L u'u l u'u book 2 complete by huguma - Chapter 9
L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 9: L u'u l u'u book 2 complete by huguma Chapter 9. Tun kwanaki data diba mata a ranta basu cika ba sai gashi…
3,370 words
Tun kwanaki data diba mata a ranta basu cika ba sai gashi akhnan din ta gaza jurewa ta nemota?. Lallai ba shakka ta wannan fannin tayi tinjimin aiki da ya kamata ta yabawa kanta da kanta. Tayi aikin daya zame mata makami mafi muni a idanu da zuciyar morsa safiyya......ta yadda bata yadda za'ayi morsa safiyya ta iya karbe akhnan daga hannunta......har gaban abada,koda itace tace akhnan din ta koma hannun morsa safiyya din,ta juya akalar girma da biyayya shawari da matsayin uwa data bata.
"Banaso kai tsaye a barta ta iskeni......banaso ta samu ganina kai tsaye cikin sauqi kaman yadda yake a baya". Ta fada fuskarta na sake fadada da fara'a.
"An gama" Yalwa ta fada tana miqewa da hanzari da kuma sassarfa tana sauka qasa.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Sanda tazo matakalar qarshe akhnan na shigowa. Ita daya ce,ta baro birra a baya,don birra din tazo iyakacin shingen da ba wanda ya isa ya d'arashi cikin bayi ko hadimai.
Qasa yalwa tayi da kanta,duk da yadda zuciyarta ke bugun uku uku amma idar da abinda ran uwar gijiyarta keso ta kuma tsara tamkar bauta yake a wajenta.
"Allah ya taimaki hasken agadez......Allah ya baki yawan rai da nisan kwana......kamar giwa ta samu kwanciya nake zato......ko za'ayi haquri a koma zuwa gobe?". Cak akhnan ta tsaya daga daga qafarta da tayi zuwa stairs na farko sannan ta waiwayo ta zubewa yalwa idanunta.
"Kinsan dawa kike magana?" Ta furta cikin izzar data kada hantar yalwa.
"Kinsan me kike cewa?......."
"Tuba nake ranki ya dade,ayimin aikin rai" Ta fada muryarta da labbanta dukka suna rawa saboda tsananin tsoron akhnan din daya shigeta. Kamar ba zata sake cewa komai ba......amma saita jinjina kai ta juya taci gaba da takawa.
"Koda wasa karki sha'awar xaki sake maimaitawa"
"Na tuba in sha Allahu" Ta amsa mata tana jin gwiwoyinta kamar ba zasu dauketa ba.
Duk taku daya da takeyi ranta yan sake suya,yaushe tayi arahar da kamar yalwa wai itace zata mata iso?,iso fa akan mammina......mamminarta na da bau irinta kaf rayuwarta.
Kaman yadda batayi sallama ba bayan ta canko dakin da mammina din zaune,sai kawai ta jingina da qofar dakin tana harde hannuwanta a qirjinta,fuskarta shimfide d wani nannuyan yanayi.
Taji shigowartata,amma ba lokacin nuna batasan ta shigo din ba. Tana so ta sake shuka wannan qagautar a zuciyarta......tanaso komai ya kasance cikin shimfidadden tsarin da idan ta hau ha zancan sauka.....shakku ko kokwanto. Tanaso komai ya kasance daidai ta yadda zata iya fito na fito da dukkan wanda yace zai kawo naqasu ko gyara a tsarin.....tanaso akhnan da kanta da kuma hannuwanta tayi mata yaqin da ita ya cancanci ta yishi ba tare da ita din ta daga koda yatsarta ba.
Tasan tunda ta shigo ta tsaya ba zatayi magana ba,ba kuma zatace komai ba,don haka ta waiwayo kamar me shirin daukar wani abu,saita zube idanunta a kanta.
Fuskarta shimfide da alamun mamaki take dubanta.
