Kenza eBookz

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 55

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 55

L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 55: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 55. Bata gasgata da hannu zaici abincin ba sai da taga yayi…

3,310 words

Bata gasgata da hannu zaici abincin ba sai da taga yayi bismillah yakai abincin bakinsa ya sake wata lomar.

"Ya salamm" Ta fada qasan ranta. Komai nashi simple ne?,mutum irinsa amma ya tattare hannu yana cin abinci da hannunsa?.

Idanunsa ya aje a kanta yana tauna lomar a hankali,sai daya hadiye sannan yayi magana,komai nasa akwai tsari da ilimi a ciki. Yanason qure rashin cin abincinta a yau,bai taba ganin cin abincinta ba tunda suke.

"Eat properly"

"I'm eating" Ta amsa masa a hankali.

"No" Ya fada da calmness sosai cikin muryarsa.

"You’re moving food around the plate dai princess" . Lips dinta ta cije kadan cikin kunya,duk sanda ya kirata princess sai taji ya aza mata nauyi saman kanta.

"You noticed too much" Ta furta can qasan maqoshinta.

"I noticed only you". Kasa amsa masa tayi,sai wani irin shuru ya gilma,irin shurun dake nuna sabo dakeson kutsowa sosai tsakanin mutum biyun da wata alaqa me girma ta gifta tsakaninsu.

Da wani irin yanayi najin nauyi take gyara blanket din,daidai sanda ya miqa hannu ya qarasa kashe fitilar data rage ta gefan gado.

Duhu ya mamaye dakin,shuru ya sake gilmawa kafin ta jiyo muryarsa cikin duhun.

"Akhnan...."

"Uhmmm" Ta amsashi gangar jikinta na kwadayi da fatan samun kusanci dashi,saidai wannan izzar dake cikin jinin kowacce diya mace ya hana ta nuna hakan koda a fuskarta.

"I liked today" Ya fadi kansa tsaye da zahirin abinda yake cikin zuciyarsa.

".....coming back to you afterward" Ya qarasa bude mata maganan.

Wani irin laushi zuciyarta taji tanayi sanda ta tsinci dumin tattausan jikinsa yana mamaye duk ilahirin jikinta,ya ilahi....batasan sai yaushe zai qyale zuciyarta ta huta ba. Bata sani ba.....qila ko sai sanda ta soma yawo layi layi tana gaya musu haukan son prince haisam aba jifar takeyi?.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

*NANAY*

Cikin qanqani lokaci ta tashi hankalin sassanta dama gidan gaba daya wajen neman inda akhnan ta shiga. Kusan duk wata hadima a tsaye take wajen bincika cikin gidan,maganan yaje har kunnen motii sai gashi da kansa a sassan.

"Kina tunanin wani mummunan abu ya isa ya shigo ya shallake kowa yayi gaba da ita?" Motii dake boye dariyarsa ya fada yana duban nanay wadda tashin hankalinta ya bayyana muraran.

Kai ta girgiza da sauri.

"Nifa ban gamsu ba.....ba inda giiftii zata sanya qafa ta fita ba tare da sanin kowa bafa". Dariyarsa ya sake kalmashewa sosai yana duban qwayar idanunta. Har yanzu duk data girma amma yana iya ganin wannan zallar quruciyartata da yasha fama da ita a shekarun baya saman fuskarta.

"Shikenan.....a sake dubawa wataqila a dace ko tayi bacci a wnai gurin" Ya fada yana gyara zamansa kawai.

Daidai lokacin rumaisa ke shigowa gurin. Bayanta baiwarta ce obsa,rungume da 'yar magen rumaisa din fara qal wadda ke da wani irin kwantaccen gashi me taushi dake gwada irin kulawar data samu.

Idanunta akan nanay,don tun sassafe ta fita makaranta,sai kuma yanzu take shigowa gida.

"Lafiya nanay?,me yake faruwa?" Ta tamabaya adan rude ganin yadda kowa yayi carko carko.

"Giiftii ce ba'a gani ba rumaisa" Fuska tadan tsuke kadan,da alamun mamaki saman fuskarta.

