L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 51
L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 51: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 51. *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER…
3,366 words
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 90* _______________________ https://chat.whatsapp.com/IZGMwJXP8Oa5qUc4sDSKZv?s=cl&p=a&mlu=3
*_YI JOINING DON SAMUN DAMAN KOYAR ABUBUWA KAMAN HAKA_*
Abaya Stone laffaya Glitter laffaya Stone veils Glitter veils Bead work Paint work
08036027448
*_Karki bari wannan sassauqar damar ta wuceki_* ____________________________
Qarfe shida ne na safe,meye ya faru da zaice lallai saita take dokar nanay ta fito da safen can bayan sassan nanay?. Ya bari kowa ya tashi,ido na ganin ido ya shigo ganta mana?. Kafin ta sauke wannan tunanin kiransa ya shigo kai tsaye.
"Gan.....ganinan" Ta fadi muryarta tana rawa kadan. Saita zame wayar daga kunnenta tana ajiyeta. Tsoro take kada ya shigo kaman yadda ya fada,ya taho dakin kansa tsaye,taje suyi kacibus da nanay,to tace mata me?,ta kare kanta da wacce hujja?.
Slippers masu tashi ta saka bayan ta daure igiyar hijabinta a bayan kanta,wanda hakan ya bawa tudun gashinta dake boye a hijab din nunawa.
Kamar wata barauniya haka take takawa,sannu a hankali tana bude parlours da dakunan zaman baqi tana bin direction din daya gaya mata.
Har ta gama shiga da fita zuwa hanyar da zata kaita bayan sassan ba wanda ta gamu dashi,sai a qofar qarshe rumaisa ta tura tana shigowa hannunta dauke da wani file.
Baya taja da sauri tana bawa akhnan hanya fuskarta da murmushin girmamawa tadan rusuna,duk da ta girme mata kadan.
"Barka da safiya matar captain".murmushi akhnan ta qirqiro,don har ga Allah adan rude take.
"Barka kade likitarmu.....mun tashi lpy?"
"Lafiya alhamdulillah,ya gajiya,ina fatan bamu gajiyar dake ba"
"Alhamdulillah likita"
"To ma sha Allah,bari na qarasa ciki,saikin dawo" Rumaisa ta fadi tana yin gaba. Da dan mamaki akhnan tadan bita da kallo,basu da damuwa kuma basu da matsala,sanya idanu ko bin qwaqwafi. Wata rayuwa suke simple,basu matsawa rayuwar kowa ba.
Inda watace,koda bada wata manufa ba saita tambayeta ina zata je?,amma ita tayi gaba abinta tana sabgar gabanta kawai.
Maida qofar tayi tana ficewa tare da qoqarin bin hanyar daidai.
Komai fari ne a jikinsa,tun daga kan jallabiyyar jikinsa har xuwa thobe din dake matsayin kamar after dress daya dora saman jallabiyyar. Hakanan takalmin qafarsa.....da amam din daya dora(rawani),wanda ya masa wani irin nad'i dake nuna zallar qwarewa wajen sarrafa daurin rawani saman kai.
Ya fita fes.......sak matashin yariman malamin nan da duniya keyi dashi. Ilimi.....kyau sarauta da dukiya gaba daya. Qamshinsa kawai ke kai kawo a gurin da wani tattausan yanayi daya saje da safiyar ranar,safiyar da ba wata wadatacciyar alamun samun rana a wunin gaba daya,saboda yadda hadari ke lullube da ko ina.
Idanunsa ya zube fes a kanta,idanun nasa suna lumshe kansu suna kuma budewa.
Farar fata cikin fararen kaya,wani mugun kyau tayi masa,tamkar sabon fure daya fita a ranar,aka samu arashi kuma wadataccen ruwan sama ya sauka a ranar.
Wani irin abu yakeji yana fusgarsa zuwa gareta......kyawawan blue eyes din nan nata da suke juyawa a hankali,da alama tanason hango inda yake tsaye.
_ki taimakeni karki fadi.....idan kika fadi har cikin zuciyata ciwon zai kasance......ki kalli gabanki_
Saqon daya shigo wayarta kenan,idanunta ta daga a hankali bayan ta gama karanta saqon tana miqar da kallonta zuwa gabanta.
