L u'u l u'u book 2 complete by huguma - Chapter 7
L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 7: L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 7. "Kwanciyata bacci?.....shine zai zama lokacin…
3,343 words
"Kwanciyata bacci?.....shine zai zama lokacin faduwarki.........lokutan kwanciyata bacci.....sune zasu zama lokutan kwanciyar dukka wata sa'arki......zanyita bacci kala daban daban,daga nan har zuwa kwanakin dana fahimci WACE KE?. INA KIKA SAKA GABA?....kin shiga cikin lissafi na...." Ya fada qasan zuciyarsa da wata irin nutsuwa. Bai taba tunanin na'urar daya wurgar a gurin zata kawo masa amfani da wani bayanai daya shafeshi shi karan kansa ba......bai taba tunanin na'aurar zata zama me amfani me girma har haka ba. Hanyar dake gefan hagunsa ya kalla,yaji kuma a cikin ransa itace hanyar data dace ya shiga ba tare daya damu da komawa daukan na'urar ba. Bata da wani girma da wani zai gane meye,tafi kama da ba'awon gyada sak da sak,yasan ba jimawa wani zai taketa shikenan amfaninta ya qare a wajensa. Har qasan ransa yakejin matar tamkar tana da alaqa da duk wani bahagon al'amari da masarautar ta taba fuskanta,duk da bai sani ba.......amma motsinta na baya dana yanzu yana gaya mata tana daya daga cikin QALUBALEN SULTANE.....tana daya daga cikin MATSALOLINSA TABBAS!.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Yanaso yana mugun sha'awar ayyukansa subi takan mutane irinta......sa'arsa daya bai shigo agadez don ceto masarautar agadez ba......bai shigo agadez don bawa sultane ko iyalinsa ko mulkinsa kariya ba......ya shigo agadez ne kawai saboda QASARSA.....ya shigo agadez ne don ya kare rayuwar MAHAIFINSA.....hakanan ya shigo agadez ne don ya zaqulo boyayyen mai laifin nan ya damqawa qasarsu shi!. Iya wannan kawai zai iya sanyata ta tsira muddin bata zama cikin wadanda yake tuhuma ba......daga sanda ta sadashi da abinda yake muradin farauta ta fita daga AGENDA dinsa.
Tunda buhaina ta gaya mata an shiga tattaunawa tsakanin sultane mammina da nannie ta kasa cikakken sukuni. Kowanne irin zama ne ta tabbatar yana da alaqa da ita.....koda ba don ita aka zauna ba ta sani issue dinta yana abu na gaba gaba da za'a tattauna akai.
Yau da kanta ta shirya shirin baccinta,don bata dade da sallamar birra ba,wadda suka jima yarinyar na mata kuka da rantsuwar bata xuba mata komai cikin tea dinta ba.
Bata da wani kokwanto akan birra ko kadan,yadda ta yarda da ita haka ta yarda da kanta,to amma tana ji a jikinta tabbas akwai wani abu,akwai abinda ya faru......bai kamata kuma tabar komai yaci gaba da tafiya a haka ba.
Tafi karkata dukkan amincinta akan tamim......to amma a yanzun tamim din yana kan wa'adin ragowar kwanaki biyu na aikin data bashi,tana jin zata jirashi don sake bashi wani aiki na bincika mata me ya farun,wannan ya sanya ta hana a taba duk wani ruwa da kwanuka na bangarenta,har zuwa sanda tamim din zai dawo.
Sanda birra data dawo take shaida mata mammina ta shigo tana buqatar ganawa da ita. Bata kammala jin abinda birra ke fadi ba ta soma yunqurin sauka daga gadon. Net din dake zagaye da gadon ma wanda take controlling nashi da remote gani tayi yau baya saurin zugewa don ya bata hanya,saita sanya hannu ta yayeshi gefe tana saukowa. Bata ko tsaya neman flip-flops dinta ba ta soma taka tattausan tafin qafanta kan carpet din tana qoqarin cusa gashinta me tsaho da sulbi cikin bonnet da take mahadin kayan jikinta.