"Ba'a ganta ba?,tunda yaushe?,kunyi breakfast ne tare?"

"Aah....tunda sassafe fa?" Dariyarta take qoqari dannewa kadan,sannan ta sassauta fuskarta.

"Nifa naga obbo haisam din dazu" Waiwaya nanay tayi sosai tana duban rumaisa.

"A ina?"

"ta private exists.....kuma kamar giiftii din ce tare dashi,don mun hadu tana fita ina shigowa" Rumaisa ta qarasa fada kamar zata qyalqyale da dariya ganin kallon da nanay take mata dukka idanunta a waje. Data sauke idanunta akan motii kuma sai ta juya fuskarta saboda shima fuskarsa ta nuna dariya yakeson yiwa nanay din

"Subhanallahi" Tace a hankali saboda gaba daya ta rasa abun fada. Gurin ya dauki shuru,kafin kuma ta sake cewa komai Aanani dake zaune gefe da wayar nanay din a hannunta tace.

"Obbo haisam.....ya turo saqo nanay,kamar ma tun jiya.....kinji abinda yace" Ba tare data jira cewar nanay ba ta fara karantawa a fili.

_"Assalamu alaikum_ _Nanay._

_Ki yafe min rashin sanar dake da wuri._

_Na tafi da Akhnan Dubai tare da ni._

_Na san hakan ba shine tsarin da ya_ _dace ba,amma na yi _missing matata fiye da yadda zan iya_ _jurewa._

_I promise tana cikin_ _kulawa da aminci,zan riqe alqawari_

_Ki yi hakuri da ni_ _Nanay_

Wani shuru ya sake wanzuwa a falon,motii ya tattara dukkan jarumtarsa ya cinye dariyarsa yana yiwa rumaisa sign na su fita,sai itama ta baiwa kowa dake gurin umarnin hakan.

Sannu a hankali gurin ya zamana ba kowa sai shi da nanay din. Ya sake kallonta sosai yadda ta zama speechless gaba daya.

"Kin manta waye d'anki.....haisam baya hayaniya,.....but idan ya yanke abu......yana aikatashi,musamman abinda ya tabbatar yana kan daidai ne,bai kuma sabawa Allah ba" Yayi shuru still yana qoqarin danne dariyarsa kada ta tunzura.

"Amma fisabilillahi ya saceta har cikin daki kamar wani qaramin yaro?" Ta fada tana kwabe fuska kamar wadda ta rasa uwa da uba. Dole a wannan karon yabar dariyarsa kadan ta fita.

"Ya dauki matarsa ne,ba wata yarinya a waje ba...sannan ma kada ki azawa yarona duka laifin,da qafafunta ta fita itama fa,tabbacin tanaso kenan tabi mijinta,kara kawai take miki"

"Ya yaudareta dai.....dama ku maza kun iya yaudara" Ta fada a karon farko tana dan harararsa,irin wasan da suka saba can baya.

Murmushi ya sakeyi

"Tun farko dama na gaya miki,kada kice zaki tsananta tsakanin lamarin miji da mata....."

".....kaima dai kana goyon bayansa ne dama tun farko" Dariyarsa gaba daya ta subuce masa,royal father laugh dake kama da nutsuwar dake tattare akan fuskarsa.

"Dama dariya kakeso kayi ai na lura tun dazu,to kayita dariya" Ta fada tana miqewa. Hannu yasa ya riqota yana fadin

"Zo mana.....haba hadeezata" Ya jawota ta koma ta zauna a inda ta tashi.

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 98*

*DU B A I*

Lallausar safiyar da wani siririn haske da iska me dadi ke kadawa sosai tsakanin kowacce qofa da window na penthouse din nasu dake cikin Atlantis the royal.

Saman tsararren dining din dake shiyya ta musamman cikin residence din,dining din da aka cika da kalolin breakfast iri iri,tamkar mutane da yawa ne zasuci,bawai iya khadeeja da muhammad ba.

