Kenza eBookz

Mar'adams book 4 - Chapter 24

Mar'adams book 4 - Chapter 24

Mar'adams book 4 Chapter 24: Mar'adams book 4 Chapter 24. " a kallon da take masa ta fahimci ransa ya gama 'baci da maganar da tai masa shiyasa ma yake…

3,177 words

" a kallon da take masa ta fahimci ransa ya gama 'baci da maganar da tai masa shiyasa ma yake hukuntata da kwayar idanunshi "ya rabbi me yasa nayi magana ?" ta yiwa kanta tambayar tana sake jin fad'uwar gaba mara iyaka.a hankali ta sunkuyar da kanta kasa dan bazata iya jurar wannan kallon daga garesa ba, hannuwanta ta tsarke cikin juna tana wasa da yatsun hannunta ko zata samu sausauci yayinda idanunta suka cika da ruwan hawaye,ya numfasa ahankali sannan ya sake matsawa gabanta ya kai hannu nsa ya d'ago ha'barta ya sanya kwayar idanunshi cikin nata ,wannan karo atare zuciyarsu ta buga da karfi sakamakon idanunsu daya tsarke cikin juna ,wasu abubuwa ta dinga gani suna fita daga cikin idanunshi suna shiga nata idanun da suke cike da rauni .ta kasa rike hawayen dake cikinsu dan haka ta barsu suka shiga gangarowa suna tsiyaya acikin tafin hannunsa yabi hawayen da kallo yana mamakin raunita ga tsiwa ga shegen tsoro kamar farar kura ".wani irin kasala ya dinga Jin suna saukar masa bai yi magana ba sannan bai ce ta daina zubar da hawayen ba illa cire hannunsa yayi ya dangwali hawayen yana kallo kamar bai san menene ba."

Ahankali ta runtse idanunta gam tana sake jin fad'uwar gaba mara misaltuwa bata ankara ba taji saukar lip's dinsa akan nata tayi saurin bud'e idanunta had'e da zaro ido waje wanda hakan ya sake bawa hawayen idanunta damar zubowa sosai ,k'okarin kamo lip's dinta na kasa yake yaji sautin muryarta cikin karfin hali "please yalla'bai dan allah ka barni ko wanke baki ban ..." bai bari ta karasa maganarta ba ya had'e bakinsu guri d'aya atare suka sauke naunayen ajiyar zuciya still kwayar idanunsu na cikin juna,yayi mata kyakkwan riko .sotsan bakinta yake cikin wani irin salo da shauki har wani duhu duhu yake gani a idanunsa." sakwanni nata wucewa har aka fara shiga mintuna amman adamcy yaki sakar mata baki yana faman sarrafa harshenta da hokoranta da lip's dinta ganin idan batayi da gaske ba zai iya far mata uwa uba ma bazata iya jurar wannan sakonnin nasa ba dan sakonni ne masu wuyar mantawa né da tsayawa mutun arai sannan masu zama acikin kwakwaluwa da zuciya né ,sai dai duk da haka bazata yarda wani abu ya sake shiga tsakaninsu ba yaci iya rabonsa ."

A hankali ta kai tafi hannunta zuwa qirjinsa tana k'ok'arin turesa amman ina kamar dutse ta ta'ba dan ko girgiza bai yi ba bagarensa kuwa ji yayi kmr ma kara tunzirasa tayi da sake kuno masa wutar sha'awarta ya kasa sakar mata baki dan yana cikin abinda yafi qauna atare daita hannun sa ya kai bayan keyarta ya tallabo kanta da kyau yana cigaba da sarrfa bakinta kmaar ba kwana yayi yana tsotsar su ba kallonshi kawai take da matsanancin tsoro gbdy baya cikin haiyacinsa dan bai ma san tana turesa ba shima kallon cikin kwayar idanunta yake yana sake jin wata zazzafar soyayyarta mai karfi,ahankali ya lumshe mata tsumammun idanunshi yana sauke numfashi rasa yadda zatayi dashi tayi yasa ta sakar masa kukan shagwaba ."dumin hawayenta yaji a fuskarsa yasa ahankali ya bude Idanunshi da suka canza kala ganin har lokacin tana hawaye har da shesheka ya fara controlling kanshi ."

