Kenza eBookz

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 67

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 67

L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 67: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 67. “Ku koma ku gaya mata wani abu." Yayi maganan calmly…

3,340 words

“Ku koma ku gaya mata wani abu." Yayi maganan calmly kamar ba shine zuciyarsa ke zabalbala ba. Ba wanda ya iya koda motsa yatsarsa,sai ya sake magana. A hankali. Amma kowace kalma nada wani irin kaifi dake iya fede zuciya saala saala.

“Ahmad…” ya irga da nutsuwa sosai.

“Safiyya…”

“…na ƙyale ta.” Akhnan ta tsaya cak,saboda yadda muryarsa ta canza.

“Na ƙyale ta tana wasa da iko…” ya fada yana tsuke idanunsa sosai launinsu yana sake jirkita zuwa yanayin da suke komawa idan yana cikin tsananin fushi da b'acin rai.

“Saboda tana tona kanta da hannunta.” gaba daya suka qarasa daskarewa a gurin da jin irin saqon da yake aikewa mammina.

Sai ya d'an juya kadan. Ya kamo hannun Akhnan gaba d'aya cikin nasa. Riqon hannun da su kansu saida suka bi hannuwan nasu da kallo.....wani abu cikin kansu da zukatansu yana gaya musu SAQO NE DAGA ZUCIYAR WANI ZAKIN MAZA.

“But this woman?” Ya furta yana dubansu,duba irin na kai tsayen nan wanda babu sassauci a cikinsa.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

“MATATA CE!!!.” Wani irin shiru me ban tsoro ya sake ratsawa.

“And if Mammina has forgotten…” ya fada da wani nutsuwa me karya qashi da zuciya.

“…ku tuna mata.” Sai ya matsa gaba kad'an.

“Akhnan…”ya kira sunan Lower voice,amma cike da wnai respect cikin kiran sunan kawai.

“…ita ce layin da babu wanda yake tsallakawa!!!.”

Kamr jininsu ya tsaga ya ajiye wannan saqon haka sukaji. Jami’in da yake shine shugaba sai yarasa yadda zai hd'iye yawunsa.

Har a jijiyoyin jikinsa yakejin wannan ba gargadi bane kawai.......RANTSUWA CE!!!......ALQAWARI NE.

Hannunsa ya sanya,ya karb'i takardar daga hannun jami'in finally. Ya kalla na second biyu. Sannan ya zame yatsunsa daga na akhnan,ya yayyagata gida biyu.

Akhnan ta zaro ido. Gaba daya Guards d'in kowa ya shiga wani irin shock.

Saboda babu wanda ya tab'a karya umarnin Mammina haka a bude a bayyana a gaban jama'a.

Saki takardun yayi suka zube k'asa iska tana sake d'ai d'aitasu a gurin da wani yanayi na rashin daraja da tozarci.

“Ku fita.” ya fada calmly. A karon farko babu wanda ya motsa saboda tsoro. Sai ya d'an d'aga gira kad'an.

“Ko sai na manta cewa ku kuna aiki ne kawai?”

Sunkuyar da kai sukayi da sauri,suka kuma soma retreating da sauri. Amma saidai kafin jami’in ya fita,haisam ya sake kiransa.

“Tsaya.” Mutumin ya tsaya a take kamar yadda ya buqata,sai haisam ya zuba masa ido da wani irin sanyi mai kashe jiki a idanunsa.

“ka fada mata wannan da kyau.” ya furta a hankali

“Na yi shiru saboda na yarda.”

“Kar ta tab'a kuskuren tunanin na kasa tsayarda ita.” dukka gurin ya dauki shuru

“Saboda ranar da zata sa ni shiga tsakaninta da Akhnan…” ya damqe haqoransa har hakan yana nuna alama ta saman kumatunsa,ya kuma dunqule hannunsa yana son boye azalzalar da zuciyarsa ke masa.

“…ita ce ranar da zata fahimci ban tab'a shiga yaqi da ita ba tun farko.” taku uku yayi ya basu baya ba tare da sake umartarsu su fita ko su zauna ba.