"Biftu......yaushe kika shigo?". Kai ta girgiza a hankali,tana iya hangen taruwar ruwan hawaye saman qwayar idanunta dake da wani sheqi kaman an diga mai a cikinta,idanun da idan ka kallesu zaka dauka tun asali hawayen ne a ciki,saidai yanayin halittarsu kenan.
Tashi tayi daga jinginar da tayi ta tsaya da qafafunta tana duban mammina din.
"Ni nazo.....nazo mammina,tunda ana dab da shiga tsakaninmu" Ta qarasa maganan tana jin duk wani rauni nata yana dawowa sabo,muryarta na karyewa,alamu suna gaya mata kuka zai iya qwace mata daga yanzu zuwa kowanne lokaci.
Kai mammina ta girgiza,ta miqe a nutse ta soma takowa zuwa inda take. Hannayenta ta riqe a tausashe,ta kuma sanya idanunta cikin na akhnan ta fara magana.
"Bazanci gaba da kusanta kaina da gurin da zan zama abar zargi ba......ko meye zanyi cikin rayuwarki na alkhairi biftu cikin zargi nake gurin morsa safiyya da ire ir.......".
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261 KO 08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 15* __________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ____________________________
"To tayita zargin mana......uwata ce?.....ko ta haifeni ne?....mahaifiya daya ce mutum keyi a duniya,sauran saidai su zama uwaye kawai......tawa mahaifiyar kuma ta rasu.....ke na zaba.....ke kika cancani ki maye gurbinta,harma gurbin da yafi nata din,don kece kikayiwa rayuwata komai da dukkan kulawa garkuwa da kuma gata". Idanunta mammina ta lumshe tana budesu lokaci guda. Wani abu me dadi taji yana rantsa kwanyarta yana sake sanyaya mata zuciya. Iya wannan aikin kawai da tayi yana sake gaya mata ita din JARUMA ce.....me jumurin jiran shekaru dubunnai domin wanzar da fansa a inda ya dace.
"Sultane fa biftu?....kin shirya fiddani kunya?". Hannuwanta ta zame daga cikin na mammina,ta soma takawa tana zarcewa cikin dakin gami da barin mammina a tsaye a nan tana fuskantar qofa.
" Na shirya fiddaki mammina.....saboda ke daya TAK!......saboda in saka miki farinciki da sadaukarwar da kika dade kinamin......amma ban shirya samar da mafita ni daya ba.......kin barni nayi aikin da bazan iya yinsa ni kadai ba......kin sani idan ba mammina ba akhnan?" Takai qarshen zancanta da sigar tambaya tana kuma waiwayowa gami da duban mammina duk da cewa har yanzu mammina din tana tsaye ne tana fuskantar qofa ta bawa cikin dakin baya.
Dole murmushi ya subucewa mammina din. Ta sake yarda tabbas taci galaba tako ina ta wannan fannin......ta mallaki halitta mafi soyuwa a zakutan ahalin guda biyu.....halitta mafi soyuwa qirjin macen da data kasance MAQIYIYA ta biyu wadda ta maye muhalli da gurbin maqiyiyarta ta farko.
Ta sani......akhnan ba zata iya wani motsi ba cikin rayuwarta.....akhnan ba zata iya yanke kowannw hukunci ba cikin rayuwarta......akhnan bata da wani zabi cikin rayuwarta face abinda ta shirya ta kuma dorata a kai.....a haka ta raineta......a haka ta girmar da ita don ta dace da irin wannan yanayin da wannan lokacin da suke ciki A YANZU!.
Sai data tabbatar ta maida yanayin fuskarta yadda ya kamata ta kasance sannan ta waiwayo tana takawa da salon tata qasaitar gami da dawowa cikin dakin.
Dukkanin hannuwanta akhnan ta riqe tana mammina din da wani irin rauni da tsaf zaya karya zuciyarta banda zuciyar tayi wani irin nisa da koda alamun kira bataji ballantana sautinsa.