Yana jingine da wata farar mota qwaya daya,kansa da idanunsa dukka suna kan wayarsa. Ta lumshe idonta tana hadiye wani abu a hankali.
"Ya hadu" Ta fada can qasan maqoshinta tana motsa labbanta a hankali. Karo na farko da idanunta ya taba sauka akan wani d'a namiji taji ya wuce da dukka numfashinta da nutsuwarta. HAISAM.....wani namiji da yasha wucewa da numfashinta.....tunaninta......nutsuwarta dama komai nata. HAISAM d'a namiji a duniya na farko daya taba mallakar tunaninta da zuciyarta,daga qarshe ma ya mallaki gangar jikinta gaba daya......itakam ta yaya zata iya rayuwa ba tare dashi ba?.
A iya jiya kadai ta fadawa kanta wannan maganar har batasan adadi ba. Rashinsa a kusa da ita kawai ya sanya baccinta ya zama wani iri......ina ga ranar da zata bude idanu ta tsinci babu shi?.
Wannan JAN AJIN nasa......da wannan basarwar tasa yabar kansa saman wayarsa Kamar ba shine ya hangota yayi directing nata zuwa inda yake tsaye ba.
Sai zuciyarta ta soma motsawa da wannan kalar kishin nasa. Kishinta a yau akan wayarsa yake,karo na farko data fara jin tana kishin wayarsa sosai kamar d'an adam.
Yasan ta taho....me yasa bazai bar kallon wayarsa ya kalleta ba?. Tambabayar data qaraso da ita gabansa kenan,saidai tabar tazarar taku kusan biyar tsakaninsu.
"Ina kwana?" Ta furta a hankali daya daga cikin lectures na nanay suna mata tasiri ciki tunaninta.
Dukka juriyarsa ce ta qare,ya cire kansa daga wayar ya zube mata narkakkun idanun nan,wadanda da qyar suka samu bacci a daren jiya saboda matsananciyar kewarta. Baije gareta ba,saboda yanaso ya yiwa kansa control......yanaso ya barta ta huta,yanaso ta dawo nutsuwarta ta rage tsoron daya yake gani nasa a idanunta.
Kamar wanda abinda ya kawoshi kenan kawai shine kallonta,ya tsareta da lumsassun idanunsa wanda idan kana dan nesa kadan dashi zaka dauka a rufe suke ruf,saboda yadda sukayi laushi sosai,sannan eyelashes dinsa suka sake taimakawa wajen yiwa idanun nasa rumfa.
Ji yayi kowacce kalma ta maqale a maqoshinsa,bazai iya amsa mata ba,sai kawai ya matsa daga jikin motar ya bude murfin ya juya ya mata alama da idanu na ta shiga.
Motar ta kalla sannan ta kalleshi da tambaya fal idanunta,idonsa ya lumshe mata yana girgiza mata kai alamun bayason tace komai,saita hadiyi wani yawu a hankali ta tattara qwarin gwiwarta tunaninta yanason canko mata abinda yake shirin yi
"Wannan fa kamar laifi ne" Ta fada blue eyes dinta suna tara qyallin hawayen tsoro.
Ya gani.....yaga komai dake idanunta. Ya karanci kamar sun hada baki ita da nanay ne sunason wahalar dashi,sai ya soma takawa majestically yana nufarta,bai kuma tsaya ba,sai daya cike duk wata tazara dake tsakaninsu. Qugunta ya riqe sosai ta cikin tattausan tafin hannunsa yana sake jawota gabansa sosai
Kansa yake qoqarin saukewa saitin wuyanta sanda yake bata amsa da wata kasalalliyar murya
"Noooo....." Ya fada yana sauke mata muryar da nauyi cikin kunnenta.
"It's called rescuing my wife" Ya fada yana daukarta cak yana rabata da qasa tamkar ya samu 'yar tsana.
Ta tsorata da hakan,saboda abinda bata zata bane,suata qanqameshi sosai tana riqe wuyansa. Blue eyes dinta a waje sosai,wannan sassanyan qamshin nasa yana tururuwar shige mata hanci.
"Shi bayajin kunya?,baya tsoro kowa ya gansu?,a haka?,a tsakiyar masarautar?".
