Kenza eBookz

L u'u l u'u book 2 complete by huguma - Chapter 8

L u'u l u'u book 2 complete by huguma - Chapter 8

L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 8: L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 8. Lallai akwai wani al'amarin cikin zuciyar falaak…

3,303 words

Lallai akwai wani al'amarin cikin zuciyar falaak din,saidai bata sani ba,ita kanta ta fahimci hakan ko bata fahimta ba?. Koma meye zata kasance jajiryacciyar uwa da zata saita d'iyarta,ba kuma zata bari tayi wani abu da zai zubda kimarta da martabarta ba dama martabar gidansu gaba daya.

Da sallama cikin nutsuwa ta qarasa tana zama gefan nanny din. Ta amsa mata itama tana duban morsa din.

"Me yasa ana tsaka da magana zaki tafi safiyya?" Nanny ta fada tana duban morsa safiyya. Bata iya cewa komai da ita ba,don batasan me zatace matan ba. Bataso kuma ta buda baki abinda bai kamata ba ya fita a bakinta. Nanny tana da wani irin kima a idanunta......ba kuma zata iya manta qauna da kulawar data bata ba......bama ita din ba.....SAFEENA wanda qaunar data yiwa safeena ce ta gutsirar mata kadan daga cikin ta.

"Banyi tunanin haka daga gareki ba safiyya.......na sanki.....mutum ce ke me rama halasci da halasci.....mutum ce ke me tsananin girmamawa da kyautatawa........amma kuma karon farko kina nema ki manta ki take dukkan alkhairan da mammina tayi miki?......kinsan ciwon da gorin haihuwa yake dashi kuwa?". Ta fadi maganan tana duban morsa safiyya.

Idanunta ta lumshe sannan ta girgiza kanta a nutse,still bata iya cewa komai din ba,wannan ya bawa nanny daman ci gaba da magana.

"Akwai ciwo.....akwai kuma zafi me yawa safiyya....ko bare wanda baki sanshi ba ban zaci zaki iya masa haka ba ballantana matar data dauki jininki FIYE DA KANTA.....Duk duniya ta shaida haka......ta mata riqon da ko kanta akace ta riqe iya abinda zatayi kenan,saidai wasu kusakurai 'yan kadan da basu kai ayi mata hukunci dasu ko ko a qyamaceta saboda su ba......da kuma rufewar idanuwa da soyayya kan iya jawowa kan ko waye ma". Wani abu me tauri morsa safiyya ya hadiye da ya wuce ta maqogoronta da qyar.

Tana hange tana hasashe tana kuma ji a jikinta kamar akwai wani gagarumin yaqi dake tunkarota a gaba.......tana jin kamar akwai wani gagarumin abu da zai iya faruwa a gaba......wanda batajin tana da qwarin gwiwa ko qwanjin tallafarsa da iya nata qarfin.

Sake Imani takeyi,tana kuma sake gasgatawa gami da nutsewa cikin mamaki,da gaske MAMMINA TA ILLATA KOWA A GIDAN......MAMMINA TA YIWA TUNANIN KOWA ILLA......bata ji a jikinta shirunta na shekara da shekaru yana nufin komai daidai yake tafiya cikin masarautar........nuna kishinta tsakanin ita da ita da kwantaccen salon da ba wanda zai fahimta kawai bata tunanin ya GAMSAR da zuciyar zaituna.......ya kuma bata irin nutsuwar da takeso,ko kuma ya cike wannan ramin....wannan zuciyar da kuma wannan rurutacciyar wutar fansar data gani kwnace cikin idanunta tun a ranarta ta farko.

Murmushi ta saki a hankali,cike da wata nutsuwa da zata sanyaka kayi tunanin har zuciyarta abinda ke wakana kenan.

