Kenza eBookz

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 70

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 70

L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 70: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 70. *H U G U M A*

3,322 words

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 125* ___________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0

*IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA*

*IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA*

*_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_*

*_Assalamu alaikum my loyal people_*

*_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_*

*_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_*

*_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_*

*_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_*

*_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_*

*_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_*

*_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_*

*INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA*

*Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa ameen* ____________________________

Qarya take.....ta sani itama qarya take,a yanzun a duniya akwai wani abu da zai sanyata ta qishi?. Anya kuwa?,koda ranta ya dauka kuwa tunda har ya bawa sultane wata sabuwar rayuwa?. Ya fiddasu kuma daga makauniyar rayuwar da suke ciki.

Bai barta ba bai kuma matsa mata ba.....amma da wani irin salo sai daya tabbatar ya sanyata bacci saboda zuciyarta ta huta,jikinta kuma ya karbi treatment din da aka bata. Ba bacci bane burinta ko muradinta ba.....muradinta taga sultane,amma sai gashi haisam din ya maidata duniyar baccin da bata shirya ba.

★★ Ta sake d'aga idanunta a hankali ta kalli babban royal agogon dake kafe a bango,kafin ta saukesu a nutse akan haisam.

Haisam din dake zaune saman sofa.....gabansa table ne d'an madaidaici a ajiye,samansa kuma laptop ne wayoyinsa da tarin takardun da yaketa fama cikewa tun dazu.

Idanunta suma sauka nutse akan fuskarsa,bata iya ganinta sosai,amma tar take ganin dogayen eyelashes dinsa da yake kallon takardun gabansa dasu,sai sukayi kaman sun hade da juna saboda tsahonsu,kamar kuma a lumshe idanun suke maimakon a hade.

Juriyarta ce take qarewa......haqurinta yana gazawa tana dai daurewa ne kawai. Daga d'azu da abun ya faru har zuwa yanzu haisam ya hanata fita ko ina. Ya kira mata sultane ta wayar falaak ya saka ta a handfree,kuma sultane din ya gaya mata.

"Ki zauna.....karki fita ko ina,har yanzu masarauta a hargitse take,zuwa dare....idan komai ya lafa zan shigo" Da wannan alqawarin na sultane.....da wannan idanun na haisam da yaketa tsareta dasu.....da nauyinsa na kalar hidimar da yaketayi da ita ya sanyata jan bakinta tayi shuru tana jiran lokacin da sultane yace zai shigo.

Komai dare... Komai tsahon lokaci kuwa ba zata kwanta ba. Zata yita jiransa.

Idanunsa ya daga a hankali sai suka hada idanu,ta janye kallonta daga kansa tana basarwa.

Qarin hujjarsa......tana buqatar hutu,tana buqatar nutsuwa. doctors sun hana mata stress.

Amma ita,tasan akwai wani abu daban. Tun safe yake fita yana dawowa. Long calls. Meetings. Guards daketa shigowa suna fita,duk da bata ganinsu amma tana jin motsinsu. Kuma duk lokacin data tambaya yaushe zata fita?.

"Later" Kawai yake ce mata.

Ya hana ta fita ko ina. Ya hana ta shiga council chamber. Ya hana kowa kawo mata details ya gargadi su birra sosai. Kamar yana kareta daga duniya. Ko yana boyeta daga dukkan komai.

Yanzun daya kamata tana satar kallonshi,saita zame idanunta tana maidashi akan cup din tea din dake hannunta,wanda tuni cup tea din ya riga ya huce.

Tana jin zurfin kallonsa a kanta,kallon da batasan yau adadin sau nawa ya mata shi ba.

"You’re ignoring me again?” ya furta a hankali da wannan tarin calmness din nasa. Bata amsa ba,sai kawai ta shanye tea dinta a hankali,duk da ya riga yayi sanyi ba tare data kalli haisam din ba.

