Kenza eBookz

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 39

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 39

L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 39: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 39. A hankali taji kaman qafafunta suna…

3,364 words

A hankali taji kaman qafafunta suna lanqwashewa......wannan nauyin dake cike da narkakkun qwayar idanunsa yana sauka a kowacce gaba ta jikinta. Wani irin kallo da ta jishi a yau har cikin jininta.....wani irin kallo da takejin kamar sai ya huda fatarta sannna ya huda tsokarta,ya kuma huda qashinta sannan yakai ga bargonta bayan ya tsinke kowacce jijiya ta jikinta. Wani zuzzurfan kallo da bai taba yi mata irinsa ba.....wani irin kallo da a yau karon farko ta jishi sama da kowanne kallo daya taba yi mata a rayuwarsa.

Sallama takeso tayi masa amma ta kasa......duk yadda taso motsa labbanta tayi sallamar amma abun ya gagareta,saidai ga tarin mamakinta sai taga ya motsa labbansa yana lumshe wadannan narkakkun idanun nasa yana furta.

"Wa'alaikumussalam warahmatullah" Abinda yadan qara mata rudani akan wanda take ciki. Itace ta samu nasarar yin sallamar ba tare data lura ba?,ko kuma shine kunnuwansa sukaji masa haka?.

Ta qarfafi kanta da dukkan iyawarta,ta samu takai kanta saman daya daga cikin sofas din dake daura da tasa ta zauna. Qasa tayi da kanta kada,har yanzu tana jin nauyin idanunsa dake kowanne sashe na jikinta.

"Sannu......ya jikin?" Ta fada da hausa saboda bataso ya amsa mata da French ya qarasa kassara mata zuciya a daidai wannan yanayin da take qoqarin daidaita kanta da qoqarinta.

"Alhamdulillah" Ya fada kaman wanda yake tsoron kada aji sautinsa,yana maida jikinsa ya jinginar ga massage pillow din still idanunsa a kanta,baiyi kuskuren janyewa ko sau daya ba.

"Akwai magunguna inji nanay a cikin gurincan......amma kafin sannan me zakasha?.....coffee ko black tea?" Ta fadi tana daga blue eyes dinta da wani irin sanyi tana zubesu a fuskarsa.

Ji yayi a sannan kamar yana nutsewa cikin ruwan qanqara......wani irin abu me sanyi yana ratsashi daga cikin idanunta kai tsaye zuwa cikin nasa idanun dama gangar jikinsa gaba daya.

"What a beautiful eyes" Ya furta can qasan maqoshinsa,labbansa kadai suna motsawa a hankali ba tare da sautin ya fita ba.

Duk wata laka ta jikinsa ta gama zare masa ita,bayajin bakinsa zai iya cewa komai da ita,sai kawai ya daga mata kai a hankali.

Wannan kallon nasa kasheta kawai yakeyi......wadannan idanun nasa,har yanzu bata tsinci wani abu dake kassarata ba.....wani abu dake mata illa kaf rayuwarta ba irin yadda idanunshi yake da tasiri a kanta ba.

Ta motsa tana miqewa a hankali,still ya sakejin bazai iya raba idanunshi da kallonta ba. Binta yayi da kallo da dukka idanuwanshi......irin kallon nan nakai tsaye yana kallon yadda take dagawa da sauke Qafafunta a hankali,yana kallon yadda qugunta ke juyawa kamar da gayya takeyin hakan dashi.....yana kallon yadda iska ke kada mayafinta hade da gashinta daya fito ta qasan mayafin.

Har ga Allah kallon ya mata nauyi.....har ga Allah takejin yadda idanunsa ke keta kowanne tsaro na jikinta,da wannan qarfin halin da wannan qarfin gwiwar tabi direction din dake nuna mata inda kitchen din gidan yake takai kanta kitchen din da qyar.