"Na baki wuqa da nama mammina......ki yanke duk abinda kike ganin ya dace.......ki zabarmin mijin aure......indai hakan shine burinki.......na tabbatar bazan cutu ba......ba kuma zaki zabamin wanda zai cutar da dukkan burika da mafarkaina ba".
Hannu mammina ta sake zamewa tana kada kai gami da rabe akhnan din zata wuceta.
"Sultane ya zaba miki mazaje masu yawan gaske akhnan,dukkaninsu baki karba ba,shin wacece mammina da zata aikata hakan?.....morsa safiyya ita yafi kamata ki bawa wann....."
"Mamminaaaaa......" Ta kira sunanta da wani hargitsatsen yanayi. Da gaske har cikin jini da tsokarta bata qaunar shiga ko rab'ar matar cikin dukkanin lamuranta. Kiran sunanta kawai a inda take tsaye yana sanyata tana jin kamar komai nata zai tabarbare ne.
"Da sultane da morsan dukkaninsu ke na zaba a cikin su.....zakimin wannan alfarmar ko bazan samu ba?" Ta fadi kanta tsaye sarautarta tana motsawa.
Sosai wani abu yake sake kwanciya cikin ran mammina........tana jin dadin yadda komai yake wanzuwa......amma a wannan taqin bata shirya amsa komai ba.......tanason komai ya zamana wankakke ne daga zargi,don haka ta girgiza mata kai kanta tsaye,fuskarta na nuna lamu alamu na bacin rai.
"Baza yi ba biftu a wannan karon".
Cak ta qame a wajen,kwanyarta na cika da tarin mamaki. Tana duban mammina dinne amma tana ganin kamar ba mammina dinta ba?. Me jiran kokenta a kullum don ta share mata hawaye?. Me zaman jiran jin matsalarta ta kaudar mata da ita?.
Wadannan mutanen dake kai kawo a ranta zuciyarta na sake tabbatar mata da sunyi nasara,su suka shiga tsakaninta da mammina dinta.
"Shikenan......zanje nayi duk abinda naga dama......rayuwata ce" Ta fada kawai a taqaice sannan ta juya da wani irin fusata tana laluben qofa.
Shuru tayi tana rufe idanunta,ta kuma zurfafa gami da aika kaifin jinta can nesa.
"Daya....biyu.....uku....." Taci gaba da irga takun akhnan,gami da hasashen saukarta daga stairs din zuwa qasa. Bata bude idanunta ba,bata kuma dakata da lissafa takun ba har sai da ta lissafa taku talatin da biyar cif......abinda yayi daidai da isarta dab da sassan nanny sannan ta juyo da sassarfa ta mara mata baya,so samu ta hada da kiran sunanta.......amma abune da zai zama wani irin cikin birnin iko da mulkinta,don haka sassarfar kawai ta hada da ita,tana da tabbacin zata cimmata a daidai inda lissafinta ya tsaya.
Kusan duk inda zata gifta duk da darene kauce mata hanya suke,sannan su sadda kansu cikin girmamawa da ganin yadda giwar sultane din ke tafiya da salon sassarfa.
Sai da idanunta suka fara hangota sannan ta fara kiran sunanta,kiran daya isa kunnen akhnan din,ya kuma sanyata tsaiwa cak duk kuwa da cewa so samu ta wuce ba tare data tsaya sauraren kira mammina din ba.
Dab da zata isketa nanny ke fitowa daga nata sassan,da alama ziyarar data saba fita a daidai wannan lokacin zataje,saita dakata tana duban akhnan,kafin ta maida dubanta ga mammina dake qarasowa gurin d wani irin sauri daya fita daga al'adar tafiyarta.
Kafin mammina ta iso tuni nanny ta sallami dukkan hadiman dake tare da ita,ta kuma sanyasu su tsaida wucewar kowa ta gurin har sai sun bar gurin,ta maida dubanta ga akhnan. Ita takeso ta fara tambaya.....amma ta tabbatar a yanayinta ba zatace komai da ita ba koda zasu shekara a gurin,don haka ta maida dubanta ga mammina.