Murmushi kadan ya saki.....wannan miskilancin ya motsa.....wannan izzar ta motsa......wannan jan ajin ya tashi wanda bayajin bayan mutuwa akwai wani abu da zai rabata dashi.

"learned from the best.”

Siririn murmushi ya subuce masa,ya ajiye file din hannunsa yana qare mata kallo a nutse,wannan jin kan nata yana burgeshi.

Still taqi kallonsa,sai yaji kaman ana fusgarsa zuwa gareta,ya ture gami da tattara dukkanin takardun gabansa a hankali ya miqe ya isa gabanta,takunsa masu nauyi na amsawa cikin dakin. saidai akwai tazara daya bayar tsakaninsu.

Ya sunkuya a hankali yana qoqarin kamo idanunta. Hanya qwara daya tak da zai karya alkadarin wannan rigimar.

"habibti" Ya fada a tausashe har tana jin saukar muryar a kowanne sashe na jikinta,saidai still bata amsa ba

"Kina fushi dani.....saboda naqi barinki fita waje?" Sai a sannan taso kallonsa amma ta kasa,hawaye ya taru a idanunta. Ta qagu ta sake ganin sultane,ta qagu,gani take kaman za'a sake ce mata ya sake mutuwa....gani take ban bada gaske bane shine.

"Kaine ka kulleni a nan.....kowa yaga sultane ya qara.....kowa yana samun amsoshin abinda ke faruwa a cikin gida amma bandani".

"Kina buqatar hutu" Ya motsa labbansa da wata kalar izzarsa daya saba da ita.

"No....you needed control" Wani siririn murmushi ya bayyana a labbansa.

"And if i did?" Ta zaro ido kafin ta narke fuska.

"Haisam" Ta fada a shagwabe. Takowa ya sakeyi yana sake rage tazarar dake tsakaninsu.

"Kin samu a hannuna....."

"......You think I’d let you walk into another emotional storm immediately after that?” ya qarasa fada yana dage mata dukka girarsa biyun.

Ta bude baki zatayi magana,amma sai kuma ta kasa. Cikin muryarsa akwai wani abu.....wani abu me nauyi dake bata tabbacin da dukkanin zuciyarsa yake magana. Idanunta ta sauke qasa a hankali.

"Sultane nakeson gani...."

"Zaki ganshi.....zaizo"

"You keep deciding things for me.”

"Only when I’m terrified of losing you.” Sai ya yi shiru na second biyu. Kamar yana tunanin wani abu na daban. Da alama har yanzu batasan girman matsayinta a zuciyarsa ba.....har yanzu....fake death na sultane ya karya wasu tsarukansa da yawa. Wasu shirye shiryensa. Ya shirya shayar da ita kalar soyayyar da ko cikin finafinai da litattafai bata taba cin karo da ita ba. A dubai......yaso kafa abubuwa da dama,yaso shirya abubuwa masu yawan gaske wannan issue din ya taso.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Zuciyarta ta buga da amsarsa daya bata. Duk lokacin da yake bud'e mata wani bangaren zuciyarsa,sai ta kasa ci gaba da fushi sosai dashi kaman yadda take tsarawa a bayan idanunsa.

Ya bude lumsassun idanunsa a kanta,suka hada ido,wani irin shuru ya ratsa tsakaninsu,wadannan tsumammun idanun nasa.....a hankali suka sanya jikinta ya mutu. Wani irin tsumammen kallo,kamar ita kadai ce abinda yake iya gani a duniya.

Ba zata iya jura ba,don haka ta janye idanun nata. Murmushi me sanyi ya kubce masa.

"There she is" Ya fada da wani yanayi na tsokana a cikin muryarsa.

"Who?" Ta tambaya da wani yanayi akan fuskarta. Takawa ya sakeyi yana hade tazarar dake tsakaninsu. Ya aza fuskarsa akan kafadarta,ya sanya bakinsa saitin kunnenta,muryarsa can qasan maqoshinsa da wani irin shauqi yace.

