L u'u l u'u book 2 complete by huguma - Chapter 48
L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 48: L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 48. Har abada ba abinda zai sauya wannan amincin.....wannan…
3,365 words
Har abada ba abinda zai sauya wannan amincin.....wannan yardar.....wannan damuwa da lamuran junan dake tsakaninsu,sirrin dayansu na kowane a cikinsu,saidai wannan SIRRIN nasa ne shi kadai.....wannan SIRRIN na hukumarsu ne kawai.....wannan SIRRIN kareshi yana jin ya zama tamkar wani abu na dolensa.
"Babu.....ba kowa my guy" Haisam ya amsa da muryarsa data qara dadi saboda laushi data sakeyi.
"Gangan kenan.....kaima ka fadi ne kawai khadeem,banda haka......captain ne fa?......ka manta?.....dama akwai wani abu da yake tsoro a rayuwarsa?.....akwai abinda ke razanashi?.....ka manta da forest din da kowa zai kasa shiga ya koma amma saboda yanayin weather na gurin shi dayanshi yake shiga yayi abinda ya kaishi ya dawo?". Amjad ya furta yana tuna musu lokuta masu dadi na rayuwarsu.
"I remembered" Ya amsa wa Amjad yana girgiza kai da qarfi.
"Duk da haka komai yana da dalili......meye boye a bayan wannan auren da wuri haka?.....ko dama can da wani abun kuka boye mana yaa omar?" Naseeb daya ajiye qaramar wuqar hannunsa ya fada yana sake fuskantar screen din sosai.
Da hanzari omar ya daga hannuwansa dukka biyun sama,kamar me surrender,alamun ba ruwansa,bai kuma san komai ba. Sai maleek ya gyada kai yana sake tabbatar musu da reaction din omar.
Shuru kadan ya ratsa,kafin ya motsa da cikakken nutsuwarsa yana duban fuskokinsu still. Shi ya sani,ba komai bane zai iya boye musu ba,kamar yadda suma bass iya boyewa junansu komai. Duk da cewa ba'a rasa jituwa me qarfi tsakanin wani da wani a cikinsu,kamar yadda maleek ya zama mafi qarfin jituwa shida omar a tsakaninsu,saboda gidan da suka fito shida maleek din,daidaito da kamanceceniyar jini da rayuwar yau da gobe da suka tashi a ciki me shigen kama da juna.....saidai hakan bai sauya wannan AMINCIN dake tsakaninsu ba.
Akwai dalili.....tabbas da akwai dalili.....saidai dalilin wani dalili ne da bazaiyuwu a yanzu na fadeshi ba" Ya furta a nutse. Ya riga ya barwa ransa kansa da zuciyarsa.....a gefe guda kuma yana jin dole ya kare MARTABARTA koda ba zata shiga rayuwarsa don ta wanzu har abada ba.....hakanan dole ya kare martabar sultane shima saboda AMANA ba abinda yakai girma da qarfinta.
"Hakan yana nufin ba don SOYAYYA bane captain?" Naseeb ya fadi cikin yanayin hankali da nutsuwa irin ta wanda ya ajiye iyali.
Idonsa ya lumshe sannan ya budesu lokaci daya akan naseeb din.
"Ba ko yaushe bane soyayya yake zama dalilin yin komai naseeb" Shuru ya sake ratsawa,kowannensu da nazarin da yakeyi,saidai dukkaninsu sun fahimci da gaske akwai dalilin,ba kuma soyaya bace.....amma tunda har baiji ya kamata ya fadi dalilin ba,suma ba wani hurumi ko dalili na matsa masa. Dukkansu sun yarda da haisam,dari bisa dari,yana da wani irin hankali da dattako cikin dabi'u halaye da kuma jininsa,tun sanda suka hadu a haka yake.....har yanzu kuma ba abinda ya sauyashi.
"Idan da rai....idan da rabo komai yana iya canzawa.....kabi a hankali.....wataran zaka iya b'urmawa cikin soyayyarta". Naseeb ya fadi cikin bashi tabbaci.
Murmushi ya saki kadan,can qasan ransa yana basu uzuri da RASHIN SANI.
