Mar’adam’s book 2 by aysha a bagudo - Chapter 6
Mar’adam’s book 2 by aysha a bagudo Chapter 6: Mar’adam’s book 2 by aysha a bagudo Chapter 6. daren ranar da kuma wunin safiyar data waye duk a cikin…
3,313 words
daren ranar da kuma wunin safiyar data waye duk a cikin k'unci nana hauwa'u tayisa har izuwa yanzu cin abinci kawai ke fito da'ita shima bisa takurawar mumy ce ."dan kar mumy tazo ta tarar daita a d'aki tana kuka bayi take shiga taci kuka har ta godewa ubangiji, idanuwanta sunyi jajir kamar barkono, da dare ma da mumy tazo zata d'auketa domin kaita gidanta sai da mumy tayita rarrashinta dan ji take gara ta cigaba da zama dasu akan zamanta da yaya hisham mumy ta fito tana bata kwarin gwiwa sai da abba ya sake masu wasu nasihohi masu ratsa zuciya da kuma gangar jiki sannan yaya hisham ya d'aukesu suka wuce direban mumy na biye dasu abaya domin shi zai dawo daita ."
Har suka isa gidan nasiha mumy take masu shi dai yaya hishsm bashi da wani kuzari saboda har yanzu zuciyarsa ta kasa amsarta dan bai jin zai iya mata irin son da yake wa nuzla yayinda nana hauwa'u itama jin momy kawai take amman har a zuciyarta tasan yaya hisham bazai bari su zauna lafiya ba sai 9 na dare sannan direba ya dawo da momy ta barosu su kad'ai acikin makeken gidansu. d'akin take kallo a tsanake komai yayi mata kyau most especially parlour'n wanda aka qawata shi da kayan zamani masu kyau".
Karfe tara da minti shabiyar daidai wayarsa ta soma ringing ya d'auka ya duba, ita kuwa tunda wayar ta fara ringing ta tattara gabad'aya hankalinta kacokan akanshi , bata san dalili ba taji wata irin muguwar faduwar gaba ,ta dan saci kallon inda yake a zaune a tun sanda suka shigo ,bata dauke kwayar idanunta akanshi ba har sanda ya dauka yana cewa "wallahi nuzla rigimarki tayi yawa dare fa yayi okay shikenan ganin nan zuwa yana gama wayar ya fice batare da yace mata komai ba ."
wani irin wahalallen ajiyar zuciya ta sauke tana dafe qirjinta tare da fashewa da kuka ,ahankali ta durkusa kasa ta cusa kanta cikin qafafunta tana kuka tare da kankame jikinta ,sai da tayi kuka mai isarta sannan ta mike ta shiga bayi wanka tai ta fito ta bude wordrobe dinta shiru tayi tana kallo babu abinda babu hatta kayayyakinta na gida an kawo mata ta saka kayan bacci wondo dogo da riga mai long sleeve butter colour touch of brown ta saka hijab sannan tayi sallar shaf'i da witiri tayi addua akan Allah ya zaba mata abinda yafi zama alkhairi a tsakaninta da yaya hisham ."
sai data rufe kofarta da key ta kashe fitilun dak'in tayi shirin kwanciya bacci , koda ya dawo ya tarar har tai bacci yana murda kofar d'akin yajita gam nan da nan yaji ranshi ya 'baci meye abun kulle kofa tsaki yaja ya juya ya shige d'akinsa ."
Washe gari tana farkawa daga bacci tai sallah sannan ta fito ta wuce kitchen, had'adden breakfast ta had'a masu naji da gani bayan ta kammala sannan ta d'auka ta kai dining, d'akinta ta koma tai wanka ta shirya cikin doguwar rigar abaya bak'a mai ratsin ja tai rolling kanta da mayafin abaya sannan ta saka takalmi silifas ja , ta feshe ilahirin jikinta da turare tayi kyau sosai abunka ga farar mace ta d'auki phone d'inta ta fito zuwa falo ."
tana fitowa shi kuma yana fitowa daga d'akinsa sanye da jallabiyya brown , cikin sakin fuska ta masa barka da kwana ,wani kallo yayi mata mai hade da harara sannan yaki amsa tsabar bakinciki "meye jiya zaki wani rufe daki ?tayi shiru "me kike tunani akaina ?"still dai shiru tayi masa tare da sunkuyar da kanta kasa "ko gidan nan naki ko kuma da kudin wani naki aka gina shi ?shiru tayi tana nazarin maganarsa ,a wannan shirun datayi ta fahimci inda maganarsa ta dosa yana son ta'bo yayanta ne abinda bazata d'aukar masa ba kenan muddin baya son zaman tashin hankali daita ya tsaya iya kanta kar ya ta'bo mata wani nata ita dai zata jure komai akanta amman akansu bazata iya ba ."
