Kenza eBookz

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 64

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 64

L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 64: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 64. *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na…

3,362 words

*_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_*

*_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_*

*INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA*

*Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* ________________________

Cikin kunnuwanta yake rad'a mata wasu abubuwa,wasu irin kalamai masu saukar da wani irin sanyi ga zuciya. Kalaman da suka sassauta mata zuciya ta dinga sauke ajiyar zuciya shi kuma yana sanya yatsunsa yana dauke mata hawayen.

"Kina sonsu ne gaba daya?" Ya mata tambayar ba tare data zaci haka daga gareshi ba. Jiqaqqun idanunta ta daga ta kalleshi.

"You're buying them back?" Ta fada da dusashiyar murya. Wannan murmushin dake da hatsari yayi.

"Would you rather strangers keep pieces of your father?” wani lafiyayyen murmushi ne ya qwace mata,ta riqeshi qam qam cikin jikinta idanunta suna tara sabbin hawaye. Godiya takeson masa amma batasan ta wacce hanya ba.....ta kasa magana gaba daya,sautin mammina ya sake ratsasu.

"Da wanne arziqin zaka iya siyan dawakai masu tarin daraja irin wannan?,da albashin kudin bincike?,zamu gani" Saita taka tana daga murya.

"Kowanne d'aya inaso a ninka farashinsa ga duk wanda zai siya". Idanu suka hada da akhnan,abinda ya gani a idanunta suka sanya tausayinta ya kusa narkar dashi. Kamar tana tuhumar kanta.....me yasa ta zama uwa a gareta?,kamar tana tambayar kanta ya akayi ta shigo ahalinsu?,kaman kuma tana tuhumar me yasa sultane ya aureta?. Kai ya jinjina mata yana mata wani kyakkyawan riqo,kafin ya dagata cak ya rabata da qasa yana rungumeta a jikinsa. Murya can qasa.....ya kuma kulle idanunta cikin nasa yana hanata kallon kowa ya soma mata wata magana qasa qasa,wadda ta sanyata kwantar da kanta cikin qirjinsa tayi luf.

Wani mugun tsaki mammina taja tana binsu da mummunan kallo. Ba abinda zai hanata tsinke wannan igiyar soyayyar. Tasan ibraheem.....kome akace yaronsa zaiyi akan matarsa na sadaukarwa ba zatayi mamaki ba.

"Aikin banza.....ka dauka kudin wadannan dokunan kamar kudin siyan littafi ne?". Sautin ya isa kunnensa,amma ya hana akhnan taji da zaqaqan kalaman da yake karanto mata har tana jin duk wani bacin ranta yana kwaranyewa.

★★★

A cikin kwanaki kad'an ta soma wargaza masarautar da tarin sauye sauye na fili dana boye. Kadarorin sultane......tsarukansa da komai nasa ya zama a hannunta da sarrafawarta.

Cikin wani irin qwarewa da take tunanin tana da ita....cikin qwarewar da take ganin ta kai mata take karban komai d'aya bayan d'aya. Manyan kadarorin sultane tana gwanjonsu cikin kwanciyar hankali da yaqinin ba wanda yake da kaurin wuyan qalubalantarta. Dawakan da yafiso....,manyan muqullai suna hannunta,takardu masu daraja....zinare......azurfa.....dama dukkan wani abu da tasan me kima ne. Babu me qoqarin yayi magana.....saboda abune me sauqi yanzun nan ace an rasa wane....ko an koreshi kwata kwata daga agadez din. Mutane da yawa ta siya.....kama daga mañyan fada da jami'an tsaro na cikin garin,wannan ya sake bata daman sakewa da ci gaba da aiwatar da komai yadda takeso. Masu tsaro da amintattun da suka fara canza bangare. Wasu saboda tsoro.....wasu saboda kwadayi da neman mafita irin ta son zuciya da butulcewa halacci irin na d'an adam.

A cikin kwanaki kad'an…..masarautar Agadez ta fara sauyawa zuwa wani abu daban da mutane da yawa basu tab'a tunanin zasu gani ba. Ba kuma saboda an rasa sultane kawai ba...aah. saboda mutanen da suka dad'e suna fakewa da inuwa da tsoronsa… sun fara fitowa fili.