"Lafiya zaituna d'iyarki take?". Kai mammina ta juya cike da zallae alhini tana duban nanny. A hankali ta sake sanya qafarta gaba tana barin gurin,b wanda ya sake tsaidata tsakaninsu sai kallo da suka bita dashi,kafin mammina ta tattara idanunta akan nanny
"Rigimar biftu na neman zautani nanny......ban sani ba ko ke zaki iya fahimtar da ita?" Kai nanny ta girgiza tana duban akhnan data fara nesa kadan dasu kafin ta sake kallon mammina.
"Duk wani abu da kika kasa fahimtar da biftu bana tunanin akwai wanda zai iya......bana tsammanin akwai me ita sarrafata".
" So take lallai lallai ta azamin nema mata mijin auren daya dace da ita.....ki duba wannan girman al'amarin nanny,indai ba baqinjini takeson qaramin ba?" Mammina ta fada da wata kwantacciyar murya dake nuna karaya sosai cikin sautinta.
Murmushi nanny ta saki tana dafa kafadar mammina.
"Indai don wannan ne.....banga wani aibu a ciki ba,idan ana lissafin wanda yafi kowa sanin ciwo da zafin haihuwar biftu idan aka cire safeena kece ta daya......hakan da tayi ya nuna ita din d'iyace 'yar gaske da tasan girman halacci......maza kiyi hakan indai shine zai daidaita tsakaninki da d'iyarki". Idanu mammina ta zubawa nanny,a saman fuskarta shakka kokwanto da rauni suna yawo,can qasan zuciyarta kuma wani shimfidadden farinciki ne zallah gami da taya kanta da kanta murnar samuwa da kuma tabbatuwar nasararta.
Nanny ta fahimci kamar maganan bata gama zaunawa mammina ba,don haka ta motsa tana yiwa shema'u hadimarta alama da hannu ta qaraso.
"Kibu biftu,ki shaida mata ta dawo zuwa ga sassan mammina.....injini".
" Zan sameta nanny......ta dauki zafi,rabu da ita" Mammina ta fadi tana soma takawa tana bin gwadaben da akhnan ta wucesun.
Da kallo nanny ta bisu,murmushi yana fita a fuskarta. Bata taba ganin qauna irin ta mammina da akhnan nan ba....qaunar da zata iya rantsewa koda tsakanin wasu 'ya'yan da iyayensu na asali da suka haifesu babu ita.
Batasan adadin abubuwan data saqawa zuciyarta ba zata aiwatar daga daren yau zuwa gobe ba. Ta riga ta zartarwa kanta a goben zata bar agadez zuwa Niamey,kuma ba zata sake lamuncewa kowa ya ganta ba. Koda sultane dinne,koda ita mammina din ce.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Dafa kafadarta da taji anyi shi ya tsaidata. Tasan mutum daya ce tak ta isa tayi hakan a gareta,don haka tana waiwayo ta fada jikinta ta rungumeta tana sakin kuka.
"La....la....la,wanne irin abun kunya kike shirin bari?,hawayen sarauniyar agadez haka a fili a araha?" Mammina ta fada tana goge mata fuskarta dake kwance saman kafadarta. Wani qwarin gwiwa taji yana hauro mata kamar yadda ta saba ji.......tabbas mammina itace qwarin gwiwarta. Duk wani pattern da take rayuwa akai tsarin mammina ne. Ta nuna darajar matsayin da Allah ya bata,ta nuna mata girman da take dashi......ta karantar da ita cewa ITA TA MUSAMMAN CE.....tana da banbanci da sauran yara......tana da banbanci da sauran duk wani halitta dake rayuwa cikin masarautar. Wannan motsa mata izzar tata da tayi ya sanya ta hadiye kukanta,ta kuma bi mammina wadda ke riqe da hannunta tana takawa da ita zuwa wani kebantaccen guri dake da tarin kima a gurin mammina dama duk mutumin da zata gana dashi a gurin.