Daidai lokacin da take cikin kitchen din,take binsa da kallo kusurwa kusurwa. Karo na farko a rayuwarta data samu daman taka cikin kitchen din,bama kitchen din ba,karon farko data kusanci cikin aninihin ginin nasa kenan. Tana ji a ranta zata riqe amanar haisam kamar yadda nanay ta buqata.....zata riqe amana kamar yadda tace a gabanta.....amma hakan ba yana nufin zata kasa ko zataqiyin yaqin da zata samu nata gurbin da muhallin a zuciyarsa ba. Hakan kuma ba yana nufin zata kasa yaqarta ta hanyoyin da tasan zata tsira da nata kusancin da soyayyar ba.

Tsaiwa tayi a hankali tana jingina da qofar kitchen din,tana jin adadin bugun zuciyarta,saita maida idanunta ta lumshe tana qoqarin saita bugun zuciyartata.

A baya ta dauka ita din jaruma ce,a baya idan akace mata iri ko shigen haka zai faru da ita game da wani d'a namiji.....ya sakata fargaba.....ya ninka bugun zuciyarta to zata qaryata hakan......amma cikin lokaci qanqani ya zama namiji na farko daya fara birkita lissafin qwaqwalwarta dana rayuwarta gaba daya.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

"Me yake kallo?.....me yake kallo haka tattare dani?" Ta yiwa kanta da kanta tambayar murmushi yana qwace mata tana kuma bude idanunta a hankali.

Cikin idanun samee nata idanun suka sauka,saamee din da tayi tsaye tana qarewa akhnan din kallo wani kibiyar kishi yana hudata

"Haka take da kyau?,haka take dama?" Ta maimaitawa kanta tambayar har taji kaman zata zauce cikin qasa da minti uku. Wannan shine karo na farko data ganta kusa da kusa haka,ba shigar nan me nauyi me ado da take tunanin ita ke qara kwarzantata da qara mata kyau,ashe shigar ba abinda take mata sai sake boye kyanta.

Haka kawai taji yarinyar batayi mata ba. Halittarta ce bata qaunar SHISHSHIGI sam,idan zata soka zata soka kawai.....idan baka mata ba baka mata ba. Batason a dinga shiga al'amuranta tun asalinta,wannan ya sanya tashin farko aka samu wani irin clashing me girman gaske tsakaninta da saamee.

"Barka da warhaka" Saamee din ta fadi,saidai tana cire kusan fiye da rabin irin girman daya kamata a al'adance ta bata cikin gaisuwar.

Minti kusan guda cikakke,minti gudan da saamee ta cire tsammani ta fidda rai akhnan din zata amsa mata,bayan minti gudan sannan muryarta ta motsa da

"Barka" Ta fadi tana takawa da wannan tafiyartata da saamee ta tsana. Wannan tafiyar da take sawa saamee din taji ita qasqantacciya ce.....wannan tafiyar da saamee ke jinta kamar cikin tsakiyar ranta.

"Me kike da buqata?" Ta furta tana d'an duban akhnan din da taga tana wucewa kai tsaye zuwa kitchen island din dake tsaftace ba komai a samanshi.

Bata amsawa saamee din ba,don hankalinta ma bawai yana kanta bane kwata kwata. Tunaninta da hankalinta yanzun ya tafi ne akan recipe na black tea da nanay ta aika mata cikin menu dinnan. Kayan hadin da komai daya kamata ta saka. Zata iya?,zai shawu?,a karon farko ita akhnan zata dafa wani abu a duniya?.

Yadda bata amsa mata ba,haka saamee bata sake cewa komai ba,bata kuma fita daga kitchen din ba. Taja baya ta tsaya tana qarewa akhnan kallo qasa qasa.

Yau wataqila ta zama ranar farinciki ta farko a gurinta. Ranar da akhnan din zata gaza dafa abinda ya shigo da ita kitchen din,wanda koma meye ta tabbatar haisam dinne zaiyi amfani dashi. Ta fahimci hakanne saboda kusan salo da pattern don nanay kenan. Sarrafa komai da motii zaici ko yasha da hannunta muddin tana da lafiya.

Ta sani.....ba abu bane boyayye,akhnan din ta fito daga gidan sarautar da ita daya ce suka mallaka......ta kasance SHALELE ba'a masarauta kadai ba......har a dukka qasar agadez gaba daya. Tana qarqashin kulawa da tarin hadimai....to mene zata iya?,me zata iyayi saidai komai ayi mata.

