L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 36
L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 36: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 36. Da kallo ya bita,yadda ta fita din baiyi masa ba,a…
3,371 words
Da kallo ya bita,yadda ta fita din baiyi masa ba,a gaggauce da yanayin da yake gaya masa lallai akwai wani abu da take birnewa,sai kawai ya ciro wayarsa,yayi kira dukkanin qofofin da zata fice,ya bada umarni tsare masa ita har sai ya tabbatar da komai na sultane lafiya yake.
Wayar ya ajiye,sannan ya fara takawa a hanzarce yana wucewa dakin sultane din. Ya daga labulen yana shiga bakinsa dauke da sallama,duk da ya sani babu me amsa masa.
Ba kowa kaman yadda ya zata,yaci gaba da takawa zuwa inda yake. Yana nan kwance kaman yadda ya barshi,ba wani abu daya canza daga fuskarsa ko yanayin kwanciyarsa. Yakai hancinsa zuwa bakinsa da hancinsa ya tabbatar da bugawar zuciyarsa yadda take.
Wayarsa ya ciro kai tsaye,ya kuma kira haisam,daidai sanda yake tsane kansa da towel bayan ya fito daga wanka da ruwa me dumin gaske saboda yadda mararsa har yanzu taqi sassauta masa.
Shuru yayi yana sauraren dukkanin bayanan ahmad,har sai da ahmad din ya kammala.
Ka bincika dakin,komai da komai,qasan shimfidarsa,gefe da gefan gadon,kada ka sanya hannunka,kayi amfani da hand glove,bayan labulaye,cikin pillow dinsa,toilets da bathroom" Abinda yace dashi kenan.
"Ka maida kiran video call,ka ajiye ta inda zan iya ganin motsinka"
"Yes sir" Ahmad ya amsa masa da girmamawa. Miqewa haisam din yayi,yana gyara daurin bathrobe din jikinsa sosai,sannan ya koma ya zauna yana amsa video call din da Ahmad yayi requesting masa.
Ya sani,ba yadda za'ayi tayi shiga da fitar banza. Duk sanda ka ganta akan abun hari to lallai ba shakka akwai wani saqo da zata bayar ko ta aiko a bayar din.
A nutse yake monitoring motsin ahamd,yana bincike ko ina idanunsa suna biye dashi har ya kammala,saidai ba wani abu da aka samu.
"Ka kuncemin Ac dincan" Haisam ya fada a nutse yana duban ahmad.
"Kafin ka kunce,ka samu bargo ko wani abu me laushi ka shimfida daga qasan,incase ko meye karmuyi losing nasa"
"Tom" Ahmad ya fadi,kujera da duk abinda za'a nema haisam ya lissafo masa,Ahmad din ya cire babbar rigar jikinsa yabar 'yar ciki,ya taka kujerar yana bin abinda haisam yace masa step bai st
Cikin mintuna biyar ya kwanceta.
"Ka ajiye screw driver din,kasa hannunka duka biyun ka tallafe fuskar" Yace masa.
Hakan yayi,ya kuma sauke fuskar Ac din a hankali,sai ga wasu qananun kwalabe mitsi mitsi an huhhuda tsakiyarsu kusan guda biyar.
Gaban camera din ahamd yazo ya jera masa su yana huci,zuciyarsa tana wani irin tafasa gumi yana tsatsafo masa a goshinsa.
"Me muke jira da matar nan obbo?" Ya fada a ladabce,saidai hakan bai hana bayyanuwar fushinsa ba.
Wani murmushi ya saki,siririn malalacin murmushi sannan ya maida idanunsa ga ahmad.
"Sultane ahmad......sultane kadai muke jira" Ya amsa masa idanunsa cikin na ahmad din.
*_A B A J I F A R P A L A C E_*
Babban dakin taro ne me cike da wani irin alatu na alfarma.......lafiyayyun kujeru farare da table table masu daukan hankali da nuna alfarma. Chandelier masu na asalin dutsen crystal masu tsananin tsada,masu tsaho ne sosai sun mamaye roofing dakin taron da wani irin yanayi da zai sake nuna maka zallar alfarma da IKO dake tattare da gurin gaba daya.
Rana ce data kasance ta farko cikin tsarin karbar baquwar dake aure da jinin aba jifar. Saidai al'adar ta kasance ta daban data dauki hankulan duk wani me iko da duk wanda ke rayuwa cikin masarautar.
Sati biyu......sati biyu tayi hannun nanay suna wani irin karatu wanda daga ita sai nanay din. Sati biyu nanay tayi tana bata kulawa da kanta,sati gudan da koda su Anaani nanay bata bari sun ganta ba sai da qyar,ballantana haisam da saidai wani lokaci taji muryarsa kawai.
Wani irin shaquwa.....qauna da fahimtar juna masu tarin yawa ne suka gilma tsakanin nanay da Akhnan din. Da gaske,har cikin jininta takejin nanay din kamar safeena......kamar mahaifiyar data rasa din.
Ko nanay bata fito kai tsaye ta gaya mata ba,ita din ta fahimci wata gagarumar soyayya da nanay kewa haisam.
Jiya ta fara b'aro mata wani karatu data dinga jin kamar zata nutse.
"Dokoki da qa'idar daya kamata kowacce mace ta kiyaye......mu'amalar auratayyarta da miji......yadda zaki kai kanki ga mijinki,yadda zaki karbeshi a duk sanda ya kawo kansa gareki......yadda zaki karanci yana cikin buqatarki........da yadda zaki bashi kulawa" Duka sanda nanay ta jero kasa hada idanu tayi da ita. Sarai nanay taga hakan a tattare da ita,amma tayi kunnen uwar shegu kaman bata fahimci Akhnan najin nauyi ba. Abu daya kawai dakewa nanay dadi shine......wata irin kwanya data fahimci Akhnan nata ita.....saurin ganewa da dauke komai,har wani lokaci murmushi yakan kubce mata,can qasan ranta kuma takance.
"Bansan wadanne irin yara zaku haifa ba keda Muhammad......kamar sai daya gwada ya samu mace me shige basirarsa?".
Cikin wata shiga ta alfarma ta fararen tufafi Akhnan din ke zaune,fararen tufafin da fararen duwatsun dake jiki suka qara musu wani irin kwarjini da daukan hankali.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
A iya kwanakin al'amuran sun sake sanyayar mata da jiki. Tana ganin wata sabuwar duniya.....sabuwar rayuwa.....sabuwar daular masarautar da kamar za'a ciyar da kai da lu'u lu'u. Karo na farko data fara sanin cewa SAMAN KOWANNE MULKI AKWAI WANI.....SAMAN KOWANNE IKO AKWAI WANI......SAMAN KOWACCE IYAWA AKWAI WATA.......SAMAN KOWACCE ALFARMA AKWAI WATA.
A iya suturun da aka ware mata kawai ta sani sunkai adadin abinda ta mallaka a rayuwarta......tabbas inda narka kudinsu za'ayi ba abinda zai hana sukai adadin dukiyar da take taqamar ta mallaka. Kullum idan ta kwanta zuciyarta na cika da mamakin ME YAJE YI AGADEZ?.....me yasa ya qasqantar da kanshi?,me yasa ya zabi wofantar da dukkan wannan gatan nasa da yake dashi?,ya zabi rayuwa qarqashin alfarma?,bayan alfarmar shi take bi da kanta?.
A kwanakin idan tace zuciyarta daidai take tayi qarya. Ta samu dukkan kulawa da walwala,wani irin jiqaqqen gata.....amma aduk sa'ilin da dare zaiyi sai wata irin kewa ta taso ta danneta. Sai wata irin kewa ta rugo ta lullubeta......wata irin kewa da sannu a hankali ta fara sallamawa ta fara tashi daga SABO ta fara juyewa zuwa wani abu na daban......wannna abun da har yau bata yarda da kalmar SOYAYYA bace.
Dukkanin wasu qawaye.....matan sarakuna......dama matan dake da iko da fada aji cikin masarautar aba jifar ne tattare a dakin. Murmushin dake fita daga fuskar mama oromo kawai zai gaya maka rana ce ta musamman.