Yarima haisam ne zaune kan kujerar dake opposite na akhnan

Sanye yake da pure white Tom Ford shirt da charcoal trouser,hadin color din daya fidda wani launi me kyau,irin launin da zai gaya maka ansan ainihin hada colors su bada ma'ana me kyau. Hannunsa sanye yake da black Patek Philippe watch wanda ya kwanta saman kyakkyawar fatarsa da gargasa ta yiwa ado me daukan idanu. Sanda yake fitowa,idanunta sun sauka akan berluti shoes din dake qafarsa,wanda yake bayyana asalin tsada da dukiya,saidai bada murya me amo ba,don zaka dauka gama garin takalmi ne,amma kuna sananne ne a idanun wadanda ke rayuwa daidai ko kusa da mizanin nasa arziqin.

A nutse yake sipping coffee din nasa,yana qare mata kallo cikin wata doguwar riga midnight blue data haskata kamar zaka saceta ka gudu. Shi ya zabi rigar da safiyar nan,yace ita yake buqatar gani a jikinta,zai kuma zabi shigar da zata masa da dare idan ya dawo.

Bata iya zama haka ba,sai data dora qaramin farin baby hijab daya nuna fuskarta a tsakiya da wani irin kyau da kwarjini. Ya sani,ta masa rowa,don ta rufe abinda yake matuqar mararin kalla wato albarkatun qirjinta

A zahiri suna zaune ne cikin shuru,saidai a badini wata hira ce akeyi tsakanin idanuwa da zukata,wannan karon baki baida rawar takawa ko abun fada.

Karo na hudu ya sake sauke idanunsa akan qirjinta daya ciko fam ta rigar,amma ta hanashi ganin komai banda wannan tudun. Kasa jurewa yayi,ya miqa hannunsa a hankali dake daure da agogon,yasa yatsunsa don hanye inda hijab din ya rufe. Da sauri ta riqe hannunsa caraf zuciyarta tana bugawa. Har yanzu ta kasa goge abinda ya faru daren jiya,bai mata komai ba.....amma ya fidda dukka maitarsa da soyayyarsa da gurin,har yanzu kuma tana jin kowanne feelings a jikinta.

"No" Ya fada can qasan maqoshinsa yana sarqe idanunta cikin nasa.

"It's my halal,karki hanani kalla.....kinaso idan na fita na kalla na wasu a waje?" Ya fada yana langabar da wuyansa kamar marayan dake neman tallafi.

A hankali ta sakar masa hannun,NA WASU A WAJE daya fada sai taji kamar ya dauki mashi ya caka mata a qahon zuciyarta......sai taji zuciyarta tana mata nauyi da wani irin kishi.

Idanunta suka dan sauya kadan tana kallonsa. Kamar yanzu ne ta fara fahimtar cewa......Haisam mutum ne da mata zasu kalla. kuma duniya cike take da irin kallon da take masa yanzu.

"Kada ka qara fada.....don Allah....banaso". Wani irin abu me sanyi yaji yana ratsa dukka jikinsa.

"Kishi.....kishi na take?" Ya fadawa kansa da kansa. Wannan dabi'artata ta masa,bata iya boyen komai,muddin dai ta daukeshi da muhimmanci.

Hannunsa ya miqe a nutse ya kamo yatsunta cikin tashi ya saka a nasa hannun yana murzawa softly. Kai ta dauke taqi kallonsa,ya sake sakin murmushi dan kadan

"Hey..." Ya furta softly yanason sake ganin wadannan blue eyes din.

"I was joking" Ya fada a nutse. Kallonsa tayi saita sake kauda idanunta. Da gaske taji zafi,wani irin zafi da batasan zuciya na iya jinsa ba,kuma har yanzu zafin takeji

"Ni banason jin kana kallon wata" Ta motsa labbanta a hankali ta fada kamar zuciyarta tana karyewa.

Wani soft smile ne ya bayyana saman labbansa,not mocking.....fond.....very fond.

"My princess....." Ya kirata da wannan sautin dake kasheta.

"“I barely look away from you.”. Idanunta ta lumshe saboda yadda muryarsa tayi taushi da yawa.

Yadda ta lumshe idanun sai ya hade eyelashes dinta na sama dana qasa,saita sake masa wani irin kyau me daukan hankali. Gaza jurewa yayi,yakai hannunsa ya shafi gefan fuskarta.

"There’s nothing outside more interesting than my wife.” ya motsa labbansa a nutse yana hada kalmomin. Ya rasa da wanne sabulu take amfani,baisan da wanne abu take kula da fatarta har haka ba......amma yanasan ran wataran zai gani.....zai kuma tambaya.

Da dukkan wata kalma daga bakinsa sai da zuciyarta ta buga.....wannan karon ba saboda kishi ba.....aah.....saboda shi. Saboda shi dai....wannan malamin.....saboda shi....wannan yariman.....saboda shi....wannan boyayyen identity din da take xuba idanu taga ranar da zai gaya mata komai da bakinsa.

"Kaine mutumin hippodrome?" Tambayar ta subuce mata sanda yake maida cufflinks dinsa.

A bazata maganar tazo masa,amma sai ya daga kansa da murmushi yana dakatawa daga sanya cufflinks din. Da wannan dangerous smile din nasa yake takowa inda take zaune,hannayensa zube a aljihun wandonsa da ya yiwa tucking. Ya lura wannan tambayar na daya daga cikin manyan tambayoyin dake damunta.

Sunkuyawa yayi daidai fuskarta,ya bata lite kiss kaman yadda ya saba,sannan a nutse yace.

"Nayi alqawari.....zan baki amsarki.....not now,idan na dawo". Ta gamsu da maganansa,kuma yadda ya amsa matan sai ya qara zumudinta nason jin amsar tasa.

"Da shehnaz da aisa.....zasu iso dubai yau in sha Allah,nan da hour biyu.......zasuje bikin bude wancan kamfanin dana gaya maka,dukkanmu fan na brand dinne" Tayi maganan qwayar idanunta bata kallon nasa. Murmushin gefen baki yayi,a nutse ya dakata daga takawar da yakeyi.

"Ma sha Allah....dubai na musu barka da zuwa" Yadda yayi maganan kamar dubai mallakinsa ce ta sanya ta daga kanta tana dubansa,sai ya basar yana jawo briefcase dinsa.

"Zanje tarbosu......don Allah.....zasu sauka a five falm Jumeirah". Shuru ya danyi sanda yake bude briefcase din nasa. Ta lumshe idanu tana dan jin fargaba. Idan ya hanata zuwa tarbarsu.....kenan hakan yana nufin yawon da zasu d'an fita susha iska ma bazai bari ba.

"Karsu sauka a Jumeirah......zan saka a bude musu dayan suite din dake cikin residence din nan su sauka a ciki" Jerarrun fararen haqoranta ne suka fito,wadanda suka qara mata wani irin kyau. Tsaiwa yayi cak yana kallonta gami da jin komai yana tsaya masa da murmushinta kawai.

"Na gode.....na gode sosai" Idanunsa ya lumshe yana budewa,sai kawai ya bude mata dukka tafukan hannayensa.

Batayi tunani na biyu ba,ta miqe a hankali,tana takawa kamar me tausayin qasa,yanayin takunta da yake sanyawa wani lokaci yake kishinta idan tana tafiya a waje....saboda yana ganin kamar kowa idanunsa yana kanta.

A nutse ta fada faffadan qirjinsa tana sauke ajiyar zuciya......shi kuma ya maida hannuwansa ya kulleta a ciki yana matseta a tausashe.

Ko sau dubu jikinsu zai hadu.....sau dubu idan zai sake rungumeta yana jin kamar yau ne.....yanzun ne runguma ta farko a rayuwarsa da zaiyi mata.

"......sannan" Ta fada a hankali tana fargabar gaya masa,amma husky voice dinsa data cika mata kunne ta bata qwarin gwiwa.

"Fadi kawai.....aminci ne tsakaninki da mijinki......ba tsoro ba"

"Zamu fita......sunason small outing.....na kwana biyu ko uku" Shuru ya ratsa tsakaninsu,sai bugun zuciyar junansu dake ratsa kunnuwansu. Na wasu mintuna,ya zane jikinsa a hankali,sai itama taja baya tana sauke idanunta a kansa.

"Shikenan.....bazai bari ba,dama aisa ta fada i wasn't like i was before,ina da aure yanzun" Ta fada a hankali idanunta yana son tara hawaye ganin baice komai ba yana komawa cikin daki.

Jikinta a sanyaye ta koma saman sofa tana zama,tuna zurfafa tunaninta.

"Take the security team" Taji soft voice dinsa a gefanta yana furtawa a hankali sanda yake zama a sofa din dake dab da tata yana maida socks din qafarsa.

Idanunta da suka cicciko da qwalla ta daga tana dubansa,sai shima ya nutsa nasa qwayar idanun sosai cikin tata sanda yake maida safar cikin lallausar qafarsa.

"Da gaske?" Ta fada da wani irin ban mamaki. Murmushi ya sakar mata ne laushi wanda ya narka wani abu me sanyi cikin zuciyarta.

"Did you expect me to say no?” ya tambayeta yana dage mata girarsa gaba daya bayan ya kammala maida socks din yana soke yatsunsa duka cikin na juna.

Kunya ta kamata na yadda ta yanke hukunci haka kai tsaye,sai ta danyi qasa da kanta. Ya saki siririn murmushi yana janye idonsa daga kanta. Wallet dinsa dake gefe ya dauko ya bude.

Wani black card ya ciro,da wani car key,sai wani katin na daban ya dorasu saman table din dake tsakaninsu.

"Use this" Ya fadi a taqaice,maganan data sanyata daga kai tana duban inda ya ajiye kayan.

Sanda ta saka hannu ta dauka sai taji komai yana mata sanyi. Keys ne na motoci kusan kala biyar,black card wanda base an gaya mata darajarsa da kuma a hannun waye ake samunsa ba.....sai wannan card din data gaza gane ne meye.

"Haisam" Ta fada a sanyaye.

"Oh my god" Ya furta softly. Baisan meye a muryarta haka ba,da idan ta kirashi komai yake kwancewa daga cikin kansa ba. In zata maimaita sunanshi sau dubu yanaso,bazai gaji daji ba,har baya fatan wataran ta sauya sunansa da wani sunan na daban.

"Wannan fa?" Ta fada tana dan jin nauyin tambayar,amma kallo daya ya masa ya amsa mata kaman bai fahimci nauyin abinda takeji ba.

"It gives you access....." Yadan dakata.

"........to restaurants.....lounges.....shopping floors" Sake tsayawa yayi kadan.

"........dama duk inda kikeson zuwa" Sake bude wallet din nasa yayi,sai ya ciro wani slim metallic card yana sake ajiye mata.

".....And this one is for restricted places.”

"Restricted?" Ta fada can qasan zuciyarta lamarin yana fara girmamar kanta.

"Yeah.....So they stop asking questions the second they see you.” kasa magana tayi,har sanda ya sake takowa gabanta,ya kama hannunta yayi kissing deeply.

" Ki kulamin da kanki.....sannan 2days yayi yawa kina fita.....if possible zan sadaukar musu da kwana biyu.....kwana dayan nawa ne.....zamu huta saboda next day kinaso kije kiga grand opening right?" Kamar wadda kanta ya karye haka ta gyada masa kai a hankali. Ya lumshe idanunsa yana sake budesu dukka a kanta,yanason ta tashi ta rungumeshi so samu,ta bashi deep kiss,amna bayaso ya cika matsa mata,don haka yayi waving mata hannayensa yana fita da baya da baya har ya kammala fita gaba daya.

Da taimakon ambaton Allah yanayinta ya daidaita. Ta zauna kawai tana juya duka cards din daya bata. Batasan wanne kalar tunani zata sakeyi kuma a kansa ba,kawai maganan jiya ne da zuciyarta ta gaya mata. Ta samawa kanta salama,ta kalli komai kawai.....ta jira sanda ya shirya fito mata a mutum.

Aiki suke da agogo ko aiki da lura ko zallar sanin makamar aiki ne bata sani ba. Amma abinda yafi bata mamaki sanda security alert ya gaya mata security team din suna jiranta don rakata airport dauko su shehnaz.

Haka kawai ta samu kanta kalar shigar data lura idanunsa sunfiso,shigar da zata rufe komai nata banda zagayen fuskarta da tafin hannunta.