Kamar masu turereniya suka soma fita,kamar suna son barin wajen kafin wani abu ya faru.

Tsaiwa kawai akhnan din tayi tana kallonsa. Tsahon saninta dashi.....tsahon sanda ta fara ganin fuskarsa idan ka cire randa tamim yaso tafka wannan gangancin bata taba ganin fuskarsa a haka ba.

Wani irin sautin bugu zuciyarta take bayarwa.

"Ya salaaammm......ya ilaheeee" Ta fada cikin zuciyarta. Zaki ta nema.......sai kuma ta samu sama da abinda yafi zakin. Jarumta.....qarfin zuciya da zallar kwarjini me yagalgala zuciya.

A hankali ya juya gareta,nan take yanayin idanunsa ya canza,ya sake komawa wannan haisam din......SOFT HAISAM da take gani kowacce rana.....ba wanda ya gama magana yanzu haka a gabanta ba. Sai ya d'ago hannu ya shafi gefen fuskarta cikin kulawa.

“No one will touch you.” ya fada da dukkan zarrarsa.

“Na miki alqawari.” ya sake tabbatar mata.

A yinin ranar gaba daya,wani yanayi daban take gani tattare da haisam din.

Wani abu ya sauya a cikinsa...... Ba a fuska ba. Ba a kalamansa ba.Amma a idanunsa… akwai wani irin yanke hukunci da ya fara bayyana.

Kamar zuciyarsa ta gaji da jiran lokaci. A daren ranar.......akhnan ta soma lura da kowanne canzawar motsi na haisam. Kad'anne.....wata irin kakkaifar alaqar zuci data qullu tsakaninsu ba tare da dukkaninsu sun ankara ba ya sanya take gane komai nashi a yanzun.

Yawanci idan dare yayi yakan kasance kusa da ita. Ko yana karanta wani abu. Ko yana karatu a library dinsa. Ko kuma kawai yana zaune yana kallonta idan ta kasa bacci.

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 121* ___________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_*

*_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_*

*_BONONZA DA PROMO akai akai_*

*dukka sai a HUGUMA CLOSET*

*Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka*

*shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami*

*_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_*

*_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝

https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX __________________________

Amma a yau yawan fitarsa ya qaru. Wayarsa tayi ringing da yawa sama da yadda ya saba ji. Yana amsa wayarsa cikin low voice. Yana fita balcony. Ko ya shiga private study.

Dogayen calls,muryarsa low da wani irin controlled a cikinta. Ko kusa.....ko alama bata d'auka zata tsaya koda a gefan wannan matsayin da take ganin ya azata ba. Bata taba zata ko tunanin matsayinta yakai har yau haura haka ba sai a yau din. Saboda ita.....saboda ita kawai ya rasa dukka nutsuwarsa?.

Cikin dare sau biyu tana farkawa ba tare da ta ganshi kusa da ita ba kaman yadda ya saba.

Ta miqe a hankali tana sauka daga gadon,ta shiga toilet tayi fitsari. Shi yasa takejin wani emptiness a cikin baccin nata,ashe rashinsa ne a kusa da ita?. Mamaki ya sanyata sakin murmushi duk da jagulewar da har yanzu zuciyarta take ciki game da lamarin mammina.

Tana fitowa daga toilet din sai ta hango haske a kunne ta corridor.

Ta taka a hankali ta tsaya bakin qofar. Idanu ta zuba sosai,qofar bata kammala rufuwa ba,akwai siririn space da yayi ragowa,wanda ta nan ne hasken ya samu daman fitowa. Ta nan din ta hangeshi,idanunta ya sauka a kansa a hankali.

Haisam zaune cikin dim light. Files da takardu sun cika table din dake gabansa.

Wayarsa a kunnensa. Wani old map a buɗe gabansa. Qasa qasa takejin muryarsa,wannan muryar da yau tun dazu amonta ya canza da wani launi na daban.

