iya jin sautin tar,ta maida idanunta ta lullube sautin yana sauka saman zuciyarta duk da yadda taketa qoqarin hana kanta hakan.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261 KO 08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 49*
Wata kalar nutsuwa ce da batasan daga inda ta sameta ba take ratsa zuciyarta,duk da yadda taketa kokawa da kanta wajen hana kanta da kanta sauraro ko jin dadin sautin karatun nasa.
A nutse ya sallame sallar,yana jin yadda jikinsa ke sake daukan dumi sosai da wani irin weakness. Ya waiwayo cikin girma da dattako yana fuskantar manyan mutanen dake fada aji a agadez da sukayi sallah a bayansa ya soma musabaha dasu kaman yadda ya saba yi a jimma.
Maleek ne na kusan qarshe da sukayi musabaha din,sai ya riqe hannun haisam din kadan yana tambayarsa da idanu jin yadda dumin jikinsa ya qaru. Dukkaninsu magana da kuma bada umarni da ido bai zame musu baqon abu ba,saboda fita daga tsatson sarauta,tsatson izza da mulki,don haka suke da saurin karantar body language,da idanu ya yiwa Hakeem sign din baya jin dadi ne,sai ya zame hannun yana maida hankalinsa ga wazeer.
Qasa qasa yake masa maganan waliyyan almaz su matso kusa,don sosai yakejin raunin yana ratsashi,yana kuma jin kamar bazai iya qara mintuna goma cikin masallacin ba.
Wani babban hadimi ne ya miqe yana shelar neman waliyyan almaz din,wanda cikin qasa da mintuna uku kacal suka soma tasowa daga muhallan da sukayi sallah suna matsowa.
A nutse ya daga kyawawan idanunsa yana karantar kowanne mutum dake matsowa gurin. Can qasan ransa yana wassafa abun,ba yau ne karon farko daya fara daura aure ba,daga manyan gidajen alfarmar na yankinsu,mutanen motii da yawanci suke damqa daurin aurensu cikin babban masallacinsu,wanda duk sanda ya kasance haisam din yana nan shi motii ke wakiltawa ya daura auren. Da yawan lokuta waliyyan angon yakan gansu a sahun gaba cikin sallah,wadannan sai gasu a warwatse guri daban daban suke tasowa suna isowa gurin da aka tanada don qulla auren,a haka suka kammala a gaban haisam din.
Still dai a nutse yake kallonsu,can qasan ranshi yana jin wani abu yana motsuwa. Yana jin kamar ya sallamesu ya kuma hana qulla auren,akwai abubuwan da haka kawai yakejin bai masa daidai da tsarinsa ba,akwai abubuwa da yawa da yake ganin kamar basu zauna a muhallansu ba,saidai kuma ta yaya?.
Ta yaya zai watsa taron wadannan mutanen da sukayi tattaki daga unguwannu da garuruwansu yace ya fasa bada auren akhnan din?.....a matsayinsa na wa?......wacce hujjar yake da ita wadda zai gamsar da sultane da dukkan me tuhuma akai?. Baya ga haka ma me yayi ruwansa da shiga sha'anin mara kunyar yarinyar da sam GIRMA baya cikin dabu'unta? Sai dukka ya kauda wannan,ya kuma lumshe idanunsa ya soma bada sigar daurin auren.
Daidai sanda ya kammala bada auren,dukkanin shaidu suka shaida da AKHNAN din a yau ta zama mata ga ALMAZ IDRISSOU daidai lokacin ya miqe tsam yana bada uzuri sannan ya fara ratsa mutanen a hankali don ficewa daga masallacin yana bi ta qofar baya gami da barin wazeer dasu. Tsam maleek ya miqe ganin yadda ya wuce,sai yabi bayansa shima a nutse ta hanyar daya fita din.
*_MUKAN BUDE WASU QOFOFIN QADDARA DA HANNUWANMU........YAYIN DA WASU QOFOFIN QADDARAR SUKAN BUDE KANSU DA KANSU KODA BAMU SHIRYAWA HAKAN BA_*
*_NACE BA🙋🏽♀️,karkuyi qasa a gwiwa.....kuma kada ku sare.....ku biyoni muje_*
*_Akwai QOFOFIN da suka bude kansu da kansu.....akwai wanda sheikh muhammad haisam ya budesu a wannan ranar......a wannan lokacin.....a wannan gurin ba tare daya sani ba_*
Ya manta da maleek sam cikin masallacin,har sai da yaji ya taba kafadarsa,a nutse ya juya yana duban maleek gami da zura hannunsa sosai cikin na maleek din.