"My stubborn wife" Kusan daukewa cak numfashinta yayi. Sai daga baya ta samu ta jashi da wani irin qarfi tana saukeshi a hankali,kafin tace ko shi yace komai aka sanarmusu

"Sultane ya iso" Abinda ya sanyata miqewa cak kenan. Hannunta ya kama softly yana zaunar da ita.

"Relax" Ya fada yana duban tsakiyar idanunta,saita dakata tana kallonsa har zuwa sanda ya ta ka ya bude qofa wa sultane.

Daga bakin qofar bayyana.....yana tsaye kyam,wadannan kamannin nasa na cikakken ba'abzine tana bayyana. Giant tsaho da murjewar jikin da a yanzu akhnan taga kaman ya sake qiba ne,jikinsa ya sake yin kyau da murjewa,ya sakeyi fadi kamar wanda yaje hutu wani guri ya dawo.

Shi daya ne.....shi kadai......yana me amsa sunan MAHAIFI bawai SARKI ba. Ba shigar sake nuna saraura ko mulki. Ba guard ko daya,hakanan ba komai sai farar jallabiyyar data nuna kyans,falaak na biye dashi qafa da qafa,kamar wadda akace mata itama zai sake ba'acewa rayuwarsu. Akhnan tayi sak tana dubansa,idanunta suka cika sosai da hawaye tana kallonsa

"Zan iya shigowa?" Ya furta cikin salon neman izini,abinda ya azawa haisam kunyarsa. Girmansa yana sake qaruwa a idanunsa. Sarki ne.....amma yana neman izini ga d'iya da surukinsa.

Baya haisam yaja,yana bashi hanya cikin girmamawa. Ya soma takowa a nutse idanunsa akan akhnan. Kasa jurewa tayi ya iso gareta,sai taji kaman yayi nisa tazarar dake tsakaninsu,ta miqe cak,ta kuma kwasa da wani irin gudu da ya sanya haisam sadda kansa,quruciyarta sosai tana bayyana.

Juyawa haisam yayi ya soma takawa don ficewa da zummar basu space,saidai sultane dake rungume da akhnan a jikinsa bayan sun zauna ya dakatar dashi.

"Koma ka zauna...".

Dakin yayi shuru na wasu mintuna,bayan sultane ya kammala warware mata komai. Kuka take da wani irin laushi karyewar zuciya da nadamar irin rayuwarta ta baya. Tsanar mammina.....dama tsanar komai daya shafeta yana sake ratsata. Wanne abune yafi wannan ciwo da muni?,maqiyinka ya girmar dakai?,ya dinga bin rayuwarka yana rusata d'aya bayan daya?. Har yanzu zuciyarta bata gama amincewa da wai sultane bane raye a gabanta. Wani abu da tasan koda tafi kowa qaunar sultane a duk duniya ba zata sameshi ba,wato dawo dashi daga mutuwa,sai gashi wata babbar almara ta rayar dashi daga mutuwar da akewa shirin yiwa sadakar arba'in a jibi.

Ta kasa d'auke idanunta a kansa......idan ta tuna duka abinda mammina tayi.....ta kuma juya ta kalli sultane dinta a raye.....sai taji komai yana kwaranyewa daga zuciyarta.

"Ki yimin afuwa da barinki kika shiga wahala haka da yawa" Sultane ya fada cikin kulawa. Tabbas kowanne d'a da irin son da Allah ya azawa iyayensa a kansa,ita kam akhnan wannan tabbaci ne na cikin 'ya'yansa soyayyarta tafi ta kowa tasiri a ransa.

"Kada kace haka bappi.....bansan me zan kwantata wannan yanayin ba......na binneka.....na soma koyon yadda zanyi rayuwa babu kai....sai kuma gaka?,me yafi wannan dadi a gurina." Murmushi ya saki,ya waiwaya yana duban falaak. Shigen abinda tace dashi kenan sanda ya zauna dasu bayan sakin morsa safiyya ta dawo gida. Morsa safiyyan da har yanzu ta kasa cewa komai. Shima ya hanata cewan,yace ta huta....ta huta daga dukkan abinda ta fuskanta.