Fadar agadez ta fara rasa tsohon numfashinta na asali,dokokin da sultane ya kafa shekaru masu yawa an rushe wasu,an sauya wasu. Sabbin fuska suka fara bayyana cikin fadar.....sabbin umarni da sabbin tsare tsare da sabbin dokoki. Komai yana sauyawa cikin sauri me ban tsoro da d'aure kai.

Mutum daya.....mace daya data zame mata qarfen qafa.....macen dake tsaye wajen qalubalantarta da dukka tsarinta MORSA SAFIYYA sai lafiyarta ta fara rauni,wannan ya sanya hairaan yanke shawarar hanata jin komai. Ba morsa SAFIYYA kadai ba.....harda akhnan dinma da falaak da suke kyautata zaton laulayi takeyi. Don sam taqi yarda taje asibiti bare a gwadata. Morsa SAFIYYA tayi tayi kuma tabi mijinta su wuce tunda anyi bakwai.....amma tace sai anyi arba'in tukunna.

A hankali tsoro ya shiga zuciyar kowa,tsakanin masu aiki sam ba sakewa.....babu aminci saboda kowa ji yake bai tsira ba. Cikin kowanne second....cikin kowanne minti kowa yana iya shiga TARKO na giwa mammina. Uwa uba a yanzun ba kowa ke yarda da kowa ba cikin masarautar. Kana zaune da mutum yanzu,anjima zaka tsinceshi ya koma dan bayan mammina dari bisa dari.

Masarautar ta fara zama wajen zargi,tsoro da siyasa,da kuma murmushi na jabu,murmushin da zai iya hallaka wanda ya rud'u da ganinsa saman fuskar mammina din.

Sauyi ne daya fara tun daga manyan corridors har dakunan masu aiki na gidan,bayi dama hadimai. Anajin wannan sauyin. Ana ganinsa. Kuma kowa na tsoronsa.

Tutar masarautar tana nan a tsaye.....masu tsaro suna tsaye a bakin dukkanin qofofin.....dattawa suna nan a majalisar zartarwa ta fadar agadez,amma RUHINTA ya fara canzawa.

A hankali sunan SULTANE ya fara zama kamar wani abu da ake qoqarin turawa baya. Aka fara cire manyan hotunansa daga dogayen private halls na gidan.

Ambatar sunan SAFEENA ko 'DA SULTANE YA RAYE' ya fara zama babban zunubin da ba za'a gafartawa wanda ya aikatashi ba. Kalmomi suka fara zama abubuwa masu hatsari cikin masarautar AGADEZ.

A hankali akhnan ta fara jin kamar tana kallon gidansu yana zubewa a idanunta.

Mammina ta fara zagayawa cikin fada da wani irin nutsuwa da jin gamsuwar nasara ta tabbata a hannunta!.....nasara a hannunta tayi nisan da ba wanda zai iga qalubalantarta. Ba gudu take yi ba....Ba rikici kawai take tayarwa ba. A’a. Ta fi amfani da: umarni masu laushi......murmushin karya,dokoki,tsoratarwa.....da kuma rashin tabbas data saka a zukatan kowa da rayuwarsa.

Wani lokaci zata yi magana cikin taushin murya…..amma bayan awa guda wani hadimai ko bawa ya rasa aikinsa. Ko wani cikin masu tsaro ya b'ace.

A hankali sai mutane suka fara fahimtar mulkinnan na mammina......sannan mulkin mammina ba ihu bane. Mulkin Mammina… shi ne ka kwanta lafiya,ka tashi ka tarar an canza rayuwarka.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Jama’ar Agadez sun fara shiga rud'ani. Wasu suna kuka da gaske saboda rashin Sultane. Wasu suna tsoron future ɗin masarautar. Amma kuma.....ba wanda ya isa ya fada da qarfi.

Fadar agadez ta fara zama wajen sirruka. Qananan qungiyoyi suna had'uwa cikin boyewa. Ana kai takardu cikin duhu. Ana canza masu gadi a tsakar dare. Ana jin jita-jita marasa dad'in ji kala mala.

Wasu daga cikin tsoffin masu biyayya ga sultane sun fara ja da baya cikin tsoro. Saboda sun kasa gane.....wa za’a yarda dashi?......wa yake siyar da bayanai.......wa zai biyo bayanka idan kayi kuskure???.

Duk sanda wani zai magana amsa daya ce.