ya sakar mata baki ya zauna kusa daita yana matsota tare da sauke numfashi,ta d'an matsa kad'an daga jikinsa dake gugan nata dan gbdy yanayinsa ya canza har hakan ya nuna acikin kwayar idanunshi ya sake matsota ya janyota jikinsa qara ta saki mai sauti "ouch! tana kallon kasanta " muryarsa sanyaye yace "sorry kibi ahankali karki fama ciwonki ".tai masa banza tamkar ba daita yake magana ba ta cigaba da rera masa kuka, matsota ya sake yi muryarsa a can kasan makoshi saboda halin da yake ciki" "princess bari muga gurin "?ta d'ago ta kallesa kawai ta Ina zata iya bud'e masa duk ya wani takureta "sorry ki daina kuka kinsan bana son ganin hawayenki ? shiru tayi tana kallonsa kamar yadda shima yayi shiru yana tsareta da idanunshi ta runtse idanunta wasu hawayen na zuba tana jin kamar ta gudu ta barshi dan gasky ita bazata iya da wannan jarabbaben nacin nasa ba mutun kamar wani maye jiya kwana yayi yana romance dinta yanzu kuma gashi yana neman takura mata ita dai gasky bata son wannan naci nasa ya fara damunta,"

"yanzu dan na d'an tsotsi bakinki ne kike kuka haka?ta d'an bud'e idanunta tana kallonsa ta kasan idanunta acikin zuciyarta tace "d'an tsotsa ma kayi kenan ? da zan barka Kenan sai kayi fiyye da haka kenan ?kai tsaye yace mata"Eh!mana zan sake cinki ! ya bata amsa da hakan a she a fili tayi maganar "sosai ta d'ago tana duban sa tare da mamakin jin furucinsa yanayinsa sam zakace zai iya sakin layi haka ba ya cigaba da magana muryarsa a kasalance "ok am really sorry nayi kokarin kar nayi hakan ban san abinda yasa ba "yayi maganar yana shafa gefen fuskarta,ta buge masa hannu tana cewa"stop !"lallai kina da aiki ".ya fad'a acikin ranshi "bai fita ba kamar yadda ta bukata sai daya mata ruwan zafi sau biyu sannan ya barta tayi wanka yana fita ta sauke wani wahalallen numfashi tana girgiza kai ."tayi wanka ta fito tana dafe bango yana ganinta ya taso ya kamota da taimakonsa ta shirya kanta ta soma kokarin yin sallah ."kayan jikinsa ya cire ya janyo towel ya d'aura ya samu waje ya zauna yana kallonta tana ruku'u da sujjada da kyar a daddafe tayi sallah ta mike tsaye da kyar take d'aga kafafun ta."

Tafiyar da take yi yake wa murmushi har ta samu daidaituwar zaman akan katifa ta juyo tana hararshi cike da shagwaba tac"kai ko!"ta fada cikin dubanshi tana cije lip's dinta hankali ya Karaso inda take, ya dafa kujerar da take zaune ya sakala hannunshi ta baya ya kai bakinshi kan karan hancinta ya sumbata ta hararesa tana cewa "wai wankan ne baka son shiga ko kuwa ka wani zauna da towel d'aure sai jajibo abin mgn kake, tunda 'anki atanka ai sai ka yi hakuri ka yi abinda ke gabanka."ya zagayo ya zauna kusa da ita ya dan jawota jikinshi yana kallon kyakkyawar fuskarta tare da yin shiru yana nazarinta ajiyar zuciyar ta sauke sannan tayi kasa da idanuwanta domin bata jurar dogon kalloshi.wani irin kwar jininshi yake mata kai tsaye kallonsa ke kasa ta sarrafa kanta ,koda ta dage akan lallai sai ta fuskanceshi da kallo mai cike da nuna tsantar so sai wannan kwarjinin nashi ya hanata.ahankali ta janye jikinta dan tasan halinsa yanzu ne tunanin sa zai canza "

ganin haka ya tashi ya shige bathroom ,bai wani jima ba ya fito ya shirya kanshi cikin kananan kaya ya fito daita zuwa parlour'nsa dan tuni an kawo masu breakfast ahankali ya zaunar daita akan dining table yana mata sannu shima ya zauna a gefenta ya soma had'a mata tea tana zaune tana kallonsa idan yana yin wasu abubuwa zaka rantse bashi bane wannan miskilin mutumin mai firgita mutane. mutumin da kusan kowa tsoronsa yake ita kanta da'ace ba ita ya aura ba bazata ta'ba yarda zai zame wa matarsa kamar haka ba saboda tsananin tsare gira da yake dashi ." "Bayan sun gama breakfast ya kamota ahankali suka dawo kan kujera yace "bari na kira miki umma ku gaisa ko hankalinta ya kwanta dan naga missed call dinta, Ina ganin fa jikin umma ya bata diyarta ta zama cikakkiyar mace dan tun jiya take kirana naki d'aga kiran dan ban san mai zance ba "da idanu ta bisa tana kallon bakinsa dake zagaye da saje abun sha'awa da burgewa."tana matukar son sajen nan nasa a duk lokacin data d'aura idanunta akai sai taji wani natsuwa aranta ".