Daga wucewarta yaji parlor din ya masa shuru.....daga wucewarta sai yaji kamar ta wuce da komai....komai kamar ya tsaya kaman yadda wayarsa da omar ta katse ba tare daya sani ba.

Baiyi wani tunani na biyu ba kawai ya miqe a hankali,ya zura tattausan slipper din daya dace da yanayin shigarsa ya soma takawa a hankali kanshi tsaye yana nufar kitchen din.

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 70*

Ta gama duba duka kayan hadin,ta kumayi qoqari sosai wajen fidda komai ta ajjiye saman mulmulallen bar counter dake kitchen din,wadda aka zagayeta da wasu irin kyawawan kujeru masu tsaho.

Sake komawa tayi tana duba bangaren electric din dake ajiye guri guri cikin tsari a kitchen din,duk wani nau'ikan kayan wuta kala kala,a nutse ta zabi coffee maker dan madaidaici daya,ta dawo dashi saman bar counter din ta ajiye.

Kayan hadin tea din take dubawa da daya da daya tana zubawa,kai zakace batasan da tsaiwar saamee cikin kitchen din ba. Koda motsinta bazai nuna maka tasan da tsaiwarta ba ballantana aikinta.

A nutse ya tura qofar kitchen din da sallama a bakinsa cikin sautin nan nasa. Husky voice dinsa me wani irin zurfi da sautin amo me tsayawa a rai da zuciya.

Idanunshi a kanta yana mata wani duba me dauke da mamaki,ta masa wani irin kyau da tsaiwarta a kitchen din,sai ya ganta wata mace ta daban.

Ba wannan akhnan din ba yake kalla ba.....ba wannan biftu din ba.....ba wannan khadeejan ba princess of agadez ba. Wata matar gida....responsible matar gida. Da iya tambayarsa kawai da tayi me zaisha din?,ta gama kwance masa tunani.....da iya tambayar data masa kadai a dazun ta goge masa tunani.....ballantana yanzu da yazo ya sameta a tsaye da nufin zata dafa abinda zata bashi da hannunta?.

"Ya salam....." Ya fada a hankali,mamaki yana sake kwance masa kai.

"Barka da warhaka obbo......fatan ka fito lafiya" Saamee ta fadi da wani iri narkakken ladabi yana lanqwashe kanta.

"Barka kade" Ya amsa mata idanunshi da zuciyarsa gaba daya suna kan akhnan dake auna adadin kayan hadin tana zubawa cikin mini coffee maker din.

"Ya jikin?,Allah ya qara lafiya me dorewa". Ta fada tana satar kallonsa.

" Ameen" Ya amsa mata,daidai sanda idanunta sukayi kyakkyawan gani. Hankalinsa da gangar jikinsa dukka akhnan suke nufa. Wani abu me nauyi ya danne mata zuciyarta. Bataji zata iya bar musu kitchen din,bata jin zata iya basu wannan space din,duk da adoka da qa'ida barin kitchen din ya zama wajibi a kanta.

Taji shigowarsa......sallamarsa da takowarsa.....amma bata daga idanu sam ta kalleshi ba,saita zabi ci gaba da abinda takeyi.

Wani bala'in burgeshi tayi.....wani bala'in tafiya tayi dashi. Wannan jan ajin.....wannan basarwar,wannan dauke kan data sake masa sanda yake jan daya daga cikin kujerun bar din ya zauna idanunsa zube a kanta.

Baice mata komai ba kaman yadda batace masa ba,sai wani irin kallo daya kafeta dashi tamkar an bashi gadinta da aikin lissafa duk wani motsi nata.

Taji idanunsa a kanta,amma still bata dago ba,kallonshi yakeso tayi....koda sau daya ne da wannan blue eyes din nasa,amma akwai alamu gilmawar wani irin izza a idanu da fuskarta da yake hange.

Ya fahimci da gaske ba zata kalleshi ba,sai ya miqa zara zaran yatunsa ya zare cokalin da take saka amount na hadin tea din yaci gaba da zubawa shima ba tare da yace komai ba. Hakan baisa ta kalleshi ba,taci gaba da tsaiwa kawai tana harde hannayenta a qirjinta.

