Kenza eBookz

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 87

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 87

L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 87: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 87. An fara shirye-shiryen musayar dalibai,qwararru da yan…

3,359 words

An fara shirye-shiryen musayar dalibai,qwararru da yan kasuwa. Haka kuma an ƙ Qarfafa harkokin yawon bude ido da ayyukan raya al'umma, wanda ya sanya sunan Agadez da Jimma ya fara karadewa a idon duniya.

Sai dai cikin dukkan sababbin abubuwan da Haisam ya aiwatar, babu wanda ya ja hankalin jama'a kamar shirin Hawan Daba na Jimma.

Tun lokacin da ya halarci wasu bukukuwa a Arewacin Najeriya, ya kasance yana sha'awar yadda sarakuna ke fita cikin jama'a domin sada zumunci da talakawansu. Wannan al'ada ta burge shi qwarai.

Ya yi imani cewa shugaba bai kamata ya kasance a bayan katanga koyaushe ba. Saboda haka ya gabatar da sabon tsari da zai bawa motii damar kusantar jama'arsa,musamman wadanda ke zaune a yankuna masu nisa kuma ba sa samun damar zuwa Aba Jifar Palace domin ganinsa.

Daga sanda aka sanar da ranar hawan, Jimma ta sauya gaba daya. Baqi suka fara kwarara daga sassa daban-daban na Ethiopia, har ma daga qasashe makwabta.

Masana tarihi suna son ganin yadda za a hada tsohuwar al'adar Habasha da salon hawan sarakunan Hausa.

Masu yawon bude ido suna son zama shaidun wani sabon tarihi.

Talakawa kuwa suna dokin ganin sarkinsu a cikin irin wannan biki da ba a taba yin irinsa ba a qasar baki daya.

A wannan lokacin kuwa, gidan Haisam da Akhnan ya cika da baqi fiye da yadda aka saba.

Babbar villar da Haisam ya gina shekara daya baya. Ya fidda sassanni daban daban masu daukan hankali da sabon salo,musamman bangaren underground villa wanda ya kasance mafi soyuwa a wurinsa.

Tun bayan ya lura da irin nutsuwa da farin cikin da Akhnan take samu a can, sai ya sake sanyawa akayi ginin gidan qasan ta hanyar amfani da sabbin fasahohi da kayan alatu na zamani.

Komai a gidan yana aiki ne ta hanyar fasaha. Daga ƙofofi masu gane fuska,tsarin tsaro mai amfani da basirar na'ura, har zuwa fitilu da tsarin kula da yanayin zafi da sanyi automatically kawai gidan zai sauya duka,idan dumi ko sanyi ake buqata.

Ginin kuwa yana da wani irin shimfidadden tsari mai daukar ido. Kafin mutum ya ankara, kansa zai dauke shi daga abin da yake yi ya tsaya yana kallon qawatuwar wurin.

Da daddare idan fitilu suka haska lambunan gidan, ruwa yana kwaranya a cikin mabubbugan da aka tsara da fasaha, yayin da iska mai sanyi daga tsaunukan Jimma ke ratsawa cikin bishiyoyi....wurin yakan yi kama da wani sashe na aljanna da aka saukar a doron qasa.

Kuma a tsakiyar duk wannan ni'ima da yalwa....abin da ya fi daraja a wurin ba gine-ginen ba ne. Ba dukiya ba ce. Sai dariyar yara da ke cike da gidan,iyali daya fara tarawa me yawa,da kuma zaman lafiya da qaunar da Allah ya albarkaci iyalin haisam da Akhnan da ita.

Dukka yaran falaak guda hudu....yaran shehnaz guda uku.....saina aisa guda biyu suna gidan. Haka yaran rumaisa da takanas suka taho da rumaisa sunqi zama a aba jifar palace sai nan gidan. Itama ta samu albarkar haihuwa,duka yaranta maza guda biyar,sai Anaani dake da yammata biyu qaramin namaji ne da yaci sunan ahmad sultane of agadez,yaci sunan kakansa ahmad ajani.

Da taimakon sultana data fara zama 'yammata shekara goma sha biyu data hadiman gidan ta samu suka saita yaran. Kowa yaci ya qoshi,sukayi wanka suka shirya cikin kayan bacci,suka kwanta sannan ta dawo nata sashen.

Ta manta rabonta data kwana a dakinta,don tuni haisam ya rabata da dukka dakunanta. Tana nan underground villa dinsa da idan ka shiga bakasan ma me yake faruwa a duniyar ba. Daga ita saishi kawai.