“No.” ya fada da low and cold voice

“I said before sunset” sai yayi shuru yana sauraron dayan b'angaren. Ya motsa a hankali yana daga wata takarda yana kallonta.

“Everything must be ready.”

“No mistakes.”

Idanunta ta lumshe tana kuma budesu lokaci daya dukka a kansa. Duk wannan yaqin da akeyi hakan bai hana soyayyarsa ginuwa cikin ranta ba. A yau yadda yayi matan sai ta sake jin tafi kowacce mace sa'ar samun miji da ba irinsa. Sai ta jita tana komawa sarauniyar matan duka duniya....bawai sarauniyar agadez kawai ba.

Bata tab'a ganinsa cikin irin wannan tension din ba.

Komai na iya taku da tsaro yabi jikinsa.....don haka a jikin nasa yaji kamar motsinta.

Baya taja kadan,sai kuma taga qofar ta bude. Haisam ya fito. Sanye da black qatar thobe da bai rufe maballan gabanta ba,wannan ya sanya lallausar gargasar dake qirjinsa a kwance ta fito.

Hannunsa ya sanya a hankali yana shafa gurin maballan,shima ya manta.....ya mañta a bude suke tun dazu,sau yasa hannunsa daya da yatsunsa yana qoqarin ballewa. Kunya ta kamata,ta dauke idanunta gefe. Hala yaga tana kalle masa qirji shi yasa ya ankara da bai balle ba yake ballewar. Idanunsa suka sake sauka a kanta instantly. Na second biyu,tsigar jikinsa na tashi a hankali saboda yadda farar night gown din ta mata kyau ta kuma karbeta duk da kaurinta,gashin gaban goshinta ya fito sosai ya kwanta,ya sake fidda kyanta.

“Me yasa baki kwanta ba?” yayi tambayar calmly.

Akhnan ta kalleshi cikin shakku.

“Kai fa?” ta fada softly

“Tun ɗazu baka huta ba.” Sai ya d'an yi shiru. Kallon da yake mata yanzu,cike yake da tunani

“Akwai abubuwan da ya kamata su motsa kafin lokaci ya kure.” ya fada da tattausan sautin nan nasa.

“Wane irin abubuwa?” ta tambaya cikin rashin fahimta tana matse girarta. Ta masa kyau....wani irin mugun kyau,sai ya kasa riqe kansa ya matsa kusa da ita a hankali.

Hannu ya daga yana gyara mata gashinta daya biyo ta cikin dankwalinta me santsi ya kwanta gefan kunnenta,sannan ya sake gyara mata zaman dankwalin. Gentle habit nasa data lura dashi kenan,yana killace komanta.

“Things that should’ve been done earlier.” idanunsa take kalla,wadannan idanun masu taushi da tsananin haske,amma a yanzun idanun sunyi nauyi,kamar bai yi bacci ba kwata kwata,cakude da wani boyayyen sirri.

“Haisammm…” ta kirashi da sound da yanayin nan da yakeso a muryarta.

“Me ke faruwa?” Sai ya zuba mata ido na wasu seconds. Wani irin kallo mai zurfi. Kamar yana jin ciwon ganin ta cikin wannan halin yake sake kallonta sosai.

“Trust me a little longer.” bata gane ba....sam bata fahimci me yake nufi ba,wannan amsar tasa,ta qara mata rud'ani.

Ta sani......haisam baya roqon trust,yawanci kawai yake daukar mataki ne. Sai ta zabi ta matso kusa da shi.

“Yana da alaqa da Mammina?” ta tambaya kai tsaye. Ya matse haqoransa guri guda.

“It has to do with ending this." Sai ya kamo hannunta ya sanya cikin nasa. Yanason wannan kyakkyawan lallausan tafin hannun.

“Ki koma ki kwanta" Ya fada yana murza mata bayan hannunta a hankali.