"Ina tattalin masarauta.....ina tattalin mutuncinta.....ba abinda zai sake gudanawa sai an tabbatar da wanda ya kashe sultane.....sai bayan bincike ya kammala tare da kama duk wanda ke da hannu cikin mutuwarsa". Wanda yayi wannan maganar har ya samu amsa.....ba lallai bane gobe a sakejin motsinsa ko a sake ganinsa ba. Wannan ya zama wani abun tsoro da kowa ke shakkar magantuwa akai.

A wannan lokacin ne akhnan ta fara jin cewa.....ba fadarsu bace wannan kwata kwata.... Ba masarautar mahaifinta bace......duk inda ta juya sai ta ga canji Wani sabon tsari. Wani sabon umarni. Wani sabon tsoro a idanun kowa.

Sai dai abu d'aya bai sauya ba. Kallon Haisam!. Duk lokacin da idanunta suka had'u da nasa.....tana jin kamar. Akwai wani abu daya sani da kowa bai sani ba!. Kuma wannan abu… shi ne kad'ai yake hana masarautar rushewa gaba ɗaya.

*HAISAM* mutum d'ayan da ya ci gaba da kasancewa cikin nutsuwa mai tada hankali da sanya mamaki. Haisam....yana gani.....yana sani. Amma bai hana komai ba. A kallo… ba a fili ba......a filin kuma KAWAI bawai a bad'ininsa ba. Badinin da ba wanda ya sani sai Allah saishi.....sai team dinsa dake qoqarin tattara dukka wata hujja data motsin mammina!.

Wannan shurun nasa......wannan nutsuwar tasa....shine ya fi tsoratar da wasu daga cikin dattawan fada. Saboda sun kasa gane?......shin yana jiran komai ya rushe ne?......ko kuwa yana jiran wani lokaci ne da zai maida komai hannu d'aya?.

Mammina naci gaba da jin d'and'anon nasara. Karo na farko cikin shekaru,ta fara tafiya cikin masarautar kamar ita ce ke da ikon qarshe a duniya gaba daya. Ba tare da idon sultane a kanta ba.......Ba tare da wani dake iya tsayar da ita ba.

Ko a zuciyarta da a farko take shakka da kokwanto......ta fara gaskata cewa...... A iya yanzu kadai TACI YAQIN DATA SHEKARA DA SHEKARU TANA JIRA!!!.

★★★

Babban zauren majalisar masarautar Agadez cike yake da manyan mutane,dattawa da masu riqe da dokokin fada. Masu kula da kadarorin masarauta. Hakimai da manyan masu fada aji.

Zaman an yishi ne don a tattauna rabon gadon Sultane,karo na farko tun bayan mutuwarsa,ganin yadda kwanaki ke dada nisa. Cikin manyan malamai aka samu wani ya fidda tsoro ya kuma shirya zaman saboda qaunar da yakewa sultane din da kuma fatan sauke masa nauyi koda hakan zai zama silar faruwar wani abu a kanshi.

Wurin ya yi shiru mai nauyi,irin shirun da yake nuna kowa na taka-tsantsan da kalamansa,sannan kowa na kallon kowa da zargi da rashin aminci.

Mammina na zaune cikin baqar alkyabba mai nuna iko da isa. Fuskarta babu alamar wata damuwa irin ta macen data rasa mijinta masoyinta kuma jigonta.

A gefe guda kuma morsa safiyya ce,zaune cikin nutsuwa duk da alhini da gajiyar da suka bayyana a idanunta dama gangar jikinta data nuna rama sosai.

Kusa da ita kuma akhnan ce zaune,tashin hankali ne kwance saman Fuskarta yana nuna kansa muraran.

Tun bayan mutuwar sultane ta fara jin kamar masarautar tana zamewa daga hannunsu. Tun biyowar bayan sabon takun mammina da har yanxu yake daure mata kai takejin komai yana dagulewa cikin rayuwarta.

A can gefe kuwa haisam ne,yana zaune shiru. Cikin wannan tarin nutsuwar tasa,haiba cikar kamala,yana kallon komai cikin idanun da basa bari a gane me ke zuciyarsa. Baiso zuwa zaman ba.....amma takanas morsa safiyya ta sameshi da roqon alfarmar ya shiga zaman.