"Ko kadan......ban qyamaceta......ban toxartata ba,ban kuma hukuntata ba......koda karen daya rayu tare da safeena yafi qarfin wulaqanci a gurina.......kawai abu daya na sani......bana bari a wafce abinda yake haqqina ne a gudarmin dashi xuwa muhallin da komai zai iya kasancewa.......bana kuma iya zuba idanu haqqin JINI ya toxarta......bana kuma iya tozarta alqawura mafi girma da aka dauka a lokacin da ruhi ke bankwana da gangar jikin data kasance mafakarsa ta shekara da shekaru,yake kuma bankwana da iskar data kasance mahadinsa tsahon wanzuwarsa a duniya........zaituna zataci gaba da kasancewa UWA ga akhnan kamar yadda ta tsara hakan ya kasance.......amma hakan bawai yana nufin na koma baya bane ya shige na kuma saje da 'yan kallo da wadanda suka saki ragamar sarrafuwar tunaninsu a hannun wani........taci gaba da amfana da wannan damar......taci gaba da zama UWA ga akhnan......saidai kuma akwai guguwar da idan ta taso a nan gaba kadan......ba wasu hannuwa da zasu iya tareta.....na gode sosai da karamcinki nanny....ke din 'yar uwace ta gari ga d'an uwanta.....xan qoqarin yiwa zuciyata saiti amma a sanda ya kamata".

Ta sani....nanny din ta sani,akwai zaurance kalmomi masu harshen damo masu damar gaske cikin maganganun morsa safiyya.......saidai saninsu fahimtarsu ko warwaresu basu take buqata ba....salaama take buqata da wanzajjen zaman lafiya don dorewar shugabancin da mulkin sultane cikin nutsuwa da kwanciyar rai.

♣️★Wannan nazarin......da wannan nutsuwar da take buqata sune suka kwashe mata darare biyu cif ba tare data iya sarrafa tunaninta ta fidda maslaha guda daya a cikinsu game da hukuncin sultane ba.

Tana jin kamar kota ina a daure take.........bata sakeji daga mammina ba......bata kuma sake yo aike daga sashenta zuwa nata ba.....sai takejin komai kamar baya tafiya daidai,saita fara jin kamar ta rasa wani bango da zata jingina dashi......ba jimawa kuma ta fahimci mammina itace qarfinta......itace jigonta......itace qashin bayanta. A hankali ta sake tabbatarwa tana buqatar mammina a kowanne hali......tana buqatar shawararta......ita daya ce tayi imanin zata samar mata da mafita. Da wannan tunanin a wannan daren ta shiga wanka,ta kuma wanke kanta da hair gel dinta ma qamshin strawberry.

Maimakon ta busar dashi da tarin nau'ikan drayers din da take dasu kusan kala goma.....kawai sai taji a daren iska take buqata me kyau data fuskanci ita ke kadawa ta hanyar buda curtains din windows din dakin,iskar kuma dake tashi da wani dadaddan yanayi na qamshin qasa daga farkon damina.

Tanason yanayin,amma kuma tana tsoron damina......tana tsoro ruwan sama ya tabata da yawa,ta sani iska irin wannan tana bata wani irin nishadi,tana kuma rage mata nauyin zuciya sosai.....don haka sai kawai ta shirya kanta cikin wata cotton night gown fara qal,wadda tsananin haskenta yake kashe idanu.

Har qasa take,ta kuma suturce jikinta sosai,hakanan hannunta yakai har gwiwar hannu,saita dauki comb kawai bayan ya fesa turare ta kuma shafe tsadajjiyar fatar nan tata da designer cream dinta na dindindin.

Kyawawan idanunsa ya sake zubewa dukkaninsu saman screen din system din dake gabansa. Wanda ya dauki a qalla awa daya zaune cikin balcony din yana qoqarin zana abun hannun nata exactly kamar yadda ya ganshi. Baya son koda qwarzane daya daya gani a jikinsa ya canza idan aka tashi qerashi,tun daga adon dake jiki da kuma nau'in color dinsa girma da fadinsa yanaso ya kasance daidai da yadda ya ganshi.

Qaro hasken system din yayi,abinda ya sanya ya qara masa yawa a ido,dole ya sanya hannu qasan foldable table din daya dora system din,ya zaro farin glass din da yakanyi using lokaci lokaci idan hasken na'ura ya fara damunsa,ko buqatar sakashi ya tashi a wasu lokuta,musamman da eye glasses din ya kasance na musamman,don yana iya connecting nashi da wayarsa yayi receiving call ba tare da kowa ya gane waya yakeyi ba.

Idanun nasa ya janye yana lumshesu guri daya ganin komai ya zanu kaman yadda yakeso,relaxing bayansa yayi jikin kujerar yana jin yadda gajiya ke saukar masa saboda dadewar da yayi a zaune din. A hankali ya furxar da sassanyan iska daga bakinsa,a lokuta da yawa irin wadannan idan ya gaji,karatun qur'ani ne kawai ke bawa zuciyarsa dama gangar jikinsa wani irin hutu da nutsuwa,don haka a hankali yayi bismillah,cikin muryar nan tasa me zurfi dake kamanceceniya data sheikh afif muhammad taj ya soma karatu da sassauqar murya cikin surar da yafi so cikin suroron qur'ani.

A hankali take takowa zuwa farfajiyar veranda din saman nata,tana sanya hannunta tana warware gashin nata da suke sarqafe da juna. Sautin karatun da taji irinsa kwanaki ya fara sauka cikin kunnuwanta a hankali,saita ci gaba da takawa tana jin yadda karatun ke shigarta a hankali da wani irin yanayi.

Shuru tayi tana ci gaba da wara gashinta cikin wata irin mutuwar jiki data saukar mata daga shigowarta gurin,wadda bata shigo da ita ba,ta tabbatar daga fara sauraron karatun dake mata wani irin mugun dadi ne yanayi ya fara ratsa gabbanta.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

"What a beautiful sound" Ta furta can qasan ranta da qaramin turancinta da yaren faransanci ya rinjayeshi,saita taka a hankali zuwa saman daya daga cikin kujerun hutawa na alfarma dake wajen,zaman nata kuma a wajen sai ya sake kusanto mata da sautin sosai kusa da ita.

A nutse take sauraron karatun,kamar bata qaunar wani harafi ko daya ya subuce mata. A hankali zuciyarta ke wani irin sanyi,kamar bacewar walqiya ta dinga ji tunanikan dake cunkushe a kanta suna bajewa. Nutsuwa da daidaito yana samuwa cikin dukkanin tunaninta da zuciyarta.

Ta nutsu sosai ta kuma shagalta wajen sauraron sautin karatun tare da mamakin daga inda sautin yake fitowa. Daidai lokacin yakai qarshen surar ya kuma yanke karatun a hankali kamar daukewar ruwan sama,abinda ya sanyata daga kanta da sauri kaman me neman wani abu nata daya bace mata.

A nutse ya ware idanunsa,ya miqe ya zauna sosai jin sautin alamun shigowar saqo ta system din nasa,abinda ya bashi tabbacin duba saqonshi na zanen bracelet din daya tura ga SHAKUR shakur din yayi,sai ya zauna sosai yana maida idanunsa ga system din,saidai kuma idanunsa fadawa sukayi side line na system din nasa dake daukar masa duk wani motsi dake gaban ginin hagu da kuma damansa.

Yanayin motsin daya gani daga gaban veranda din nasa ya sanya jan arrow din ya dora saman camera ta farko ya budashi sosai,take ta bayyana tsaye cikin veranda din nata. Sassalkan gashinta da bai kammala bushewa ba ya kwanta sosai daga gaban goshinta kafadunta zuwa bayanta. Rigar ta zauna a jikinta sosai,saita maidata kamar wata 'yar tsanar roba da aka zauna aka yiwa kyakkyawan qira da zabin halitta me daukan hankali.

Juyawa tayi zuwa baya sannan ta sake juyawa zuwa gaba,abinda ya bashi tabbacin akwai abinda take nema kenan. A hankali ya zame idanunsa daga saman system din ba tare daya motsa komai nasa ba banda idanun ya maidashi kan ainihin veranda din nata direct. Cikin wani nutsuwa idanunsa suka sauka a kanta,sanda ta sanya hannunta tana tattare tulin gashinta tana daureshi tsakiyar kanta,waiko hakan zai bata daman sake jin sautin da qilan zai mata jagorar da zata fahimci daga inda karatun yake fitowa.