"Bazaiyuwu bane na sota.......bana planning din son kowacce diya mace a rayuwata.....don zata iya zame min BARAZANA......zata iya kuma zama itace RAUNINA.....samun RAUNI ga ma'aikacin security intelligence kuwa barazana ne ga rayuwarsa......ka auri wadda ke sonka.....wadda kawai zata yarda ta sadaukar maka"
"Ba'a yiwa so iyaka.....ba'a yiwa so irin wannan dabarar" Naseeb ya fada yana girgiza kansa sosai.
"Inaji kamar akai naseeb,saboda banga kuma banji muhallinsa ba sam sam" Yana kaiwa qarshe qarar wayarsa ya dauki hankalinsa. Ya aje dubansa a nutse,sai yaga motii ne yake kiransa. Hakan ma ya masa,don yasan a bakunansu,maganganu ne fal tarin tambayoyi da kuma qalubale masu yawa. Da hannu ya basu uzuri,ya miqe kuma anutse yana haurawa zuwa sama,yayin da dukkaninsu suka bishi da kallo had ya bace,sai kuma tattaunawa ta koma tsakaninsu.
Duk wani magana da yayi akan auren suka ajiye gefe,suma tashin nasa yayi musu,sai kawai suka fara tsara yadda komai zai gudana,koda kuwa bazaiso hakan ba,amma sunsan bata yadda za'ayi captain sheikh din zai daura aure koda sadaka za'a bashi matar subar komai ya tafi a haka. Koda ba a ranar da za'a daura auren ba,dole suyi wani abu da shi kansa zaisan YES aure zaiyi.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261 KO 08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 83*
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
"Assalamu alaikum warahmatullah" Haisan yayi sallamar da cikakken nutsuwa sanda yake zama saman stool din dake gaban madubin.
"Wa'alaikumussalam" Motii aba jifar ya amsa muryarsa dauke da wannan tarin dattakon kamala da kuma kamewar.
"Barka da warhaka ranka ya dade" Haisam ya furta da yaren oromo yana rusunawa tamkar motii aba jifar yana gurin.
"Barka kade muhammad". Cikin asalin girmamawar da yakewa me martaba aba jifar ya soma gaidashi,cikin tsananib kulawa da tarin girmamawa. Shuru ya ratsa na sakanni,yanajin nauyin abinda zaice da motii dinne,yana jin kamar baiyi abinda ya kyauta ba. Aure rana tsaka?,aure kuma a kwanakin da duka duka ko bakwai basu kai ba?. Sai yakejin nauyin motii sosai,abinda kuma ya hanashi kiran nanay kenan,don baisan da yadda zai mata bayani ba.
Kamar me martaba aba jifar yasan tunanin dake ran yaron nashi,sai ya kira sunansa da wani irin nutsuwa qauna fahimtar juna da girmamawa.
"Muhammad"
"Ranka ya dade" Haisam ya fadi da harshe na girmamawa yana rusunar da kansa kamar yana a gabansa.
"Naji saqo daga bakin bobbo......na kuma karba dukka bayanai daga bakinsa,na kuma fahimci komai,kuma koda baimin kalar wannan bayanin ba......ni nasan yarona bazai taba tozartani ko ya kunyatani ba......ko kuma ya aikata wani abu na ba daidai ba......na amince na kuma yarje maka ka auri diyar Muhammad hammud......domin kuwa shi din mutumin kirki ne,tsohon aboki daya kasance amintacce,kuma ma'abocin halaye da kuma dabi'u masu kyau. Na aminta bazan bayyana ga muhammad hammud ba saboda yanayin tsarin aikinku.....zan bada goyon baya dari bisa dari......saidai kuma abu guda daya da zan gaya maka muhammad....." Me martaba ya fada yana dan dakatawa.
"Muhammad" Ya sake maimaita kiran sunansa
"Na'am me martaba"
"Kaji tsoron Allah......aure ba wasa bane,nasan ka fini kusan sanin hakan,domin kai me karantarwa da nusashe da mutane ne akan hakan........kada ka yarda koda wasa ka qudurta a ranka zaka auri d'iyar hammud don ka fake a bayanta......don ka cimma wata manufa taka......koda sultane ya roqi ALFARMAr ka auri diyarsa.....kada ka manta hakan bazai canza MARTABA KIMA DARAJA DA TATA ALFARMAR BA......koda yace GARKUWA kawa yakeso ka zame mata......bafa hakan yana nufin yayi wasarere da ita da qaunar da yake mata ba,don haka kaji tsoron Allah,ka tsarkake niyyarka" Sosai maganganun motii ke masa yawo saman kai,sai ya tuna masa da maganganun sultane a jiya.