"Nanay zata...." Ta fadi sanda ya bude motar yasa qafarsa yana qara bude murfin motar sosai ya kuma sakata cikin motar kamar qaramar yarinya,saidai yadda ya zube mata narkakkun idanun nan nasa ya sanya ta kasa qarasawa.
"She'll forgive us eventually....." Ya amsa mata da yaren French da a yau taji ya sake taushi cikin harshensa.
Sukunyawa yayi ya bata wani soft kiss,ta lumshe idanunta tana jin sanyin labbansa akan goshinta. Ta kasa bude idanun tayi shuru tana sauraren yadda zuciyarta ke bugawa cikin nutsuwa,har zuwa sanda ya rufe murfin motar,taji shuru nadan sakanni sannan ta jishi ya shigo gefanta.
"Mu tafi" Ya fada da muryar umarni cikin yaren oromo.
"Ina zai kaimu"? Ta tambayi kanta a nutse sanda take bude idanunta lokacin da taji wannan tattausan tafin hannun nasa cikin nata.
Ya sauke wani abu a kowanne sashe na jikinta,wani irin dumi da tafin hannunsa ke dashi.....wani irin laushi da tasha tambayar kanta.
"Dukka maza haka tafin hannunsu yake?,ko nashi ne haka?"
Kansa taji ya kwantar a hankali saman kafadarta,da wani irin yanayi na shagwaba da narkewa.
"Good morning my princess......." Ya fada yana matse tafin hannun nata a cikin nasa ba tare daya qarasa fadin abinda yaso ya fada din ba,yana jin wani yanayi yana mamayar jikinsa a hankali.
"......Good morning to the woman currently occupying most of my thoughts" Ya sake fada da wani irin taushi yana saka hannunsa ta baya ya zagaye qugunta.
"Morning" Ta fada tana jin yadda harshenta da muryarta suke sarqewa gaba daya. Wani irin kusanci yake bata......wani irin kusanci yake kawowa tsakaninsu da takejin ba zata jure ba. Batason ta sake wani abu da zata bada kanta irin wanda tayi daren shekaran jiya.
"Ina zamuje?banaso nayi nisa" Ta tambayeshi kai tsaye tana jin fargaba kadan.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Murmushi ya sake kawai,sai ya zame ya maida kansa saman cinyarta,ya kwanta rigingine yadda zai samu damar kallon kyakkyawar fuskarta data fito da wata irin kamala ta tsakiyar hijabin,wanda daga qeya acucin da tayi da tudun gashinta ya fito sosai.
Hannunsa ya miqa a hankali ya shafi gefan fuskarta data masa kyau sosai,kaman dazun idanunsa suna lumshewa sannan su bude da kansu. Wani irin murmushi.......classy murmushi da bata taba ganinsa saman fuskarsa bane yake fita akan fuskartasa a yanzu.
"Ina zamuje?" Ta sake maimaitawa tana qoqarin riqe hannunta da a yanzu ya sanya yatsarsa yana zagaya siraran labbanta.
"Wata duniya......" Sai ya dakata kamar me jiran wani abu.
"......inda daga ni saike"
"Hh.....hais" Saita gaza qarasawa ganin yadda ya zubawa labbanta idanu. Ta tuna....sunansa duk sanda zata furta kamar yana kunna wani emotions ne cikin kansa,saita yanke kiran sunan. Da wanne suna zata kirashi ne?,wanda bazai tayar da wata fitina ba?.
Murmushi ya kuma kasheta dashi,wannan soft dangerous smile din nasa kafin ya sake motsa labbansa.
"Zan kaiki wajen da hayaniyar duniya ba zata samemu ba......" Shuru
"Wajen da babu kowa da zai rabamin ke" Shuru
"Wajen da ba wanda zai sake daukemin ke" Shuru.
"Khadeejaaah" Ya kira sunanta da wannan unique accent din da daga bakinsa kawai take jinsa.
"Na gaji da sharing attention dinki da kowa" Ya qarasa fada yana ciro tarin ma'anoni daga qwayar idanun nan nata dake masa haske koda kuwa cikin duhu ne.
"Me zamuyi a duniyar nan ko?" Ya fada yana dage mata dukka girarsa biyun sama. Idanunta ta kawar tana jin kansa sosai har cikin naman cinyarta,tana jin sauti sa muryarsa kallonsa da idanunsa dukka suna sake narkar mata da zuciya lokaci guda a tare.