"Gidan nan yayimin hayaniya da yawa maleek,mu qarasa gurin motoci,ka kira salana ya matso da mota kusa,zan dan fita gida kadan na huta,kaina sosai yake ciwo" Haisam yayi maganar yana dan riqe kan nasa da yatsunsa.
"Yakai kwana biyar baka a daidai haisam......qin maganinka ne kawai yasa kake pretending you're okay" Maleek ya fadi yana riqe hannun haisam din sosai cikin nasa,don da gaske ya lura jikinsa yana qara zama weak ne,daya hannun kuma ya fiddo wayarsa yana qoqarin kiran omar,don yana ganin kamar zaifi salana saurin zuwa,don su din kam basa wasa da damuwar d'ayansu.
Ido ya runtse sosai sanda sanarwar ta shiga kunnenta. A hankali kuma sai ta budesu,tana jan wani qaramin tsaki gami da gyara kwanciyarta sosai. Bata dauki almaz a matsayin miji ba bars ya zama takurarta,don me zata aza damuwa a kanshi?,saidai abu daya data gaza kankarewa kanta da kuma kankareshi daga zuciyarta shine TSINTACCIYAR MAGE YA ZAMA MADAURIN AURENTA? ta tambayi kanta da kanta tana jin haushin abun yana tsumata sosai,saita sake jan tsaki,fuskar sa ta jiya cikin majigin tana gilmawa a idanunta,cikin tsaiwar na tasa ta lafiyayye kuma ingarman namiji.
Yatsunta ta sake azawa saman fuskarta.kamar tana gargadin idanunta da kwanyarta akan tuna komai daya shafeshi,saita girgiza kai tana hade rai kamar d wani take magana.
Cike da girmamawa duka hadiman dake kai kawo suke kai masa gaisuwa sanda yake tattaki shi da maleek din da ficewa daga gidan. A hankali idanunsa suka kai kan wasu gungun motoci dake tsaye a gurin,inda maroqa da masu busa irin na sarauta suka baibaye gurin. Sosai kuma a fakaice ya saka hankalinsa a gurin yana karantar yanayin mutanen dake gurin.
Daidai lokacin da wani yaketa faman rabon kudi tsakanin maroqan,yayin da idanunsa suka sauka a hankali akan fuskar almaz da tamim ke cusashi a mota.
Sosai wani irin abu me kaifi da haske ya gilma ta cikin kwanya da idanun haisam,ya qanqance idanunsa a hankali yana sake kaifafa ganinsa ta guraren ko zai sake nasarar ganin fuskar almaz din,saidai bai samu nasara ba don tuni tamim ya rufe qofar motar,alamu kuma suna nuna barin gurin zasuyi.
"Salaaana ya qaraso?" Haisam ya tambayi maleek dake duban wayarsa.
"Ya qaraso mu yake jira"
"Oya hurry up" Ya fadi yana qara daga qafa cikin wani irin zafin nama da kuzari,abinda ya sake motsa bugawar da kansa yayi har sai daya runtse idonsa.
Suna shiga motar motocinsu almaz suna wucewa suka wucesu da wani irin gudu. Da zafin nama haisam ya shiga yana bawa salaana umarni da yaren oromo wanda har ya manta rabon da ya yishi cikin agadez
"Ka bisu da sauri" Cikin cika umarni salaana ya tayar da motar ya kuma bi bayansu cikin qwarewa da hikimar iya tuqi gami da bin diddigi.
Idanunsa kan motocin da suke bi a hankali,yana nazartar lambar kowacce mota yanayinta da kuma tsadar da take dashi.
A tsakanin mararrabar titunan motoci biyu suka bi wani titi daban,dayar data rage kuma gangara wata hanya.
"Wacce zamubi a ciki?" Salaana ya tambaya a hanzarce gudun kada su bace musu. Shuru yayi na second biyar sannan yace
"Hannun dama" Wato mota daya data gangara kenan.
A hankali suke bin titin har zuwa sanda suka fada wannan layin. Wannan layin dai daya sanya tsaro da sanya idanu a kansa,wannan layin daya dasa zarginsa a kanshi. Daga nesa ya sanya salaana ya kashe motar,ya bude murfin yana nufin sauka tare da cewa salaana din.
"Ka janye motar zuwa street din dake bayan wannan.......zan qaraso da qafa idan na kammala". Har ya sanya qafa maleek ya riqe hannunsa,ya waiwayo yana duban maleek din.
"Amma kasan baka da lafiya ko?" Kai ya jinjinawa maleek har yanzu yana jin yadda kansa yake sarawa da gasken gaske kaman zai fadi.
"Na sani maleek.......amma akwai wani nauyi da ya hau kaina yanzu yanzunnan daya zama dole na bincika akai.....banason Allah ya tuhumeni bani da bayanin bashi ranar qiyama"
"Amma bai kamata ka tafi kai kadai ba"
"Ni kadai ya kamata na tafi maleek.....kada ka damu zan dawo in sha Allah" Yana kaiwa qarshe ya sanya qafafunsa cikin zafin nama ya fita.
Da zafin naman kuma cikin takatsantsan yake sake kutsawa cikin layin,yanajin qarar tashin motarsu salaana a bayansa,yaci gaba da aza hankalinsa akan wannan gidan da tun ranar basu sake samun komai akai ba sai a yanxun.
Qofar gidan motar ta tsaya,sannan cikin qasa da second talatin murfin ya bude. Tamim ne na farko daya fara fitowa, sannan fuskar da yake sake son gani ta sake bayyana a fili. Almaz ne,da wani irin yanayi na rashin qwarin jiki da ya riga ya zame masa al'ada saboda yawan kasancewa cikin shan kayan maye koda ba mayen yake ciki ba.
Zuciyarsa ta wani motsa da qarfin gaske sanda almaz ke juyawa yana shiga cikin gidan tamim yana biye dashi.
"Me ya hada tamim da angon?" Tambayar farko da taxo kansa kenan sanda yake sake laluben kwanyarsa kan neman inda yasan almaz din.
"Takardun zaituna" Amsar tambayar ta haska cikin kansa. Wani mugun bugawa ya sakeji kansa yayi,har sai daya sanya tafin hannunsa ya riqe goshinsa sannan ya zare hannun nasa a hankali,zuciyarsa da kwanyarsa tana son ganar dashi tarin sarqaqiya da abubuwa masu yawa da yanzu suka harba cikin kansa.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Kai yake girgizawa a hankali,ba'a iya takardar kawai ya soma ganin fuskarsa ba. A nutse sunan gidan marayun ya dawo kansa,ya soma maimaitashi a jere har sai da yaji kansa kamar zai buga.......sai kuma hoton komai ya sake haska masa......gani sau daya daya taba yi masa cikin gida marayun na YATAAMA......a bangaren wadanda ake bawa horo da tarbiyya. Da kansa yaji zuciyarsa tana kokwanton shine ko ba shi bane......sai yaji gaba daya tunaninsa yana rikicewa da wani irin yanayi daya tilasta masa juyawa yana barin gurin,saboda yana jin yadda jikinsa yayi zafi sosai da wani irin zazzabi,sai ya aikewa beeno saqo kawai,ya tabbatar zaizo yaji da komai a gurin.
Ga mamakinsa maleek ya soma hangowa tsaye jikin wata motar daban bata dazu ba. Maleek din ya sauke hannayensa ya fara takowa zuwa inda haisam ke kusantoshi shima.
"Kasan bazam iya tafiya na barka ba.....hankalina bai kwanta ba sam" Ya fadi yana miqawa haisam hannunsa. Zafin da yaji jikinsa ya qarayi ya sanya ya kalleshi.
"Mu tafi gida" Ya fadi a hankali yana takawa,abinda ya alamtawa maleek shuru kawai haisam din yake da buqata ba tarin tambayoyi ba.
Tafiyar mintuna qalilan suka qarasa gidan,dukkan wani guard da security na gidan suka soma kawo gaisuwa,don ya kusa sati biyu rabonsu dasu ganshi. Kowa yayi kewarsa a cikinsu,bawai don wasa da dariyarsa ba,aah,sai don kyautatawarsa a garesu.
Maleek bai tsaya ba har sai daya taka masa har zuwa master bedroom dinsa. Yalwataccen bedroom dake nuna zallar izzar sarauta da kuma tarin dukiya dake kwance muraran a cikinsa dama tsarin ginin gaba daya.
"Kana buqatar magani captain....."