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽

💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 126*

Bawai ta wahala bane.....hasalima kulawa ta musamman da kebantattun dakuna cikin estate guda da haisam ya ware yake ajiye duk wanda yaso daga cikin jama'ar dake da gaskiya da mammina ke kora a nan suke. Estate din da ya ajiye mutane masu yawan gaske,ciki harda su yalwan da yake jiran randa zaa wuce da mammina Ethiopia ya fitar dasu gaba daya suma. A ware masu gaskiya.....irin yalwa wadda amfani akayi da ita,ita kuma tayi amfani da son zuciyarta ta zauna da mammina din a matsayin uwar d'akinta.

"Wait" Akhnan ta fada tana miqewa ta zauna sosai tana duban sultane din. Yadda tayin yaja hankulansu gaba daya.

"Bappi.....waye ya shirya wannan fake death din?". Shuru sultane yayi na sakanni,sai kuma ya saki murmushi a hankali. Ya daga idanunsa a nutse yana duban haisam.

Da sauri tabi kallon sultane din,sai nata idanun suka mata jagora zuwa ga haisam. Kansa ya kawar kad'an daga idanun akhnan din kamar wanda aka kama.

"Kai?,kaine ko?" Ta fada fuskarta tana narkewa a kansa.

Sultane dariya yayi,haisam na boye murmushinsa. Ya sani akwai abinda zai biyo baya duk ranar data karanci wannan gaskiyar.

"Shi ya tsara komai.....the hiding place....devices da ake komai kamar ina gurin,koda tari ko motsi daga masarautata.....the timing,muhammad haisam.....the silent one......alsaamit" Idanu ta zaro a hankali,saita juya inda haisam ke zaune gaba daya tana kallonsa.

"You!"

"YOU DID THIS TO ME?" Ta tambayeshi tana sake shiga mamaki. Yadda ya gudanar da komai......yadda yayi kaman da gaske sultane ya mutu alhali yasan yana raye. Yadda darare da yawa ya hana idanunsa bacci saboda ya bata comfort na gangar jiki dana zuci. Yadda yayi haquri da komai daga gareta. Duka wannan?....duka wannan kuma bayan yasan sultane yana raye ne?.

Ajiyar zuciya ya sauke quietly..... Already yasan wannan reaction din nata yana zuwa. Sunne kai kawai falaak keyi. Batasan sau nawa komai nasu zai dinga burgeta ba. Ita da maleek.....suna burge mutane da yawa......amma ita akhnan da haisam ne suke burgeta,duk da wanzuwarsu tare ba na wani lokaci me tsaho bane,amma ko na minti daya inde zasu kasance a guri daya sai taga wani abu daya tafi da ita.

"Akhnan" Ya kirata da ainihin sunanta murya qasa qasa saboda sultane dake gurin.

"No" Ta fada tana maqale kafada gami da d'aukan pillow ta jefa masa. Hannu yasa ya cafe.....wannan kallon tuhumar da take masa ya sanya ya kusa manta waye a gurin ya marairaice mata.

Tari sultane ya danyi,wanda ke cakude da dariya,kusanma don ya boye dariyar tasa ya saki tarin kadan.

"A idanunka na dinga kuka.....a idanunka na dinga jin zafin rasa sultane kana kallo......na suma duk don saboda kai?" Ta sake fada tana marairaicewa idanunta suna sake hada hawaye.

"You knew every single thing!”

"And you kept looking at me like nothing was happening!” ta qarashe fada da jefa masa harara.

Sultane dai yana gefe......still yana qoqarin adana dariyarsa bayaso ta fito. Ya lura rigima ce take jinta sosai,wadda shikam bazai iya sasancinta ba,da alama tafi qarfinsa.