"We'll breathe" Ya dakata a tausashe har yanzu hannunsa yana shafa fatar fuskarta da ya sakeji ta masa wani irin fitinannen laushi.
"We'll rest" Ya sake dakatawa a kasalance
"And may be......" Ya sake tsayawa
"......finally learn each other properly" Idanunta ta lumshe a hankali. Yadda yake maganan a rarrabe kanshi wani abu yake saukar mata. Tamkar dai yana zaben kalmomin da yakeso yayi maganan ne dasu,ko yana qoqarin kiyaye abinda tafiso cikin dukka jimlolinsa.
Hannu ya miqa a hankali yana shafa kwantaccen gashin dake gefan kunnenta,wanda a baya yake kira da sajen mata. Daya daga cikin wasu abubuwa da yakeso matuqa a fuskar diya mace.
"Inaso wajen da idan na kalleki....." Sai ya sake dakatawa,muryarsa kuma ta sakeyin qasa fiye da dazu kamar me tsoron wani zai iya jinsa.
".......bazan riqa jin lokaci yana gudu daga gareni ba"
"Kana magana kamar a mafarki?" Ta fadi ba tare data shiryawa fadin hakan ba,sai don abinda yake kai kawo kenan a ranta. Wanne guri ne wannan?,wanne abu ya shirya mata?.
"No...." Ya fada da murmushi ne dan sauti Yana laluben qwayar idanunta yanason ya riqeta sosai cikin tasa,saboda yana son ta dauki duk abinda zaice mata seriously.
"I'm talking like a man who finally found peace......" Ya sake sauke wani numfashin,ya juya ya koma rub da ciki yana qanqame cinyoyinta sosai.
".......and is terrified of to losing it".
Wani irin shuru ya ratsa tsakaninsu,wani irin shuru da bugun zuciya kawai ya bari a tsakaninsu.
Bayan kowanne second sake kasheta yakeyi da kalamansa......da ayyukansa dama shigarsa gaba daya. Kalamansa zata iya rantsuwa da Allah bata taba jin masu zaqi irinsu ba.....bata taba jin zababbun kalamai irin nasa ba,wai dama haka malaman suke?,ko shine na daban?,ko shine ya fita daban a cikinsu da cikin maza gaba daya?.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 91* _______________________ DEA’S MODEST ARTISTRY ✨ Aminataccen wajen samun ✔️ Abaya masu kyau ✔️ Lifaya & Veils masu tsari ✔️ Handmade paint work ✔️ Shadda designs ✔️ Elegant modest wears ✔️ Accessories masu kyau da inganci Muna kawo muku kaya masu kyau, tsafta da araha domin kowane irin event 💫 Ko na daily wear, outing, wedding ko special occasions — DEA’S MODEST ARTISTRY na tare da ke 🖤 📍Quality first 📍Affordable prices 📍Neat finishing 📍Classy & Modest styles Ki kasance cikin kyau da nutsuwa ba tare da tsada ba ✨
https://chat.whatsapp.com/IZGMwJXP8Oa5qUc4sDSKZv?s=cl&p=a&mlu=3 _________________________
Hannunsa ya miqa mata a hankali sanda yaji alamun motar ta tsaya. Ba don baya da ikon kamosu ba
"Akhnan....." Ya kirata softly,yana kan cinyarta,har yanzu a rub da ciki,idanunsa kuma a kulle kaman bai shirya su sauka a motar ba.
"......come with me please,na miki alqawarin baki duk kalan space din da kikeso......ba takura.....ba matsantawa.....just ni dake kawai,mu raini soyayyarmu....." Ya qarasa fada yana juyowa rigingine hadi da bude qwayar idanunsa dukka a kanta.
Batasan me yajata ba,batasan yaushe ba. Ita dai ta miqa masa hannunta a hankali,ya riqe cikin nasa da murmushi.
"Bazan saki kiyi regretting ba har abada.....but.....kafin na sauke qafafuna qasa,kice kina sona.....ko sau daya ne.....don Allah" Ya fada yana langabe kai.....ya fada da kalar wannan sakalcin da taga yana yiwa nanay.