Amma ayau din sai data ratse dakinta,ta sake wanka,ta fito fuskarta tana qyalli da sheqi da sabulun Mg's soap,wanda duk dare dashi take wanka. Wannan ya sanya fatarta ta sake gogewa da wani irin glowing da kullum sai haisam ya tanka.(0806 299 1549).

Sabbin kayan bacci ta bare,wanda kusan kullum cikin sanya sabbin design take. Ba kasafai ta fita maimaice ba a dukka suturarta,ba ita kadai ba hatta da haisam dinma,har gwara yaran idan wani ya musu suna nacewa shi zasu maimaita.

Idanu ta lumshe saboda qamshin turaren shuwa incense and more da yake fita a jiki,kabbasar da aka musu tun shekaran jiya ke tashi kamar yanzu aka turarasa.(+234 704 229 3387,ina sake maimaita muku,tasted and trusted ne🙌🏽🙌🏽🙌🏽).

A nutse ta dauki hijab dinta kawai don sallar dare,wanda ta saba zuwa yanzu,kota tasheshi ko shi ya tasheta,ta zura lausasan slippers dinta ta soma sauka zuwa gidan qasan.

Daka shiga zakasan gurin yana da banbanci da kowanne sashe na gidan. Kulawa da gyara na musamman take bashi da kanta,bata bari kowa ya shiga gurin.

Har zata wuce bedroom dinsa ta fasa,ta wuce zuwa kitchen ta hada masa special tea din da yakesha duk dare don warware gajiya.

Ta shirya komai da wani irin tsarin saman wani royal tray,sannan ta taka a nutse taka wucewa dakinsa.

Qofar na scanning face dinta ta bude kanta da kanta cikin abinda baikai second biyar ba,ta qara turata tana shiga bakinta dauke da sallama.

Yana tsaye daure da fari qal din towel me laushin gaske. Iyakarsa qugunsa,don haka wannan gymnastic body din nasa na waje a bayyane.

A wannan lokacin.....ba shine ya dauki hankalinta ba. Aah....wayar dake hannunsa wanda tana sallama ya ajjiyeta saman sofa bed yana aza idanunsa a kanta.

Murmushi ya sakar mata yana takowa inda take tsaye,haka kawai yau saita samu kanta da gaza jin murmushin nasa har cikin zuciyarta. Ta sakar masa tray din ta taka a nutse tana wuceshi zuwa saman sofa din.

Wayar ta kalla ta dauke kai,ba abinda yake dawo mata sai kiran daya dinga shigowar wayar tasa a dazu. Ba suna a number din......amma kuma duk wanda zai kirashi wayar zata sanar masa ko waye koda bai sani ba.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Menelik ta gani a rubuce a jiki. Wani suna guda daya da bazai dusashe daga kanta ba. Idanunta ta dauke a hankali daga kan wayar ta maida kansa. Saita sameshi shima ita yake kalla yana sipping tea dinsa a hankali.

Saqo ne ya sake shigowa,sai ya miqa mata hannu kai tsaye. Mamaki ya daskarar da ita ganin yadda yake dubanta kai tsaye.

"Omar ne.....muna magana dashi network ya dauke,inda yake ba network me kyau......" Bata tsaya qarasa ji ba kawai ta bude saqon kai tsaye,kasancewar komai na wayarsa ta sani. Pin da komai....ba iya na waya ba,komai nasa dake da password ko pin ta sani.

*_Muna hanyar zuwa kallon hawan Durban,koda ban samu ganinka a kusa ba....a nesa kawai ya wadatar....menelik_*

".....suna son zuwa da saamee,to amma yace batajin dadi....zai taho kawai shida yaran" Ya qarasa fada yana ajiye mug din saman table din.

"Saamee?" Ta fada da sigar tambaya,kansa ya daga yana dubanta jin sound dinta ya sauya.

"Ko ba saame ba?,saamee ta tafi.....amma ga wata saame dinnan" Ta fada tana wurgar da wayar gefe wani irin bacin rai yana mata tasiri.

Wayar yabi da kallo yadda ta kangarar da ita,saura kadan takai qasa,kuma tabbas data fadi fashewa zatayi.

"Eh saamee" Ya maimaita yana dubanta kai tsaye wani abu me kama da fushi yanason masa tasiri.

"A baya saamee.....yanzu kuma menelik?,menelik dai?,wa yasan sauran dauke boye da ban gansu ba?" Ta fada wani wutar kishi tana tasiri a ranta.

"Akhnan" Ya kirata a nutse yana ajiye turaren da yayi niyyar fesawa.

"Ki kula da yadda kike magana" Ya fada calmly saidai ransa yana sake baci.