"......ba yanzu ba maleek" Ya dakatar da maleek din yana qarasawa saman wata irin sofa kewayayya dake da wani dan madaidaicin table wanda ke dauke da qananun na'urori. Idanu maleek ya zuba masa,yana mamakin qarfin halin haisam. Sam shi bata lafiyarsa yakeyi ba,ta aikinsa yakeyi,duk da yasan halinsa dama,ko a baya wani irin mutum ne da sai ya gama ciwonsa baisha maganin komai ba. Sau tari sanda suna secondary school sai sun hada da kiran nanay,ita zatayi tsaye cikin waya kafin ya maida hankali yasha din. Ja masa qofa kawai maleek yayi ya koma da baya,bawai don ya qyaleshi bane gaba daya,aah yayi hakanne kawai don bashi space saboda ganin yana hada system da na'urar daya samu a dakin. Cikin ransa kuma yana ganin tsananin jarumtar dake tattare da haisam din,risk da rashin sakewa dake cikin aikinsu gaba daya,lallai aikin ya dace da sunan INTELLIGENT SECURITY. Aiki ne tabbas da bai cancanci kowa ba,aiki ne kuma da ba kowa ne zai iya yinsa ba da gaske,sai jajirtacce irin haisam din,wanda kwanyarsa ke gudu yadda ya kamata..
Idanu ya zubawa system din yana jiran ta qarasa kunnuwa,cikin jikinsa yana jin yadda zazzabin ke nuqurqusar qashinsa,kansa yake sake masa nauyi har yana dan lumshesu kadan kadan saboda yadda yakejin zafin zazzabin yana shiga da kuma yadda yakejin ciwon kamar yana sauka masa a idanun ne.
Yana jin ciwon sosai a jikinsa,amma baisan me yasa yakejin wani takura da qunci cikin zuciyarsa ba sama da abinda yakeji a gabbansa. Hannu ya sake miqawa da hanzari yana bude saqon da noorah tace ta aike masa,wanda ta aika ne ta email kuma system din a nan gidan ya barta,don haka koda ta gaya masa dama ya ajiye sai yau ko gobe zai ware awanni yazo ya duba hotunan.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261 KO 08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 50*
Fes suka fita hotunan,don dama yana cikin dabi'un noorah din daukan hoto. Tana da son dauke dauken hotuna,don har shi da kansa ya siya mata tarin cameras da sauran tarkacen daukan hotuna,wannan ya sanya ta cika dakinta da hotunan tsuntsayenta da take kiwo masu tsananin tsada da daukan hankali,wanda takanas tayi order dinsu daga nigeria ta hannun HALY JASHERU VENTURES 07046665338,ta samu sauqin isowar saqon saboda akwai wani company a nan Ethiopia din da suke order man kitso daga gurinsu suna kaiwa nigeria. (Suna kawo original kayan islamic chemist masu kyau,original body suit na jarirai,harda na manya ma,track suit da sauransu,masu neman nau'in aku,dawisu,irin tattabarun nan masu tsananin kyau farare qal da nau'ikan kaji masu tsada,har na million daya qwaya daya hajiya akwaisu😂,ki sana'a ki samu riba me yawa,ko kuma idan SARAUTA takai irinsu haisam maleek da akhnan,kawai sai a siya a ajjiyesu saboda su qawata farfajiyar gida ko garden idan kina da 07046665338).
Zooming na hoton yayi sosai,abinda ya sanya gabansa wani irin faduwa har sai daya motsa labbansa yana furta.
"Subhanallah" Kamanni yake gani sosai,duk kuwa da cewa asalin wadda ya sani da kamannin bai taba mata kallon daya wuce na minti guda ba kacal......amma yaga kamanceceniya me yawa a gurin,hatta da dimples din dake kumatunta a duk sanda qaramin bakin nan nata na rashin kunya ya motsa itama wannan tana da,banbancin wannan nata qwaya daya ne ta hannun dama.
Ipad dinsa ya matso da ita,ya kunnata ya dorata a saiti,sannan ya miqe a hankali yana jin kamar jiri zai kayar dashi ya shiga toilet. Alwala ya daura ko hakan zai rage masa tururin da yakeji tun daga gangar jikinsa har zuwa zuwa zuciyarsa,bayaso kuma nanay ta fuskanci komai tattare dashi,nutsuwarta da labarin data jima tana basu shi a tsintstsinke yake nema ya jishi a yau full.
Qaramin towel ya sanya ya goge damshin daya jiqa gargasar hannunsa,sannan yaja kujera ya zauna yana kunna camera din ipad din sannan ya kira nanay. Wasu bayanai ta tafa da sauri,kai tsaye kuma ya aika wa bobbo muhammad dawud yayi highlight na YATAAMAH ORPHANAGE. Bayanai yake buqata akan gidan gaba daya,da duk wani yaro da ya taba bata ko ya fita a gidan,da saninsu ko bada saninsu ba,na shekaru talatin baya. Yasan aikine babba daya bayar,amma yana buqatar gano bakin zaren komai a tsakanin nan.