"Kai kadai muke kalla yanzu a matsayin wakilin sultane da muka yarda dashi" Ta fada muryarta tana rawa. Magananta da yanayinta yaso karya masa zuciya. Yanajin kamar ya bayyana mata nanay ko zata samu sassauci daga radadin da takeji.

"Zanje.....zanje in sha Allah" Ya amsa mata.

D'aya daga cikin dattawan majalisa ya gyara zamansa kafin yayi magana ta farko tun bayan zamansa a gurin.

“Kamar yadda dokokin masarauta suka tanada…” ya fada yana bud'e wasu takardu

“…akwai kadarorin da baza’a tab'a ba har sai an tabbatar da sabon tsarin mulki.” bata ko d'aga qafa ba mammina ta d'ago kai da sauri. Mamaki take......dama akwai wanda ya rage da zai qalubalanci abinda ta tsara tana so?. Duk da komai yana hannunta,abinda yayi saura baida yawa.....Shima tana da interest a kansa gaba daya. Don har yanzu wannan ZUCIYAR DUKIYAR AJANI din da take kyautata zaton na hannun sultane iya bincike bata ganta ba.

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽

💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 116* _________________________ *_Mg's ORGANIC SOAP_*

*_Shin kin gaji da banke banken sabulu wa fatarki?_*

*_Kullum ba ci gaba?_*

*_Kullum jiya iyau sai sake lalacewa ma da takeyi?_*

*_matso maza ga maganin matsalanki da izinin Allah_*

*MG'S ORGANIC SOAPS*

*_kamfanin da ya shirya tsaf don samar miki da sabulun da zai sanya fatarki KYAU ta goge tayi haske ME AJI bana bleaching ko me bata fata ba_*

*_KALAN 'YAN ABUJA.....kalar hutu hajjaju,asalin kalar fatarki ta anihin_*

*_Masu matsalan SKIN irinsu PIMPLES,SPOT,ACNE,SUNBURN in sha Allah kukanku ya qare....matsalarku ta qare_*

*AKWAI PACKAGE DA SUKE HADAWA GAME BUQATA*

*yammata.....zaurawa....amare.....da iyayen gida masu capacity wanda ya hada da* Soap Facewash Face cream/body cream Scrub Serum Cleanser Glow oil Toner *duka cikin package din*

*_INA MASU FAMA DA NANKARWA(STRETCH MARK)MG'S ORGANIC SOAP bata barku a baya ba_*

*Ku nememu kai tsaye a wannan number don GYARA DA MAGANCE MATSALOLIN FATARKU* 0806 299 1549

*MG'S ORGANIC SOAPS* *_takenmu (MAIDA TSOHUWA YARINYA....A SABUNTA YARINYA ZUWA SABUWAR HALITTA)_* _________________________

“Sabon tsarin mulki?” ta tambaya da gadara cikin muryarta.

“Mijina ya riga daya rasu......”

“.....Dukiyarsa mallakin gidan sarauta ce.” Safiyya ta amsa cikin nutsuwa jarumta da rashin tsoro.

“Kuma gidan sarautar yana da magada." Ta qarasa maganan tana sauke idanunta akan mammina.

Wurin ya d'an kaure da maganganu qasa qasa. Wasu suka fara kallon juna.

Mammina ta d'an matse lips d'inta,tana jin wannan qasqancin da takeji cikin jininta a duk sanda safiyya ta qalubalanceta,a magana ko a aiki ko a ra'ayi,tun sultane yana raye.

“Magaji yana prison.”

“Ko ba haka ba?” mammina ta fada tana sanya idanunta cikin na safiyya da nufin bar mata wani ciwo.

Da sauri cikin fushi akhnan ta d'aga kanta tana duban idanun mammina.

“Ke kika shirya masa!” ta samu kanta da fad'a ba tare da wata shakka ba.

Hayaniya ta tashi cikin hall d'in,cikin mamakin qarfin halin akhnan din,wasu amsarta itace daidai da ra'yinsu tuntuni,amma basu da 'yancin bayyanawa.

Juyawa mammina tayi kanta a hankali zuwa ga akhnan

“Ki kula da harshenki Akhnan.” ta fada cikin sanyin murya mai razanarwa

“Rashin ubanki bai kamata ya koya miki rashin hankali ba.” Kafin Akhnan ta sake magana,qofar hall d'in ta bud'e da sauri.