Hannayensa zube cikin aljihun wandonsa yana nazartar gurin cike da tarin mamaki. Yana da kusan dukkan map na gidan amma bai taba lura da wanzuwar gurin ba.
A yanzun da yake nazartar gurin da idanunsa da zaka dauka a rufe suke.....yana iya hangen yadda gurin zai iya linking nasa da wancan kebantaccen dakin ajiyar da ya zama guri na biyu da yake buri da muradin shiga ya duba wasu abubuwa da jikinsa ya jima yana bashi akwai bayanan da zai iya buqata cikin gurin.
Lokutan da agogo ke bashi yakeso yayi amfani dasu a tsakanin lokutan,ya tabbatar yana cikin lokutan da dan bibiyarsa ba lallai ya sake kasancewa dashi ba har zuwa awa daya a gaba. Zai iya ci gaba da kasancewa dashi daga awa dayar har zuwa awannin biyun da zai samu tabbacin ya kwanta......daga nan kuma zai dora aikinsa ne bayan ya tabbatar asubahi tayi,wadannan sune hasashen jadawalin lokutan daya tabbatar zaiyi amfani dasu gurin bibiyarsa. Bazai dawo nan kusa ba saboda yayi motsin da ya fuskanci yaja hankalinsa har ya miqe ya maida qofarsa ya rufe A ZATONSA baisan cewa TARKO bane kawai haisam din ya D'ANA MASA don tabbatar da cewa sun fara aiki da umarninta?.
Motsin sawayen da yaji ya sanyashi sake nutsuwa da kyau......muryarta kuma ta zama abu na farko daya fara shiga kunnensa.
"Kin taba ganin inda uwa ta iya qyale yarinyarta tasha wahala?.....kin taba ganin inda d'iya tayi fushi da uwarta?". Ya haddace muryarta da kyau,sautinta yana da banbamci da sauran sautukan da yake ji cikin masarautar,duk da yadda yake qure qoqarinta gurin daidaita harshenta dana kowa su saje a ma'auni guda daya......ma'aunin da sai kana da qwaqwalwa da fikira irin tasa zaka iya sansani banbance banbance a tsakanin abinda aka gauraya guri daya.
Ta ganshi a ranar nan,a yanzun kuma bazai zama lokacin daya dace ta sake ganinsa ba,don bai shirya ajiye zargi ko kokwanto a kansa a zuciyar kowa ba,don haka ya taka a hankali ya shiga tsakanin bishiyar dogayen yaro masu tsahon gaske guda biyu dake gurin.
Wayarsa ya zaro a hankali jin alamun shigowar saqo,ya rage hasken sosai yana duba saqon daya shigo masa. Bobbo muhammad dawud ne,ya sani akwai tattaunawa da zasuyi,duk da ta chart ne ta kebantacciyar manhajar da sukanyi musayar tattaunawa,amma bai dauka zai nemeshi haka da wuri ba. Tsaiwarsa ya gyara yana maida hankalinsa kan wayarsa,ya soma maida messages din bobbo din,duk da ba hakan yaso ba,yaso yana daki a nutse,amma idan yace zaya jira kaucewar kowa baisan yawan tsahon lokacin da zai dauka ba.
"Zauna a nan ki saurareni da kyau" Mammina ta fada tanawa akhnan nuni da daya daga cikin kujerun dake ajiye a gurin.
A nutse ta qarasa ta zauna,sannan mammina din ta taka itama zuwa kujerar dake daura da ita.
Dukkanin hannuwan akhnan ta kama ta aza saman cinyarta,ta sanya idanunta sosai cikin nata.
"Inaso ki saurareni sosai da kunnen basira......inaso ki bani duk wani hankali naki da kike dashi" Kai ta gyada a hankali,batajin akwai wani sauran abu da mammina zata buqata daga gareta ta kasa yi mata shi.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261 KO 08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 16* ___________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX __________________________
"Kisa a ranki ni din tamkar mahaifiya nake a gurinki ba UWA ba.......ba wani tsanani da zaizo da zan iya juya miki baya.....to amma dole wataran kaza take taka d'anta badon bata sonshi ba.....aah,saidai kawai ta bashi wata tarbiyya.....idan nace a komai na rayuwarki zanci gaba da zaqewa.....zanci gaba da kasancewa a gaba gaba hakan zai iya zame mana matsala......" Takai qarshen maganar tana sauke numfashi.