"ko nasa akawo miki ita ne yau tazo taga lazy maryamarta ?" harara ta maka masa "saboda ka tona min asiri a wajenta kamar yadda ka tona min anan ba ?"ta k'arasa maganar cike da shagwa ba,ya kamo yatsun hannunta cikin nashi yana massaging ahankali "meye aciki idan kowa ya sani bayan raya sunnah kikayi ?"ya fad'a yana d'an sakar mata murmushi "nafa ji dadi sosai da ni ne na samu damar kar'ba budurcinki"runtse idanunta tayi alamun bata son jin maganar "ana magana kina wani nonokewa kina sabawa na shiga uku ,wata rana ma har kuka zaki dinga min idan banyi miki ba "inna lillahi!" ta furta tana bud'e idanunta ta zuba masa tana kallonsa kamar zatayi kuka .yana murmushi yace" ashe fa bakya son ana maganar sex ?".aiko nan take ta sake had'e fuska sannan taki cewa komai dan ta fahimci idan ta biye masa sarai zai maida irinsa duk su taru su lalace dan ba kunya garesa ba."

" my princess na gode kwarai da kika killace min kanki zuciyata tana matukar alfahari da samunki a cikakkiyar budurwa zan cigaba da godewa allah daya bani ke a matsayin matata hakika kin zamo wani jigo acikin bargon jikina ina sonki maryama soyayyar da ban san iyakarta ba aYanzu na k'ara yarda soyayyarki a jinina take inshaallahu mutuwa ce zata raba mu kalamansa sun faranta ranta sai dai tasan zamnasu ba mai d'aure bane duk yadda yake son su rayu tare tasan yan'uwansa sai sun rabasu zamewa yayi ya kwanta akan kujera ya kwantar daita ajikjnsa ya kai hannusa saman ruwan cikinta yana shafawa yana kiran layin umma kira biyu yayi mata ta d'aga da sallamarta alokcin da maryama ta zare hannunsa acikinta ta kwanto jikinsa tana kallon fuskarsa .bayan adamcy sun gaisa da umma tace"adamu ya kuke da fatan dai kuna lafiya ?"yace lafiya lau ga maryama tana son magana dake yana jin sanda ta sauke numfashi sannan tace "to bata wayar !"sa wayar a hands free yayi wanda yake nufi a nan zatayi wayar wanda ita sam bata so haka ba ."

cike da sanyi murya tace"umma Ina kwana ?"lafiya lau maryama fatan dai kina lafiya?"lafiyata lau umma ya aunty da habib?""duk suna lafiya duk sun damu da rashin samun layinki kiyi kokarin ki dinga rike waya ahannunki dan rashin jin murayarki akai akai zai saka mu cikin tsananin damuwa "in sha allahu umma babu wani damuwa ko ?"maryama tace" babu damuwar komai !"fatan dai kina zuwa gaishe da mahaifiyarsa kamar yadda nace "Ina zuwa umma! ." to!shikenan Allah yayi miki albarka kiyi hakuri a gidan aurenki ,Ina miki adduar Allah ya sakawa mijinki tausayinki acikin zuciyarsa,Allah ya shiga cikin al'amarinku Allah ya tausaya miki acikin rayuwar aurenki Allah ya rabaku da sharrin duk wasu sheidanu namiji ko mace ".maryama tace "ameen! kwayar idanunta na cikin nashi ya natsu yana sauraron hirarsu yana kallonta "

"ki sakè jajurcewa da addua sannan kiyiwa mijinki biyayya ,adamcy ya d'age mata girarsa d'aya yana shafa lip's dinta da finger's dinsa "banda mutsu akan komai duk abinda ya umarceki muddin bai sa'bawa addinin ba lallai ki tabbatar da kiyi masa sannan ki tayasa yiwa mahaifiyarsa biyayya,Allah ya sake had'a hankularku ,ya baku zaman lafiya da zuria masu albarka "muryarta a sanyaye tace "to umma !in sha allahu "fatan alkhairi sukai sallama."tayi shiru ta kasa cewa komai "yayinda adamcy ya gyara mata kwanciya ajikjnsa ya Kai bakinsa cikin kunneta ya soma mata magana cikin rad'a "kin dai ji abinda umma ta fad'a ?"duk abinda nace shi zaki yi amman nasan wannan kunne tauri ne dashi" yayi maganar yana ciza gefen kunneta k'ara ta saki mara sauti tana kokarin mikewa sai dai d'an zafin da taji ya ratsata yasa ta koma tana masa kukan shagwaba "ka gani ko zaka sa na fama ciwona "sorry !ya fad'a yana shafa bombom dinta sannan ya cigaba da magana ."