Wata dariya ta saki wadda tafi kama da kukan bacin rai.

"In kula?,wai nice ma zan kula?,Na bude saqo da idona na gani. 'Ko da ban samu ganinka a kusa ba, a nesa kawai ya wadatar...' Wannan ma ba komai bane kenan?"

Ya sauke numfashi a hankali, yana qoqarin danne haushinsa.

"Kin gama?"

"A'a, ban gama ba." Ta miqe tsaye.

"Abinda nake son sani shine, me yasa har yanzu take turo maka irin wadannan saqonnin?"

"Saboda bansan da zamanta bama,don haka ban hana ta ba."

Kalmar ta fito daga bakinsa cikin sauqi,da kuma dukka gaskiyarshi.....amma ta sauka a kunnenta kamar dutse.

"Ban hana ta ba?" Ta maimaita cikin rashin yarda.

"Eh" Ya amsa mata kansa tsaye da gaskiyar nan tasa.

"To ni kuma na ga laifin saqon." Ya miƙe daga kujerarsa a hankali.

"Saboda kina kallon sa da wata ma'ana daban."

"To ka gaya min wace ma'ana yake da ita?" Ta jefa masa tambayar kai tsaye. Shiru ya dan ratsa tsakaninsu,ya fuskanci shaidan keson tasiri a ranta akan abinda shi baida muhimmanci ko kadan a tare dashi.

Sai ya dauki wayar daga inda ta jefar, ya ajiye ta a gabanta.

"Kin san password dina. Kin san komai nawa. Ban taba boye miki komai ba. Amma idan har za ki riqa neman abin da zai bata miki rai a cikin komai, ko ni kaina ba zan iya taimaka miki ba.....wannan ba komai ban....."

"Mace tana cewa ko daga nesa ta ganka ya wadatar mata. Kai kuma kana zaune kana bani labarin wai ba komai bane." Ta fada da daga muryar da ya jita har tsakiyar kansa. Ya runtse idanunsa a hankali yana qoqarin controlling kansa.

*_INGANTACCEN MAGANIN SANYI NE SADIDAN,WANDA BA'A CAKUDASHI DA KOMAI BA SAI ZALLAR SASSAQE DA ITATUWA MASU AMINCI_*

*_KAYAN GYARA MASU INGANCI DA WARWARE MATSALAR MATA TA FUSKAR CIWON SANYI WANDA YA KASA JIN MAGANI_*

*_GARZAYA A SIRRANCE KI WARWARE MATSALARKI,KI TUNTUBETA TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE_*

+234 810 914 9876

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 160* _________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_*

*_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_*

*_BONONZA DA PROMO akai akai_*

*dukka sai a HUGUMA CLOSET*

*Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka*

*shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami*

*_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_*

*_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝

https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________

"Wannan ba maganar da ya kamata ki rikide ta zuwa wani abu daban ba ce."

"To ka gaya min me ya kamata in dauka?" Ta matsa.

"Ko kuwa zan jira ta zo ta tsaya a gabanka ne kafin in fahimta?" Wani irin shiru ya ratsa falon. Ya dube ta na wasu dakiku.

"Ki mayar min da wayar."

"Ba zan mayar ba."ta fada kai tsaye,mamaki sosai ya kamashi,abinda bata taba gwadawa ba.

"Akhnan."

"A'a,ba wata Akhnan,yau sai ka gaya min gaskiya."

Ta ga yadda yanayin fuskarsa ya fara sauyawa, amma hakan bai sa ta ja baya ba.

"Ko ita ce dalilin da yasa ka shirya Durban din?"

"Ya isa."

"Ko kuma kana fatan ganinta ne? Tunda ita ma ai zata zo." Ya rufe idanunsa na dan lokaci kamar mai qoqarin danne wani abu. Amma Akhnan ta ci gaba.

"Ko me yasa ma ba zaka gayyace ta kai tsaye ba? Tunda dai....."

"AKHNAN!" Muryarsa ta daki falon da qarfi har ta yi shiru nan take.

Ya miƙe tsaye gaba daya.

"Na ce ya isa!" Numfashinsa ya dan yi nauyi, idanunsa a kanta,har tsakiyar zuciyarsa yana jin quncin yadda ta tilastashi yayi abinda bai taba tunanin zaiyi ba.

"Kin tambaya, na amsa. Amma ba zan zauna kina jujjuya maganata yadda kika ga dama ba......ba tsoronki nake ba....ko kadan,idan inason ganinta....ko inason gayyatarta kai tsaye....kai tsayen zan aikata hakan" Ji tayi kamar jiri zai kayar da ita,hawaye take suka cika mata idanu.