“And no matter what happens tomorrow…”

“…stay beside me.” saita tsaya kallonsa,tsalle zuciyarta takeyi. Me kuma zai faru goben yake neman hakan a tare da ita?. Zata rasashi ne?,shin zata rasashi ne kaman yadda ta rasa komai da kowa nata?. Idan ta rasa kowa ta iya jurewa.....anyaaaa......anyaa zata iya jumurin rasashi?.

"And no matter what happens tomorrow… stay beside me.” ta sake maimaita kalmar,saboda yadda ya fadi maganar. Kamar mutum mai shirin shiga wani yaqi ne.

“…Tomorrow?” ta tambayeshi a fili. Haisam bai amsa nan take ba,sai ya sauke idanunsa kan hannunta dake cikin nasa,kamar yana tunanin abubuwa masu yawa a lokaci guda.

“Some truths…” shuru

“…change everything.” qara rikitata yayi.

“Haisam…” ta sake kiransa tana sake hade tazarar tsakaninsu. Tsoro takeji.....bataso komai sabo ya sake tasowa a yanzu. Cikin matsala masarautar take sosai.....basa buqatar qarin wata.

“Kana bani tsoro.” Sai ya dago idanunsa zuwa cikin nata a hankali da wani lallausan kallo.

“I’m trying to protect you from it.”

Sai ta kalleshi cikin shiru,saboda yadda yake magana yau daban yake da sauran ranaku da lokuta. Kamar yana bankwana da wani zamani ne.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Iskar dare na motsa labulen corridor din a tausashe. Wani irin shuru ya rufe tsakaninsu.

Idanunta dake narkewa a kansa suka lura da gajiyarsa. Fararen idanun nan da suka zama jajaye. Yadda kafad'unsa suka sake.

A hankali ta d'aga hannunta ta taba gefen fuskarsa. Karo na farko cikin kwanakin nan,taji ita takeson lallashinsa ba yadda shi ya saba yi mata ba......ita ce take son ta kwantar da damuwarsa.

“Ka huta kad'an…” cikin murya me kama da rad'a,duk da rudanin da tunaninta ya shiga.

“Please.” ta qara da fadin hakan ganin yana tsaye kawai yana kallonta.

Ya lumshe idanunsa na second daya da hannunta a fuskarsa. Kamar tabashin kad'ai yana rage masa wani abu.

Ya bud'e idanunsa a hankali,sai ya kamo hannunta ya sumbaci bayan tafin hannun nata a tausashe.

“After tomorrow.” cikin low voice

“I’ll rest after tomorrow.” ya fada cikin coolness.

Wannan kalmar tasa,ta sake bugun zuciyarta da qarfi. Saboda ta fara jin wani tsoro da fargaba sosai akan kalamansa.

Ta matso jikinsa da wani irin sanyi,ba tare data furta kowacce kalma ba,ta jingina kanta a qirjinsa,wani yanayi dake bata nutsuwa.

A nutse da taushin nan nasa haisam ya sauke hannunsa a bayanta,da wani yanayi na bada kariya ta gaske. Na wasu seconds babu wanda yayi magana.

Bugun zuciyarsa ke sauka a kunnuwanta,da wani yanayi me sassauci a cikinsa. Abinda ya fi bata nutsuwa a yanzu.

“Ka yi min alqawari." muryarta can qasa

“Ba zaka barni cikin duhu haka ba.” Sai ya sauke habarsa a saman kanta.

“I promise…” da dakusashiyar murya irin ta me rad'a

“…when it’s over, you’ll know everything.”

"Komai?” ta tambaya da zaquwa a muryarta. Juyo da ita yayi sosai suna fuskantar juna,sai idanunsa suka tsaya cikin nata. Da zuzzurfan kallon nan.....da wannan gaskiyar da take gani ko yaushe fal idanunsa.

“Komai" Ya bata tabbaci.

A hankali ya riqe hannunta yana tafiya da ita zuwa room bedroom din. Wannan lokacin,ba kamar wanda yake lallashin mai kuka ba,aah....da wani irin tattalinta suke takawa.