"Na gode sosai muhammad.......na gode daka martabani.....ka karramani ka kuma karbi qoqon barata hannu bibbiyu.....ko iya haka ya isheni muhammad,ka kuma nunamin halascin D'A na halak.....don Allah na roqeka.....koda baka zamo miji cikakke ga akhnan ba kaji tsoron Allah kada ka cutar da ita.....koda baka zamo miji cikakke gareta ba.....ina nema mata ALFARMA ka zame mata GARKUWA......ka zame mata GATA ka zame mata SUTTURA"
Dukkaninsu kalamansu idan aka tattarasu abu guda suke nunawa. Dukkaninsu kalamansu idan aka tattarsu guri daya zasu hadu,sai yakejin kamar sunason sauya masa manufar komai a zuciyarsa ta qarfi da yaji.
"Ina fata komai yana tafiya lafiya?" Haisam ya tambayi motii bayan sun gama maganan data shafi auren.
"Komai lafiya Alhamdulillah.....bisa dafawar ubangiji da qoqarinka". Kai ya jinjina a nutse,a duniya to su waye yake dasu sama dasu din?. A koda yaushe yana nan ne amma hankalinsa yana can jimma. Abu daya yanzu da yadan sake saka masa nutsuwa,gano anihin kan matsalar,sanin wacece ZAITUNA ya sauqaqe masa abubuwa masu yawan gaske,ya sake saka qarin saka idanu sosai a kanta da wata irin boyayyar matsin lamba da ita kanta batasan da ita ba.....abu daya ya rage masa a yanzu........iya adadin rassan da take dasu a Ethiopia......iya adadin idanunta a Ethiopia din.
"Ma sha Allah......"
"Ranar juma'ar nan ma da izinin Allah zanje na duba al'ummata na qauyen Dass" Motii ya fada a nutse yana duban nanay data shigo wanda tun dazu ya nemi ganawa da ita.
Sam abun sai yaji bai kwanta masa ba,ya miqe a nutse yana duban fuskarsa a madubi.
"Amma motii.....wakilci kawai bai wadatar ba?" Kai ya girgiza yana murmushi.
"Ambaliyar ruwa aka samu......lamarin yafi qarfin wakilci muhammad,ina tsoron ranar da Allah zai tsaidani ya tambayeni ne nayi akai?,wacce gudunmawa na basu?" Shuru haisam yayi.....su din rainon me martaba aba jifar ne,wannan ya sanya zukata da ruhika suke da wata irin nutsuwa.
"Hakanma yayi motii,amma da zaka iya jinkirtawa,zan aiko da wasu qari da kuma musaye na masu tsaron lafiyarka daga hukuma" Kai motii ya girgiza yana sanya hannunsa cikin na nanay daketa kallonsa
"Babu wani abu da zai faru damu sai abinda Allah ya rubuta masa,ga Allah ne kadai muminai suke dogara" Kansa ya gyada,motii na sake zama masa wani role model a rayuwarsa,tun daga quruciya har kawo yanzu.
"In sha Allah motii.....in sha Allah".
Sauke wayar me martaba aba jifar yayi daga kunnensa yana duban khadeeja data zuba masa idanu. Mace daya tamkar da dubu a gurinsa.....uwar gidansa kuma uwar dukkanin 'ya'yansa......matar da har yanzu ba wata mace daya taba jin zuciyarsa tanaso koma bayan ita.
Murmushi ya saki a hankali yana ajiye wayar a gefansa.