Kawai takejin batason wanzuwar yarinyar a kitchen din. Haka kawai takejin zamanta a kitchen din bai mata ba. To amma ba zata bata kalmomin bakinta ba ko sau daya a kanta ba. Tunda tazo Ethiopia ko sau daya ba wani wanda takejin bai mata ba......amma akan saamee taji wannan,bawai tana da wani babban dalili bane,don bata da lokacin saka hankali da idanunta akan kowa sai akan abinda ya shafeta tun asalinta SHISHSHIGI shine kawai abinda bataso bata qauna.

"Saamee" Abinda ya fadi kenan idanunsa akan coffee maker din da yake duba adadin kayan daya zuba. Ba tare daya qara kowacce kalma ba saamee din ta soma takawa tana fita daga kitchen din. Zuciyarta kamar zata fashe.....fadin qirjinta tana jin ya yiwa zuciyarta kadan,wani abu ya dunqule mata ya fidda wani zazzafan hawaye daya sauka saman kuncinta.

Kunnata yayi ya saitata,sannan a hankali yaja kujerarsa baya yana zube idanunsa akan Akhnan. Still miskilar tasa ba abinda ya sauya,kamar tasan me yake buri?,sai kawai ya miqe a hankali yana aza hannunsa saman sassalkar sumarsa da duka yau take a hargitse yana sake hargitsata hade da wani yanayi da yaji yana yamutsa kwanyarsa gami da saukar masa da wani irin tashin tsigar jiki.

Ganinta yake son yayi in full details bada wannan mayafin ba.....so yake ya ganta gayarta,don haka ya soma takawa a tausashe,ya kuma mamayeta ba tare data ankara ba,saiji tayi ya debe.mayafin kanta gaba daya ya duqunquneshi cikin hannunsa. Sanda ta juyo yana dunqule mayafin ne,ya kuma zuba mata ido yana ganin yadda sumarta ke warwarewa daga dan qulletan da tayi da sirirn band.

"Ma sha Allah" Ya fada can qasan ranshi yana hadiye wani yawu. Yadda sumar ke sauka tana bajewa zaman bayanta har dab da mazaunanta ya sake harba wani abu me qarfi gaske zuwa ga sassan jikinsa. Ta zube masa blue eyes dinnan da yaga tsoro qarara a cikinsu. Taku daya yayi ya isa gareta,ya kuma.jawota cikin jikinsa,wannan karon bai jira komai ba ya mata wani kyakkyawar runguma data amsa sunanta cikin jikinsa.

Wannan karon.....bada gangar jiki kawai ya rungumeta ba,wannan karon da dukka zuciyarsa ta dinga ji kaman ya rungumeta,ya narke mata sosai cikin jikinta,ta motsa kadan amma sautinsa ya sauke mata komai.

"Jinyata nanay tace kiyi please,ba haka nanay takeyimin ba....idan bani da lafiya na kwanta akan cinyarta.....bata cewa na tashi......kada kici amanar da nanay ta baki mana" Ya fada yana sake shigewa cikin jikinta kamar dukka burin rayuwarsa dama maslahar rayuwar tasa ta ta'allaqa da dogon wuyanta ne.

Tana da saurin amincewa da maganar mutumin duk da ta bawa fili har ya shiga rayuwarta,don haka bata ji cewa maganansa ba haka bane,saita daina yunqurin zamewar,ta tsaya sosai kaman yadda yakeso,wannan ya bashi daman sake laqumeta cikin faffadan qirjinsa yana sansanar qamshinta sosai kamar zai zuqe duk wani qamshi da yayi saura a jikinta.

Cikin mintuna qalilan yaji ya fara birkicewa. Itama birkicewar ta fara yi,don ba qaramin dafi yake saukar mata ba daga zazzafan numfashin da yake saukewa wuyanta,sannan taji ya fara sauya akalar yana kawo hancinsa saman qirjinsa kaman yana son cusa kansa tsakanin halittun qirjin nasa.

Fuskarsa ya zare a hankali sanda coffee machine din ya kashe kansa da kansa bayan yakai inda ya kamata yakai. Ta dauka zai zare jikinsa ne.....amma ga mamakinta sai kawai taji ya dagata cak ya dorata saman kitchen island din.