Daga daya bangaren tana zaune ne cikin rukunin kujerun da iyali kuma jinin nanay da abba jifar ke da ikon zama. Saamee ce,da dukkanin idanunta da motsinta yake kan Akhnan,ba'a iya yau kawai ba......a dukka kwanaki goma sha hudun bata yarda koda kwana daya ya kufce mata ba tare data kusanta kanta da ita ba,ta kuma bar mata shaida da tabon da zata gane ITACE SAAMEE ba.
A kwanaki sha hudun,tayi dukka qoqarinta na neman kusanta kanta da dukka hidimar data shafi sheikh muhammad haisam din,a sanda al'ada ta nesantashi da Akhnan din. Kwanakin sun mata dadi,sun kuma maido abinda take kalla da sunan kulawa tsakaninta da haisam din.
Saidai a yau dukka farincikinta yana neman rushewa,muddin wannan taron ya gudana yadda al'ada tace.....to Akhnan ta taka mataki na farko mafi girma da qarfin da zai tabbatar da sunanta cikin na haisam dama na masarautar.....zata koma amsa sunan KHADEEJA MUHAMMAD HAISAM JIFAR maimakon KHADEEJA MUHAMMAD HAMMUD.
Amsa wannan sunan kuwa shi yake nufin nan da kowanne lokaci zata tare a gidan da zata zamto sarauniya mafi girman iko,gidan da jaridu suketa maganarshi,ya shiga bakin 'yan media da al'ummar gari saboda baqon tsarin ginin da aka masa da tarihi bai taba zuwa da wani wanda ya mallaki irinsa cikin Ethiopia da kewayenta ba.
"Takwarata ce......wadda ta fito daga tsatson mutum mafi soyuwa a gareni.......saidai daga yau tabar amsa sunan Akhnan......." Muryar nanay tayi amsa kuwwa cikin dakin taron daya dauki wani irin shuru kamar babu me rai a cikinsa.
"Tun daga yau.....tun daga yanzu ba baquwa bace......" Ta sake fadi a nutse,sautinta yana ratsa shurun. Sai ta miqe sannu a hankali da wannan haibar nutsuwar da tarin kamala.
Gaban Akhnan ta qarasa,ta miqa hannunta ta riqe hannun Akhnan din sosai cikin nata,sannan tadan dagashi sama kadan
"Za'a kiraki......." Ta sake dakatawa tana numfasawa da wani irin zaquwa tarin qauna da soyayya
"GIIFTII(giiftii a yaren oromo yana nufin mace me daraja ,macen data fito daga gidan sarauta iko ko matsayi,ko macen da ake girmamawa sosai)"
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 65*
"Giiftii" Sunan ya maimaitu cikin kan saamee tare da muryoyin da suka maimaita sunan a tare.
Tasan kuwa abinda ta fadi yanzu hakan nanay din?. Sunan giiftii?,ta yaya zata dauki suna me daraja irin wannan ta bawa macen da bata fito daga asalin qabila da yarensu ba?. Ta yaya zata bari haka ta faru?.
Qasa Akhnan tayi da kanta,tana jin wani nauyi hawaye suna taruwa a idanunta. Me yasa ya zabi daukota ya kawota cikin wannan tarin girmamawar?,bayan ba wani babban abu da tayi masa data cancanci haka?. Meyasa ya tsallake kowacce mace sai ita?,meyasa ita ya zaba?. Wannan kalar halittan bai cancanci SO ba kuwa?.....me zaki sadaukar masa da zaiyi daidai da karamcin daya shimfidawa rayuwarki?" Tuhumar da zuciyarta keyi mata kenan. Wani irin girmansa taji yana hauhawa cikin ranta. Wannan sunan shekaran jiya cikin bincikenta akan qabilar ta gano girma da matsayin sunan.....ta gano irin masu girman matsayin da suke ake bawa shi.....yaushe ta cancanci haka?,wacce irin qauna ce haka tsakanin nanay da mamminta?.