"Irin wannan kallon kamar ranar da muka fara haduwa?" Ya fadi yana kashe mata ido daya. Qaramar dariya ta saki,tana jin kunyarsa kadan tana saukar mata. Duk tsahon shekaru da kuma haife haifen da tayi ba abinda ya sauya tsakaninta da IBRAHIM. Har yanzu wannan kallon qauna rahama da soyayyar yana nan a inda yake,takan kalli haisam a yawancin lokuta,tana kuma rayawa a ranta tana yiwa diyar duk data sameshi a matsayin miji murna,musamman idan ya dauki halayen mahaifinsa. Wannan dalilinne ya sanya take tsananin yiwa saamee sha'awarsa,ko don maraicinta,ko don kuma nata nutsuwar da kuma hankalin.
"Allah yasa ba wani laifi nayi ba ake tuhumata da idanu.....abu daya dana karanci a gurinki muhammad haisam ya gado" Sake sunne kanta tayi a nutse tana murmushi.
"Ko daya Allah ya baka yawan rai,....ina na isa na tuhumi mijina haka?" Murmushin ya maida mata shima yana dan jan hannunta.
"Magana nakeso muyi Allah yasa aban aron hankali duka da tunanin a nan"
"Ba aro za'a baka ba,domin kuwa hankalin tunanin da wadda ta mallakesu dukka naka ne"
"Na sani,na gode da aka sake tabbatarmin" Ya furta yana murmushi.
"Khadeeja....." Ya kirata da sunanta na asali.
"Sanin kanki ne komai muqaddari ne daga Allah,sannan sanin kanki ne muna rayuwa ne akan rubutacciyar qaddararmu......sannan sau da dama akwai abinda muke hanga ga yadda zai kasance sai Allah ya canzashi ya kasance daban da yadda muke tunani.....duk Allah yana yine don zaba mana maslaha da kuma abinda xai dace damu....wasu suna shiga rayuwarmu a sanda bamu zacesu ba,wasu kuma suna fita a sanda bamu tsammacesu ba.....haka rayuwa take. Ka marabci dukkan wanda Allah ya kutso dashi rayuwarka don bakasan dalili ko manufar haka ba....kada ka koreshi kada ka qyamci kalar qaddararsa.....hakanan duk wanda ya zabi fita daga rayuwarka kada ka tsaidashi,.......bakasan manufar Allah na koreshi daga cikin rayuwarka ba,wataqila bai cancanci zama da kai ba......wataqila wanzuwarsa a rayuwarka matsala ce" Kai ta jinjina a nutse tana jin jikinta yana sanyaya,hankalinta kuma yana gamewa guri daya.
"Kin tuna sultane hammud na yankin sahel?" Ya tambayeta yana duban idanunta. Nazari kadan tayi sannna ta girgiza kai da sauri tana murmushi.
"Wanda yazo barkar haisam?.....yace in sha Allah shi din babban malami ne da ba'a taba irinsa ba?.....ga sarauta ga ilimi.......dan gatan malami.....isa takai isa kenan malamin dake da sarauta" Sosai murmushi ya qwacewa motii,ya sani zai wahala nanay ta manta sultane ko don saboda wadannan kalaman. UWA bata manta wanda yayi KYAKKYAWAN FATA ga yaronta.....kamar yadda bata manta wanda yayi mummunan fata a gareshi. Lokaci lokaci takan tambayeshi ina hammud na sahel?,saidai shi kansa bayace ba,don baisan ainihin sunan qasar ba har suka rabu,sadarwa ta yankewa kowa a cikinsu,tun a Egypt.
"Yana ina kuwa?,har yanzu ba wani labarinsa?"
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Ya dawo khadeeja......ya dawo rayuwarmu ta hanyar bawa haisam auren diyarsa me sunanki khadeeja......auren da zaa daurashi nan da kwana biyu ko uku a madeena". Wani iri taji xancan,kwata kwata saita gagara fahimta,ta zubawa motii idanu tana neman qarin bayani.
Murmushi ya saki,ya miqa hannu yana lakace mata hanci.
"Dauke idanuwannan ma'abota kwarjini.....irin idanun sheikh muhammad haisam sak" Tare murmushi ya qwace musu,tana kallonsa ne bawai don bata aminta dashi ba,ta yarda da mijin nata dari bisa dari,da wata irin yarda da d'a yakewa iyayensa.
"Bani labari motii" Ta fada cikin son jin yadda wannan bahagon al'amarin ya kaya. Nutsuwa yayi sosai yana sake riqe hannunta cikin nasa.