Ya jima yana lalubenta kafin a daga,fuskar Anaani ta fita saman screen din.
"Captain obbo......barka da warhaka" Kai ya gyada mata a hankali muryarsa can qasa ya amsa mata,sai tasha jinin jikinta,zuciyarta kuma ta fara raya mata 'yan miskilancinne tabbas a kusa,don haka bata tsaya wahala ba tace
"Bari na miqawa nanay" Baice komai ba har zuwa sanda wayar ta isa hannun Nanay din,Anaani ta saita mata wayar sosai sannan ta kauce ta basu guri tun kafin a qwaqulo mata laifin da zataci qaniyarta a gurin Captain din.
Sassanyan murmushin nan nata daya sanya yaji wani nauyi na raguwa a zuciyarsa ta sakar masa.
"Assalamu alaikum warahmatullah" Tayi cikakkiyar sallama. Zai iya cewa sallama tarbiyyarta ce,a gurinta suka fara sanin muhimmancinta da kuma tarin ladan dake cikin sallama da alfanun dake cikin yawaita yada sallama tsakanin musulmai. Murmushin ya maidata mata,murmushin da ita daya ke samunsa duk duniya,koda su anani hussam noorah da Aarif ba zasuce ga kalarshi ba,harma gwara noorah saboda ta hannun damansa ce ita din.
"Nanay na biyo labarina" Ya fada cikin tausasa murya da kwantar da kai daya saba,saboda duk sanda yake gabanta yana jinsa ne kamar wani jariri,saidai yau din hakan ya hade masa da ciwon kan dake sara masa,da yadda jikinsa ke qara daukan dumi. Murmushi ta saki wanda ke qara mata wata irin kamala.
"Shi alqawari abun tambaya ne,zan cikashi yanzu in sha Allah" Ta fadi tana gyara zamanta a nutse.
*KHADEEJA YUNNUS JALLATA(NANAY)*
"Kamar yadda ka sani,nice d'iya ta biyu da mahaifina ya haifa,bayan babban yayana Aliyyu yunnus jallata,sarki alimayu na yanzu da ya zama d'a na farko a gurin mahaifiyata data kasance mace ta biyu a gurinsa,mata ta farko a gurin mahaifina itace FALMATA,wadda sam ba 'yar qasarmu bace,kuma har yanzun mu kasa fadin ainihin sunan qasarsu,abinda ya zama silar matsala da kukan da nakeyi kenan har yanzu. Mummu falmata haka muke kiranta dashi,ta samu jinkirin haihuwa abinda yayi sanadin auren mahaifinmu ga mahaifiyarmu. Mahaifina shine sarkin gumma kaman yadda ka sani daya daga cikin yankunan da qabilarmu na oromo suke rayuwa. Samun magaji namaji abune me girma a gurin basarake,wannan shine silar auren mahaifiyata BELKIS.
Gidan mahaifina wani irin zama ne da sam basusan KISHI BA,wani irin zama ake na yaya da qanwa tsakanin falmata da belkis,zaman dake bawa kowa mamaki da sha'awa. Ba wanda yayi zaton a gidan sarauta irin wannan za'ayi irin wannan zaman,wani irin xama me matuqar daukan hankali tamkar 'yan uwan da suke uwa daya uba daya.
Bayan mamana ta haifi alimayu ne da shekaru biyar mummu falmata ta dauko d'iyar qanwarta da suke uwa daya uba daya data rasu,wadda tare sukazo Ethiopia gumma,kuma itama anan aka aurar da ita,don haka bayan rasuwarta mummu falmata itace UWA a gareta,kuma dole ta daukota don duka duka watan yarinyar me suna SAFEENA biyu a duniya.
Ba jimawa da dauko safeena din mamana ta samu cikina,cikin wani ikon Allah sai mummu falmata ta fara ciwo,daga qarshe ya tabbata itama ta samu juna biyu ne,don haka ko da aka tashi haifarmu ni da SAFIYYA sai ya zamana tazarar kwana bakwai ne akwai a tsakanin mu,wannan ya sanya ake kiranmu da TAGWAYE.
Mun tashi dukkaninmu tamkar 'yan uku,ni safeena da safiyya,har baka iya banbance uwar kowa daban,mun zama tamkar taurari da samun wata iri cikakkiyar kulawa da tarbiyya daga gurin motii yunnus. Iyamu daya samu yana jin ya toshe masa duk wata damuwa ta rashin samun haihuwa.