L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 32
L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 32: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 32. *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER…
3,357 words
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 57*
Duk da haka ya taka a nutse yana wucewa bathroom. Ta mirgina tana sake qudundunewa cikin duvet. Da gaske kuka take,tana jin ranta yana baci,ba wani d'a namaji daya taba ganin koda singalilin hannunta,amma shikam yanzu ba inda hannunsa baikai a jikinta ba sai gu d'aya tak.
"Dama shima haka yake?" Ta fada can qasan ranta tana tuna falaak. Falaak din da har yanzu take mamakinta,don zuwa yanzun ma ba'asan a wacce qasar suka yada zango ba,don ba'a maganan zuwansu Ethiopia yanzu.
Motsin fitowarsa ya dawo mata da tunaninta,ta daga idanunta a sace ta qasan duvet tana satar kallonsa,saidai ba shiri ta zuqe kanta ta.maidashi cikin duvet din jikinta na rawa.
Towel kawai ya dauro,towel din da ya fara ne kawai daga qugunsa ya rufe iya shafaffen cikinsa. Dukka muscles din da suka lullube jikinsa a bayyane suke,wani siffan qarfi sosai da dama koda ta cikin jallabiyyarsa kana iya ganin alamun hakan.
"Zaki iya tashi?,ko kina buqatar taimako?" Ya fadi sanda ya kammala maida kayansa neat,saidai kuma bai saka 'yar saman suit dinsa ba,hakan ya sanya kana iya ganin dan squeezing din rigar tasa tayi. Yayi maganan ne yana tsaye daga can gefe,ya saba 'yar saman suit din nasa a kafada.
Zabura tayi da maganan da yayi,tana tuna wancan ranar da yaso daukarta cak ya kaita bathroom din,saita tattare duvet din yana rinjayarta tayi bathroom din.
Murmushi kawai yayi,wani kalan murmushi dake qunshe da manufofi da dama. Akwai wasu abubuwa masu yawa tattare da ita......wasu suna bashi mamaki ne suna kuma sauya akalar tunaninsa a kanta,wasu kuma sanyashi suke yana tantamar anya itace?.
Ta jima sosai a bandakin,ita daya tana kumbure kumbure gami da share hawaye. Itakam inda tasan haka yake da bata yarda ta biyoshi ba,koda meye sultane zaiyi kuwa. Yanzu da wanne ido zata kalli sultane?,me zatace dashi?. Ba sultane kadai ba,kowa ma gani take zai iya ganin komai a jikinta.
Amma abun haushin,abun takaicin,maimakon taji tsanarsa a ranta ko haushinsa.....saita laluba zuciyarta taji babu ko daya,sai alamun saukar hannuwansa a jikinta da takeji tako ina,kamar a yanzu komai yake faruwa.
Ta fito daga wankan bayan dadewar da tayi,tanaso ya tafi ne don batasan da wanne ido zata kalleshi ba. A yau dai kam bata da wannan juriyar.....bata da wannan zarrar da zata iya hada idanu sam dashi.
Knocking da akayi na qofar ya saka gabanta faduwa,ba'a shigo ba,saidai taji sautin muryarsa daga waje.
"Idan kin gama shiryawa ki fito,lokacin sallah zai wuce". Baki ta tura gaba,me yasa bazai tafi ba?,wai me yasa ma bayajin kunyarta ne?,sai ya gama lalubeta hankali kwance kuma yaci gaba da harkar gabansa hankalinsa kwance?.
Da qyar ta kammala shiryawa cikin wata yalwatacciyar abaya royal blue data haska fatarta sosai. Kamar me tsoron haduwa da wani abu take kowa inda yake.
Yana zaune very calm,kamar ba shine ya danneta dazu dazun a daki ba ya gama lalube komai nata ba. Coffee yake sha cikin wani mug,idanunsa suna kan wayarsa daya ajiye a table din gefansa,batasan abinda yake kalla ba.
Narkakkun idanun nan nasa ya dago ya zuba mata,ta janye dubanta da sauri. Me yasa a duk sanda ya gama mata wannan abun maimakon taji ta tsaneshi.....ko tana jin haushinsa.....ko girmansa da kimarsa sun zube saidai taga ya sake mata wani kwarjini na musamman?.