D'aya daga cikin jami'an da aka zube cikin gidan tun rasuwar sultane wanda ba wanda yasan amfanin me suke ya shigo. Sai wani jami’in ya shigo da numfashi sama-sama kamar wanda yaci gudu.

A hannunsa akwai wasu takardu masu hatimin masarautar agadez.

“An samu wasu sabbin hujjoji.” Wurin ya yi tsit nan take maganansa na amsa kuwwa cikin hall din.

Idanu haisan ya aza a kanta yana tattara dukka attention dinsa a kannata,mammina ta d'an jingina bayanta jikin kujera.

"Calm....too calm" Ya fada can qasan ransa.

Jami’in ya qarasa gaban majalisar ya bud'e takardun.

“Wasiku ne…” muryarsa cike da nauyi ya dora

“…da suka shafi wani shiri na tayar da tawaye.”Jami’in ya ci gaba da karantawa.

Lissafowa ya fara yi,sunayen guards,lokutan ganawa da kuma sirrin shirin fasa prison d'in da Ahmad yake kulle. Komai a tsare daki daki. Sai ya karanta layi na ƙarshe.

“zuzzurfan bincike ya bayyana cewa dukkan umarnin sun fito ne daga MORSA SAFIYYA". Maganar tazo da wata irin razani.....wani irin gigitaccen yanayi da hankali bai taba kawoshi ba. Wurin ya hargitse da surutai. Wasu suka mikewa tsaye cikin mamaki.

“QARYA NE!” falaak ta fada da wani razanannen sauti. Bata gane komai akhnan,kawai hannunta ta miqa gurin da jami'in dake daura da ita yake tsaye ta fizgi takardun daga hannunsa.

Da sauri ta fara dubawa,zuciyarta na bugawa. Tunaninta taji kaman zai juye lokaci guda,saboda hujjojin sun yi kama da gaske sosai.

“No…” ta fada da harshen faransanci a razane. Cikin rawar murya ta sake cewa

“Wannan ba gaskiya bane…”

Mammina ta miqe tsaye a hankali,wani kwantaccen murmushi da ba kowa zai iya ganeshi ba kwance qasan Fuskarta

“Hajiya Safiyya…” ta fada cikin izgili da cikin cikakken iko

“Bisa dokar masarauta…”

“…ana zarginki da had'a baki wajen tayar da tawaye akan karbar karagar mulki"

"Ina jami'an tsaro?" Ta fada da muryar gaggawa. Kaman a shirye suke daman,umarnin kawai suke jira,nan take suka shigo cikin hall d'in. Makamai d'aure a jikinsu,kamar wadanda sukayi shirin shiga fagen yaqi.

Da sassarfa akhnan ta miqe tana matsawa gaban morsa safiyya. Wani irin tashin hankali.....burin bata kariya da bata taba jinsa ba na har abada ya taso mata.

“Babu wanda zai taba ta!” ta fada tana fidda manyan blue eyes dinta waje.

Dakatawa sukayi,kaman sunji umarni daga gareta ne,saidai ba haka ba. Har yanzu ita din d'iyar sultane ce,wani abu bai sauya wannan matsayin nata ba,kuma ita din matar sheikh haisam ce,babu wanda zaiyi kuskuren kaudata koda giyar wake yasha.

Mammina ta lura da hakan,sai idanunta suka qanqance. Wai me yasa har yanzu da sauran wannan mutucin nasu a idanun mutane?,harda mutanenta ma ballantana nasu mutanen?.

“Wannan rainin hankalin ne ya lalata wannan gida!” ta fada tana duban kowa dake gurin.

"Tana ganin ta isa ta sauya doka kota hana zartar da ita?." Ta fada da sigar tambaya me cike da zafi.

A hankali,kuma cike da tarin nutsuwar nan morsa safiyya ta miqe tsaye. Cikin alhini. Cikin mutunci. Kamar ba ita aka karantowa wadannan munanan zarge zargen ba,ta gyara mayafinta cikin nutsuwa,sai ta kalli Mammina kai tsaye.

“Ina miki jaje.....Kin kasa cin galabata yana raye.”

“Shi yasa kika jira mutuwarsa......wannan itace CIKAKKIYAR FADUWARKI....WANNAN KE NUNA KIN KASA KIN GAZA....ina sake jajanta miki akan gazawarki" ta qara fada wani murmushi yana fita daga saman labbanta.