"Gidan sultane haisam ya sauka,acan kuma yame gudanar da bincikensa,saidai cikin binciken ya samu gidan sultane a hargitse......ya samu komai baya tafiya daidai dalilin hatsabibiyar matarsa......akwa tarin abubuwan da suke a rufe da sultane bai sani ba bai kuma fahimta ba har yanxu......akwai abubuwan da suke tafiya akan hadari da ba daidai ba......ciki kuwa harda d'iyarsa da aka yiwa saki uku kwana uku kacal da daura auren da ko tarewa batakai gayi ba.......MARAINIYA ce data rasa uwa......marainiyar data rasa UBA ba kuma don baya raye ba......sai don kawai yadda aka kifar da tunanin mahaifin da nata tunanin dukka,bara gane daidai daba daidai ba cikin rayuwarta,an amintar da ita duk wani kuskure da za'a yiwa rayuwarta daidai ne.....duk wata halaka da za'a jefata daidai ce...... Bamu sani ba addu'a ce?,Allah masani,sultane ya yanke bawa haisam diyarsa wanda haisam din ya dade da zama cikakken d'a a gidan.....ya kuma dade da zama amintacce ga sultane din ba tare da yasan daga inda ya fito ba......sun sake haduwa da bobbo.....yasa bobbo ya nema masa izini,ni kuma na yarje......haisan ya yarje shima saboda ceto......duk da banda tabbaci d'ari bisa d'ari akan dalilin da ya sanya ya amince haka da wurwuri shi din.....wannan shine abinda ya faru". Yayi mata bayanin a dunqule ba tare daya buda mata dukkanin abinda ya shafi aikinsu haisam ko hukumar tsaro ta sirri ta farin kaya ba.
Shuru tayi tana rasa abuncewa,wani bahagon al'amari ne daya kamata ya zame mata me nauyin gaske,auren d'anta a wata qasar,a sanda ba'a shiryawa komai ba. D'anta mafi soyuwa a gurinta,d'anta na fari.....to amma kuma komai tasan tsarin Allah ne kamar yadda motii ya gaya mata a yanzu. Uwa uba kuma MARAICIN yarinyar da rayuwarta a baragurbin hannu shine abinda yafi tsaya mata. Tana tausayin maraya sosai,tun sanda ta fada nata maraicin. Batun shiri akan aure ko biki dukka tasan wasu abubuwa ne da za'a iya yinsu daga baya......wasu abubuwa ne da za'a iya maye gurbinsu a wani lokaci na daban,bata da haufi ko matsala a kansu.
"Shi kuma muhammad tasa qaddarar ta auren marayun mata ce....Allah ya qara cika zuciyarsa da tausayinsu da kyautatawa" Ta furta a sanyaye. Furucin yaja hankalin motii a kanta.
"Marayun mata?" Ya sake tambayarta. Murmushi ta saki tana dubansa.
"Eh.......ina da burin ya auri saamee Allah ya taimakeka......saidai hakan baya nufin na tursasashi.......zan bashi dama har sanda zaiji ya gamsu,zan bawa saamee dama itama idan tana jin zata iya riqe soyayyar ita kadai.....kada kace komai don bazan tilasta daya daga cikinsu ba,duk yadda nakai gason wanzuwar abun" Idanu ya zuba mata sosai,yana jin kamar ya hadiyeta. Komai nata akwai sauqin kai a ciki,komai nata akwai hankali nazari da kuma fahimta,bata da zafafawa akan komai,mu'amalarta sassauqa ce,iya wannan yana qara yawan sonta a zuciyarsa,yana jin bazai samu wata mace kamarta ba.
(Yake me karanta wannan littafi.....muddin kina biyayya ga mijinki da kuma qoqarin kyautatawa tuquru,soyayya da zama bisa amana,ina roqa miki Allah ya kadaitaki a gidan mijinki......ya kadaitaki a zuciyarsa dama rayuwarsa gaba daya ki zama KE DAYA CE TAK!).