Yadda take saukowa daga stairs din a gaggauce ya sake sanya mammina cilla plan dinta da qara masa wani adadi.
Ido ta lumshe tana sake budesu akan akhnan din,wani irin kishi yana ci mata zuciya. Har tana jin kamar wani ciwo ciwo na dunqulewar da zuciyarta tayi guri daya.
Wani irin sassanyan kyau yarinyar ke dashi,kyan data tabbata banda wasu dalilai ba abinda zai sanya akhnan ta rufa shekaru goma ba tare da an aureta ba zuwa ga ahali mafi daraja da sukafi na mahaifinta. Ita kanta akhnan tana mata kyau,saidai kyan yana tsaye mata a rai da wani irin ciwo saboda tuna daga inda ta samo ASALIN KYAN nata. Daga gurin safeena ne......wannan kyan nata da tayi imani yana daya daga cikin abinda ya sanya ta rasa wannan martabar.......ta rasa wannan darajar.......ta kuma rasa wannan MATSAYIN da TAMBARIN na MATAR FARI a gurin sultane.
Bayan kyan ya mata wannan sanadin......wannan KYAN HALIN da a wajenta ba komai bane face zallar kissa da kisisina ya sake zame mata silar qara rasashi a KARO NA BIYU,ya sake cillata can nesa da matsayin zamowa MATA TA BIYU ga sultane din.
Ware idanunta tayi akan akhnan sanda take kusa isowa da inda take. Tuna baya kadan da tayi ya sake rura wata sabuwar wutar a zuciyarta. Ta zubawa akhnan idanu,tana tuna fuskar safeena da wani lokaci zaka ganta shimfide akan fuskar akhnan din.
Sau da dama tana mamakin kanta na yadda ta tsaya bin akhnan ta wannan doguwar hanyar. Tana ganin imaninta da yawa idan ta tuna shekarun data dauka kawai tana dakon ta dauki FANSA akan abinda tana iya aiwatar dashi cikin kwana uku kacal. To amma zuciyarta tasha gaya mata cewa.
"Daukar fansa yafi ciwo a sanda aka manta......yafi ciwo a sanda aka saki jiki.....yafi ciwo a sanda zamani da shekaru suka cilla......a sanda akayi imanin komai bazai canza ba......komai bazai kuma faru ba" Ta yadda da wannan magana ta zuciyarta.......kuma itace take mata jagoranci a dukka tsahon shekarun nan kawo yanzu. Safeena zallar muguwa ce.....muguwar da bata da kamanceceniya,salon muguntar da batajin idan zata dawo duniya ta mutu sau dubu hakan zai sassauta abinda takeji a kanta kota yafe mata,a sanda ta tabbatar rabuwa tazo tsakaninta da sultane......a sannan ma bata barta ba,bata bar sultane ba,saida tayi abinda ya sake jawo mata asarar matsayinta,ya kuma kusa sake jawo mata rasa sultane din rashi na har abada,ta yaya zata manta da dukka wadannan abubuwa?,ta yaya zata yafe cikin sauqi?,don dai ita ta kawo wawanci duniya?.
Yadda taga akhnan na kallonta ya sanyata sakin sassanyan murmushi
"Ina tunanin irin halin da zan shiga yanzu iwarhaka inda na rasaki......biftu......kina taba tunanin inda muradinki ya cika masarautar agadez gawa biyu zasu sallata?" Kai ta kada tana duban mammina. Batasan me yasa a wannan lokacin mammina ta gaza yarda ba ita ta aikatawa kanta haka ba?.
Ta lura da irin kallon da akhnan din ke mata,don haka ta nuna gefanta dab da ita.
"Zauna a nan" Bata musanta ba ta zauna din,mammina ta zuba mata ido tana tattara nutsuwarta a kanta.