Bar chair din ya jawo dab da ginin da take kai a zafafe sannan ya zauna akai,ya raba cinyoyinsa tsakanin nata,nata qafafun suka kasance tsakiyar nasa.

A yau yana jin duk wani qarya da yakewa kansa tana warwarewa.....kafiya da taurin kansa yaji gaba ana kwanceshi daya bayan daya.

Yasa hannunsa,ya kamo zara zaran yatsunta ya cusa tsakiyar nasa ya matsesu gam,saidai a tausashe yadda ba zataji zafi ba. Ya zuba musu idanu yana kallonsu kafin ya maida dubansa ga fuskarta sannan qirjinta dake wani irin bugawa.

"Bugawar da zuciyarki takeyi a kullum tana wuce kima" Ya furta softly yana lumshe idanunsa kamar wanda ya tashi daga baccin da bai isheshi ba.

Qoqarin daidaita numfashinta da bugun zuciyarta ta soma yi,saidai ya hanata wannan damar ,yama sake rikita mata lissafinta gaba daya sanda yace da ita.

"Sau nawa zuciyarki zata gaya miki sona kike kafin ki amince da abinda yake gaya mikin?" Saura kadan,saura qiris numfashinta ya qwace mata,saura kadan ta rasa fitar numfashinta na daqiqa ta samu ta riqeshi da qyar ta hanyar zaro idanunta waje......amma wadannan tsimammun idanun nasa.....wadannan idanun nasa masu cike fal da dafi da maganad'isu suka hanata masa qarya,illa furta kalmar.

"Ni?" Da tayi adan birkice.

Duk da abinda yakeji cikin jikinsa amma hakan bai hanashi sakin wani siririn murmurshi ba bayan ya lumshe idonsa ya kuma.budesu yana gyada kansa.

"Yes.....ko kin bani dama na fiddo gaskiyar hakan?". Wani sabon kallon daya watsa mata ya sanya ta fara jin kamar narkewa takeyi tana bin jikin island din,sai kawai ta yanke ture yatunsa a gigice tana fadin.

"Tea dinka ya zama ready"

"I know" Ya amsa mata kai tsaye yana sake hanata damar sauka daga kan island din kamar yadda tayi niyya da farko.

Yana sake mamayeta da hannuwansa.

Ta bayan mazaunanta ya zagaya da hannunsa,ya kuma soke yatsunsa cikin na juna,ya mata qawanyar da babu damar ta motsa,gwiwoyinta suna tokare da qirjinsa,sai kawai ya sanya kafadunsa ya raba tsakanin qafafunta ya shige ciki yana dora kansa saman tattausar cinyarta.

Gigicewa tayi gaba daya,ta dora duka hannunayenta saman kansa da niyyar ture kansa,saida dogayen yatsunta tuni suka samu daman nutsewa cikin tattausan gashinsa.

Wani irin abu yaji yana ratsashi,ya lumshe idanu yana sauke wata ajiya zuciya. Kaman susa take masa cikin kan kasa yaji,wani abu me dadi yana ratsa tsakiyar kansa nasa har cikin kwanyarsa.

"Karki janye......don Allah....." Ya fadi a hankali sanda take zare yatsunta ganin yadda ture kan nasa bai tsinana mata komai ba.

"Pleaaseeeeee" Ya sake fada da wata irin raunanniyar murya.

"Don Allah.....amana nanay ta baki.....na tabbatar nanay tace ki kula dani" Ya sake fadi yana qara matse cinyoyinta zuwa mazaunanta tare da nutsa kansa sosai cikin cinyarta kamar zai narke ya zama daya da fatar jikinta.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Yadda yayi maganan.....yadda ya fada din sai ya kasheta jiki gaba daya,saita samu kanta da tura yatsun nata kamar yadda ya buqata a hankali da wani irin yanayi da batasan zai haifar masa da komai ba.

"Biftuuu" Ya kirata a nutse yana karya shurun daya ratsa tsakaninsu,idanunsa suna lumshewa da budewa gami da sake jirkicewa daga launin kalarsu.