"Zan aika jama'ata in sha Allah zuwa nan da gobe ko jibi zuwa madeena,zan yiwa sarkin Gibe da sarkin kaffa. Ki sanar da me martaba sarkin gumma don ya zama wakilin mahaifiya da d'an yar uwarsa" Murmushi ya qwacewa nanay......yadda motii ke girma ahalin yunnus jallata na dada burgeta,har yau har gobe ba abinda ya sauya. Yayanta sarkin gumma motii yana kallonsa ne a matsayin mahaifinta,duk da kuwa kusan sa'anni suke da junansu. Murmushi ya saki,ga jawota kadan yana rungumeta cikin jikinsa
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261 KO 08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 84*
"Ya kamata a samu yawaitar shaidu......kowa yasan ibrahim aba jifar ya aurar da sheikhun malamin d'an nashi,duk da mun boyewa sultane har yanzu baisan nine asalin mahaifinsa ba.....har yanzu kuma baisan daga wanne DANGI daga wanne AHALI haisam ya fito ba......duk wani hidima da shirye shirye zasu biyo baya......ba abinda xan hanaku aiwatarwa khadeeja......haisam na musammanne,kuma na dabanne a raina" Kanta ta ajiye a qirjinsa tana sauke ajiyar zuciya,gurin da kullum idan ta sanya kanta a gurin sai taji wata tarin nutsuwa da kasancewa cikin aminci a zuciyarta da jikinta.
"Allah yayi mana zabi mafi alkhairi,ya shige mana gaba"
"Ameen......a ranar ina da tafiya duba mutancan da asara ta samesu na qauyencan,inaso a duba yadda za'a biyasu diyya su rage radadin asarar da sukayi" Hannunsa ta matse cikin nata tana sake alfahari da kasancewarsa mijinta uban 'ya'yanta. Ba shakka da yawa daga cikin halayen nagartar haisam daga gurinsa ya gado.
"Allah ya qara maka suttura arziqi da rufin asiri"
"Ameen ya rahman ya raheem" Ya amsa mata yana jin wani farinciki yana ratsashi.
*WHEN FATE SPOKE IN MASJID ANNABAWI*
_(MADEENA ALMUNAWWARA)_
Tun asubahin ranar juma'a ya fita kamar yadda ya saba duk lokaci irin wannan don samun sallar juma'a a masallacin ma'aiki a guri na gaba daura da liman. Duk kuwa kasancewar yana cikin jerin sahun manyan mutanen daka iya tsaiwa dab da liman a kowacce sallah,amma yafi zabar sammako don dacewa da dukkan falalar da ranar ke dashi.
A yau din juma'ar ta zame masa ta daban,juma'ar ta zame masa ta musamman,juma'ar da yakejin kamar itace juma'a ta farko a gurinsa.
Da qyar a jiya bobbo ya tilastashi kan ya koma masauki yayi bacci koda na awa uku ne kafin asubahi tayi. Baisan iya adadin addu'ar da yayi akan auren ba a kwanaki ukun kacal,baisan iya adadin rahamar Allah daya nema ya sauka akan auren ba,kariya da albarka. Baisan kalar addu'ar samun shaquwa da qauna me zurfi da yayi ma ma'auratan ba. Tunda ya sani.....wani aure ne da dukkaninsu zaizo musu da wani bahagon yani bahagon al'amari. Yasan haisam me sauqi ne,kamala dattako da sanin ya kamata,ya san muddin maganan sauke haqqi na iyali da kulawa ake magana akai bazai bashi da haufin khadeeja dinsa ta gama samun dukkan wadannan,saidai bayan wannan din......yanaso ta samu SOYAYYA soyayyar ma irin ta haisam daya tabbatar muddin ta sameta ta gama samun cikakkiyar kamala dacewa da jin dadin duniya harda na lahiran ma yana sanya mata rai.
Shi kansa bobbo muhammad dawud bai sake gasgata yadda sultane ya dauki girman al'amarin ba sai da baqi suka iso daga agadez. Aqalla mutum biyar dukkaninsu saboda halartar daurin auren da kuma sauke umra. Sun hadu da sarkin nigeria daya kasance amini na sosai ga sarki sultane.....wanda a take ya baiwa muhammad sunusi lamido sunusi waliccin daura auren da zaa daura din bayan kammala sallar juma'a a masallacin manzan Allah.