"Ina matukar son umma saboda tana da matukar kirki gashi tana son abinda nake matukar so ," ta d'an kallesa tace "me kake matukar so ?"ya harareta yace"ban sani ba tunda baki san abinda nake so ba "dariya ya bata tare da mamaki irin hararar daya zabga mata "bari naje naga sweet heart na dawo "tayi shiru tana tunani kafin ahankali tace "itama tasan abinda ya faru ne ?"haka nan ya tsinci kanshi da boye mata yace " aa menene idan tasani ?"wani irin ajiyar zuciya ta sauke tace "babu komai bana dai son ace tasani ne kunyarta nake ji "ah lallai kuwa zan fad'a mata dan Ina son tasan adamcynta ya tsinci dame a kala "ya mike daita ajikinsa ki kwanta anan ba zan dade ba zan dawo ya kwantar daita yana kissing din foreign head dinta "Ina sonki sosai !ta lumshe masa idanunta tana riko yatsun hannunsa cikin nata "dan Allah ka rufa min asiri karka fad'a mata dan wallahi bazan iya had'a ido daita ba ".

"Amman mai yasa bazaki bari tasan cewar budurwa ce ke ba bazawara ba ?ni dai dan Allah karka fad'a mata "okay naji !"ya shafa gefen fuskarta ya mike "ka gaisheta !"zataji! ya fad'a yana taku a natse kamar bai son taka kasa bayansa tabi da kallo da sallamarsa ya shiga d'akin mami tana zaune tana breakfast ta d'ago ta kallesa a natse tana amsa sallamar da yayi fuskarta babu yabo babu fallasa ya k'araso gareta ya zauna a kujerar dake gefenta yana kallonta "sweetheart kin tashi lafiya ?"alhamdulilahi fatan kai ma ?"yace lafiya!"ya fad'a fuskarsa da alamun fara'a "ya wannan yarinyar da jiki ?"taji sauki tace na gaisheki"ya fad'a yana shafa sumar kanshi".ba tace masa uffan ba,haka shima shiru yayi ya rasa me zai ce mata wanda zai sakè kwantar mata da hankali akanshi , kawai yaji zuciyarsa tace masa ya tambayi khaira zata ji dadin haka "sweetheart ya khaira take ?".

"wannan kuma bani zaka tambaya ba idan kana son kasan lafiyarta ka nemi uwarta ko kuma wad'an suke tare dasu "sarai ya fahimci abinda take nufi shi da yayi tunanin zataji dadi sai yaga sa'banin haka .yace "in sha allahu zan kira uncle naji lafiyarta" tai shiru tana cigaba da tura irish potato a bakinta a ranta kuwa haushi taji da ba maryam zai kira ba ."ta kasa hakuri tace "me yasa bazaka kira ita maryam ba ?" shiru yayi kawai batare da yace mata komai ba "kasani yanzu ba kamar da bane ,a yadda ka nuna baka yinta a yanzu bazan iya misalta maka irin tsanar da maryam tai maka ba ,gara ma ka ajiye komai kayi abinda ya dace dan itama yanzu bata sonka baka gabanta "still dai shiru yayi yana kallonta kawai dan shi babu ruwansa da wata kiyayyarta da ta cigaba da son shi ,ko kinsa duk d'aya ne a wajensa shi yanzu farincikinsa da jin dadinsa yadda tai nesa dasu kuma baya kaunar abinda zai sake dawo daita cikin rayuwarsu."

"khaira ce atsakaninsu kuma da zarar ta kai shekara biyu zai kar'beta a hannunta" ya d'an jima zaune yana janta da hira domin dai yana son ya dawo daita asalin sweetheart dinsa mai saukin kai da son duk wanda ya ra'beta. ahankali ya mike yayi mata sallama d'akin hajiya zulfa'u ya shiga tana zaune tare da hisham ,ya k'arasa shiga cikin d'akin sosai , hisham ya sakar masa murmushi yana cewa "ango kasha kamshi "bai san sanda murmushi ya bayyana akan fuskarsa ba, ya mika masa hannu suka gaisa sannan ya samu waje ya zauna yana gaishe da hajiya zulfa'u fuskarta cike da farinciki ganinsa tace "ya kake adam ya maryama take "?" "tana lafiya! ."ya fad'a atakaice."sun d'an ta'ba hira sannan suka fito tare hisham na tsokanarsa "ATA Kaga yadda lokaci d'aya ka wani canza fuskarka sai wani kyallin angonci take "kaga banson shirme anan ko ka manta cewar ni surukinka ne? hisham yayi dariya yace "nabi suruki da gudu !amman kyallin haka da alamun ango ya shige daga ciki." "kololuwa ne ba ciki ba !"adamcy ya fad'a haka yana jan tsaki hajiya zulfa'u dake tahowa ta bayansu tai murmushi kawai tana girgiza kai sannan ta d'auki hanayr parlour'n mami".