Numfashi ta sauke tace "ga breakfast can akan dining idan ka tashi ci ".ta fada haka né dan kawo qarshen maganar sai dai bata kai ga k'arasa rufe bakinta ba yayi saurin cewa "to baa ci ina miki magana kina min maganar wani abinci d'an yunwa kika dauki ne ko me ?" yadda yayi maganar sai da ya gigitata "na fahimci haushin nuzla kike ji a zuciyarki "idan har fahimtata gsky ne wallahi kiyi maza ki cire a zuciyarki daman munafurci ne yasa kikace kin amince idan zan aureta na aureta well idan na tashi aurenta ba amincewarki nake nema ba ."
A natse ta durkushe a gabansa tana kuka "karka min mummunar fahimta bazan iya bacci ba matsawar na bar kofar a bude tunda kofar shigowa falo a bude take amman kayi hakuri bazan sake ba maganar nuzla kuma wallahi babu ruwana ko mata goma zaka aura byn ita kana dama "saboda ga dan iska ba ?"ka rufa min asiri ba abinda nake nufi ba kenan yaja tsaki ya juya a fusace shifa ba lalla'ba yake son tayi ba so yake ta biye masa daga nan komai yazo qarshe ."
nana hauwa'u ta mike da sauri ta rungumeshi ta baya tana rera masa kuka mai cike da jan hankali "yaya hisham dan Allah ka bari na samu natsuwa a gidan nan idan kuma har baza ka bani wannan kwanciyar hankalin ba kana iya sakina Kmr yadda nace ,sosai ta shige jikinsa tana goga masa dukiyar fulaninta sannan ta cigaba da magana "nasan baka sona amman ni ban ta'ba jin tsanarka ba zan iya mutuwa akanka yaya hisham dan allah me nayi maka da ka tsaneni haka ?"dan allah kayi hakuri ka daina tsana haka bana bukatar komai bana son kuma daga gareka ni dai mu zauna lafiya cikin sheshekar kuka ta qarasa mgnr."
Sosai ta rud'a yaya hisham jikinsa sai rawa yake ya juyo ahankali tana jikinsa ta sake narkewa a qirjinsa "kada ka canza yaya hisham kowa yabonka yake yi akan nayi saar samun mijin da babu kamarsa gurin kyakkwar halayya kana da kirki bazaka ta'ba barin nayi bakinciki ko kuka ba , samunka amatsayin miji ba qaramin nasara nayi ba amman why kake son canza halinka?runtse idanunshi yayi tabbas haka né shi kanshi yasan ya canza amman duk ita ce silar komai da bata amince da aurensa ba dole iyayensu su hakura ."
kuka take sosai har da shesheka tausayinta ya kamashi ya soma jin kamar ya bata hakuri ta daina kuka amman ya kasa magana, dago kanta tayi taga ita yake kallo ta matso da fuskarta kusa da nashi ido cikin ido suke kallon juna suna shakar numfashin juna, gbdy wani iri suka dinga ji ajikinsu ya bude baki zai fara magana ta matso da lip's dinta kan nashi tana kallonsa tana motsa lip's dinta akan nashi "am sorry yaya hisham I don't mean to hurt you bansan rufe kofar zai 'bata maka rai ba da ban rufe ba "ta fad'a tana kamo lip's dinsa ta shiga tsosa cikin salo kamar ta samu sweet ,cikin son qara rusa shi ta kamo harshensa tana mai wani irin sha tana goga masa qirjinta ."
wani nishi yaya hisham ya saki cikin fitar hankali da mamaki ya zare bakinsa yana já baya tare da cewa "meye haka ?ya fad'a Kmr bai ji dadin abinda tayi ba sunkuyar da kanta kasa tayi tana mai jin wata irin kunya "kayi hakuri" lumshe idanunshi yayi yana jin wani sanyi na bin jikinsa "muje kaci abinci dan allah ba dan ni ba" bai ce uffan ba suka wuce dining a tare itace tai saving nasa sannan ta zauna ta d'auki spoon ta kai bakinsa "bude bakinka na baka da kaina mamakin abubuwanta yake wani lokacin ta nuna masa Kmr tana son shi wani lokacin kuma sa'banin hk most especially idan tace ya auri nuzla ita kuma ya saketa ko ya qara wasu matan ma a bayan nuzla yasan ba so bane kawai biyayya takewa mahaifiyarsa "
Tana bashi abinci shi kuma sai kallonta yake wani irin bak'inciki yake jin yana taso masa da takaicin bai wani ci sosai ba ya tashi ya wuce, tabi bayansa da kallo har sai da ya bace mata sannan ta daina kallonsa tana jin fad'a uwar gaba ta d'auki wayarta ta soma chart din maryam ."tana zaune ya fito cikin shirin fita aiki tayi masa adawo lafiya ya amsa ta hanyar taga mata hannu ,yana fita ta sauke numfashi ta kira maryam domin taji muryarta dan chart dinta ya nuna mata tana cikin damuwa ".
