L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 33
L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 33: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 33. Tayi bismillah tana sako qafafunta waje sanda haisam ya…
3,347 words
Tayi bismillah tana sako qafafunta waje sanda haisam ya bude mata motar da take ciki,hadiman da suke tare da ita suka matso don gyara mata rigarta ta baya,ya daga musu hannu yana dakatar dasu. Ba gwanar fita bace nanay sam,zai wahala ace maka yau bata nan,amma duk sanda zata fita din haisam ke hidimar rakata yana kula da lafiyarta da motsinta har su dawo. Shi ya matsa da kansa ta bayanta ya gyara mata komai,idanun samee dake cikinsu Aaanani yana kansa.
Wani sake burgeta yakeyi,tana ji har cikin zuciyarta ba zatayi asarar wannan ba,shi din mallakinta ne. Tana ji a ranta inama ace itace tsaye haka a gabansa yake hidima da ita?.
Jerawa sukayi shi da Nanay din suna takawa a hankali,su rumaisa na bayansu,hadimanta mata a bayansu rumaisa din,sai guards da dogaran da suke cikin fararen kaya da suka cika gida kaca kaca sama da yadda yake a baya.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 59*
Cikin kamalar nan tata,uwa mabada maama khadeeja yunnus jallata......baya goya marayu,tayi tata tayi ta saura,uwar tausayi da taimako,MAMA OROMO kaman yadda da dama jama'anta ke kiranta take takawa zuwa cikin gidan,hannunta cikin na haisam yana riqe da ita.
Wani kalan kwantaccen murmushi ne akan fuskarta,murmushin da iyashi kadai ya isa ya gaya maka labarin dake cikin zuciyarta. Sanye take da wani lallausan tufafi daya kasance ainihin suturar qabilar oromo,saidai dinkin da aka mata dinki ne dake nuna sarauta da kuma girma irin da dattijantaka.
Cikin parlor na biyu suka yada zango,yayi tsaye riqe da hannun nanay,daidai sanda hadiman gidan sarautar aba jifar sanye da fararen kaya suka fara shigowa da wasu akwatuna,wanda shi kansa baisan sanda suka taho dasu ba.
Wasu irin akwati ne,4corner me masifar daukar idanu,wanda baka da tabbacin da meye aka tsarashi,off white ne da aka yiwa adon royal gold a jiki. Idanunsa ya lumshe a hankali ya bude yana azasu kan nanay. Baisan wacce irin qauna takewa akhnan ba tun yanzu?. Wadannan akwatuna ne masu tsananin tsada da daraja,wadanda suka kusa guda ashirin da hudu,iya akwatin kawai baisan ma meye a ciki ba.
Murmushi ta sakar masa a tausashe,tasan abinda ke kai kawo a ransa,tasan meye a zuciyarsa. Iya hussam da yaga kayan sai daya fara qorafi.
"Iyyeee......matar d'an lele,anya zamu samu sauran space kuwa nanay?" Murmushi kawai tayi tana girgiza kanta. Ta sani bawai hussam ya fadi bane har zuciyarsa,yana da wasa da barkwanci,amma da gaske haisam daban yake a zuciyarta,dole ko meye yazo daga gareshi ya zama na daban.
"Zamuje ganin d'iyata goben....."
"Banda ni nanay,kinsan halinsa ko,zaice ne zamuje kalle masa mata,daidai sa Aareef Allah yasa ya barshi,idan ta fito zamu hadu a nan,Allah ya dawo daku lafiya,gobenma inajin zanje addis ababa jibi zan dawo" Dariya ya sake bata,yasan halin yayanshi kaf.....amma wani lokaci tsabar wasa da ya yiwa hussam yawa ne yasa basa shiri da haisam din.
Dukkaninsu kowa ya samu guri ya zauna,hakanan duk hadiman dake cikin gidan suka qaraso cikin matuqar ladabi da girmamawar nan da suka saba da ita suka diban gaisuwa.
Cikin mintina qalilan suka cika gabansu da abubuwan ciye ciye,zenabu taja baya kanta a qasa tace.
"Wannan aike ne daga uwargijiya,tana ciki yanzun nan zata fito,tace ayi mata afuwa da rashin kammala shirinta kafin isowarki mama oromo.....yanayin shigar ne yasha banban da tasu" Murmushi nanay tayi,tana sake dafe hannun haisam da har yanzu yake cikin nata,saidai kafin tace komai haisam din ya rigata magana.
"Ki gaya mata zamu shigo ciki nida nanay mu sameta"
"In sha Allah" Zenabu ta furta ta miqe tana shaidawa bara'atu,ta tattaka itama tana komawa ciki.
Tsaye kawai tayi gaban babbab madubin,tana kallon zaman doguwar rigar da aka dinkata daga asalin yadin alharir na asali me tsadar gaske. Ko ba'a gaya mata ba kayan ta sani sun nuna alaman kaya ne masu dadadden tarihi,bawai saboda tsufa ba.....aaha,hasalima kayan kaya ne masu madaukakiyar darajar da idan za'a kaisu kasuwa yanzu tabbas za'a bada kudade masu nauyi sa dimbin yawa a kansu kafin a karbesu. Kawai ta fahimci tsohon yadin alharir ne kasancewarta me mu'amala da yaduka zararruka auduga da dukkan wani yadi me tsada,fara gudanar da kamfaninta na sahel couture ya sanya take iya fahimtar abubuwa da dama dangane da suturu na alfarma masu daraja.
Abu na biyu kayan sai taga suna mata kama da wata sutura,wani tufafi da ta taba ganin kamar cikin kayan da momma ta bata.....a jikin wata kaman ranar aurenta data gaza tuna wacece?. Ta sake kallon sarqar wuyanta dama bracelet din hannunta,duka abu guda yake gwada mata.
"Ga wannan......itace kyautar da zaki miqa mata bayan kun gaisa" Birra ta fada tana miqawa akhnan wani nannadadden abu me qyalli,shiba paper ba shi ba leda ba. Juyashi take kawai cikin hannunta,kafin ta dago tana duban birra.
"Birra.....me yasa duka wannan......me yake faruwa?,zuciyata kamar tana fadamin akwai wani abu" Qasa birra tayi da kanta,tana jin zuciyarta na mata nauyi kadan.
"Babu komai.....babu komai ranki ya dade sai alkhairi" Kafin ta sake cewa komai bara'atu ta shigo,ta kuma isar da saqon haisam.
"Ki shiga dasu duk inda suka zabi shiga" Ta fadi tana sake maida dubanta kan madubi.
Kayan sun mata kyau,shigar ta mata kyau sosai ita kanta ta gani,hakanan kayan cif cif jikinta kamar don ita aka dinkasu. Ta lumshe idanunta sannan ta budesu a hankali,tana jin zuciyarta na wani irin motsawa kamar akwai wani abu daya tabata.
"Mu qarasa ciki nanay.....akwai kyautar da nakeso nayi miki,ina fata kuma ta zama kyauta mafi karbuwa a gurinki da bazaki manta da ita ba" Murmushi tayi a hankali ta soma takawa tare dashi,ta amsa masa a hankali saboda ita kanta tana jin wani yanayi a zuciyarta da gangar jikinta
"Bayan wannan kyautar da kayimin na suruka sukutum da guda?,harda wata kyautar ta daban muhammad?" Kai ya gyada mata a hankali
"Akwai nanay.....akwai saura" Jinjina kai itama tayi.
"To na gode,Allah yayi maka albarka"
"Ameen" Ya amsa yana jin wani sanyi cikin ransa. Addu'arta ta daban ce a gurinsa,ba wani abu a duniya ke masa dadi sama da yadda addu'arta ke masa.
Qawataccen parlor ne wanda yasha banban da sauran falukan gidan,tunda tazo gidanma ba'a taba budeshi ba bare a shiga,iyakaci a gyarashi a tsaftaceshi.
Bismillah nanay tayi ta zauna saman tattausan kujerar data lume a ciki. Dubansa tayi sanda taga yana shirin zama kusa da ita.
"Ya haka?"
"Nanay?" Ya furta a hankali.
"Jeka da kanka ka tahomin da ita,jeka da kanka ka taho da matarka" Murmusawa yayi,sannan ya miqe a hankali yana takawa. Hakan yakeso,zaiso hakan sosai,amma yake alkunyawa nanay.
Zuciyarsa a matse take da wani abu da yafi masa kama da zumudi. Daren jiya da qyar yayi wani wahalallen bacci da bai taba wahala irinsa ba. Ciwon mara sosai yayi shi kadai cikin sassansa. Yasha kanwa yasha lemon tsami har doze din yaso ya wuce,sai gab da asuba ya samu sassauci,don bai farka ba sai bayan an kammala sallar asuba da wasu mintuna,jikinsa sharkaf da gumi da janaba,yayi wanka a daddafe yayi sallar sannan ya koma ya kwanta yana jin marar har yanzu a daure,hakanan ba wani kuzari a jikinsa sam.
Ta bawa qofa baya,tana tsaye har yanzu gaban madubin,wannan ya bashi daman fara arba da wadannan blue eyes din nata da haskensu yake cika masa idanu.
Fes komai ya dawo kanta,abinda ya faru tsakaninsu jiya. Wata irin kunya ta kamata har taji kaman qafafunta sun soma rawa.
"Ya ilaheee......ya rahman" Ya furta can qasan maqoshinsa yana hadiyar wani abu,adam apple dinsa daya fito sosai kaman zaka sanya hannu ka ciroshi ya motsa sama da qasa.
Ta zare nata idanun daga kansa,don bata da juriyar kallonsa tun daga jiya da abinda ya mata ya zarta na wadancan kwanakin,tayi qasa da kanta kawai tana murza bracelet din hannunta tana jinta kamar tana nutsewa a qasa.
Idanunsa ya lumshe sanda ya iso gabanta,numfashinsa yana masa wani irin nauyi,yana jin kamar akwai wani abu dake fusgar zuciyarsa. Saidai duk yadda yakeji bugawar da tata zuciyar takeyi ta danne tashi. Wani irin salon dressing take gani a jikinsa karo ma farko tunda ta fara ganinsa,ya fito sak MATASHIN OROMO da shigar kayansu na al'ada da aka zamanantar dasu.
Kayan sun bala'in kwanta masa sunyi biyayya tamkar sunsan a jikin wanda suke. Hannunsa ya miqa zai riqe hannuwanta da bracelet din suka zauna mata tamkar dama can mallakinta ne,amma daya tuna nanay nacan zaune tana jiransu sai ya janye hannun nasa da sauri. Ya sani,zai wahala ya tabata ya iya jurewa wani abu bai biyo baya ba,bayason kuma yanayinsa ya sauya kwata kwata,don yasan tsaf nanay zata dago wani abu.
"Barka da warhaka" Ta samu kanta da fadi tana rusunar da kanta da alama ta girmamawa.
Idanu ya zuba mata,karon farko da yaji tayi wani irin burgeshi,yanayin gaisuwar ya mata kyau,cakude da izza da quruciyarta da yake gani muraran tun daga jiya..
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Gaisuwarta tayi,cikin yanayin dake nuna tarbiyyar masarauta da qabilar oromo ta fara shigarta. Saidai shi ko kadan baya ra'ayin irin wannan gaisuwar,ba irinta yakeso ba. Ya jima da tsara rayuwarsa da dukkan macen da Allah ya qaddara zai aura. Koda da gaisuwa yana fadin zata zama ta musamman ne.
"Kinyimin kyau sosai princess of agadez......na jawoki kusa ki kiramin bappi" Ya furta muryarsa a narke yana karya wuyansa idanunsa na narkewa a kanta,kamar ya manta gaban wa yake.
Har cikin b'argonta taji wannan muryar......wannan husky voice din nasa da yayi wani irin laushi da taushi,cikin nutsatsen sautin da kamar zabarsu yayi ya kuma jerasu kafin ya furta mata su.
Shi kansa baisan me yakeji ba....baisan me yake fusgarsa a kanta ba....baiji kuma yanason ya dauke kallonsa daga kanta ba. Wani yanayi ne me cakude da tausayi,tausayin batasan ainihin suturar wadda take sanye da ita ba.....suturar wata sashe na jikinta.....suturar halitta mafi qaunarta a duniya,suturar halitta mafi soyuwa a gareta a duniya.
Qasa ta sakeyi da kanta tana sake murza bracelet din. A hankali idanunta suka sauka kan qafarsa,wannan qafar dake mata wani irin kyau,wannan qafar dake burgeta cikin baqin takalmin daya fito da zara zaran yatsunsa ya kuma haska farar fatar qafar tasa dake kwance lumui kaman batasan wani abu wai qasa ko qura ba.
Batasan me yasa komai ta kalla yake burgeta a tattare dashi ba......batasan me yasa komai nasa yake jan hankalinta ba,komai nasa kaman ya zaba kaman ya tsara,har wani lokaci sai taji zuciyarta tana gaya mata,ya fiki kaza.....ya fiki kaza.
Tafin hannunsa ya sanya qarqashin idanunta yana bude mata su,ta dora idonta a nutse akai. Wani guri da a koyaushe take samun nutsuwa koda a rude take muddin zai cakuda zara zaran yatsun hannunsa da nata. Tana jin wani lokacin idan yayi hakan,kamar wani assurance yake bata na samun nutsuwa.
"Zamu iya tafiya?" Ya fada da French din nan nasa me cike da wani accent da take yawan gwadawa ko zata iya magana dashi.
"Inaso a sanda idanun nanay ke kallonmu......ta kallemu a matsayin cikakkun ma'aurata,wadanda basu da matsalan komai.....ma'auratan da sukayi auren qauna da soyayya......ba wadanda sukayi auren yarjejeniya ba" Yayi maganan ne cike da tarin nutsuwar nan dake masa ado,amma sai kalmarsa ta qarshe ta haifar mata da wani faduwar gaba.
"Auren yarjejeniya.....na manta" Ta fada can qasan ranta. Har yanzu yana riqe kenan da maganganun mammina?,har yanzu kenan yana kan alqawarin mammina?....hakan yana nufin?" Sai zaren tunanin nata ya tsinke tana jin wata fargaba.
"Hakan yana nufin wataran.....komai zai qare?" Tambayar da bata lalubo amsarta ba,ta tsinci wannan lallausan tafin hannun nasa cikin nata.
Wani space ya bata nayin shuru saboda heart rate dinta ya daidaita.
"Kin shirya?" Ya fadi a hankali. Bata ja da nisa ba kawai ta daga masa kai. Batason kowa yaga sun dade a cikin dakin da daga ita saishi ballanta a zargi wani abu,ya jinjina kansa a hankali ya soma takawa tana biye dashi.
Qarar taba qofar ya sanya nanay maido hankalinta ga hanya maimakon TV din daketa aiki ba wanda ke zama ya kalla,wanda suke hasko labaran qasa na yammaci a gidan tv mallakin gwamnatin qasar Ethiopia din.
Da farko haisam ta fara kalla,sannan a hankali ta aje idanunta akan fuskar akhnan.
Wani irin abu me qarfin gaske ne ya fusgeta,wani irin yanayi da yafi kama dana Mitumin da aka tasa a bacci ba tare daya shirya ba.
Idanu sosai ta zubawa akhnan din,wani irin abu take gani yana gilmawa akan fuskar ta,wasu kamanni na sak da sak......kamannin da suke cikin dukkanin baccinta na shekara da shekaru.
Da fari qafafunta da hannayenta ne sukayi wani irin sanyi,don kamannin da take gani yanzu a gabanta ta sani wani abune me wahalar kasancewa. To amma koda ta matso kusa da ita....koda ta zubawa shigarta idanu sai take ganin safeena a gabanta,safeena cikin shigar kayan aurenta Randa za'a kaita gidan ajani......safeena da quruciyarta ta sake dawowa baya kaman wadancan shekarun da suke lokacin 'yammatancinsu.
"Ki nutsu Khadija......wannan din surukarki ce,kada ki koma maganan badini zahiri ne a gabanki" Wannan tunasarwar da zuciyarta tayi mata shine abinda ya sanyata miqewa. Idanunta fes akan Fuskar akhnan data sunkuyar da ita qasa kadan. Wani irin nauyi taji tana ji daga kallon fuskar matar sau daya tak. Wani irin kwarjini taji tayi mata matuqa da gaske,kwarjinin da taji zuciyarta a take tana gaya mata.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 60*
"Ga asalin inda kwarjininsa ya samo asali da alama". Kallo daya tayi mata,amma sai take ganin wani yanayi tattare da matar. Nutsuwa kamala da cikakkiyar haiba,ga wata irin kunya da batasan abinda ya kawota ba,kalan kunya da bata taba jinta dangane da wani dan adam ba.
"Ma sha Allah,tabarakarrahman" Nanay ta gaza jurewa sai data furta. Duk da akwai wasu kamanni saman fuskar akhnan din da take hange yanzu haka......amma hakan bai gaza banbanta wannan kyan da wancan kyan ba,wasu banbance babance da tana sake qarasowa gabanta tana ganinsu.
Hannuwanta dukka biyun ta miqa akhnan din tana dubanta da wani irin tarin qauna da takeji ya saukar mata,qaunar da ta ninka wadda takeji kafin takai ga ganinta.
"Bismillahir rahmanir rahim......ina miki maraba da shigowa cikinmu,ina miki maraba da shigowa masarautar oromo.....ina miki kuma maraba da shigowa ahalin aba jifar" Tayi maganan dukka tana miqawa akhnan hannunta.
Ji tayi ba zata iya ci gaba da tsaiwa a gabanta ba,karon farko data rusunawa wani dan adam akan gwiwoyinta bayan sultane dinta,saita fara sulalewa zatakai qasa,abinda ya dauki hankalin haisam matuqa da gaske d wanin irin yanayi na burgewa da mamaki,saidai amma caraf nanay ta kama hannuwan nata tana fadin.
"A'ah.....ke a gareni diyace,tamkar dai Aanani noorah rumaisa balqees hasnaaa husssss......." Sai maganan Nanay ya datse daga sunayen da take jero mata sakamakon sauka da idanunta sukayi akan abun hannun akhnan din.
Cak komai ya tsaya mata.....kwanyarta ta kwasheta da wani irin gudu tana maidata shekarun baya. Shekarun da safeena ta kawo mata ajiyar wannan abun hannun.
"Ki ajiyemin,kinfi safiyya iya adani,Ahmad ne ya bani,haka kawai nakw tsoron ajiyarsa cikin gidan" Ta ajiyeshi da matuqar muhimmanci,saidai safeena ta karba daga baya tana shaida mata yanzun ta samu tabbacin zata iya ajiyarshi.
"A......a ina kika samoshi?" Ta furta idanunta a waje tana dan girgiza hannun akhnan da sauri.
Da hanzari akhnan ta daga kai gabanta yana faduwa,tanaso ta gane akan me dattijuwar ke magana,saita fuskanci idanunta da hankalinta suna kan abun hannun ta.
Da sauri ta daga kai tana kallon haisam,gabanta yana tsananta faduwa,tunani kala kala yana sarqa kanshi da kanshi a zuciyarta,ina ya samo ya bata?.
"Nine na bata" Ya fada calmly bayan ya zare idanunsa daga kan akhnan dake masa kallon da ya gama fassarashi,ya kuma tafi kai tsaye zuwa ga ma'anar kallon dake cikin zuciyarta.
Still nanay bata saki hannun akhnan ba,ta maida dubanata ga haisam a rikice.
"Nine na bata nanay,nace ta saka don ki sake gamsuwa da gaske ita din jinin SAFEENA ce". Maganan ya saukowa nanay da wani mugun nauyi,har sai da tayi taga taga kaman zata fadi,saidai kafin yakai ga qarasowa gurin tuni akhnan ta sanya siraran yatsunta ta taro bayanta sosai,yana qarasowa sai ya tallafeta ta hanyar tsaiwa ta bayan nata.
"Baka tabamin irin wannan wasan ba" Ta fada tana maida Fuskarta da dukka idanunta akan abun hannun akhnan.
"Baka qarya muhammad,baka tabamin qarya ba....kuma a yanzun ma nasan ba zaka fara ba,ba halinka bace" Ta qara fadi tana sakin hannayen akhnan.
Tafukan hannayenta dukka biyun ta sanya tsakanin gefe da gefe na fuskar akhnan,ta juya fuskar tata daga hagu zuwa dama,ta saketa,ta kama gefan mayafin dake lullube a kanta ta murza,sai ta sake saki tana sake kamo hannuwan akhnan din.
Yatsunta ta kalla dogaye wadanda har yanzu da sauran jan lallen da yayi dishi dishi,sai ta juya tafin hannunta tana qare musu kallo da kyau.
Ba wanda ya zata a cikin su shi da ita,sai wata wawar runguma kawai da sukaga ta kaiwa akhnan din tana fashewa da kuka mara sauti,saidai muryarta ta nuna kukan takeyi
"Allahu akhbar......Allah akhbar,Allahumma lakal hamdu kulluh,wa lakashshukr kulluh.... Lallai ba shakka ke din jinin SAFEENA ce,tsatson safeena ce ke" Ta qarasa fada dukka jikinta yana girgiza da alamar abune me zurfi da taba rai.
Bata gane komai ba har sanda haisam ya kama nanay ta tayashi suka zauna. Banda sunan safeena data fahimta a dukka maganganunta,safeena mahaifiyarta bata gane komai ba,ta zuba ma nanay dake riqe da hannunta har yanzu idanu,sannan ta maida idanun nata ga haisam dake matsa hannun nanay din a hankali cikin wani yanayi na tausar zuciya,hannunsa saman kafadar nanay din yana shafawa a hankali kamar me lallashin yaron goye dake rigima.
*_BAYAN MINTI TALATIN_*
"Nanay" Akhnan ta furta sunan a hankali kamar meyin rada muryarta tana rawa. Kalmar ya fito mata ne ba tare data shirya hakan ba. Idan bata manta ba,cikin diary din safeena wanda bata bude koda third page dinsa ba har yanzu.....amma daga page na farko zuwa na biyu cikin sunaye sahun farko da taga anata maimaita rubutawa akwai KHADEEJA NANAY. a yanzun tana iya tuna haka.
"Karki qara kirana da kowanne suna sai wannan" Nanay ta furta hannuwanta cikin na akhnan din tamkar anace mata idan ta saketa zata bace a shafe babin wannan farincikin da yayewar damuwar data samu.
Lumshe idanu akhnan tayi,sai wasu hawaye suka biyo ta qasan lumsassun idanunta. Har mutane nawa mamminta ta rasa ne a rayuwarta?,mutane nawa ta tafi tana kewar rashinsu?,da fari ahmad.....ance akwai wani yaron nata daban inji momma.....yanzu kuma ga nanay?. A yanzun ko zata samu salama idan tasan an samu mutum biyu a cikinsu?.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Hannu nanay ta sake kaiwa gefan fuskar akhnan tana dauke mata hawayen,ta bude idanunta a hankalin jin hannunta saman Fuskarta,hannun sai ta jishi da wani irin sanyi da wata irin rahama,kwatankwacin yadda takeji akan na morsa safiyya.
"Kina da irin idanunta.....kina kallona kamar yadda take kallona" Nanay ta furta da wani murmushi da hawaye ke kwance fal qasan qwayar idanunta.
Dauke idanunta tayi ta maida kan haisam,wanda ke tsaye goye da hannuwansa a qirjinsa yana dubansu. Yana ji kamar an kwantar da zuciyarsa ne ana yankar namanta. Kuka na mace baya sonshi sam,ballanta kukan nanay dinsa?. Ya dauka kukan nanay kawai zai masa zafi,amma sai yaji kwantankwacin wannan ciwon sanda yaga gangarowar nata hawayen.