Ita haisam yake gayawa haka?. Kansa tsaye?,yana kallon cikin idanunta?. Kawai saita sauke masa wayar ta doshi qofa da sassarfa tana ficewa.

Komawa yayi ya zauna,yana jin wani abu mara dadi yana mamayarsa. Karon farko....karon farko kenan da wani abu mara dadi ya taba shiga tsakanin su.

"Me yasa baka jure ba....me yasa baka sake kai zuciyarka nesa ba?" Zuciyarsa da ta kasa ganin laifin Akhnan ke tuhumarsa. Tunda ya kwanta bacci ya kasa zuwar masa. Fuskarta kawai yake gani cikin idanunsa da suka cika da qwalla. Amma me yasa?,me yasa zata tursasashi yayi abinda baiyu niyya ba?,abinda ba halinsa ba?.

Da qyar ya taushi zuciyarsa.....ya hana kansa binta. Yanaso ta gane tayi kuskure.....yanaso ta fahimci duk girman son da yake mata idan tayi kuskure dole zai gyara mata.

Da asuba yabi duka yaran mazan ya hada kansu suka wuce sallar asuba,saidai kafin su wuce din ya biya dakinta,yana kulle bata bude ba,ta cire kuma security check na qofan bare ta bude masa automatically,amma still ya mata knocking ya kuma kira sunanta. Ya tabbatar taji,don ko bacci take muddin ya kirata da sunan nan nata zata farka ta kuma amsa.

Da gaske ta jishi.....don bayan ta dawo dakin tayi kuka sosai,zuciyarsa tayi sanyi sai ta soma hasaso abinda ta aikata. Itama batasan dalili ba....batasan meye yahau kanta ba.....saidai tana danganka hakan da zallar sonshi daya mata yawa....da kuma sauyin da takeji a jikinta da yake sake gaya mata anya ba ciki bane?. Kusan shigen yanayin irin na cikinsu ashraf ne,ta kasa gwadawa koda da pt stripes ne.

Wani kunyarsa data rugo ta lullubeta ita ta hanata amsa masa. Kuma ko yanzu bayan ta idar da sallar asuba,a gurguje ta fita ta bada umarnin duka abinda zaayi sannan tace musu kada subar yaro ko daya ya tasheta har su wuce gurin hawan,idan ta gama abinda takeyi zata fito da kanta.

Saqon da haisam yaji suna gayawa su ashraf kena da suka nufi dakin da zummar shida gaidata. Ba dashi suke ba....amma sai shima yayi amfani da wannan ya qyaleta bai sake komawa ba.

Shi ya kula da komai,da taimakawar hadiman.

Gidan ya cika da annuri. Tana daga daki amma tana jin hayaniyarsu. Ranta ya sake baci ganin haisam bai biyota ba,kamar ma ta manta ita ta buqaci kada wanda ya dameta.

Dole ta tashi tayi wanka,ta shirya cikin wasu kaya daban ba wanda sukayi zata saka ba. Don gaba daya abun ya fice mata a rai,jin laifi da haushi kawai takeyi tattare da ita.

Jin hayaniyarsu kamar kusa da dakinta yasa ta gaza ci gaba da jurewa. Da alama sun gama shiryawa. Shirin data ciwa buri,shirin data tsara ita zata shirya mijinta da kanta,sai kawai ta karya billenta,ta bude security na qofar ta fito.

Sai ta tsaya cak. A falon...sanda ta qarasa fitowa.

A parlour din nata.....haisam da yaransa takwas ne tsaye. Bayan yaran nasa da sauran yaran 'yan uwansa da nata 'yan uwan.

Dukkansu cikin fararen shaddoji sukayi,saidai nasa da na garansa yasha banban dana sauran.

Babbar riga iri daya,fara qal sai maiqo take da wani qwataccen qamshi. Dinkin anko da mahaifinsu. Kamar an zare su daga juna,kamar daga jikinsa aka dinga tsagosu,don hatta da takalmi da agogon hannunsu iri daya ne.

Ashraf......asif......afeef.....ahlam.....ahsan....da ajmal. sauran 'yan matan kuma su biyu wata farar Royal abaya ce a jikinsu da yasa aka saqa musu qwaya biyu kacal saboda wannan ranar.

Dukkansu suna kama da Haisam ta wata fuska. Duk da wani lokaci su yumna da ita ake cewa suna kama sak da sak.

Haisam yana tsaye a tsakiyarsu,yana gyara hular Ashraf,yaron dake da wani irin tsaho kamar yanason taddo mahaifinsa ne.

A jkinsa yaji fitowaeta,sai ya dago kai,idanunsu suka hadu,wani irin chemistry ya ratsa tsakaninsu me qarfin gaske. Shiru na wasu dakikoki,karon farko da suka kwana gida daya amma a mabanbantan dakuna. Ciwo ko lalura lafiya ko rashinta bata taba rabasu haka ba.

"Ammeee" Yumna ta fada,t ruga gurinta da gudu,abinda ya jawo hankalin sauran suka biyo baya.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Nan take yaran suka kewaye ta,wani ya rungume qafarta. Wani yana gyara mayafinta. Wani yana gaya mata ya fi kowa kyau yau,duk sai taji kewarsu ta cikata.

Haisam kuwa yana kallonta ne kawai. Da wannan murmushin nasa. Yana jin wani tausayinta yana ratsashi. A jiyan baiyi baccin kirki ba. Ya kwana ne kawai yana tuhumar kansa,inda daga qarshe ya kwana yana sallah kawai. Sanda ya tuna wani zargi daya darsu a ransa tun rannan,sai yaji kaman ya tashi cikin daren ya bita,amma bayason tayar da ita.

"Anya ba ciki bane?" Tambayar data sanyashi yayita nanatata daga qarshe ya aminta da hakan. Saboda ya sani....wannan akhnan din wata akhnan ce daban,ba a banza tayi masa haka ba,yayi imani da wannan ya sani sosai. Shine na farko da zai shaidi matarsa. Bashi kawai ba....koda takalminsa da yake sanyawa girmamashi take ballantana shi.

Ruqayya ce ta shigo ta tattara kansu suka fice,a mota zasu isa jimma palace kafin a nadawa kowa rawaninsa,a bashi dokinsa,dawakan sa already suna dasu kusan uku uku kowa ke dashi.

Bayan yara sun fita zuwa motocinsu...sai ya rage su biyu. Tare suka miqe zuwa ga juna,amma sai ya tsaya ganin ta nufoshi.

A hankali Haisam ya soma takowa shima,yayi saurin kamota sanda ta zame zata zube gwiwarta a qasa. Dagata yayi zuwa jikinsa yana qoqarin lalubo qwayar idanunta amma kunyarsa tasa ta kasa bashi dama. So take ya qyaleya ta tsugunna gabansa ta bashi haquri.

"Har yanzu kina fushi?" Akhnan ta gyara mayafinta a kunyace.

"Ban ce haka ba." Ta fada a shagwabe tana cikin jikinsa,wannan lallausan qamshin nasa yana shige mata hanci.

"Akhnan." Ta qi kallonsa. Sai ya dan sunkuyo kadan yana murmushi me sauti.

"Habibti."Har yanzu ta qi kallonsa. Kunya takeji......amma da alama baima gane ba.

Sai ya yi dariya qasa-qasa.

"She called."Shiru.

"I didn't."Har yanzu babu amsa.

Sai ya matso da ita yana manneta da jikinsa,qamshin shaddarsa.....da qamshin turarensa suna bada wani kalar qamshi me taushi.

"After all these years..."Muryarsa ta yi qasa.

"...you still don't know who owns my heart?" A wannan karon ta kasa hana kanta kallonsa,ta ware blue eyes dinta sosai a kansa.

Sai ya nuna yaran da suka riga suka fita.

"Eight children." Sannan ya nuna kanta.

"And still jealous." Murmushi ya subuce mata duk da qoqarinta na hana kanta tayi murmushin.

Nan take ya gane ya yi nasara,tasa hannu ta daki qirjinsa a tausashe.

"Kayi haquri please" Bakinta ya toshe da nasa kadan,yadan tsotsi lips dinta sannan ya janye.

"Karki wani nema afuwa.....menelik ce.....tun daren jiya na miki maganinta." Idanu ta waro waje.

"Yes.....ya zan zauna ta jawomin jagwal. Ashe ba haisam dinki tazo turawa ba.....itama ta samu nata haisam din. Tayi saving same name ni dashi,zai kuma zo Durban din,ta ban haquri,tace zata hadamu don na tabbatar,ta kumayi deleting number mijinki,shikenan?" Ya fada yana jan hancinta kadan.

Sosai ta sakejin kunya,tayi qasa da kanta tana boyewa,ya saki murmushi me laushi

"......the game is over.....chapter closed..... Khadeeja ta mallake Muhammad haisam....."

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽

💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 161* _________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0

*IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA*

*IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA*

*_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_*

*_Assalamu alaikum my loyal people_*

*_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_*

*_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_*

*_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_*

*_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_*

*_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_*

*_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_*

Readers Also Read

More by Huguma