"If I told you....."

"I WOULD HAVE HELPED!” ta tari numfashinsa. Wani siririn murmushi ya subuce haisam din Shima. Rigimammiya ce ya sani......amma yau a gaban bappinta take gwada masa rigimarta ta farko.

"That’s exactly why I couldn’t tell you.”

"You can’t lie to save your life.” wannan karon daga falaak har sultane dariyarsu sai data fito.

Juyawa akhnan tayi da ragowar hawayenta tana duban sultane da falaak.

"Bappi....you're supporting him?" Ta tambaya da french.

"I'm enjoying this" Ya fada abinsa a nutse.

Juyawa tayi tana sake harara haisam,hararar da take qara mata kyau ita da blue eyes dinta gaba daya.

"I was dying from grief!”

“And you kept saying mysterious things like ‘trust me a little longer’!” MITA?. Ya tambayi kansa yana matse tasa dariyar,yaushe kuma ta koyi mita?.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

"Giiftii....did you survive?" Ya tambaya a nutse,tambayar data saka falaak cusa kanta a pillow kaman wadda ta kwanta kawai,saidai dariyar ta take cinyewa. Baki akhnan ta bude cikin mamaki tana dubansa da idanunta dukka a waje.

"That's not the point wallahi" Ta fada hawayenta suna gangarowa. Tuhumarsa take a baki.....amma kimarsa ce take ninkuwa a zuciyarta. Da qyar sultane ya saita dariyarsa.

"Haisam...." Ya kirashi.

"Ka cancanci fushin nan fa"

"Na sani bappi.....na sani" Ya fada da sauri.

Ta lura kaman shi da sultane abu daya ne.... Bakinsu daya,sai ta hade hannayenta a qirji tana duban haisam.

“I’m not talking to you.”

Sai ya d'an sunkuya kusa da ita.

“You said that yesterday too.” yana jin kamar ana fusgarsa cikin wannan sabuwar character din tata.

“And I mean it today.”

“Habibti…” ya kirata.

“If I could choose between you hating me…”

“…or losing you to Mammina’s plans…”

“…I would hide it all over again.”

Kasa magana tayi,har na kusan second uku,saboda duk da haushinta— zuciyarta ta kasa qin fahimtar dalilinsa. Komai ya furta sai taji ya samu gurbi.....ya samu kyakkyawan muhalli a zuciyarta.

Kauda kanta tayi.....tana pretending fushi dashi.

“I’m still angry.” wani murmushi me cike da nutsuwa da kwanciyar hankali ya sauke. Ya sani.....komai da take pretending ne. Zuciyarta a tafin hannunsa take. Bayan a tafin hannun nasa ma......a bude kamar budadden faifai. Lokaci kawai yake jira isashe ya fara dura mata duk abinda yakeso.....ya sake maidata yadda yakeso ta kasance.

“Good.” kawai yace,bayaso aci gaba.....zai iya sauka hanya a gaban bappinta.

“What’s good about that?!” ta tambayeshi tana dan tsuke qaramin bakin nan nata.

“It means you finally have the strength to fight with me again.”

"Sai da safenku" Suka tsinci muryar falaak tana fada.....sai a sannan suka lura sultane ma shi tuni ya kusa bakin qofa abinsa. Kunya tadan kamasu.....amma sultane kamar baiga komai ba ya dakatar da haisam dake shirin masa rakiya.

"Ka zunguro sama da kara.....ka koma ka kashe wannan sabuwar qurar data tashi kuma" Maganan ya sakashi sakin sassanyan murmushi,yayi qasa da kansa yana fadin.

"A sauka lafiya" Ya maida qofar ya rufe yana durfafo akhnan din idanunsa a kanta,yanason tantance meye dalilin sabuwar rigima da sabuwar tsiwar data koyo?.

★★★Asubahin washegari......Sanda yake takowa a nutse zuwa dakin bayan fitowarsa daga sallar asuba.