"kaga muje naga fuskar amaryarmu naji wani irin kalar abinci ta dirka maka haka mai canza mutun cikin kankanin lokacin ?"ahankali suka haura samansa adamcy na cewa "hisham banason iskanci fa ka iya bakinka ?"Iskanci kuma na nawa ai Ina ganin a wuce gurin, killa ma idan da rabo ka harba mata ".a kofar shiga parlour'n adamcy ya tsaida shi "kaga tsaya nan bari na fara shiga" bayan kamar minti biyar yace" ya shigo"! zaune ya iske maryama sanye da hijab kanta a sunkuye cikin tsananin jin kunya,hisham ya kalleta yana murmushi sannan ya samu guri ya zauna yana kallon adamcy alokcin maryama tace"sannu da zuwa Ina kwana ?"yace "lafiya lau amaryamu ya bakunta da fatan kina lafiya ?kanta a sunkuye tace "Alhamdulillah !"sosai ya yaba da zabin adamcy yayi masu addua tare da fatan alkhairi a rayuwar aurensu sannan ya mike tsaye ya nufi kofar fita ."

adamcy ya shiga d'akin ya d'auko mata waayrta ya mika mata" ni zan fita amman ba dade zanyi ba idan kina bukatar wani abu ki danna wancan bell din ya nuna mata wani farin abu ajikin bnago "direct kitchen ne! yayi kissing dinta lip's dinta ji tayi kamar tace ya zauna kar ya fita ya barta ita kad'ai kallonta yayi tare da cewa "menene?"kamar tace masa ya zauna sai dai ta girgiza masa kai alamun babu komai "sai ka dawo Allah ya tsare !"ameen ya fad'a yana kai wa bakinta light kiss lumshe idanunta tayi tana tsananin son shi ya sake samun kyakkwan mazauni acikin zuciyarta bata san lokacin daya bar parlour'n ba sai bud'e idanunta tayi taga baya nan ." tare suka fito zuwa haraban gidan da hisham suna magana kasa kasa ."bayan fitar adamcy daga gidan mami ta kira shahida tace "idan suna da lokacin su shigo yau su gaishe da maryama . "kai tsaye tace "to! hira sukai kad'an ta katse kiran inda aunty shahida ta kira aunty khadija tace ta shirya zata biyo ta d'auketa suje gaishe da maryama aunty khadija ta yatsina fuska sannan tace" ki wuce kawai zani wata yar unguwa dan bazan iya zuwa gaisheta ba ."

"karki yi haka mana wannan fa umarni mami ne " ai wallahi aunty shahida bana son ganin fuskar yarinyar nan dan zan iya gaggaura mata mari idan na d'aura kwayar idanuna akanta "ko ni nan na tsaneta khadija kuma zuwanmu ba yana nufin munje gaisheta bane umarnin mahaifiyarmu zamu bi daga nan muci uwarta aunty khadija tai murmushin jin tana cewa yar iskar yarinya kawai abinda nayita jaddata mata karta kuskura ta bari wani abu ya shiga tsakninsu .shine ya zamo a farko anan dai suka ajiye magana zasuje zuwa anjima ." Karfe d'aya da rabi adamcy ya dawo lokacin maryama tana bacci tana cikin baci taji ana shafata ta bud'e idanunta kad'an shi tagani kwance ajikinta tace "stop pls! stop what? ya tambayeta a d'an rikice "abinda kake yi né banaso wallahi wani iri nake ji ajikina dan Allah ka daina bai san sanda ya kai bakinsa daidai wuyanta ya fara lasar skin dinta ba ,wani sabon bakon alamari taji yana bin sansar jikinta mai tattare da shaukin son shi ya zarce har cikin kunnenta yana hura mata iskar bakinsa wani irin zillo tayi jin wani sabon dadi daya ziyarci sansar jikinta dan dole ta natsu tana amsar sako ."

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull