L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 62
L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 62: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 62. "Karku kuskura.....karku soma sanya wadannan qarafunan…
3,374 words
"Karku kuskura.....karku soma sanya wadannan qarafunan a hannun sarkinmu na gobe!" Kaman an watsa musu ruwan sanyi haka karsashin kowa a cikinsu ya ragu,sai suka dakata suka tsaya cak da abinda suke shirin yi din.
"Ku tafi dashi cikin girmamawa......jinin sultane ya wuce qasqanci.....gobenku zatazo muku dashi a matsayin sarkinku.....sarkinku na agadez.....kada ku manta da wannan" Ta qarasa maganan tana zube idanunta cikin idanun mammina.
Wani kallon kallo ne ya wanxu tsakaninta da ita,tamkar tana bawa mammina tabbacin INDE INA RAYE BA ZAKI CIMMA NASARA BA. Yayin da mammina ke fadin MAMAKIN QARFIN HALI DA TAURIN KAI IRIN NAKI SAFIYYA!.
Kuka falaak ta saki wanda ya gauraye ilahirin hall din,akhnan tayi yunqurin miqewa zuwa ga d'an uwanta itama sanda guard ke zagayeshi. A tausashe haisam ya jawota zuwa jikinsa yana mata wani kyakkyawan riqo.
"Hasbunallahu wa ni'imal wakeel" Ya fada rada mata a kunnenta,abinda ya sanya jikinta dukka ya sake da wani irin kuka da laushi da zuciyarta tayi,tayi luf a qirjinsa tana jin sautinnan nasa yana ratsa kunnenta,zuciyarta kuma tana mata zafi na yadda yaqi yin komai akan tafiya da ahmad din.
Matsowa gabansa tayi kadan,boyayyen murmushin nan da shi kadai yake iya ganinsa ta saki.
"Thank you for respecting the law of this palace". Ta fada ne da yaren oromo,a yau din,kanta tsaye,muraran ba tare da tsoro boyewa ko shakka ba. A yau ta amsa ta yarda ita din 'yar qasad Ethiopia ce.....a yau ta karbi wannan
"WATA BABBAR NASARAR" ya furta a hankali yana aika umarnin datse wannan sautin cikin muryarta da yaren oromo.
*B A Y A N A W A H U D U*
Abubuwa da yawa suka faru cikin masarauta a wadannan awannin hudun da sukazo masa da tarin matsi da wahala. Bawai wahalar aiki bincike tattara bayanai da hujjoji ba....aah....sam. Hasalima komai wahalan aiki yana samun wani karsashi da qwarin gwiwa wajen aiwatar dashi.
Abu daya da ya sanya wannan gajiyar da wahalar shine. Tarin tuhuma da zuciyarsa keta aike masa kan HAWAYEN AKHNAN. Me yasa baiyi komai akai ba?,zuciyarsa ke tuhmarsa. Me yasa zaibar hawaye masu nauyi cikin idanunta?.
Duk inda ya jefa idanunsa sai yaga masarautar kamar ta hargitse. Ba kuma kamar bane....a hautsine din take,ba wai don yawan jama'a ba.....aah. Hasalima ba wani baqo da aka sake bari ya shigo masarautar tun bayan wadancan awannin. An kammala sadakar ukun sultane......mammina kuma tace a dakatar da zuwa karbar gaisuwa ya isa hakanan. A yanzu lokacine na iyalinsa,lokacin iyalin daba wanda ya fahimci me take nufi da hakan,don bayan tsare yarima ahmad wanda labarin ya matuqar girgiza masarautar saidai ba wanda ya isa ya magantu.....ta tsare WAZEER an kuma kama mutanen da suke da fada a ciki cikin fada sun kusa su goma. Shi ya hana maleek shigowa cikin masarautar gaba daya,duk da yace bazai fita daga agadez yabar matarsa ba.
"Na maka alqawari.....bakin rai bakin fama. Zan kula da falaak kamar yadda zan kula da akhnan,ba falaak kawai ba.....dukka jinin sultane da iyalinsa gaba daya sun rataya a wuyana" Yasan waye haisam.....ya kuma gasgatashi ba na jiya ko yau ba. Idan yace zaiyi IN SHA ALLAH kaman yadda ta zame masa jini cikin dukka maganganunsa.....to zaiyi din. Idan yace bazaiyi ba.....zai wahala wani abu ya sauya matsayinsa akan wannan.
Ko a yanzun da yake takawa zuwa cikin gidan,dab da magariba ne da yanayin yammacin ya sake sanyayar da masarautar dama jikin dukka wanda ke rayuwa a cikin ta. Saidai akwai mutanen da idanunsa suke nuna masa. Ba wannan kamannin sam a tattare dasu,mutanen da ya sanyawa kowanne d'aya daga cikinsu jan fenti.
"Abeer......hold on" Ya fada a nutse yana zurfafa kallonsa tsakanin wasu shuke shuken dogon yaro masu tsaho sosai,inda yaga gilmawar wani motsi. Motsin da tuni yayi marking nasa......kuma ya fahimci akwai wani ta gurin.
Cikin jarumta da dakewar zuciyar nan tasa yake matsawa gurin,dab da zai isa ya dakata yana ci gaba da zubawa gurin idanu,yadan dauke kansa yana jan numfashi.
"Fito" Ya fada calmly,yana kuma sauke maganansa ta bayyana.
Tafisu ce,saidai bada wannan shigar tata ta asali ba,da wani launin kayan na daban,fuskarta a lullube da yanayin da ba lallai ka gane ita bace,amma shikam,ba wani motsi ko gilmawar mutumin daya sani da zata boye masa.
"Ta shirya korar nannie daga masarauta a daren yau da mafi munin sharri....." Shuru yayi yana zubawa tafisu idanu,hannunsa zube a aljihunsa. Cikin nutsuwar nan daba abinda ke girgizata ya motsa labbansa
"Yayi kyau.....yayi daidai,na gode,zaki iya komawa....amma haduwa ta gaba.....a wani gurin daban,ba cikin masarautar nan ba" Qasa tayi da kanta ba tare data iya dagowa ba,har zuwa sanda ya juya yana shigewa ciki.
"Abeer" Ya kirashi softly.
"Ranka ya dade" Ya amsa masa a girmame.
"Nannie zata bar masarautar nan,daga yanzu zuwa kowanne lokaci,a shirya mata sashenta itama.....a shirya mata gurin zama"
"An gama".
"And then....." Ya fada da yanayin daya karkato da hankalin abeer din.
"Sir...." Ya fada don nuna alamun yana saurarensa.
"....don't let anyone suffer"
"Done sir" Ya fada da girmamawa.
"Ina jabeer?"
"Yana online".
" Cut the connection abeer.....jabeer ina jinka" Ya fada yana ci gaba da nufar sassansa. Nufar da yakeyinta amma yana jin kamar ba tafiya yake ba. Yana buqatar sirri,dole yayi maganar akan hanya ba cikin daki ko wani gida ba. Ya saba idan yana aiki irin wannan.....koda katangu da bishiyoyi baya amanna dasu,yafi ganewa yawo cikin iska har zuwa mission dinsa zai kammala.
"She started already sir......" Jabeer ya fada dukka muryarsa tana nuna bacin ransa. Yasan bacin ran jabeer qwarai,wannan ya sanya aikinsu na farko da yasan yana buqatar haquri.....da daukan dogon lokaci kafin bincike ya kammala sai bai sanyashi ba.
"💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 111*
Jabeer" Ya kirashi da wata murya me taushi cike da tarin nutsuwa,tamkar ba shine yake fuskantar abu irin wannan ba.
"Don't forget jabeer.....karka manta" Ya tuna masa da yarjejeniyarsu,alqawarin danne fushi da janye dabi'arsa ta gaggawa cikin aikin kafin ya aminta ya shigo dashi ciki
"In sha Allah sir...." Ya fada a hankali. Shuru ya ratsa tsakani,ya kuma bawa jabeer dinne space ya shaqi iskar nutsuwa.
"Zaka iya ci gaba?" Ya tambayeshi a nutse.
"Yes sir....."
"Ehnnnn.....what did she take?" Haisam ya tambayeshi idanunsa suna kallon shimfidaddun duwatsun gurin kamar meson tantance nau'in wanne dutse aka fasa aka samar dasu,iskar yammacin me cakude da sanyin hamada da Sahara da ruwa ya jiqa tana busowa.
"Treasury access.” sai ya dakata kamar fadin kawai ciwo yake masa.
"Archive wing too.” idanunsa haisam ya dauke daga kan duwatsun a hankali yana duban gabansa. Ba wani mamaki saman fuskarsa,kaman dama yasan zata aikata hakan. Already ya riga yaga alamun faruwar hakan,tun a jiya.