"Duk wank hukunci naki da zabi naki ina tare dashi biftu......duk wani kalan abu da zai saka rayuwarki a nishadi ina tare dashi biftu.......zakiyi aure kamar yadda sultane yake da buqata.....zaki aure amma zaki auri mijin da zai zamana qarqashin juyawarki umarninki da kuma haninki......zaki auri mijin da kece zaki shirya ki kuma tsara kalar rayuwar da kike buri da mafarki......mijin da bai isa ya sakaki ko ya hanaki ba,zai kasance qarqashin sarrafawarki". Idanu akhnan ta lumshe tana sake budesu lokaci guda hade da wani irin lafiyayyen murmushi.
Lallai ba shakka duk wanda ya rigaka kwana dole ya rigaka tashi.......duk wanda ya girmeka ya girmeka har abada. Abadan duk duniya bata da wani masoyi daya d'ara mammina.....a wannan gabar har cikin tsakiyar zuciyarta da ruhinta tana jin cewa koda sultane SAI YA JIRA a soyayyar mammina a gareta......ta sake gasgata cewa idan ba MAMMINA babu ita AKHNAN.....tabbas ba zata taba kai labari ba idan ba mammina na gefanta ba.
To wai me yasa tun baya ita batayi irin wannan tunanin ba?......namijin da zai zama miji a idanun sultane kawai amma cikakken HOTO a idanunta da bazai hanata aiwatar da komai da ta tsara cikin kundin rayuwarta ba?.
"Kina jina?" Muryar mammina ta dawo da ita daga tunanin data fara nisan zango a cikinsa. Kai ta gyada mata tana sauke blue eyes dinta da rashin wadataccen haske ya sake sanyawa ya zama wani me qyalli da daukan idanu.
Sama ta daga kanta mammina din,saboda digar yayyafi da taji cikin jikinta gami da haskawar walqiya,alamu ke nuna ruwan saman farko zai sauka kenan da yardar me duka yau a qasar agadez. Idanunta ta mayar kan akhnan,wadda yayyafin ruwan bai sanyata ta qifta idonta daga kan mammina ba.
"Ki nemo mijin ki kawo......zan tsaya don tabbatuwar dukka wadannan sharud......"
"Mammina manaaaa......" Ta furta da wani sassanyan yanayinta daya fusgi hankalinsa daga inda yake tsaye,inda hankalinsa yayi nisa sa maganganunsu ya tura dukka hankalinsa da nutsuwarsa zuwa ga bobbo muhammad dawud.
Kyawawan idanunsa ya daga yana kallon gabanshi,duk da bai iya ganin komai sai alamunsu a mazaunin dake gaba kadan dashi. Tafin hannunsa ya sanya yana goge yayyafin ruwan daya sauka saman screen din wayar nasa yana kuma qoqarin hanashi ci gaba da sarrafa wayar saboda yadda yake dan qara yawa.
Baisan me yasa sautin nata ya fusgi hankalinsa ba.......sai ya sanya tafin hannun nasa yana yiwa wayar rumfa da xummar rage saukan ruwan saman screen din,saidai a wannan karon kunnuwansa sun gaza kaucewa daga tsintar maganganunsu.
"Da gaske nake mammina......na baki wuqa da nama......ki kawo duk wanda kikaga ya miki.......fatana na rayu cikin 'yanci,irin 'yancin da kowacce mace maras igiyar aure a kanta zata rayu dashi......ban taba sha'awar soyayya ko tarayya da kowanne namiji ba.....don har yanzu bana zaton an halicci irin ajina daya dace da MARTABATA".