Yalwatacciyar abayar da asalin matan sarakuna a qasar dubai ke amfani da ita,sakakkiya sosai wadda ba abinda zata nuna nata.

Daga bakin residence dinsu ta fara cin karo da security uku. Abun mamakin dukka mata ne,su suka karbi jakarta suka riqe mata suna gaidata cikin girmamawa,sannan suka shiga private elevator din suna sauka qasa.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 99*

Mota hudu ne,kowanne akwai security a ciki. Qwaya daya ce kawai maza amma duka sauran mata ne a ciki.

Tafiyar mintuna kadan suka isa dubai International Airport,kuma suka samu tuni jirginsu shehnaz ya sauka,don duk duka batafi jiran minti sha biyar tayi ba taji ana kiran sunanta.

Ko bata waiwaya ba tasan shehnaz ce,wani tattausan murmushi ya subuce mata sanda take juyawa.

Sanda idanunsa suka hadu itama saita gaza jiran qarasowarsu,ta fara takawa don isa garesu,da sauri daya daga cikin security din tayi mata magana

"Easy ma'am.....please allow us to secure the area first". Tsaiwa tayi tana sake tattara nutsuwarta,kaman yadda shehnaz ta dakata cak tana bude idanunta cikin mamaki.

" Ba zaki qarasa gurinta ba sai an tabbatar da ingancinki" Aisa ta radawa shehnaz tana qyalqyalewa shehnaz din da dariya.

Clearing hanyar suke mata da gaske,cikin wani strict professionalism.....kamar tana qarqashin important protection da dukkaninsu idanuwansu suka gani.

"Ku daina kallona haka mana" Akhnan ta fada sanda suke takawa qarqashin kulawar security zuwa inda motocinsu suke suna damqe da hannun juna dukka su ukun

"Wallahi sai yanzu nakejin kamar kina wata different duniya da tamu" Maganan ya saka akhnan sakin dariya kadan,mai hali baya fasa halinsa,ba abinda xai sauya shehnaz dai da gaske.

Ko a cikin motar bakinsu dukka yaqi mutuwa,kada ma shehnaz taji labari. Ba abinda ta rage daga abinda idanunta suke gane mata.

"Wacce empire din ya kaiki ne akhnan?" Shehnaz ta fada tana kama bakinta idanunta cikin na akhnan.

"Shehnaz manaaaa" Ta fadi da irin salon yadda take magana idan shehnaz din ta dameta a baya da dogon surutunta.

Murmushi aisa tayi,sannan tace.

"Na baki shawara?....ki qyaleta kawai,duk abinda yake cikinta saita fada,gwara ki rabu da ita"

Cikin girmamawa da sanin aikinsu daya daga cikin security din data fuskanci itace shugaba take tambayarta,zasu ci gaba da tsaiwa suna jiranta ne?,kamar ance zata sake fita,ta amsa musu kafin ta juya suna shigewa ciki,kunnuwanta suna cika da maganganun shehnaz.

"Tun a elevator.....ba button na floors.....sai access card kawai.....private royal suit guda.....ni da aisa kawai?....biftu....wannan ba hotel bane.....Masarauta ce" Ta qarasa fada tana fadawa saman lallausan gadon dake da girma da fadi bayan da akhnan ta nunawa aisa nata dakin daban. Dauke idonta akhnan tayi daga kan shehnaz tana maidawa kan aisa

"Don Allah har yanxu jamaal baice komai ba?......na gaji da wannan bakin inaso a kullemin shi" Batasan magananta ta bada wata ma'ana ta daban ba,sai da taji sun sake mata shewa su biyun. Hannuwanta ta daga musu.

"Don Allah,kada ku fassarani".

Hutawa sukayi sosai,cikin mintina aka wadatasu da dukkan abinda suke da buqata. Ba shehnaz kawai ba,aisa da kanta daga qarshe kasa shuru tayi itama.

Awa daya kawai dukkaninsu suka shirya suka fito,suka samu security team din suna jiransu kamar yadda suka umarta.

Readers Also Read

More by Huguma