Wata kunya ce ta dabibayeta,ta maida idanunta ta kulle a hankali. Ta yaya zata iya......
"Pleeeeeeeeaaaaaaseeeeeeeeeeee....."
"I love you" Ta fada da sauri labbanta suna rawa saboda yadda ya gigitata da sautin da ya yiwa sound din wani mugun ja.
Idanunta kawai ta kalmashe sanda suke takawa hannunta cikin nasa. Wani takun girma,royal walking suke dake bayyana iko ba tare da hayaniya ko qaqarin nuna kai ba. Komai da kowa yasan girmansa ba tare da yace komai ko yayi wani motsi ba.
Dukkan ma’aikatan private terminal ɗin, manya da qanana, suna sunkuyar da kai cikin girmamawa yayin da suke wucewa.
Kyakkyawan private jet din da suke tunkara,idanunta cike da tarin tambayayoyin data gaza hadiyesu sanda suke step na qarshe na jirgin.
"Ina zamuje?" Ta tambaya tana langabe kanta a wannan karon. Ta gaji da tarin mamakin da yake bata,ta fahimci shi din wani allo ne da har yanzu bata kammala karantarsa ba.
"Dubai" Ya amsa mata a taqaice yana gyara mata gefan hijabinta cikin kulawa.
"Dubai?" Ta fada da mamaki fal muryarta idanunta suna dan fita waje kadan.
"Eh...." Ya amsa yana satar kallon reaction dinta.
"Ina neman na abinci ne a wani kamfani,sai suka gayyaceni wani taro da zasuyi" Shuru tayi bawai don ta gamsu da hujjar daya bata ba dari bisa dari. Saidai tayi shurun saboda tasan ba zata fahimci komai ba sai idan shi yaso ta fahimta din.
Abu daya kawa daya sanyata mutsu mutsu,ta dinga jin kamar ta roqeshi.amma ta kasa,kasancewar bata saba neman alfarma akan kowa game da komai ba.
"Me yake faruwa?" Ya yambayeta tana dubanta da lumsassun idanunsa.
"Akwai wani bikin bude company branch na favourite perfume dina.....a dubai ne.....date din saura kwana biyar.......don Allah.....zaka barni naje?" Ta fada da wani salo da yanayin daya qarasa karyashi gaba daya.
"Ya salaammm" Ya fada yana duban qwayar idanunta. Ashe ta iya magiya?,ashe ta iya karyar dakai har haka?,wanne irin so takewa kamfanin da turaren haka.
"Sun iya turare......best perfume brand ever" Ta sake fadi duk a qoqarinta nason amintar dashi. Yadda take magana yana burgeshi,yadda idanunta ke budewa sosai,take sakewa tana magana dashi tafiya yakeyi dashi. Bayason wannan yanayin ya yanke da sauri haka,don haka bai amsa mata ba,sai yaci gaba da kallonta kawai.
"Don Allah.....zan aike musu email na neman invitation din. Nasan zasu bani indai sukaji daga agadez ne. Ko ban samu shiga ba,zan tsaya na jira ganin founder na company din".
" Zakije....zaki shiga.....in sha Allah".
"Na gode" Ta fada da wani irin murna har tana rungumarsa bata lura ba. Sai kuma tayi yunqurin janyewa da sauri,saidai ya rigata da zafin namansa,ya jawota zuwa cikin jikinsa yana cewa.
"Good girl,wannan shine lada na ai,ya zakimin rowa?" Murmushi ya qwace mata a kunyace,ta saka fuskarta tsakanin qirjinsa,ta lumshe idanunta tana jin sassanyan qamshin dake fita daga tsakiyar gurin
"Ya Allah......Wani irin qamshi ne wannan?..…Too elegant for one man.” saita sauke numfashin a hankali tana zame jikinta,ya saketa a nutse ba tare daya qalubalanci hakan ba.
*_DUBAI INTERNATIONAL AIRPORT_*
A hankali private jet dinsu ya sauka akan runaway cikin tsari,ba'a babban airport na gama garin jama'a ba,aah...cikin private Royal terminal . Guri ne da luxury jets kawai ke sauka ta nan,gwamnoni....sarakuna....da kuma manyan billionaire's.