“Should we interfere?” jabeer ya tambaya cikin zaquwa. Kai haisam ya girgiza masa a nutse.
"No" Ya amsa masa a hankali. Da sauri jabeer din yace.
"But if she gains control over the palace records......".
" She thinks power is in keys....." Ya fadi wani kasalallen murmushi yana subuce masa.
"Let her" Ya fada da wani irin confidence a muryarsa..
"The more confident she becomes…” ya sauke numfashi.
“…the more careless she’ll be.” wata nutsuwa ta saukarwa jabeer,sai ya gyada kansa sosai. Sai yanzu ya fara fahimtar ogan nasa..... isn't defending......he's trapping.
Ya murda handle na qofar bayan ya wuce dukka faluka,ya kuma duba duk inda ya kamata ya duba din.
Ya sallami birra a falon qarshe bayan ya karbi record na awanninta tare da akhnan din.
A kwace take kawai,saidai bata banbamce a wacce duniyar take rayuwa a yanzu?.
Ba abinda ke mata yawo a yanzu cikin zuciya da idanunta sai yadda aka wuce da ahmad zuwa prison. Prison fa?......abun yana mata nauyi da yawa. Yayin da zuciyarta ta cika da mamakin data dinga ji kamar zai hallakata akan mammina.
"Me yasa ta koma haka?,me ya sauyata?" Ta dinga maimaitawa cikin kanta.
Maganganunta.....kallonta.....ayyukanta dama idanunta.
"Ko ta qullaceni ne?,ko tana jin haushina ne shi yasa take shirya komai?,shi yasa ta shirya hucewa akan ahmad?,saboda me?,me nayi?,don naqi bin tsarinta ne?,don naqi bin umarninta ne?,don na karbi zabin sultane hannu bibbiyu?,me yasa ta zabi ta zama haka?,me yasa ba zatayi komai a kaina ni daya ba?". Sai ta runtse idanunta da gaske tana sake dawo mata da komai akan mammina.
Sai kuma ta soma girgiza kanta. Abinda take gani a idanun mammina ya d'ara wannan......abinda take gani a fuskarta yana gaya mata ba iya wannan bane.....ba iya matsalar kenan ba. Idan iya itace ina ruwan wazeer daba ahalin gidan ba?,ina ruwan sauran mutanen da aka gayawa morsa dazu suma an kamasu?. Ta sake rufe idanunta tana dawo da fuskar mammina.
Fuskar babban MAQIYI take gani yanzu shimfide a tare da ita.
"Me yake shirin faruwa?" Ta tambayi kanta tunaninta yana hargitsewa,ta kuma yi tambayar daidai sanda haisam ya buda qofar da sallama a nutse.
Idanunta ta maida ta kulle a hankali. Zafinsa take so taji.....haushinsa take so taji koda d'an kad'anne amma zuciyar taqi karbar wannan yanayin.
"Me yasa ba zakiji haushinsa ba.....me yasa?" Ta tuhumi kanta,idanunta a lumshe amma tana jin takunsa da sake kusantotan da yakeyi a rubuce cikin zuciyarta. Duk da idanunta a lumshe suke....amma tana jin hakan a qasan zuciyarta.
"Assalamu alaikum warahmatullah" Ya sake maimaitawa bayan wadda yayi da farko bata amsa ba,ya sake maimaita sallamar a sanda ya iso dab da bakin gadon inda take kwance,ya kuma tsugunna a gaban gadon saitin kanta.
Bata motsa ba,bata kuma amsa masa ba,sai ya miqe tsam yana isa ga tarin jerin abincin awannin duka da aka ajjiye mata. Suna nan kamar yadda birra ta gaya masa,daidai da ruwa kadan tasha.
Ya waiwaya ya sake kallonta,ko motsi har yanzu batayi ba,ya sani....idanunta biyu,ba wani motsi nata da zai boyu a idanunsa.
"You didn’t eat.” ya fada softly bayan ya dawo gefan bedside drawer ya zauna daf da ita.
Zuwa sannan zuciyarta ta game matsewa guri daya. Zuciyarta tana gaya mata bai kyautu taqi kulashi ba....bai kamata taqi amsa sallamarsa ba.