Ta zauna gefen gado tana binsa da ido yayin da yake cire agogonsa. Yana aje wayarsa. Yana sake duba wani saqo da ya shigo. Kuma duk lokacin da screen din wayar ta haska,fuskarsa qara yin serious take.

Ta runtse idanunta na taqaitaccen lokaci. FARGABA....fargaba takeji sosai,cikin sanyin murya tace.

“Haisamm…”

“Hm?” ya amsa,amma bai juyo ba tukuna

“…duk ko me kake shiryawa…” sai ta dakata kafin ta qarasa da sanyin muryar dake cakud'e da tsoro.

“Ka dawo min lafiya.” ta qarasa fada muryarta tana rawa,zuciyarta na motsi a cikin qirjinta.

Haisam ya tsaya cak. Kalmarta ta sauka a zuciyarsa da nauyi.

A hankali da tarin nutsuwar nan tasa ya juya gareta. Kallon da yayi mata yanzu,ya fi kowanne taushi. Sai ya qaraso kusa da ita. Ya sunkuya gabanta. Ya d'ora goshinsa a nata.

“There is nowhere in this world…”

“…I would go without coming back to you.” ya fada suna musayar numfashi shi da ita.

*_Uhmmmm😍🥰🥰,ita wannan soyayyar......koda a filin yaqi suke inajin ba abinda zai dakusheta_*

*_to dani daku sai nace mu jira goben.....muga abinda goben zatazo mana kuma dashi_*

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 122* _________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_*

*_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_*

*_BONONZA DA PROMO akai akai_*

*dukka sai a HUGUMA CLOSET*

*Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka*

*shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami*

*_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_*

*_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝

https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________

*SECRETS BENEATH THE CROWN*👑

Tun a asubahin ranar masarautar agadez dama wajenta ya cika da sanarwa me matuqar qarfi data girgiza hankali da tunanin kowa. GIWAR AGADEZ mammina.....na gayyatar duk wani isashe wanda ya isa ya fada aji cikin agadez dama masarautar zuwa kotun masarautar domin yanke hukunci. Hukunci akan AKHNAN......d'iya ga sarki sultane. Hukuncin da ba na komai bane......face ta raina umarnin masarauta........ta wulaqanta dokar masarauta ita da mijinta......ta kuma yaga takardun aike na fada wanda babban laifi ne aikata hakan.

Ba'a aikesu musu direct ba......saidai ya tsinci maganan sanda yake fita zuwa sallar asuba. Sallar asuba da shine ya jagoranceta a asubahin wannan ranar. Idanunsa cike da bacci.....gangar jikinsa fal gajiya,kansa yana sara masa da masa ciwo kadan kadan,to amma a duk sanda zuciyarsa ta tuna masa gagarumin abinda zai faru a safiyar ranar sai yaji gajiyar da baccin dukka sunyi nasu guri.

Ya shigo ya samu akhnan saman abun sallah. Yanayinta ya canza ba kaman sanda ya fita ba. Ya zargi taji wani abu.....amma kuma inda taji din yana kyautata zaton tashin hankalinta da rud'aninta zaifi yadda yake gani a yanzu tattare da ita.

"Ta hada taro don zartarmin da hukunci" Ta fada tana duban fuskar haisam daya zauna a hankali saman sofa.

Idanu yadan zuba mata,kafin a hankali ya miqa hannunsa ya riqe nata a ciki.

"Wannan jarumtar da nake gani a yanzu cikin idanunki.....daga ina?" Yayi maganan da wani salo daya sanya murmushi qwace mata. Tadan murmusa kadan,duk wutar dake ruruwa a zuciyarta me tsananin gaske,amma zuwa yanzu.....tana jin yarda dashi,tana jin aminci a dukka kalaman daya gaya mata daren jiya. Bayan wannan kuma......a yanzun tana jin ta shirya fuskantar komai......ta shirya fuskantar kowacce rayuwa da zata zo mata. Ta sauke fararen blue eyes dinsa a nutse a kansa.