A hankali ya sauke idanunta ta cikin window din tana kallon qasa,jerin motoci ne baqaqe dake sheqi da daukan idanu a jere cikin tsari suna jira. Luxury SUVs. Rolls-Royce Phantom. Sai security convoy..
Da idanun ba kuma tare data sauka ba ta fahimci yadda komai na gurin ke dauke da nutsuwa da wani irin tsari ba tare da hayaniya ba. Irin tsarin da zai gaya maka akwai mutum me daraja da girma da ake jiran isowarsa a gurin.
Ya miqe tsaye daga kujerarsa cikin nutsuwa. Cuff din hannunsa ya gyara,sannan ya dauki agogonsa yana qoqarin maidawa tsintsiyar hannunsa.
A sace ta kalleshi,komai nasa yana nuna old money discipline,ba hayaniya.....ba nuna kai,saidai a jikinka kana iya jin presence nasa saboda kwarjinin da Allah yayi masa. Komai nasa cikin nutsuwa da sanin girma kai,yana komai cikin yanayin da zai gaya maka nutsatsen mutum ne shi da bai taba gaggawa ba a komai.
"Ready?" Taji ya furta a hankali,abinda ya sanyata saurin janye idanunta daga kanshi kenan ta sake maidawa ga window din zuciyarta tana wani irin bugawa.
Kada dai ace yaga yadda take qare masa kallo?. Ya yanke mata tunaninta sanda yake sunkuyowa inda take,ya sanya hannuwansa gaba daya yana dagata tsaye,sassanyar iskar hancinsa tana dukan fuskarta wadda ke cakude da turarensa dan amana.
"I'm your halal.....dukkanina khadeejah....halal dinki ne,ki kalleni as much as you can.....ba laifi...." Sai ya dakata kaman yadda maganansa yake a tsare. Yatsansa ya daga yana nuna saitin qirjinta dashi.
"Kibar wannan mallakin tawa ta huta....ki daina razanata haka kina sanyata tana gudun wuce kima". Tsit tayi tana kasa hada idanu dashi,gaba daya ya qarasa qona mata ruwan kai,ta fahimci al'adarsa ce.....yana da basarwa,ya gani yayi kaman bai gani ba.....yaji yayi kaman baiji ba,haka tayita gasa masa magana akan French language,amma yanzu ta zama tamake 'yar koyo a gabansa,har ba komai takeson tayi magana akai da yaren ba.
"Ready again?" Ya sake fada yana tsaronta kayarsa da qwayar idanunnan nasa.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Kalma daya.....amma daya fadeta sai taji kamar umarni ne da zuciyarta ta riga ta yarda dashi kafin karan kanta.
Hannunsa ya sake miqa mata,a yanzun ma ba wani haufi ta saka nata a ciki. Matseshi yayi softly yana duban blue eyes dinta. Bada qarfi ba,amma kuma kaman yanason ya tabbatar mata da ownership dinsa ce ita me cike da kariya daga garesa.
Daya bayan daya suke takawa har zuwa bakin jet din. Royal walking,wata irin nutsuwa me bayyana girman da basai an fada ba.
Daddadar iskar dubai ta soma sauka saman fuskarta,warm elegant dauke da wani qamshin alfarma.
Idanunta ya sauka akan mutanen dake tsaye suna jiran saukowarsa. Hotel representatives.....business officials.....security chiefs da personal staff's wadanda kowanne shigarsa ta bayyana matsayinsa.
Bayansa kadan ya sanyata,kamar wanda ke boyonta kada a kalle masa ita,cikin madaidaicin takunsa ya soma sauka,me cike da ginshira da qasaita. Tana biye dashi,still hannunsa bai zame daga nata ba.
Haka kawai wannan karon tsaiwar tarbar tasa yaji ta takureshi. Gani yake kaman kowa ita yake kalla,kaman ita daya tayi saura halittar diya mace a duniya. Musamman abayar dake jikinta yanzu,royal silk ne me asalin tsada da kauri da kuma daukar idanu. Shi da kansa data kammala shiryawa ta fito sai daya jima zaune,ya sanyata tana tsaye a gabansa yana qare mata kallo,ya fusgi kalmar
"Ma sha Allah" Da wani sanyin jiki da kasala da kallonta kawai yake saukar masa dashi.