Wannan murmushin dai.....wannan murmushin data tsana a fuskar safiyya. Wai sai yaushe?,sai yaushe zata samu nasarar dakushe wannan murmushin?. ta d'an matse hab'arta tana jin murmushin safiyya kamar zubar garwashin wuta saman fuskarta.

“Ku tafi da ita.....doka ta hau kanta” matsawa sukayi,saidai kowa ya kasa saka mata qarfe ko tabata.

"Muna iya tafiya" D'aya daga cikinsu ya fada muryarsa da nauyi sosai.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Kuka falaak ta rushe dashi,yayin da Akhnan jikinta ya dauki rawa da wani matsanancin fushi. Gaba daya hall d'in ya rikice da wani yanayi me taba zuciya.

Duban akhnan morsa safiyya tayi,sannan ta kama hannunta a tausashe tana murzawa da wani yanayi daya taimaka wajen tattara nutsuwarta na dan lokaci.

“Ba kowanne yaqi ake cinshi da ihu ba.” cikin nutsuwa ta d'ora

“Wani lokacin gaskiya tana jira ne kawai......tana jiran lokaci ta bayyana kanta tayi yado da yabanyar da kowa zai ganta". Saita zame hannunta daga cikin na akhnan din ta fara takawa cikin nutsuwarta.

Dab da haisam ta dakata,ta tsaya ta kalleshi still da murmushi.

"Ga amanar 'ya'ya na nan.....ina da tabbaci da yaqini a kanka,na yarda dakai d'ari bisa d'ari,ba zaka taba cin amanar sultane ba.....ba zaka gaza daga riqon amanarsa ba.....ba kuma zaka kasa ba har abada" Ba tare data sake kallonsa kota sake cewa komai ba,taci gaba da takawa tana fita,jami'an tsaro a gabanta wasu a bayanta.

Kallo daya kawai. Amma kallon ya isa ya saka wasu daga cikin dattawan majalisar jin tsoro. Saboda har yanzu Haisam bai motsa ba. Bai hana komai ba. Kuma wannan shiru nasa… shi ne mafi tayar da hankali a cikin duka masarautar. Baga mammina kawai ba.....ga kowa da kowa,kowan din da ajin da yake sanyashi.

"Sun hada kai ne da mammina"

"Shima tsoro yake"

"Bazai iya da ita ba" Da sauran maganganu masu kama da wannan.

*BAYAN SHUDEWAR WASU AWANNI*

Daren Agadez ya yi nauyi da tashin hankali mara misaltuwa a zukata da rayukan al'ummar masarautar dama na wajen masarautar.

Tun bayan tafiya da morsa safiyya sam akhnan ta kasa samun nutsuwa. Tayi kuka irin kukan daya ninka wanda tayi randa ta tako agadez ta tarar ba sultane babu dalilinsa.

Komai yana mata yawo a kai,kama Ahmad,canjawar masarautar da wani mummunan yanayi mara dadin ji ko saurara.

MAMMINA......yadda komai ya sauya cikin d'an lokaci. Yadda komai ya fara ta hannunta?. Komai ya soma ta sanadinta?. Komai ita ta shukashi?,ita ta farar dashi?.

Ta kasa yarda d'ari bisa d'ari akan haka kawai komai ke tafiya haka,saboda a duk rayuwarta,ko da Mammina tana da tsauri… ta tab'a d'aukarta a matsayin uwa......da idanu irin na uwa take kallonta.

Ita ta raineta tun shekarun quruciya har ta girma ta zama mutum......ita ta koya mata abubuwa masu tarin yawa. Ita ta rungumeta lokacin da tana qarama,lokacin da batasan komai ba,batasan kowa ba,lokacin da batasan hagunta ba batasan damanta ba.

Ko da akwai nisa a tsakaninsu wannan nisan baya hana mammina sanyata ta jita kamar tana a gabanta.

"Amma me yasa?,me ya sauyata?,me ya birkitata ta zama cikakkiyar maqiyiya kuma abokiyar gabar sultane iyalinsa dama masarautar agadez gaba daya?" Ta yiwa falaak tambayar wadda ke kwance a gabanta saboda jirin daya kusa kayar da ita

Readers Also Read

More by Huguma