"Tunda ina auren jarumi......dole ne nima na zama jaruma ko?" Maganan ya sanya wani tattausan murmushi subuce masa. Ya zuba mata idanu sosai idanunsa suna lumshewa gami da bude kansu da kansu.

"Na gode.....na gode da wannan amincin.....da wannan shaidar" Ya fada yana gyada kai.

"Ba abinda zai sauya alqawarinmu na jiya......zaki zamana a gefe na kaman yadda zan zama a gefanki......komai dadi komai wuya.....har abada" Kai ta gyada masa a hankali,sai ya sakar mata hannu a hankali,ya sake miqa hannunsa ya dauki wani alqur'anin ya miqa mata.

Bata musa ba,ta saka hannuwanta dukka biyun ta karba,ta bude daidai iya yadda karatunta yakai,ta fara karantawa kamar yadda taji yana rera karatun a nutse da wannan lallausar muryar tasa da zata iya sanya mutum manta damuwar da yake ciki.

★ Babban courtyard na masarautar Agadez cike yake da jama'a. Dattawa. Masu fada aji. Guards. Talakawan dake rayuwa cikin masarauta,kuma qarqashin kulawar masarautar. Kowa ya hallara.

Wani irin farinciki takeji.....wata irin annashuwa da walwala,musamman idan ta aza idanunta akan duk mutanen dake zaune a gurin,taga kowa yana zaune ne bisa umarninta.....yana so ko baya so. Kowa biyayya yakewa umarninta yana so ko baya so. Kowa gudun saba mata yakeyi da dadi ko ba dadi. Taja iska sosai tana jin cewa.....yau zata kauda katanga ta qarshe......yau zata zubda katanga ta qarshe da zata qarasa bata cikakkiyar dama qarasa tattarewa da nade tabarmar data shimfida na rayuwa cikin agadez na shekara da shekaru.

Saidai idan ta juya inda tasa aka shirya don akhnan da mijinta su tsaya su fuskanci hukunci,taga gurin empty. Ta kalli agogo taga yadda suka shanya ta. Ba ita kadai bama kowa da kowa sai taji ranta ga baci. Dole ne ta tozartashi shida matarsa a yau din,a bainar jama'a. Dole ta bashi guzurin da zai isa Ethiopia dashi.....guzuri mafi muni kafin ta tattara ta bishi a qarasa yaqin a can.

Safiyar ranar da mammina zata fito ta yankewa Akhnan hukunci a gaban fada.

Private royal chamber dinsu ya yi shiru.

Daga waje ana jin motsin guards. Surutan bayi. Motsin mutanen da suka cika courtyard din. Saidai tana magana kowa yaja bakinsa ya tsuke yana saurarenta.

"A shaidawa akhnan cewa......ba zamanta muke a nan ba.......ta gaggauta fitowa zuwa gaban hukunci" Juyawa me isar da saqon yayi yana fita da gaggawa.

Daga can sassan haisam.....cikin qawataccen bedroom din nasa dake da wani yanayi na nutsuwa. Kaman a jininsa ne.....komai nasa nutsuwa yake nunawa. Koda doki ne.....muddin mallakinsa ne zaka ganshi da wannan tambarin.

Akhnan ce tsaye gaban babban mirror din d'akin,sanye da wani elegant dark royal attire. Black da deep gold. Wani luxury hijab ta dora a sama na luxury silk mai laushin da yake nuna matsayinta.......matsayin nan na sarauniyar agadez......matsayin nan na akhnan muhammad hammud.....suna da matsayin da ba wanda ya isa ya qwaceshi. Haisam ne......haisan da kansa ya zabar mata wadannan kayan......wannan shigar......tamkar yanason amfani da wannan damar ya tabbatarwa da duniya matsayinta.

Tayi wani irin kyau.......amma duk kyawun da tayin idanunta sun gaji. Irin gajiyar dake bayyana kanta koda anyi nufin boyeta.

Readers Also Read

More by Huguma