"Munci sa'a,munci kuma nasara.......sultane ya janye maganan hakeem a kanki......labarin abinda ya faru ya isa kunnensu,don haka sun janye,nasara taki ce". Manyan idanun nan da sukan rusuna wani lokaci kamar name jin bacci ta ware gaba daya. Labarin yazo mata a bazatar da bata taba kawota nan kusa ba,ta rasa me zata yiwa mammina?,kawai saita shige jikinta gaba daya tana mata wani wawar runguma.
Wacce irin qauna ce haka mammina ke mata?,anya yadda mammina ke sonta ko mahaifiyarta idan ta dawo duniya zata qaunaceta irin haka kuwa?.
"Bansan me zance miki ba,bansan wanne kalar godiya zanyi miki ba" Akhnan ta fada idanunta suna cika da hawaye,tana jin kamar an warware mata wani qaton dauri da aka yiwa rayuwarta gaba daya.
Rungumar data matan tana mata kamanceceniya da sanya buhun qarfe na wuta a jikinta,amma hakan bai hanata shafa bayan akhnan din ba,kafin ta janyeta a jikinta a nutse da tausasawa tana cewa.
"Da abu guda daya tal zaki biyani". Tsaida idanunta akhnan tayi kan fuskar mammina tana kallonta.
"Sultane yayi rantsuwa ba abinda zai fasa ko ya hana daura miki aure nan da watanni biyu masu zuwa.......amma da zabin kanki da zaki kawo........saboda haka karki bani kunya......yadda na tsaya akan al'amarin nan har aka fasashi......inaso ke kuma cikin qasa da wata biyun ki fidda miji ki kaiwa sultane kaman yadda ya buqata". Idanunta ta sake warewa a karo na biyu tana duban mammina a hargitse.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261 KO 08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 11* ___________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________
Bata ko tsaya neman flip-flops dinta ba ta soma taka tattausan tafin qafanta kan carpet din tana qoqarin cusa gashinta me tsaho da sulbi cikin bonnet da take mahadin kayan jikinta.
Yadda take saukowa daga stairs din a gaggauce ya sake sanya mammina cilla plan dinta da qara masa wani adadi.
Ido ta lumshe tana sake budesu akan akhnan din,wani irin kishi yana ci mata zuciya. Har tana jin kamar wani ciwo ciwo na dunqulewar da zuciyarta tayi guri daya.
Wani irin sassanyan kyau yarinyar ke dashi,kyan data tabbata banda wasu dalilai ba abinda zai sanya akhnan ta rufa shekaru goma ba tare da an aureta ba zuwa ga ahali mafi daraja da sukafi na mahaifinta. Ita kanta akhnan tana mata kyau,saidai kyan yana tsaye mata a rai da wani irin ciwo saboda tuna daga inda ta samo ASALIN KYAN nata. Daga gurin safeena ne......wannan kyan nata da tayi imani yana daya daga cikin abinda ya sanya ta rasa wannan martabar.......ta rasa wannan darajar.......ta kuma rasa wannan MATSAYIN da TAMBARIN na MATAR FARI a gurin sultane.
Bayan kyan ya mata wannan sanadin......wannan KYAN HALIN da a wajenta ba komai bane face zallar kissa da kisisina ya sake zame mata silar qara rasashi a KARO NA BIYU,ya sake cillata can nesa da matsayin zamowa MATA TA BIYU ga sultane din.
Ware idanunta tayi akan akhnan sanda take kusa isowa da inda take. Tuna baya kadan da tayi ya sake rura wata sabuwar wutar a zuciyarta. Ta zubawa akhnan idanu,tana tuna fuskar safeena da wani lokaci zaka ganta shimfide akan fuskar akhnan din.
Sau da dama tana mamakin kanta na yadda ta tsaya bin akhnan ta wannan doguwar hanyar. Tana ganin imaninta da yawa idan ta tuna shekarun data dauka kawai tana dakon ta dauki FANSA akan abinda tana iya aiwatar dashi cikin kwana uku kacal. To amma zuciyarta tasha gaya mata cewa.