"Bismillah" Ya fada yana hawa saman lallausar abar sallar dake shimfide tana fuskantar alqibla.
Wata irin nutsuwa,wani irin kwanciyar hankali taji yana ratsata sanda yake rera karatun alqur'ani a duka sallolin. Har taga kaman ma yayi saurin idar da sallolin gaba daya,duk da bayan sun idar ta duba agogo sai taga mintunan daya dauka sun ninka adadin mintunan data saba yi idan zatayi sallarta ita kadai.
Wani irin shuru ya ratsa gurin,tayi qasa kawai da kanta,tanason miqewa ta wuce ciki amma zuciyarta ta gaza bata wannan qwarin gwiwar,kawai sai ganinsa tayi ta juyo yana fuskantarta,ya kuma zauna sosai saman dardumar.
Dukkan idanunsa ya zuba mata,a hankali kyawawan labbansa suna motsawa yana karanta azkar din bayan sallame sallah. Kafin ya kammala azkar din ya sanya zuciyarta tana dab da rikicewa,ya shafa addu'ar sannan yaci gaba da kallonta kamar abinda yazoyi duniya kenan.
"Me yasa kike fushi?" Yayi tambayar kansa tsaye yana tsareta da idanu. Da sauri ta daga kanta sai kuma ta sauke,batason ko yaya ta bashi qofar karantarta,don haka ta tattara dukka qwarin gwiwarta tace.
"Fushi?....."
"Karki qaryata.....kada ki musa,na gani a idanunki" Ya furta can qasa yana sake dafata da idanunsan nan masu tarin dafi da wani magnet me qarfin gaske.
"Ba zaki iya kokawa da abinda yake cikin zuciyarki ba.....amma idan zaki iya na baki dama" Ya fada yana miqewa tsam yana gyara daurin agogon hannunsa.
"Gobe zakiyi baqi" Maganansa na yanzun ya sakata daga kanta badon ta shirya ba,sai shima akayi sa'a idanuwanta yake kalla.
"Mama na.....mamana zatazo" Idanun ta sauke qasa a hankali. Sai taji wani abu me nauyi yana ratsata,wani yanayi da ya saukar mata da tsananin kewar mahaifiyarta lokaci daya.
Ashe yana da uwa?,yana da mahaifiya?. Haka kawai saita samu kanta da son ganin mamarshi,idanu da zuciyarta suka shiga wassafa mata yadda take a cikin tunani da hasashenta.
"Ba wani abu.....bakya buqatar komai?" Ta tsinci muryarsa dab da ita. Kadan ta motsa baya tana lumshe idanunta bugun zuciyarta yana son canzawa. Kai ta girgiza masa,saidai har lokacin tana jin alamunsa a kusa da ita,har lokacin bataji alamun ya janye ba
"Goodnight" Taji ya furta a hankali da yaren France da yake sake fusgar hankalinta dashi.
Bata iya bude idanunta ba har sai data daina jin alamunsa. Ta waresu a hankali tana sauke dubanta akan hanyar daya wuce din. Zuciyarta ta matse kadan sanda take raya mata ya fita.....ya fita daga gidan,wani fili taji zuciyarta tayi,wani sarari da zuciyartata take raya mata kamar akwai wani abu da yayi nesa da zuciyarta.
Abubuwansa da yawa mamaki suke bata......amma irin wannan abinda yake matan.....baya masa nauyi?,bayajin kamar be kyauta ba?. Wa zata kira tayi maganan dashi?.
"Falaak" Wata zuciyar ta gaya mata. Shuru tayi tana juya abun a ranta
"Eh falaak.....itace ta biyo ta hanyar" Zuciyarta ta sake jadda mata. Amma ta yaya zatayi irin wannan maganan da falaak din?.
"Ita kadai ce zata fahimta" Wani sashe na zuciyarta ya sake bata amsa.
Wayarta ta jawo,ta bude watsapp dinta da takan kwana biyu bata hau ba. Wancan satin kaman taga saqon falaak din ta watsapp ta sabuwar number da bata tsaya tantance code din wacce qasar bane,tayi copying number din ta dawo wajen kira ta dora number din sannan ta kirata.
Tayita ringing ba'a dauka ba,sai dab da zata katse sannan taji an dauka,saidai maimakon muryar falaak ita kadai,sai muryoyinsu a cakude ita da maleek da suka fara shiga kunnenta.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Cikin shagwaba take masa magana shi kuma ya lalace yana rarrashinta. Gaban akhnan ya tsinke ya fadi,ba shiri ta kashe wayar. Kunnuwanta ba zasu iya jin abinda suke fada ba,maganganu ne masu nauyi sosai,da alama ma batasanma ta daga wayar ba gaba daya. Jefar da wayar tayi gefe tana jan siririn tsaki,yaushe falaak ta lalace haka ne?. Yaushe falaak ta koma haka?. Ba doguwar mu'amala bace a tsakaninsu......amma ta sani ba haka halinta yake ba. Ta lumshe idanunta ta budesu a hankali,ya tafi ya barta da qamshinsa,ya tafi ya bar mata memories masu yawa a tare dashi.
"Girmama na gaba.....girmama baqo" Ta tuna daya daga cikin lesson data dauka a zamanta cikin gidan. Ta bude idanunta a hankali,dole kenan tayi practicing daya daga cikin abinda ta koya kodon ta samu a kammala wannan zaman waqafin na rules din rayuwar masarautar da har yanzu ita batasan a wanne matsayi take ba.
~Ta cikin motar da yake tafiya idanunsa zube kan hasken farin watan daya haske sararin samaniya. Baisan murmushi yakeyi ba,baisan murmushi bane akan fuskarsa ba sai da yakai hannu ya shafa fuskarsa a hankali.
Ya tsinci abubuwa da yawa da baiyi zatonsa ba tattare da ita. Quruciya.....zallar quruciya take gwadawa da suka sanya ya sake raina shekarunta. Iya yadda takeyi kawai ya tabbatar masa quruciya ta mata yawa,kuma ba kowa zai.gane hakan ba sai wanda zama ya hadasu kaman hakan. Kwarjini kawai takewa mutane.....wannan izzar da sarautar dake jikinta mutane ke mata kallon girma da manyance.
"Da gaske batasan komai ba?" Ya sake tambayar kansa da kansa cike da mamaki still. Inda ace ya aureta ne kawai fa don sha'awa?,inda ace ya aureta ne don ya biya buqatar ransa a kanta fa?. Lallai inda hakanne da babbar matsala za'a samu.
Ya lumshe idonsa yana tuna yanayin data sanyashi,ya sake murmusawa a hankali kaman wanda ya samu tabin qwaqwalwa. Tunda yazo duniya bai tana jin yanayi irin wannan ba,ko shi yasa maleek yace sun dade a matsayin buhunhuna kuma bahuna?,akwai abinda maleek yaji kenan sama da abinda yaji a nasa jikin?. Iya tambayar kawai ta saukar masa da wani tashin tsigar jiki,kwanyarsa da zuciyarsa suka fara masa hasashen can inda maleek yaje,sai yaji kawai ya kasa zama shi kadai,ya jawo pillow din dake cikin motar ya sakashi a qirjinsa yana jin yadda mararsa take qullewa sosai.
Bai iya sake bude idanunsa ba sai sanda motocinsa suka sauka cikin masarautar aba jifar. Kowa ya tsaya suna jiran motar da yake ciki ta bude kanta da kanta. A nutse ya ajiye pillow din,ya zura qafafunsa qasa a hankali,kyakkyawan takalminsa qirar qasar italy ya fara fitowa,sannan gangar jikinsa yana sabe da 'yar saman suit dinsa.
Jikinsa a mace yake gaba daya,yayi wani laushi sosai,amma hakan bai boye kwarjininsa ba ko kadan.
Kaman kullum,duk inda ya taka hadimai ne da bayi suke zubewa suna gaidashi da girmamawa. Sashen nanay ya nufa,don qa'idarsa ne kome dare idan ya fita ya dawo sai yaje ya ganta,ballantana yanzun daya dauki kwanaki biyar ba tare daya sanyata a idanunsa ba.
Ciki lafiyayyen parlor din dake da girma da yalwa,cikin wani yanayi na kayan qawa da suke nuna zallar isa qasaita da qarfin ikon da masarautar oromo ke dashi.
Iyalin khadeeja yunnus jallata ne zaune a ciki,cikin wani yanayi na walwala qauna da fahimtar juna. Balqees,khansaaa,rumaisa,Aaanani,sai auta noorah wadda ke zaune gefe daban da camera dinta a hannu da alama wasu hotuna take dubawa.
Kaya ne fal a gabansu suna shiryasu cikin wasu irin abubuwa masu kama da akwati,suna yi suna hira cikin harshe da yaren oromo. Sallamarsa ta sanyasu tsagaita hirar tasu,cikin girmamawa da qaunar juna a tsakaninsu ya qara so suna masa sannu da zuwa.
A girmame ya gaida balqees da hasnaaa,sannan sauran suka gaidashi,noorah na maqale da hannunsa tana qoqarin nuna masa hotunan data dauka.
Hannu yasa da murmushi ya karbi camera din yana kallon hotunan,hotunane na wasu kyawawan tsuntsaye da shi kansa sai daya tsaya yana kallonsu. Hannu yasa yayi zooming hoton da kyau,harda aku.....dawisun da yasan bata dashi a baya cikin tsuntsayenta,ga wasu tattabaru da suka burgeshi sosai.
"Yaushe akayi wannan auta?" Ya tambayeta da murmushi kan fuskarsa yana waiwayawa gefansa inda take tsaye.
Murmushi itama ta saki daya qara bayyanar da kyan yarinyar,taji dadi sosai yadda obbo dinta idanunsa suka nuna burgewar da kayan sukayi masa.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 58*
"Wancan satin da baka nan obbo"
"Ma sha Allah,Allahumma bareek,daga ina kika siyosu?"
"Nigeria" Ta fada qasa qasa,yadda tayi maganan kuma ya bawa kowa dariya a parlor din. Ya fidda manyan idanunsa waje.
"Nigeria kuma?" Kai ta jinjina tana dariya.
"Eh obbo,a HALY JASHERU VENTURES(07046665338)obbo......harda kaji tana siyarwa fa,masu kyau sosai obbo,zaka iyayin ado dasu......" Kai yake jinjinawa,yana mamakin qaunarta da tsuntsaye sosai,gari ya gari har Nigeria?.
"Taya kuka hadu noorah?" Balqees dake zaune riqe da habarta ta fada tana duban noorah din da mamaki.
Siririyar dariyar data bayyana quruciyarta tayi tana sake riqe hannun haisam.
"Tana zuwa nan qasar sarin pure mayukan zaitun,hulba,habbatussauda da man kwakwa dama sauran ire irensu". Kai ya jinjina sosai yana murmushi. Mutum ne shi da yakeso yaga dan adam me dogaro da kansa,zuciyarsa bata mutu ba sam,kuma duk cikin 'yan uwansa,tarin dukiya da mulki da suke ciki ba wanda baya juya business dinsa hatta da Aareef da yake bin noorah
"Ma sha Allah.....zan qara jari da alama a siya tattabaru,nima a kawomin dawisu da aku guda daya" Wani tsalle tayi tana d'aneshi,farinciki yana cikata,
"Na gode obbo na gode" Ta fada da harshen oromo farinciki yana cikata.
Tabe baki Aanani tayi,itakam haushi takeji idan noorah ta zauna tana bayanin riba da ake samu akan tsuntsayen.
"Kome yake cikin siyan wadannan dabbobin oho". Da sauri hasnaa ta juyo yana duban Aanani.
"Sirri ne....noorah ta fiku wayo,bansan ya akayi tasan abinda ake samu cikin kasuwancinsu ba.....riba ce ba qarama ba,ina kyautata zaton nan gaba kadan cikin mata na gidannan itace me arziqinmu" Maganan kusan ya saka kowa dariya,duk da suna lura da kusan hakanne abinda hasnaaa ta fada.
Tsautsayi shine abinda ya fito da ita daga daki. Zaman dakin a kwanakin ya fiye mata komai,ya fiye mata fitowa ta zauna a cikinsu,daga sanda ta fahimci tarin walwalar da suke ciki saboda auren captain sheikh,daga sannan ta sanyawa ranta nisantarsu dama zama a cikinsu. Ba yadda za'a zauna a tashi ba tare da sunyi wata magana data danganci matarsa da aurensa ba. Ba yadda za'a zauna lafiya ba tare da an tabo batun aurensa ba,saita zabi ta yita kwanciya cikin daki da sunan jikinta ne har yanzu baiyi qwari ba.
Ruwa take nema Don haka dole ta fito nan din,don freezer dinsu an fiddasu duka za'a sanya sabo,kuma basu qaraso ba har yanzu.
A hankali take takowa,sosai duk wanda ya kalleta zaiga ramar da tayi. Tana jin kamar iska tana yawo da ita cikin sararin samaniya ne kawai. Muryarsa taji sanda yake fadin.
"Nanay fa?". Kalma daya ce tak amma tasirinta a zuciyarta me girma da fadi ne. Sautinsa da muryarsa wani abu ne da har yanzu tasha kwatantata data sauran maza amma ba wanda ya dace tasa tayi daidai da tata a mizani.
Kaman ta juya ta koma saboda tsananin bugawar da zuciyarta takeyi amma saita kasa. Tayi kewarsa sosai,tana kuma buqatar ganin wannan kyakkyawan kamilalliyar fuskar dake da wani irin kamewa da nutsuwa.
Da sallama ta shiga,idanunta kuma a kansa. Sun amsa duka,amma shi kyawawan labbansa ne kawai taga sunyi motsi. Waigowa yayo shima kaman sauran mutanen cikin parlor din,sai da numfashinta ya kusa qwacewa na wucin gadi.
Wani kyau.....zallar kyau taga yayi mata duk da ya cire suit din saman sai T-shirt din cikin. Bata sani ba.....ko don ganinsa cikin qananun kaya wani baqon abune a tare dashi shi yasa?.
Idanunta ta lumshe zuciyarta na tsananin bugawa a qirjinta.
"Sannu saamee.....kin fito?" Balqees ta tambaya tana kallon idanunta. Kai ta daga a hankali ta motsa labbanta tana amsawa da
"Eh" Sannan ta daga idanunta tana zubewa akan fuskarsa. Ba ita yake kalla ba,still hankalisa yana kan camera din noorah yana ci gaba da kallon tsuntsayen da yaji sun burgeshi sosai. Lafiyayyu dasu da irin salon kiwon daya tabbatar sun samu kulawa.
"Barka da dare,ina yini" Ta fada da yaren oromo. Kansa ya daga yadan kalleta.
"Lafiya lau malama.....ya jikin naki?"
"Alhmdlh da sauqi" Ta bashi amsa wani abu yayi mata tsaye. General kulawa ce normal yadda ya saba. Yadda ya saba yiwa su noorah Aanani da rumaisa,harma sai taga kaman yafi nuna musu kulawa akan yadda yake nuna matan.
"Allah yasa kaffara" Ya fada yana miqawa noorah camera dinta.
"Nanay ta kwanta ko?" Kai noorah ta daga masa.
"Tun dazun,tace tanaso gobe ta tashi da wuri...."
"Nanay ta rasa sukuni fa,kaman gobe ba zatazo ba,tace surukarta kawai takeson gani......anya kwanan nan ba zaka rasa matsayinka gurin nanay ba?" Murmushi ya saki kadan yana jin jikinsa har yanzu ba qwari,murarsa kaman tanason yin gana,still mararsa a daure take har yanzun kaman tanason masa ciwon data saba lokaci lokaci.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Banajin akwai me iya qwace wannan".
"Saini" Muryar hussam ta cika parlor din sanda yake shigowa hannunsa dauke da mangwaro da aka yanka.
Harara ya juya ya watsa masa,hakan ya sanya hussam shiga taitayinsa,yadan koma da baya yayo sallama sannan ya shigo,kai tsaye kuma ya wuce kusa da Aanani zai zauna.
"Tashi" Haisam yace dashi kai tsaye. Shi da Aanani dukkansu ba haquri,abokin rigimarta ne sosai,kaman ba rumaisa bace sakuwarsa Aanani ce. Yayi narai narai da idanu yana sauya gurin zama,saidai ko sakewa haisam bai bari yayi ba yace masa.
"Ina report na ma'aikatan kamfanin can na dubai?". Idanu ya narke,bai taba ganin mutumin da baya gajiya da sabga ba irin haisam din.
"Obbo.....an kammala komai,kawai na d'aga qafa ne a gama biki sannan"
"Ni nace maka?" Ya fadi kansa tsaye idanunnan nasa na cikin na hussam.
"Kayi haquri......hukuma ta bamu sha biyar ga sabon wata zamu iya bude kamfanin mu"
"Alhamdulillah" Ya fada a hankali ya miqa hannu yana karbar wayar hussam din da yake miqa masa.
Hotuna ne na dukka sassan kamfanin,kamfanin da haka kawai ya shiga ransa saboda yawan abokan hulda na kasuwanci da suke dasu a qasar Dubai din. Haka kawai yaji a ransa wannan karon hussam yayi abun arziqin da bai taba yin irinsa ba,ya daga kai ya dubi hussam din dake bada labarin shima ya hada tasa walimar.
"Inde da shashashanci a ciki ka tabbatar ba za'a yita ba"
"Aah obbo....walima fa,ba party bane wannan na rantse" Idanunsa kawai ya maida kan wayar,sai baice komai ba yaci gaba da kallon hotunan. Yana ji a ransa ya kamata kawai yasa hussam ya fidda mata yayi masa aure,kaman hankalinsa sai yafi haka nutsuwa. Duk da ba wani shashashanci yake ba....jinin aba jifar dukka Allah ya shirya masa,kawai rawar kansa wani lokaci ke sanyawa basa shiri da haisam. Yana da tara abokai kala kala,hakan kuma baiwa haisam din ba,don yana iya kawo matsalar tarbiyya.
Da qyar takai kanta kitchen din tana ci gaba da sauraren maganganu da hirarrakinsu. Gaba daya sai yanzu take jin kanta lallai ita bare ce,lallai ita din wata dabance da babu wanda ya damu da ita.
"Zanje nima.....tabbas zanje" Ta fadawa kanta tana qoqarin hadiye abinda yake taso mata.
A yanzun ta shirya fuskantar matar haisam.....ta shirya tsaiwa taga wacece ita?,ta kuma shirya karbar haisam din koda dadi ko bata dadi ba.......zata gwada mata itace bare.....zata gwada mata itace ta shigo rayuwarsu.....itace ta fado muhallin daba nata ba.
"Sha biyar ga wata.....wata daya kenan a gaba?" Ta tambayi kanta.
"Lallai ne a wannan lokacin bikin aure zai hade dana bude kamfani" Ta fadi can qasan ranta,saima ta fasa daukan ruwan,ta fito tana ficewa,wanda harta fice dimma basu kula da ita ba saboda hirarrakinsu da sukeyi,amma ta lura haisam din baya gurin da alama shi ya fice ne.
*_W A S H E G A R I_*
Cikin girma isa da qasaita jerin motocin masarautar aba jifar ke shigewa gate din palace learning residence wanda ke dauke da wata fakadediyar harabar da zata cinye dukka adadin motocin da zasu shigo cikinta ba tare da sun takura ba.
Wani abu me sanyi nanay keji yana ratsata tunda suka shigo farfajiyar gidan. Wani zumudi ne yake kamata da zaquwar data kwana da ita tun a daren jiya. Daga jiya zuwa yau ta rufe idanunta tayi addu'a cikin zuciyarta har batasan adadi ba. Tana roqon Allah yadda ya tanqwara zuciyarta ya bata ikon daidaita adalci tsakanin 'ya'yanta,soyayyar dayansu bai sanya ta fifitashi a gaban idanunsu ba.....Allah ya bata ikon yin adalci tsakanin surukanta da duk za'a auro mata..
Batasan me yasa ba.....ko don haisam din na dabanne a ranta shi yasa komai nasa.....komai daya shafeshi yake zama na daban a ranta?.