"Subhanallah" Ya fadi a hankali yana zare idanunsa daga kanta gami da saukesu saman keyboard na system dinsa yana sauraren wani bugu qwaya daya tal da zuciyarsa tayi daya aika jini me gudu da yawa zuwa sassan jikinsa gaba daya.

Shuru yayi yana sauraren kowanne motsi da amsawar da jikinsa yayi gami da yanayin bugun zuciyarsa,can qasan ranshi ayar nan da Allah madaukakin sarki ya saukar zuwa ga muminai maza da mata kan runtse gani tana masa yawo akai(lowering gaze).

Numfashi yaja sosai yana saukeshi,yana kuma qara imani da gasgatawa cewa babu kuskure cikin dukka umarnin da Allah ya bayar. Akwai fitina me yawa cikin KALLO kawai......shi yasa Alla sw t yayi qoqarin datse fitintinu ta hanyar kallo da dama wajen umartar bayinsa su runtse ganinsu.

Numfashin ya sake saukewa a karo na biyu........wani baqon yanayi ne da bai taba jinsa ba akan kallon kowacce diya mace......duk da kasancewarsa ma'abocin kame ganinsa daga kallon dukkan abinda yake ba halalinsa ba.....amma wani lokaci yanayin aiki ko tafiya yakan hadashi da matan da ba musulmai ba da suke shigar data sabawa shari'a,amma bai taba jin komai game dasu akan wannan ba.

"Dole ka sake nisantarta" Zuciyarsa ke gaya masa tana kuma tariyo masa yadda arashi ya dinga hadasu shi da ita da irin kusancin daya kusa zame masa alaqaqai kowanne kwanciya baccinsa.

Kauda idanunsa ya sakeyi daga kan camera din,yana miqa hannu cikin qwarewa yayi cancel front camera din dake kawo masa hoton gaban balcony dinnata ba tare daya kalli system din ba. Sai daya samu wannan tabbacin sannan ya maida dubansa kai yana ci gaba da aikin ba tare daya sake maida idanu ko hankalinsa a kanta ba.

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261 KO 08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 14* __________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________

Ba wani naqasu ko kasawa da saamee ke dashi......ta cika macen da za'a sota da dukkan quality dinta,to amma hakanan baisan me yasa yakejin a ransa bata hau mizani ba. Ya jima yana bincikar kansa me yasa yakejin kamar saamee ta rasa wani abu?.....me yasa yakejin kamar akwai wani hali dabi'a da yake nema da saamee ta rasa?. Ya dade yana tambayar kansa indai har saamee nada wani dabi'a ko halayya data rasa.....wacece?.....wacece zatayi?,wacece kuma zata cika?. Amsar daya ce har yau BAI SANI BA.....BAISAN ME TA RASA BA.....BESAN KUMA ME TAKE NEMA BA.

Abu daya daya sani wanda baisan ko yana da alaqa da ganin gazawar saamee ba bawai don ta gaza din ba?..... Mutum ne da komai yafison ya mallakeshi da JARUMTARSA......komai yafison yayi YAQI kansa bawai ya sameshi daga kwance ba. Jininsa na GWAGWARMAYA NE......yana ganin komai akayi yaqi a kansa yafi zama da kima da daraja.....anfi kuma riqeshi da dukkan qarfi.......har abada kuma idan zaka kalli wannan abun zakafi tuna kanka da sunan JARUMI bawai LUSARIN NAMIJI BA.

Idanunsa da suka shanye ya daga a hankali,daidai sanda yaga gilmawar inuwa ta bayan labulen dake tsakanin parlor din Bedroom din nasa. Kamar gilmawar walqiya komai ya bace,ya zubawa gurin idanu a hankali kafin kuma wani miskilin murmushi ya subuce masa.

"Wannan shine iya zurfinka?......wannan shine iya qwarewar taka?" Ya furta can qasan ransa yana gyada kansa da cikakkiyar nutsuwa sannan ya miqe yana takawa a nutse yana nufar parlor din.

Baiyi zaton komai zaizo da sauqi har haka ba.....bai dauka kuma zatayi zaben lusarin me binkice irin wannan ba. Amma ta wani gefen sai ya mata uzuri,tabbas ya sani,inda tasan girman had'arin da yake dashi......dan sanya idanu na gaske zata nemo ta hadashi dashi ba wannan qaramin halittar ba........amma ko meye shi ya masa daidai......zaiyi wasa da hankalinta yadda ya kamata.

*AKHNAN*

Komai batace musu ba,illa kunnuwanta kawai data basu tana sauraren mitarsu a kanta sanda birra ke miqa mata kayanta tana shiryawa da kanta.

Tanaso komai zasuyi cikin daren nan da mammina suyishi a qare.......mafita take nema,ba kuma mafita irin wannan da sultane ya bata ba. Mafitar da zata fita gaba daya daga cikin sharuddan sultane,taci gaba da rayuwarta kamar yadda take a baya.

Duk kusan mita da qorafinsu akan ta koma sahel couture ne. Jinsu kawai takeyi.....yadda takeji da kamfanin.....yadda kamfanin yake qunshe da wani irin tasiri a rayuwar qasar niger gaba daya,da yadda aikinta tuquru yakai kamfanin wani tudu da bata taba tsammani ba ko a mafarki abun ya bata tsoro. Daidai da sultane abun ya daure masa kai.......ya kuma sake daga darajar akhnan a zuciyarsa da idanunsa. Wasu irin tarin nasara da ninkuwa da komai na kamfanin yayi wanda ba wanda a cikinsu ya taba hango masa nasara irin haka a kurkusa.

Sahel couture wata kyauta ce ta ba zata da sultane ya taba mata a rayuwa. Ruhin dukiyarsa gaba daya,kuma sirrin dukiyarsa,ba zatan data girgiza mutane da yawan gaske,ta sake kuma haska girman matsayinta a zuciyar sultane din,wanda hakan ya sanyata alfahari me yawan gaske. A wannan lokutan bata taba tunani ko kawowa ba akwai wani abu me suna DAMUWA da yake da tasirin nesanta da Niamey ma gaba daya bare sahel couture din kansa ba.

A nutse ta karbi bakin mayafin da birra ke riqe dashi,ta kuma soma Rolling saman sumarnan tata me sulbi da data kwanta luf saboda yadda birra ta gyarata sosai ta matse mata ita cikin siririn band da bazai takurawa darenta ba.

"Ba wani tunani nawa da yake daidai a yanzu.....ba wani sauran qwarin gwiwar data ragemin da zata ban damar jagorantar sahel couture yanzu.....mammina tasan da hakan,ta kuma gaya miki ke kikafi cancanta kici gaba da jagorantarsa......bansan me kike jira ba" Tayi maganar a nutse da tasirin izzarta cikin fitar kowanne lafazi daga labbanta.

"Kinsan wani abu?" Shehnaz ta fada tana qarewa akhnan kallo,wadda tayi wani irin sassanyan kyau,kai ba zakace nan da wanni zata kwanta ba,saika dauka ta shirya ne don fita wani guri daban a wajen gidan.

Akhnan bata amsa ba,sai aisa data dubi shehnaz alamun ita suke saurare.

"Ke kika maida komai me zafi akhnan.......amma inda zaki sassauta zuciyarki......wallahi na hango miki wani kyakkyawan zabi....zabin da nake da yaqinin zaki samu nutsuwar da baki taba hange ko tunani ba......sheikh haisam akhnan......."

Wata irin wawiyar juyowa akhnan din tayi......sannan ta zubewa shehnaz idanun nan nata dake da surkin kwarjini irin na d'iyoyin da sarauta ta game jininsu.

"Koma meye kikeson fada abu mafi alkhairi ki barshi a bakinki.......idan kuma har shaye shaye kika fara shehnaz daga yau ba zaki sake marmarin kusantar irin abinda kika sha ba ballantana ya suranta miki qazamin tunani irin wannan har abada.........ba wani namiji daidai dani a yanzu a duniyar nan......bansan ko gaba ba,koda qaddara ta sanya na amsa sunan MATAR AURE.....to koma waye wannan mijin....." Sai bata qarasa ba ta girgiza kai da wani irin yanayi daya tabbatar musu da tarin abubuwan dake binne cikin zuciyarta,take ganin baki yayi kadan ya furtasu daidai.

"Zanje naga mammina" Iya abinda ta fada musu kenan ta soma takawa tana fita a dakin.

Cikin qasaita da jinta cikin cikakken tsaro take takawa a filin da zai kaita kai tsaye zuwa sassan mammina din. Wata irin iska ce me ratsa jiki take kadawa gami da kai kawo daga kowanne kusurwoyin duniya.......idanunta ta zare daga duban qasaitattun katangun dake zagaye dasu,wadanda iya kallonsu kawai na sake sanya mata jin izza da qasaita. Tabbas.....lallai inda za'a tasheta a wata rayuwa ta daban,a kuma bata zabi,babu shakka zata yita zabar kasancewarta cikin ahalin SARAUTA.

Iya ginin da masarautar agadez ta mallaka da wani irin tsari da aka zamanantar dashi tayi imanin zai wahala a samu tsarin masarauta tasu kaf Africa.

Sararin samaniya ta maida dubanta,duk da cewa duhun dare mamaye saman gaba daya,hakana bai hana hasken farin wata nuna hadarin dake lullube a saman ba,hadarin da ya jima yana haduwa,kuma a yau kamar yana nuna ya tumbatsa da yawa,nan da wasu mintuna ko awanni yana iya hade jikinsa dukka tsaf,ya kuma jirayi umarnin sarkin sarakuna wajen shayar da al'ummar agadez dama na nijer gaba daya ruwan farko.

Iskar ta mata dadi qwarai.....kamar yadda yanayin ya mata dadi.......saidai hakan bai hana kalaman shehnaz yin suya sosai a qirjinta ba.

Iya fitar furucin daga bakin shehnaz sai takejin kamar ta qasqanta......kamar neman kai ake da ita......yanzun har araharta takai haka?......me yasa sultane yakeson lallai sai ya zabtare dukkan wani girma nata da darajarta ya watsar?,har wadanda kimarsu da martabarsu batakai ba suyi tsammanin sunkai tsaikon da zasu kusanci iyakokinta?. Ba wani taku da zatayi ba'a zube a qasa bisa saman gwiwoyi ba cikjn gaisuwar ban girma,wanda ko daya bata amsa ba sai birra dake amsa mata.

Wannan din dabi'arta ce......kaman yadda yake girmanta ne......baka isa tana takawa a farfajiyar guri ba kaima naka qafafun suci gaba da takawa ba,zaka jira har sai sanda ta bada baya ko tabar gurin. Girman da dukkan al'ummar masarautar ke bata banbancinsa kadanne dana sultane,kowa fata yake......qoqari yake ya kyautata mata da dukkan girmamawa saboda farincikin sultane.

Tun daga qofar mammina ta farko masu tsaron qofar ke janyewa gami da sauke idanunsu qasa tare da kaucewa kallon akhnan din da yake kasancewa zunubi ne ga kowanne d'a namiji cikin masarautar muddin ba ita ta lamunce maka hakan ba.

*MAMMINA*

Zare wayar dake kunnenta tayi a nutse tana duban bakin qofar inda yalwa ke durqushe ta yadda bata iya hangota.

"Ina neman izinin yin bayani idan an lamuncemin haka" Ta fada da wani yanayi da ya gayawa mammina akwai labari a bakin yalwa din.

"An baki" Ta fada tana gintse wayar gami da ajiyeta.

"Gimbiya akhnan na dab da shigowa sassannan". Shiru mammina tayi......kafin wani shu'umin murmushi ya subuce mata.

Readers Also Read

More by Huguma