"Daukar fansa yafi ciwo a sanda aka manta......yafi ciwo a sanda aka saki jiki.....yafi ciwo a sanda zamani da shekaru suka cilla......a sanda akayi imanin komai bazai canza ba......komai bazai kuma faru ba" Ta yadda da wannan magana ta zuciyarta.......kuma itace take mata jagoranci a dukka tsahon shekarun nan kawo yanzu. Safeena zallar muguwa ce.....muguwar da bata da kamanceceniya,salon muguntar da batajin idan zata dawo duniya ta mutu sau dubu hakan zai sassauta abinda takeji a kanta kota yafe mata,a sanda ta tabbatar rabuwa tazo tsakaninta da sultane......a sannan ma bata barta ba,bata bar sultane ba,saida tayi abinda ya sake jawo mata asarar matsayinta,ya kuma kusa sake jawo mata rasa sultane din rashi na har abada,ta yaya zata manta da dukka wadannan abubuwa?,ta yaya zata yafe cikin sauqi?,don dai ita ta kawo wawanci duniya?.
Yadda taga akhnan na kallonta ya sanyata sakin sassanyan murmushi
"Ina tunanin irin halin da zan shiga yanzu iwarhaka inda na rasaki......biftu......kina taba tunanin inda muradinki ya cika masarautar agadez gawa biyu zasu sallata?" Kai ta kada tana duban mammina. Batasan me yasa a wannan lokacin mammina ta gaza yarda ba ita ta aikatawa kanta haka ba?.
Ta lura da irin kallon da akhnan din ke mata,don haka ta nuna gefanta dab da ita.
"Zauna a nan" Bata musanta ba ta zauna din,mammina ta zuba mata ido tana tattara nutsuwarta a kanta.
"Munci sa'a,munci kuma nasara.......sultane ya janye maganan hakeem a kanki......labarin abinda ya faru ya isa kunnensu,don haka sun janye,nasara taki ce". Manyan idanun nan da sukan rusuna wani lokaci kamar name jin bacci ta ware gaba daya. Labarin yazo mata a bazatar da bata taba kawota nan kusa ba,ta rasa me zata yiwa mammina?,kawai saita shige jikinta gaba daya tana mata wani wawar runguma.
Wacce irin qauna ce haka mammina ke mata?,anya yadda mammina ke sonta ko mahaifiyarta idan ta dawo duniya zata qaunaceta irin haka kuwa?.
"Bansan me zance miki ba,bansan wanne kalar godiya zanyi miki ba" Akhnan ta fada idanunta suna cika da hawaye,tana jin kamar an warware mata wani qaton dauri da aka yiwa rayuwarta gaba daya.
Rungumar data matan tana mata kamanceceniya da sanya buhun qarfe na wuta a jikinta,amma hakan bai hanata shafa bayan akhnan din ba,kafin ta janyeta a jikinta a nutse da tausasawa tana cewa.
"Da abu guda daya tal zaki biyani". Tsaida idanunta akhnan tayi kan fuskar mammina tana kallonta.
"Sultane yayi rantsuwa ba abinda zai fasa ko ya hana daura miki aure nan da watanni biyu masu zuwa.......amma da zabin kanki da zaki kawo........saboda haka karki bani kunya......yadda na tsaya akan al'amarin nan har aka fasashi......inaso ke kuma cikin qasa da wata biyun ki fidda miji ki kaiwa sultane kaman yadda ya buqata". Idanunta ta sake warewa a karo na biyu tana duban mammina a hargitse.
Wani sabon tashin hankalin takeji yana saukar mata yana maye gurbin nutsuwa da walwalar data samu na sakannin baya da suka wuce. Wanne irin daurin talala ne wannan?......wanne irin d'aurin goro sultane yake mata?,wanne irin bahagon hukunci ne?,wanda banbamcinsa da hukuncin baya daya janye kadanne?.
"Mammina....." Ta kira sunanta labbanta suna rawa kadan,idanunta a kanta wani kalan tashin hankali yana sauko mata.
Tsareta mammina tayi da idanu.......irin abinda takeson gani shine a kwance saman fuskar akhnan din. Irin yanayin nan take buqatar gani,kuma ta ganshi,wannan shine abinda yake sake tabbatar mata da qarfi da kuma kaifin nasararta.
"....banaso kice komai biftu.....muddin abinda zaki fada din bai dace da hukuncin sultane ba" Ta qarasa maganan tana girgiza mata kai.
Itama kai take girgizawa tana duban mammina din.
"Mammina.....meye bambancin wannan hukuncin da wanda sultane ya janye?,.......ina zan samo miji cikin watanni biyu?.......ya manta wace akhnan?......khadeeja muhammad hammud?......ya manta cewa rayuwar wani d'a namiji bata cancanci ta gauraya da rayuwata ba?.....ya manta cewa ba musaye nakeso ba?......ba dakatarwa kadai nake buqata ba?.......nesantawa nakeso.......ya nesanta rayuwata daga rayuwar kowanne d'a namiji".
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Kai mammina ke girgizawa tana dubanta.
"A yanzu.....a kuma qadamin da sultane yake kai komai zai iya faruwa......wannan ra'ayin naki dole ki saukeshi.......wannan tsarin naki dole ki warwareshi......dole ki fuskanta kibi dukkan abinda yake tsarin sultane.......mun fara kaiwa wata gaba dashi......gab'ar dana fuskanci sai munyi da gaske zamu b'ulle......sai da takatsantsan zamu sha a hannunsa,saboda tunaninsa a yanxu ba nashi bane shi kadai.....ba shi kad'ai yake tunaninsa ba".
"Amma mammina........me yasa?....."
"Ya isa akhnan" Mammina ta furta a hankali tana canza yanayin fuskarta,sai kuma ta miqe tsam tana zame jikinta.
"Bazan yarda naci gaba da baqinjini ba......bazan bari aci gaba da yimin mummunan kallo ba......aci gaba da fassara tarin alkhairaina zuwa wani abu na daban ba.......kiji kiyi tunani da kyau.....amma karki manta......ko da zabinki ko babu zabinki kina iya zama rabon me rabo,kamar yadda sultane ya tsara hakan......yanzu dukka ragowar aikin yana hannunki......na gama nawa aikin" Mammina ta fadi a nutse sanda takai dab da qofar fita daga parlor din.
Bata motsa ba.....batayi kuma yunqurin fita ta bita kota dakatar da ita,don a karan kanta takeji duk wata kafa ta tunaninta ta toshe ta kuma tsaya mata cak.
Lallai tana buqatar nisan tunani da kuma nisan nazari......lallai tana buqatar kebancewa,tana kuma buqatar qure duk wani nisan tunani da zatayi akan MEYE MAFITARTA?.
★Idan tace zata iya wassafa adadin abinda takeji a jiki da zuciyarta tasan tabbas tayi qarya. Wani irin yanayi ne dake d'auke da wani irin tsukewa qunci da tashin hankalin da batasan ta ina zata bullo masa ba.
Abu guda daya ta sani shine.......ba zata taba bari zaituna taga rauninta ba,ba zata taba qyaleta ta fahimci tayi rauni tattare da ita ba.
Iya boye yanayin da zaituna ke jefata a ciki wani kalar tashin hankali ne da ta tabbatar qarfin jarumtar dake yawo a jininta ne kawai yake tallafarta ta wannan bangaren.
*_"BA'A QWACEMIN ABINDA YAKE NAWA NE NA ZUBA IDO NA QYALE,BA'A SHIGA GONATA BA TARE DA NA DAUKI FANSA BA......BAN IYA KAWAICI KO HAQURI BA......DUK WANDA YA SHAYAR DANI MADACI SAI NA SHAYAR DASHI GUBA.......DUK WANDA YA DANDAMIN ZAFI SAINA D'AN D'ANA MASA RADAD'I MAFI CIWO KODA YANA KWANCE CIKIN KUSHEWARSA......SHEKARU KO DADEWAR ZAMANI BASA HANANI KO SU MANTAR DANI AIWATAR DA FANSATA_*
Maganganu ne da suka zauna mata daram a cikin kwanyarta......cikin daren farkonta data soma kwana cikin masarautar agadez......ta kuma zama MATA mallakar sultane Muhammad.
Daren da ta fara sanya zaituna a idanunta madadin sultane......daren da kowanne ango shike marabtar amaryarsa....a daren zaituna ce ta marabceta........bayan ta sanyata ta dole ta amsa sunan AMARYA......duniya dukka sun kalleta da wannan sunan a madadin GIRMA DA MATSAYI na uwar gida da take dashi a qa'idance.
RABOn falaak ta tabbatar shi yayi rantsuwar daya tilastata a wannan daren ta tare a masarautar da sunan matar SULTANE. Banda wannan rantsatsen rabon......tako ta ina....ta kowacce fuska bata ga ta inda zata iya kutsen shigowa ba.
Har yau har kwanan gobe zaituna bata daina qoqarin binne sunan falaak......ta daina amsa sunan 'YA ga sultane ba......tana d'aga daraja tare da sunan akhnan BAWAI DON TANA SON HAKAN BA.....SAI DON FIR QARFINTA DA WATA SALON QADDARA TAYI.
Taba qofar da akayi shine abinda yaja hankalinta kadan,ta waiwaya tana ajiye ajiyar zuciya,idanunta ya sauka akan falaak.
Kamar ko yaushe,cikin suturar data suturce jikinta ko ina,rungume da daya daga cikin litattafanta na makaranta. Dubanta ta maida ga fuskar falaak din,kullum qara wani cika take da nutsuwa da haske. Tun daga sanda malamin ya shigo rayuwarsu taketa noticing canje canje sosai daga falaak din,saidai akwai wata fargaba kadan qasan zuciyarta dake sake fadada a ranta duk sanda ta kalli yadda falaak din take sake canzawa daga dabi'u zuwa halayenta. Bataso falaak din tayi SON MASO WANI......batason falaak din ita kuma qaddararta da jarrabawarta tazo ta wannan fannin.......
Kacokam ta canza course dinta na makaranta ta koma bangaren addini,wanda ada ba wannan ne zabinta ba.
"Momma.......nannie ca takeson magana dake" Ta fada tana duban idanun momma din. Kai ta gyada mata a hankali tana dauke dubanta daga falaak din,saidai maganan da falaak din ta qara yi ya dakatar da ita daga qoqarin daukan mayafinta da takeyi.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261 KO 08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 12* _________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX __________________________
"Momma.......nace idan ba damuwa.....me zai hana a dinga aikawa da sheikh haisam abinci?" Waiwayowa tayi tana duban falaak din.
"Shi yace yana buqata?" Kai ta girgiza a hankali.
"Aah.....hasalima naga me wada da daya daga cikin masu girkin sultane yakai masa shi......sannan lokaci lokaci tare sukanci abinci da sultane din.....kawai dai naga ya dace ne,kuma kaman girmamawa ce a matsayinsa na baqo na muhimmanci a wajenmu" . Idanu ta dan zubawa falaak din,tanaso tace mata aah......to amma tana ganin kamar barinta zai iya zama wata hanya ta alkhairi a nan gaba.
Ta aminta da nutsuwarta,dari bisa dari ba zata aikata abinda bai dace ba.....kaman yadda takeji akan sheikh haisam.......ta jima bataji wata irin nutsuwa me tarin yawa da tasiri akan wani dan adam.ba bayan shi.
"Ba kullum ba falaak.....lokaci lokaci".
"Kamar juma'a juma'a?" Ta tamba morsa safiyya cikin wani irin yanayi na zumudi.
"Ba laifi" Ta amsa mata tana kewayeta ta fice,zuciyarta kuma na sake bata tabbacin abinda take zargi.