"kiyi hakuri dai sister har sanda ubangiji zai kawo mana mafuta ta alheri ,In sha Allah zaku daidaita da yayana, ni dai fatana kullun kenan ubangiji ya daidai taku damu gabadaya ."wallahi babu wani gara ni sister nima hakuri nike yaya hisham ya canza sosai fiyye da tunaninki ,duk babu wannan fara'ar da wasan daya saba mana Ke wallahi tsoro ma yake bani ga damuwa ta qaru daman ba wani samun kanshi nike ba bare yanzu ga farincikinsa ta dawo jiya fa na tare a gidan nan amman ina ji kuma ina gani nuzla ta kirasa kuma ya tashi yaje ,tô ya zanyi sister bai dameni ba dan na auresa ne tsakanina da allah kuma nuzla yaruwata ce da nake so da qauna "ahankali suka cigaba da tautauna akan abinda ya shafi matsalarsu ."
a round 6pm bayan sun tashi daga aiki ya kamo hanyar gida saboda yau agajiye yake sosai yana buk'atar hutu ba zai iya zuwa gidan mumy ba ko wajen nuzla."yana isowa yayi horn gateman ya bud'e masa ya shigo yayi parking sannan ya fito tana zaune parlour'n sanye da wasu kaya ba wanda ya barta dasu ba ,tana ganinsa ta mike da sauri ta rungume shi ajikinta sannu da zuwa "yauwa !" ya fad'a atakaice yana qoqarin zareta ajikinsa dan bazai iya misalta yanayin da yaji ajikinsa ba ."
zata amshi jakar hannusa ya hana ya shige d'akinsa d'akin tabi shi alokacin ya ajiye jakar hannunsa ta shigo ta tsaya gabansa zata kai hannuta jikinsa ya rike yana cewa "out pls "Kai tsaye fita tayi ranta a b'ace tamkar wacca akayiwa mutuwa, tana shiga dakinta kiran maryam ne ya shigo wayarta ahankali ta dauka kuka ta fashe mata dashi tana furta "sister zuciyarta ta fara min zafi ". duk hankalin mrym ya tashi tana tmbyrta "sister mun jefa rayuwarmu cikin qangin rayuwa kuka take sosai maryam na rarrashinta ."
*******
Mami ta kira ya'yanta mata kan tana neman su a washegarin ranar suka kamo hanya suka zo nan mami tayi masu bayanin abinda yasa ta kirasu batare da bata lokaci ba suka amince aunty khadija tace "ai idan bai yarda ba mami ki bud'e masa wuta ,uhm uhm !! aunty khadija kin fa san halinsa mu dai bi ahankali idan aka bishi ahankali zai iya amince wa "inji cewar zabiba "wannan zaa bi ahankali ai shikenan a kirasa " babu 'bata lokaci aunty shahida ta kirasa kasancewar weekend ce yana gida ya shigo cike da izza fuskar nan tashi a had'e tamkar ta zaki yana shan kamshi".
" adamu !"aunty shahida ta kira sunansa tare da mikewa daga zaunen da take ta jawo hannusa ta zaunar dashi bisa kujera itama ta zauna akan kujerar data tashi , cikin wani irin yanayi mai cike da tashin hankali da tsoron abinda suke shirin fad'a masa ya kalli mahaifiyarsu kana ya juyo ya kalli aunty shahida ,yayinda gefen hangunsa aunty khadija ce wacce fuskarta tafi ta sauran hadewa sai zabiba ya zuba masu ido yana kallonsu da sauraronsu cikn yin kasa da murya aunty shahida ta soma magana "yaushe zaka tare a sabon gidanka musan ranar da maryam zata tare ?".
Gabansa ne ya shiga fad'uwa cikin tashin hankali yace "me yasa kuke da damuwa ne ?ya fad'a tare da jan sayayyen numfashi ya gyara zamansa yayinda ganadayansu har mami kacokan suka maida hankalinsu kanshi duk hankalinsu a tashe yake kar ya shigo masu da wata matsala ."wani numfashi ya sake saukewa kana ya cigaba da motsa lip's dinsa "da gidana da nan duk daya ne a wajena dan haka ta cigaba da zamanta anan kawai "cikin yanayi na tashin hankali suke kallon mami "mami kina jinsa kinyi shiru wannan wacce irin rayuwa ce shi babu wanda ya isa dashi sai abinda yaga dama zai yi "me maryam tayi maka daka zabi ka dinga wulakantata haka ?"inji cewar aunty Khadija ."
"ba maryam ya wulakanta ba ni ya wulakanta Ku rabu dashi kawai yayi abinda yake so rayuwa ce gani na da yake yi ne a duniya idan na mutu zanga wanda zai cigaba da wulakantawa "wani irin numfashi mai zafi ya fesar kana ya maida hankalinsa ga mami "ni ina jin ajikina mutuwa zanyi nan kusa , kawai bakincikina a yanzu bai wuce zan tafi na barku da matsala ba domin adamcy matsala ne arayuwarku "saurin runtse idanunshi yayi aunty khadija tace "ai shikenan idan ka kasheta gbdynmu zamuyi asa.."kafin ta qarasa ya jefa mata wani mugun kallo zuciyarsa na dukan tara tara idan akwai abinda ya tsani ji bai wuce mutuwar mahaifiyarsa ba "
"Kayi hakuri adam kayi abinda zai faranta ram mami kai kasan mami na matukar sonka dan allah ko sau daya ne ka faranta mata karka zo byn ka rasata kazo kana danasani, kazo kana son faranta mata babu hali kasani a yanzu ya kamata ka canza rayuwarka idan kaki farantawa mahaifiyarka rai ka sani alamuranka bazasu daidaitu ba zama su tabarbare ne zuciyarka zata qara bushewa ne matukar kaki amsar gsky ." "Sai abu na gaba ka sani acikin biyayyar da zaka wa mahaifiyarka zai shigar da kai aljanna domin bazaka shiga aljjana ba sai mahaifiyarka ta d'aga maka kafa kuma zaka samu wannan damar ne idan ka faranta mata anan gidan duniya ."
yadda maganarta ke shiga kunnensa haka sautin kuka mami ke shiga, hankalinsa yay matukar tashi "ina ganin lokaci yayi da zan farantawa mahaifiyata domin samun rabauta "yana fad'ar haka basu jira jin abinda zai sake fad'a ba suka rungume shi suna jin wani farinciki na mamaye zukatansu yayinda duhun daya tsarke a zuciyar mami gabadaya ya yaye "da gaske ka amince zakayi rayuwa da mrym ?bai bude bakinsa ya amsa da "eh ko Aa ba amman aranshi ya amince ta tare a gidansa ".hakika ka faranta mana rai allah ya yaye maka dukkanin wata damuwa dake damunka yasa alkhairi arayuwarku "karku wani wahalar da kanku wajen min addua na amince ta tare ne kawai saboda sweetheart amman fa kusani idan dan farinciki akeyin aure ni bana cikin farinciki kuma babu wacce zan bawa farinciki yana gama fadar haka ya mike juya ya bar dakin ."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗 MAR'ADAMS 💖💖💖💖 💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH AREWABOOKS USERNAME AYSHAABAGUDO bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 4
Kofar suka bi da ido cike da tsananin tashin hankali yayinda mami take kuka me karfi wanda ke fitowa daga cikin zuciyarta "me nayi wa adamcy da na cancaci wannan sakayyar bayan nayi masa komai a duniya .?"waigowa sukayi gabad'aya hankalinsu na qara tashi jin maganar mahaifiyarsu hankalinsu a tashe sosai duk sukai kanta cikin tsananin damuwa da tashin hankali "kiyi hakuri mami karki d'aga hankalinki tunda ya amince komai zai zo da sauki munyi miki alqawari muddin muna raye bazamu ta’ba bari wani mummunar abu ya faru da maryam ba ."
Hawaye yake zubowa daga idanun mami ta runtse idanunta gam tana jin wani iri a zuciyarta, zuwa wannan lokacin nadamar wannan auren ya shigeta" ina ma zata iya data bari adamcy ya sawakewa maryam kowa ya huta domin bata son mrym tayi rayuwar kunci a gidan aurenta ,kuma tasan babu tantama shi zatayi tunda gashi ya furta baya farinciki da auren dan haka babu wanda zai bawa farinciki tana tunani hawaye masu zafi na zubo mata ."
Kallon mami suke wacce ita kad’ai ta rage masu a duniyar yanzu idan akwai abinda suka tsana bai wuce ganin bacin ranta da ganin damuwarta ba hakuri da kwantar mata da hankali suka cigaba da yi inda mami tayi zurfi cikin tunanin yadda zatayi ta raba wannan auren ta huta sai dai gbdy ta rasa yadda zatayi "me zatace wa mutane?" duka aure bai wuce kwanaki goma zuwa shabiyar ba ace ta raba ai sai duniya ta zageta sam bama raba auren ne mafuta agareta ba .”
Tana cikin wannan tunanin suka dafata suna kiran sunanta a matukar rud'e suna hawaye da sanyin jiki ta dawo hankalinta tare da kallonsu d’aya bayan d’aya itama mami hawaye ne ke zuba a nata idanun, ta kamosu jikinta ta damke hannuwansu duka cikin nata tace "duk naji hakurinku kuma na..na hakura na gode Kwarai da gaske allah yayi maku albarka allah ya raya maku ya'yanku ,yadda kuka min kuma allah yayi maku haka ina alfahari daku nasan ko bayan raina zaku duba bayana allah ya tayaku kula da rayuwar dan'uwanku kuyi masa addua in sha allahu ba zai cigaba da wannan rayuwar ba zai canza ."
Cikin rauni ta cigaba da mgn "bana son kuyi fushi dashi ina son ku cigaba da yi masa nasiha da adddu’a dan allah karkuyi fushi dashi kunji ya'yana allah yayi maku albarka yayiwa rayuwarku data ya'yanku albarka shima allah yayi masa albarka da rayuwarsa na yafe masa duka laifukan da yayi min wanda na sani da wanda ban sani ba daga haka tayi shiru tana goge hawayen idanunsu amman tamkar sake qara masu take sam sun kasa cewa komai su dake rarrashinta sai gashi ta dawo tana rarrashinsu tare da jaddada masu adamcy bashi da laifi duk laifinta ne data hada auren kuma tayi nadama sannan ta bukaci suyi wa mrym nasiha akan yadda zata janyo hankalisa “nan suka cigaba da tautaunawa kowacce daga cikinsu na qoqarin sake kwantarwa da mami hankali ."
"Karku damu komai ya wuce idan allah ya kai mu jibi da yamma sai kuzo ku kai maryam gidanta "amman mami dan allah ki daina sakewa adam dayawa tunda Kinsan halinsa zuma ne sai anci sa da wuta dan wallahi mu bazamu ta'ba daga masa kafa ba muddin muka ga abinda bai mana ba na tozarci ko cin fuska akan mrym allah bazamu barshi ba dan bazamu yarda ya wulakanta maryam ba “. inji cewar Aunty khadija mami tayi murmushi irin nasu na manya kana ta soma magana a natse "Allah dai ya shirya mana shi ,mu dai cigaba da yi masa addua da kuma fatan alkhairi arayuwar aurensu ,babu yadda allah baya juya alamarinsa sai kuga komai ya daidaita a tsakaninsu “wannan haka ne allah yasa mu dace "kuyi qoqarin sheidawa maryam domin tayi nata shirin ."
A bangaren maryam kuwa wani farinciki ta tsinci kanta ciki lokacin da aka sheida mata ata ya amince dan bata yi zaton zai yarda da tarewarta ba , a zatonta lamarin zai zo da gardama ,bayan ta koma d’aki alqibila ta fuskanta tare da yin sujudul shukur cike da yalwataccen farinciki da yasa hawayen farinciki zubo mata ,alhamdulillah wannan maganar itace mafi dadin acikin dukkanin abinda ya shafi rayuwata hakika mami kin gama min komai arayuwata cike da farinciki ta kira nana hauwa'u ."
Tana d’auka taji ta sauke ajiyar zuciya sannan ahankali ta kira sunanta a can qasan makoshi wanda ya d’an d’aga hankalin maryam tace"sister lafiya ?a kasalance tace "lafiya sister bacci na tashi ya kike ?ta lumshe idanunta cike da jin dadi take fad'a mata batun tariya ranar asabar nana hauwa'u tayi murmushi jin dadi tace "to sister sai fa kin qara da hakuri akan wanda kike dashi coz gidan aure sai da hakuri it’s not easy auren mijin da bai sonka domin duk abinda zakayi bazaka ta’ba burgeshi ba ."