Sanye yake da baqar baqar silk throb data dace da hasken fatarnan tasa ta qabilar oromo,wani irin fari me kyan gani wanda ya cakuda da hutu da kula da kai da jikinsa da yakeyi.

Itace abu na farko da idanunsa suka fara sauka akai bayan shigowarsa dakin. Tana zaune sosai saman green din abun sallah,kamar yadda tufafin jikinta suke da wannan kalar. Qur'ani ne riqe a hannunta,hasken safiya dake hudowa yana sauka a hankali saman fuskarta.

Calmly ya zauna ba tare da yayi sallama ba ganin karatu take. Karon farko da ya fara jin sautin muryarta a fili cikin karatun qur'ani.

"Ma sha Allah" Yake maimaitawa saboda yadda muryar ta masa dadi,da kuma yadda yaga dabi'unsa sun fara nasarta.

Tana bacci ya fita,ya sanya mata alarm ne kawai,tun cikin dare suna tare da sultane anata shawarwari da qoqarin gyara b'arnar da mammina tayi.

Takai ayar qarshe,idanunsa yana kanta,ta rufe qur'anin a hankali ta ajiyeshi.

"Barka da asuba.....ina kwana" Ta hada dukka ta fada tana dubansa da idanuntan nan da suka rusuna suke nuna alamun bacci bai isheta ba.

Bai amsa ba,saici gaba da yayi da kallonta.

"You’re staring again.” ta fada da murmushi a fuskarta tana tuna daren jiya yadda ya gama rudata da saqonninsa ya kuma janye jikinsa ba tare daya mata komai ba. Karo na biyu kenan..... Abun sai taji kawai ya tsaye mata kadan a wuya.....zuciyarta kuma na zolayarta da YAUSHE KIKASAN DADINSA NE?. Saidai zancan gaskiya.....a jiyan abun ya tsaye mata sosai....ta zurma da yawa.....bata kuma zaci zai barta ba saboda yadda taga shima ya fita hayyacinsa.

"You’re peaceful when you read Qur’an.”

"I like watching that" Ya qarasa fada yana motsa labban nan nasa da suka fusgi hankalinta. Labban sa muddin zai azasu saman nata......sai taji komai na duniya yana kwance mata.

Sauke idanunta tayi cikin wata siririyar kunya da yaga ta mata kyau sosai. Kaman ba ita bace a daren jiya ta nemi fita daga akhnan dinta ba zuwa cikakkiyar matar aure me buqatar kasancewa da mijinta ba. Saidai wannan little izzar ita ta taimaketa ta dawo saitinta.

"Call birra.....ta taimaka miki kiyi packing abun buqatarki daya zama necessary ki dauka" Ya fada yana lumshe idanunsa a hankali. Yana tuna wayar da sukayi da nanay a daren jiya can cikin dare. Yau zata iso agadez.....zatazo taga safiyyanta. Ta gaya masa tunda aikinsa ya kammalu......tanaso taga safiyyanta kada taje ajali ya raba ganawarsu. Ta fada masa.....zasu taho da dukka yaran......balqess ce kawai ba zata samu zuwa ba..

Ta kuma sake gaya masa zasuyi daukan amarya ne.....zasu dauki akhnan idan sun gama kwanakinsu,zasu wuce da ita gidanta Kai tsaye idan suka sauka a jimma ta tare a can.

Duk jikinsa yaji yayi laushi,shi bazai sake bari wani abu ya shiga tsakaninsa da matar sa har ya rabasu ba. A yanzu bayajin yana da wannan kunyar......wannan karar tasa dukka babu ita. Yana mazewa ne kawai bayason tabata a agadez.....kada ayi abun kunya.....amma yanzu da komai ya qare......yanaso ya nuna mata zahirin RAYUWA. Yanason ta sake sanin WAYESHI?. Yana kuma son idanunta su bude sosai.

Readers Also Read

More by Huguma