"Jininmu da darajarmu giiftii.........ki riqemin muhammad kawai irin riqon da uwa zata yiwa d'anta" Nanay din ta fada da rauni sosai cikin idanunta. Nauyi maganan itama tayi mata,sai nanay ta zare idonta tana maidawa wani sashen,kamar yadda al'adar hadimansu yake,sunsan komai a sanda ya dace su yishi basai iyayen gidansu sun buqata ba.......wata hadima jakadiya ta matso dauke da wani lullubabben faranti.
Idanun saamee fes a kan farantin,har zuwa sanda Nanay ta bakadeshi,take tayi ido biyu da mayafin nanay din.
Wani mayafi ne me tsananin daraja a idanun nanay din.....mayafi mafi girman tarihi tsada da qauna a gurinta. Irinsa uku ne da ita,wanda duk tsadarsa bata yafashi,ta ajiyeshi kawai a gurin ajiya na musamman cikin kulawa.
Tsakanin hasnaa da balqees data aurar,ba wanda baiso ta bashi shi ya tafi dashi gidansa ba amma ta qiya,sai gashi a yanzun.....a gaban idanunta taga ya daukeshi,ta wareshi,ta kuma lullubawa Akhnan shi.
"An rufeki da darajarmu......kina qarqashin kariyarmu" Jakadiyar ta furta cikin girmamawa,wanda tana daya daya cikin mutanen da sukasan darajar mayafin a tattare da nanay din.
Idanunta saamee ta janye tana kullesu saboda ruwan hawayen da taji suna neman yi mata ba zata sanda su rumaisa ke dariya qasa qasa cike da farinciki.
"Shikenan wallahi,an samu me qwace matsayin captain obbo.......Allah giiftii ta zartashi yanzun dai a zuciyar nanay"
Giiftii " Ta sake maimaita sunan a ranta.
Bawai suna kawai nanay ta bata ba......wata irin daraja ce,ta dagata sama da sauran dukka matan Ethiopia gaba daya.....darajar da sai da akayi shelar dimbin mutane kafin a mallaka mata ita. Ba suna kawai Nanay ta bata ba,matsayi ne da har abada bazai tabe zame mata ba.
Kadan kadan mutane suka fara raguwa,sai mata mafi kusanci na qwarai ga nanay da motii. Sauya hall akayi,wannan hall din yasha banban da wancan,wannan din an yishi ne cikin yanayin da zai bada daman cin abinci ga kowa a sake.
Ba jimawa aka shigo da wani babban tray,wanda kallo daya saamee tayi masa wani murmushi ya subuce mata. Farinciki ne fal fuskarta da wani boyayyen murmushi,kamar ba ita bace a mintunan dazu take fakar idanu tana tsane hawayen fusarta da gefan lallausan mayafinta ba..
Kai tsaye aka wuce da farantin gaban Akhnan din. Ta daga idanu a nutse tana kallon yadda aka jera qananun cups masu qaramin faranti daga qasansa dauke da wannan coffee din na asalin noman qasar oromo.....wannan coffee din da zuwa yanzu batajin akwai wani coffee daya kaishi dadin d'an d'ano saman harshenta. A jere suke da wani irin tsari da zai burge me kallo.....to amma ita.....batasan me zatayi dashi ba.
"Gabatarwa......zaki gabatar da irin taki girmamawar zuwa ga baqinmu masu girma.....manya masu matsayi a gurin nanay dama masarautarmu....muna buqatar ganin taki qwarewar" Saamee ta furta a hankali tana sakin murmushi.
Daga inda nanay take tana jin dadi ne,a nata zaton bayani saamee din ke mata wanda zata fahimta,don haka cikin murmushi take kallo Akhnan din.
Wani abune ya motsa a zuciyar Akhnan din,a nutse ta waiwaya sashen da saamee din ke zaune tana zube mata blue eyes dinnan nata masu daukan hankali.
Tun bata shaidata......har ta fara shaidata. Yarinyar da akwanakin da tayi tare da nanay ita kadai ke matsanta shigowa gurinsu da tarin hidima da maganganu na kulawa akan haisam.
"Nanay captain sheikh bai shigo ba......nanay abincin captain sheikh......nanay coffee din captain sheikh......nanay captain sheik yayi baqi....me za'a kai musu......nanay ruwan zafi.....bazaisha girkin hadimai ba" Sannu a hankali sai abun ya fara mata wani irin. Bata da wata magana ta daban saita captain sheikh,duk wani da'irar maganarta a nan take qarewa,bata sauya suna ballantana wanda kulawarta take kai.
Ta dauka ba zataji komai ba......ta dauka ba zataji wani sauyi daga zuciyarta ba.....to amma a hankali sai ta samu kanta da fara jin wani abu yana matse zuciyarta a duk sanda ta shigo ta ambaci sunansa.
Bata tana d'aga kai ta kalleta ba sai a shekaran jiya.....shekaran jiya da tazo tana fadin..
"Kamar Captain baya da lafiya nanay........naga Dr Aawel ya fito daga sassansa"
"Zan bincika" Nanay ta fadi kaman yadda ta saba amsawa saamee da duk maganan da tazo da ita inde akan haisam dinne a taqaice,bata kuma bari aci gaba da yinta.
Abu na farko daya dasa zargi a ranta,sanda ta daga kan don ganin wacece wannan da maganarta kullum iri daya ce?,kuma akan mutum daya?,sai ta samu idanuwan yarinyar suma suna kanta,saidai kuma wani kallo take mata da yake nuna a sace take kallonta.
Suna hada idanu Akhnan din ta dauke kai tana maida idanunta kan bowl din da nanay ta kawo mata me cike da wata irin dahuwar wani nama da batasan naman meye ba. Tana jinta sanda take takawa tana fita,haka kawai taji wani abu ya mata tsaye a wuya.
Me yasa batasan komai akansa ba sai wata?. Me yasa take satar kallonta irin haka?. Duka duka saamee din kimarta da zatinta a kallon data mata da kuma nata idanun bata wuce irin nasu birra ko bara'atu ba. Bata da wannan haibar sam irin wanda takan hanga tattare dangane dasu rumaisa,hatta da noorah ma,duk da ta gabatar mata da kanta a matsayin qanwar sheikh haisam kamar sauran......amma a yau data daga kai ta kalleta sosai daban take ganinta a cikinsu.
"Zo" Nanay ta kirata da tattausan murmushi da kuma yanayi na qarfafa gwiwa. Tsam ta miqe,tana takawa a nutse tana nufar nanay. Miqewa tsaye tayi,tana duban farantin da jakadiyar ta biyo Akhnan dashi.
"Ki shayar da baqinmu da hannunki" A hankali Akhnan ta gyada kai,saidai can qasan zuciyarta wani abu daban yana harba mata.
Ba shayar da baqinsu bane manufar,abinda tafi fuskanta shine......anason auna karamcinta ne. Idanun Nanay data kalla sun nuna mata komai.....taga kuma yarda da ita da yarda da halinta dari bisa dari cikin idanun Nanay,don haka ta soma takawa a hankali.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Da idanu saamee tabi takunta,ba yau ne ta fara ganin takun tafiyarta ba......amma kuma duk sanda zata kalli takun sai ya kwance mata wani abu cikin kanta. Tana takawa ne majestically......da wani irin yanayi da burgewa a takun yake tasirantuwa cikin kanta,amma kuma wannan halittar ta KISHI take wancakalar da wannam daga idanunta.
"Jin kai ne kawai da girman kai" Shine abinda take bawa duk wani motsi na Akhnan din da takunta. Tana sane,tana kuma lissafe a kwana goma sha hudun data dauka tana shiga dakin da maganar haisam akan harshenta bata taba daga idanunta ta kalleta ko sau daya ba......hakan kuma bawai yana nuna kara ko alkunya ba,ko kuma batajin abinda take magana a kai a dukka kwanakin,aah......tana lura da ita. Wani irin izza gareta.....tarin dagawa da girman kai data lura bada kowa take doguwar magana ba.
Sai a dazun da taje da batun baida lafiyan. Ba rashin lafiyar ya sanya ta kalleta ba.....qilan yadda take maganan ne kamar zata saki kuka.
Wani abu tayi.....wani abu da bata taba yinsa ba kaf tsahon rayuwarta illa ga mutum daya wato SULTANE.
Kujera kujera ta dinga bi cikin nuna girmamawa ta miqawa dattawan cup din bayan ta tabbatar kowanne ta cikashi.
"Allah yayi miki albarka" Suka dinga furtawa ga duk wanda ta miqawa. Wani irin dadi ta dinga ji tun kafin ta gama,can qasan ranta takejin wani irin farinciki. Har cikin jikinta takejin addu'ar tana ratsata
"Haka bakin babba yake akan yaro?" Ta dinga fadi can qasan zuciyarta. Tunda take ita ake miqowa.....tunda take ita akewa hidima,yau sai gashi tayi qanqanuwar hidimar da aka tara mata tulin albarkar da batasan yawanta ba.
Sanda take komawa mazauninta sai hankalinta ya lula can wata duniyar. Sanda tana da shekaru goma a duniya......sabda morsa safiyya ke tattara mabuqata dattawa a duk ranar juma'a. A jerasu tasa a daukota ta dinga binsu da sadakar kudi da abinci kamar haka suna sanya mata albarka.
Abun yana mata dadi a sannan,haka kawai ba tare da itama tasan dalili ba,amma daga randa mammina ta fahimta saita soma sukar abun,a hankali sai abun ya fara fice mata daga rai,ta bijire ta kuma daina zuwa din,hakanan morsa safiyya ta haqura ta sanya hairaan taci gaba har zuwa sanda aka aurar da ita.
Cikin wata Royal buggy suke tafiya a nutse cikin hanyoyin masarautar. Wata qaramar mota da ta sake sanyawa Akhnan sallama irin ikon masarautar. Tana da tsananin kyau da daukan hankali,a bude take da wani irin yanayi dake nuna iko da isa.
"Zamu qarasa mu duba muhammad" Nanay tace da Akhnan dake zaune a gefanta. Batace komai ba,ta danyi qasa kawai da kanta,haka kawai taji zuciyarta tana tsalle,tana motsawa a nutse da wani yanayi data jima bata jishi ba.
Cikin qasaitaccen parlor din nasa da yake da wasu irin views har guda uku,wannan ya bashi wani irin tsari haske me kyau da kuma hangen qawatattun tsirrai data lura kamar a nan aka haliccesu. Wasu irin furanni da flowers masu kalolin dake daukan hankali,furannin da kana iya jiyo mabanbantan qamshinsu daga cikin parlor din.
Duk da kanta a qasa yake,amma hakan bai hanata fahimtar tarin banbancin da bangaren da yake dashi ba da dukkan sauran sassa na gidan. Tun daga yanayin tsari da tsarin shiga na security da hadimai dake kai kawo a sassan,yanayin sanyinsa da wani irin lallausan qamshi da iskar sashen gaba daya take bayarwa tamkar an halicci wata qaramae aljanna ce cikin gidan.
Daidai da qasan sashen da takalmanta ke takawa tamkar gaya mata suke
"Barka da zuwa wani sashe na musamman" Komai na sashen cikin wata nutsuwa yake,daidai da iska da shuke shuken da suke cikin sassan sai take ganin tamkar su kansu nutsuwa ta ratsasu,kamaar akwai wata tarbiyya ta daban tattare dasu.
Tun kafin sukai doorstep din ta fahimci akwai wani babban baqo cikin parlor din,akwai wani me girma dake zaune a ciki,saboda yawan adadin dogarai dake zagaye da kowanne taku na sassan nasa.
Tana daga gefan nanay sanda suke sallama cikin parlor din. Su biyu ne rak a ciki,wanda kafin ka qaraso zaka dauka tarin mutane ne a ciki,amma haiba da kwarjinin mutane biyun dake dakin a idanun Akhnan sai taji kaman a cike dakin yake.
Haisam.....wanda a kansa idanunta suka fara sauka. Wani irin sauka a hankali tamkar fadowar ganye daga jikin reshen bishiya zuwa qasa. Cikin ba zata nashi idanun suka nutse cikin nata.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*