"Ka damu ne?.....tunda ka bari suka tafi dashi" Ta fada da raunanniyar muryartan nan dake kakkarya masa zuciya da katse masa duk wata jijiya me amfani dake jikinsa.
Idanunsa ya lumshe yana jin nauyin kalmar qololuwa har cikin zuciyarsa. Ya kamata yayi magana.....amma yanajin kuma ya dace ya barta ta furzar da komai dake cin zuciyarta don samun sassassauci
"Na kalleka.....da tunanin zaka hanasu" Ta fada muryarta tana rawa. Shuru yasake ratsawa kaman ba zai amsa mata ba,kafin ya kira sunanta.
"Gate up" Ya fadi yana miqa mata hannunsa. Ta riga ta bude idanunta,ya kuma kulle idanunsa cikin nata,bata da daman iya musa masa,yana da wani power na iya sarrafa tunaninka ta idanunsa. Ta miqa masa hannun,shi kuma ya daga ta a hankali ta zauna sosai,ya saka mata pillow ta jingina tana fuskantarsa.
A ransa....yake yabawa da yanayin fushinta,da alama ba zata zama me dogon fushi ba,zata zama me bada daman kare kai da kuma saurare.
"Giiftii" Ya kirata da girmamawa cikin muryarsa.
"Kinaso na hana a tsare ahmad ne?.....ko kinaso gaskiyarsa ta bayyana?". Tambayar ta sauka kwanyarta da nauyin daya sanya ta shiga qoqarin farfasa maganar da kuma dogon nazari.
Ya sauke ajiyar zuciya....haka yakeso,maganansa yakai inda ya dace.
"Zan iya fidda ahmad a yanzu......zaiyi free.....amma bazan iya wankeshi a idanun kowa da kowa ba.....wanne kika zaba a ciki?" Shuru tayi,shuru me nauyi,shuru me hade da kunya.
"He's a genius" Ta fada can qasan ranta.
"Akhnan" Ya kira sunanta,sai ta amsa cikin karyewar zuciya da jin nauyinsa.
"Na'am"
"Na bari suje dashi......because some wars....are not won the moment they begin.” a nutse ta daga kai tana kallonsa,sai takejin wani abu cikin muryarsa.....cikin maganarsa wani sound da ma'ana yake bayarwa daya dasa wani abu cikin ranta. Yadda yake maganan,sai takeji a jikinta akwai wani abu......akwai wasu abubuwan daya sani fiye da kowa.
Hannunsa yakai kan fuskarta yana share mata hawayen da yayi saura softly.
"I would never stand with someone against your family.” maganan ya ratsa har can qarqashin zuciyarta. Idanunta na yawo saman fuskarsa,kamar zuciyarta ta fara gaya mata akwai wani abu me zurfi.
"I would never stand with someone against your family.” kalaman suka sake dawo mata tartar!.
Tasan gaskiya ne,tasan baya qarya....komai ya fada zai tsaya a kanshi,baya sauya magana ta dade da sanin hakan.
"But Ahmad is alone there…" ta fada a hankali. Dan murmushi ya saki me laushi,ya sani,ta fadi abinda yake cin ranta ne.
"No.....he's not" Zuba masa ido tayi tanason gane ma'anar abinda ya fada,saidai bata buda baki ta tambaya ba,shima baice komai ba sai idanun nan nasa masu nauyi daya aza mata.
Daga qarshe ya janyesu daga kanta,saboda wani yanayi da yake fusgarsa a tattare da ita,wanda yasan a wannan yanayin.....a wannan lokacin komai bazai yuwu ba. A wannan yanyin tana buqatar space sosai da hankalinta zai nutsu ya tattaru guri daya,don haka sai ya miqe,ya isa ga tray din. Tsayawa yayi ya bubbude,sannan ya zauna sosai ya diba duk abubuwan da suka dace,ya shirya saman wani tattausan kilishi zagayayye dake shimfide qasan dakin.
"Come" Ya furta a nutse,bata jin zata iya cin komai,amma bata iya musa masa ba,saita taso a nutse yana tsaye yana jiranta har ta iso,idanunsa a kanta da wannan sassanyan takun nata.
Ya zaunar da ita sosai saman shimfidar,sannan ya zauna opposite dinta yana saka plate din abincin a tsakaninsu,ya debo da spoon yana dubanta.
"Bismillah" Saita girgiza kanta.
"Banajin yunwa" Shima kan ya girgiza mata.
"Bazai yuwu ba....bakici komai ba tun da safe...." Idanu ta daga ta kalleshi.
"Yes....birra ta gayamin" Ya furta yana lumshe mata idanunsa.
Stubborn silent dinnan nata ta masa,ya narkar da idanunsa cikin nata yana langabar mata da kai,da wannan soft dangerous patience din nasa yana dubanta.
"Are you punishing your self?......"
"......or punishing me?". Lips dinta ta cije kadan,ya sanyata taji wani abu da take ganin bai kamata ta jishi ba yanzun.
Sake debowa yayi ya miqa mata.
"Take one bite" Kauda kanta ta sakeyi,batajin komai zai wuce ta maqoshinta. Shuru ya ratsa tsakani,dubanta yake,tsakanin shi da ita baisan zuciyar waye tafijin zafi ba.
"If you collapse too..." Ya fada a tausashe.
"......who will stay beside momma....falaak and ahmad?" Nan take idanunta suka sauya.
"And you stop eating....."
".…I’ll stay awake all night watching you instead of fixing this.”
Ji tayi ya qarasa karyata gaba daya,ba zata iya ci gaba da musa masa ba.
A hankali ta buda bakinta kadan,da wani kulawa da taushi ya sanya mata spoon din a bakinta.
Ta shiga taunawa a hankali yana binta da wani irin kallo. Calm,protective.....zuciyarsa dauke da wasu sirrika masu nauyin dake son rinjayarsa....💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 112*
Wata irin rana ce data kasancewa akhnan da wani irin tsananin da bata taba hasashe ko tunani ba. Wata irin rana da bata taba kawo akwai ranaku masu tsanani a rayuwa kwatankwacin wannan ba.
Ranar data bude idanu cikin masarautar.....taga ta kowanne sashe masarautar a rikice take. Komai baya tafiya daidai,idan ta kira hakan da YAQI batayi daidai ba,don komai ma ya faru,yana kuma ci gaba da faruwa.
A sannu a sannu masarautar tana fara zama shuru.....wani irin shuru dake nuna janyewa da raguwar mutane daga cikinta.
Wasu sun janye a hankali sunbi duhun dare sun sauya muhalli daga masarautar. Saboda tsoro......tsoron kame....tsoron d'auki d'ai d'ai da akebi ana yiwa ahalin masarautar da laifukan da basu taka kara sun karya ba. Laifukan da basu da wani babban dalili da za'a kama kuma a tuhumeka saboda shi. Wasu an koresu haka siddan,an nesantasu da masarautar da shekarun da ba'a qayyade musu yawansu ba da laifukan da basu aikata ba,basu kuma da hujjar kare kansu,basu ma da wannan qarfin iko kona gwiwar da zasuyi defending kan nasu. Ciki kuwa harda nannie shehnaz da a shekaran jiya suka tattara suka bar cikin masarautar.
Abinda ta kasa jura a yanzun shine,aisa data shiga sahun wad'anda aka kamesu.
"Aisa a prison?" Duk sanda ta tuna wannan sai taji gaba daya kanta ya mata nauyi......wani abu yana juyawa cikin kwanyarta.
Abu biyu.....abu guda biyu ne yake bata mamaki gami da d'aure mata kai.
Na farko haisam.......basai an gaya mata wayeshi. Ta sani a yanzu a duniya gaba daya ba inda bazaiyi magana aji ba.......amma me yasa ya zabi yayi shuru?,me yasa ya zabi ya zuba idanu ana kame jininta?.
Da farko ahmad......yanzu kuma aisa?. Nannie tabar gidan ya sani.......amma me yasa bai dakatar ba?. Sanda sultane yana rage shine wakilinsa,a lokacin......duk da tana jin haushinsa......duk da babu jituwa ko guda daya a tsakaninsu......amma ita kanta tasan ya riqe masarautar sama da yadda sultane ke tafi da ita....ya kuma taka rawar daya dace. Batasan daga gidan daya fito ba a lokacin......amma ta jima tana mamaki.
Amma me yasa yanzu yake kauda kai daga dukkan komai?,me yasa a sanda ya dace ya magantu yake yin kamar baisan abinda ke faruwa ba?.
Abu na biyu MAMMINA.....wata mace take gani daban.....muguwa azzalumar da zalincinta ya sanya kwanaki biyun nan kanta ke shirin bugawa da tunani. Me yasa ta raineni a baya?.....me yasa ta riqeni har girmana?. Amma a sanda ta soma shigowa da'irar tunani akan girmanta.....aurenta da aka yita yunqurin yi sai wasu abubuwa suka fara kwancewa a kanta. Abubuwan sa suka sanyata zama sosai saman tiles na dakin kamar wata zautacciya tana qoqarin fito da wasu abubuwa,amma koda ta zurfafa tunanin saboda ba wanda zai taimaketa ya tayata fiddosu sai kawai kanta yahau ciwo,a nan ta zame ta kwanta.
"Tana da shiri.....akwai abinda taso cimmawa muguwa ce.....ba yadda za'ayi mutumin da bai kasance mugu ba ya sauya dare daya irin wannan" Wannan tunanin ya dunga yamutsa kwanyarta.....har tayi wani wahalallen bacci da yazo mata da mafarkin sultane.
Ta manta komai daya gaya mata......amma ta riqe abu biyu zuwa uku.
"Shine mamminki.....shine bappi dinki......ba mugu bane" Koda ta waiwaya bayanta.....sai taga haisam ne,a tsaye yana kallonta yana murmushi,data sake juyowa ga sultane kuma sai taga ya bace,take ta farka firgigit.
Tana farkawa din kuma haisam din ta samu zaune a gefanta yana karatun qur'ani,ya kalleta da narkakkun idanuwan nan nasa,sannan a hankali ya soma gaya mata abinda ma'aiki yace ayi a sanda kaga wani mafarki daya firgitaka.
Ta sake tuna dalilin kama aisa a shekaran jiya. CIN AMANAR SAHEL COUTURE......sahel couture din da batasan a yanzun mallakarta bane ko mallakar mammina?. Ko mallakar wadanda batasan su waye ba da taji sun siyeshi bayan anyi gwanjon kamfanin saboda karairayewa da darajarsa tayi. To wa aka bawa kudin bayan an saida?. Oho.....itama bata sani ba,tunda ba wannan bane yanzun a gabanta ba.
"WACECE MAMMINA?" Tambayar da tun a waccan ranar take yawaita yiwa kanta ita kenan.....tambayar kuma data tabbatar akwai tarin amsoshi a qarqashinta.
Sahel couture yana da matuqar girma da daraja a idanunta.....amma darajar aisa da shehnaz kawai ya zarta nashi.....ballantana sultane dinta data rasa gaba daya?.
Itakam tunda ta rasa sultane kuma akwai wani abu da zata rasa wanda zai gigitata ko ya daga hankalinta?.
"Akwai" Taji wani sashe na zuciyarta ya fada mata.
"Haisam" Ta sake bata amsa zuciyartata sanda take zaune cikin balcony dinta tana jin yadda masarautar gaba daya take canza mata daga sunan GIDA. Gidan da take matuqar so saboda mutanen dake cikinsa......a yanzun tana jinsa yana koma mata daidai da KURKUKU.
"Haisam" Ta fada a hankali can qasan zuciyarta. Haisam.....wata halitta guda daya da a yanzun batasan gwargwdon matsuyinsa a rayuwarta ba. Wani halittar d'a namiji daya tal baya ga sultane da suka samu wani mahaukacin muhalli a zuciyarta.
Kamar wata amsa zuciyarta keson bata,saita daga idanunta a hankali haka kawai tanason tantance yanayin da sama take ciki saboda yadda take bada iska me laushin dake qara mata kewar sultane da kuma karyewar zuciya,sai idanunta suka sauka a kanshi.
Sanye da baqar Emirati thobe.....kwantaccen baqin gashin nan nasa yayi luf saman kansa yana glowing da ragowar dudashen hasken rana da sama ta barwa duniya.
Batasan me tafi so a tattare dashi ba......wannan sexy eyes din nasa?.....ko wannan lips din nasa da yake sanyata mantawa da komai?.....ko kuma idanun nan da take tunanin tun ranar farko data gansu suka fara dulmiyar da ita?. Dulmiyar da batasan tayi ba sai daga baya bayannan?. Ko wannan ginannen jikin nasa?......ko kuma coolness da calmness dinsa?. Mu'amalar nan tasa me taushi?,me tsayawa a rai?.....ko kuma wannan GIRMA da yake bawa diya mace a rayuwarsa gaba daya?. Ko kuma dai yadda bai d'auki kansa a bakin komai ba,bayan yakai ya dauki kansa wanin?.