"Na'am" Ta fada a hankali tana zare hannuwanta saboda wani irin bugawa da taji zuciyarta tana yi daga cikin qirjinsa dake kwance saman cinyoyinta.

"Akhnaaan" Ya sake kiranta,wannan karon kiran daya mata har yafi ka dazun,a daburce tace.

"Shayinka ya huce"

"Na sani" Ya fada da birkitattun idanunsa daya daga yan kallonta. Kallon ya mata nauyi,kashe mata jiki yake sosai....kwarjininsa narkata yakeyi,saita kau da kanta gefe tana jin kowacce gaba ta jikinta tana amsawa.

"Zakasha magani......ka bari na dauko maka kasha.....don Allah" Ta qarashe roqo,don neman inda zata kufce takeyi.

Kamar bazai janye ba,kamar ba zaice komai ba,sai taji yana zare hannuwansa a hankali daga jikinta yana binta da wani sassanyan kallo.

Rawa hannunta yake sosai sanda take zuba masa tea din a cup. Nisan tunanin da tayi ya sanya cup din ya kusa cika bata sani ba. Gigicewa tayi,saboda wani abune da bata saba ba. Hannunta na rawa takai hannunta kan makashin,wallahi takai ga dannawa taga dogon yatsansa me wasu irin fararen farce tamkar baisan wani abu da ake kira da dauda ba ballantana qura.

Janye hannunta tayi,saita daga idanunta suna hada ido dashi. Girarsa daya ya dage mata,ta kauda kanta da sauri tana neman hanyar da zata zame,saboda ya tazarar dake tsakaninsu duka duka bai wuce taku hudu ba tsakani.

Daga nan tana iya jin saukar sassanyan numfashinsa. Daga nan tana iya jin qamshin jarababben turarensa da ya manne mata jikin kayanta gaba daya kaman yadda ya game jikinsu gaba daya

"Ki bani" Ya furta a shagwabe da wani irin laushi yana qare mata kallo tamkar Allah ya aikoshi. Tadan kalleshi kadan a sace tana mamaki. Gashi ga tea din,asalima shine ya kashe maker din amma ya dauka baze iya ba.

"Kiyi haquri.......bani da lafiya,kula dani akace kiyi sosai,haka nanay ke kula dani idan bani da lafiya. Nayi kuka akan cinyarta....nayi bacci duka bata hanani" Ya fadi da wani irin laushi. Yadda yake maganan sai taga ya koma mata yaro qarami,irin qanqanin yaron nan da bai wuce shekara goma ba. Kasa jurewa tayi,sai data sake satar kallonsa sannan ta kauda kai da sauri.

"Baki yarda ba ko?" Ya fada sanda take miqa masa coffee din,sai ya hada da yatsunta ya riqe cikin nasa yana kasheta da narkakkun idanunsa.

Yadda yake kasheta gaba daya tana jin kamar zuciyarta zata narke ta fito daga qirjinta,sai taji me yayi saura,narke masa nata idanun tayi kamar me neman tallafi. Wani abu ya damqi zuciyarsa da wani matsa da sai daya lumshe idanunsa sannan ya budesu

"Zaki yarda......."

".......wataran" Ya fadi kalmomi biyun a rarrabe yana sakar mata hannun a hankali.

Zama yayi saman kujerar bar din yana sipping coffee din a hankali. Yayi dadi....dadin da baisan me yasa yayishi ba. Hannunsa ne ko hannunta,ko qare mata kallon da yakeyi sanda take kai kawo tana duba freezers din kitchen din bayan ya hanata dankwalinta qememe.

A duk sanda zatayi taku daya sai yaji gaba daya duniyarsa ta girgiza,ya zame mug din yana ajiyeshi sanda yaji haqurinsa yana qarewa.

"Halal dina ce.....lada Allah zai bani" Ya fadawa kansa da kansa yana jin yadda tafin hannunsa dana qafarsa suna daukan wani irin dumi.

Agogo ya kalla yana duba lokacin sallah,a hankali ya zame dubansa yana fadin

"Lokacin sallah yayi" Muryarsa a shaqe tana fita da qyar.

Readers Also Read

More by Huguma