Kenza eBookz

Nida patient dina book two by mrs isham - Chapter 17

Nida patient dina book two by mrs isham - Chapter 17

Nida patient dina book two by mrs isham Chapter 17: Nida patient dina book two by mrs isham Chapter 17. Wangale musu gate din masarautar akayi suka shigo ,…

4,108 words

Wangale musu gate din masarautar akayi suka shigo , fitowa sukayi fadar sarki suka nufa domin se sunje sun fara gaisheshi kafin su shiga cikin gida , a kishingide suka samu sarki azaad yatsufa sosai farin balarabe yana sanye da kayan sarauta yana ganinsu yafara musu marhaban duƙawa sukayi agabanshi suna gaisheshi ɗagosu yayi ya rungumesu ajikinshi yana sa musu albarka, sun jima sosai a fada tare da sarki azaad sannan suka koma cikin gida , an shirya musu kwarya_kwaryan liyafa kowa na murna da ganin matar Mr azaad manya maza da mata kowa se yabon halinta yakeyi dakuma kyanta , yanda aka martabata dakuma nuna mata zallar soyayya hakan yayiwa fanan da Mr azaad dadi duk da yasan halin dangin umminshi suna da matukar karrama mutane basa kyaran mutum duk yanda yake duk halinsu daya kuma tarbiyan da su ummi suka taso akai kenan kuma haka yaran masarautar suka taso , hakan yasa ummi ma ta gina yaranta akan tarbiyyar gidansu.

Ammu mahaifiyar ummi ce ta ce fanan bazata kwana ako inaba se awajanta, bayan sunyi Sallah isha suka hadu s babban dinning table na ahali kowa ya hallara anacin abinci cikin nishadi da jin dadi bayan an gama kuma suka koma falo ana hira, fanan tanajin larabci sosai hakan yasa takejin duk abinda suke fada kuma ake hiran da ita video call fawwaz yakira Jamal yaron kanin ummi connecting yayi ta system, ummi tayi matukar farin ciki ganin fanan acikin danginta kuma kowa na haba_haba da ita da hausa ta ce " my feena kinga danginki ko ?" Murmushi tayi ta ce " naga kowa ummi kuma sun karbeni hannu biyu nayi matuƙar jin dadi da hakan , naji dadin kasance acikin wannan ahalin " haka sukasha hira kafin sukayi sallama. Darene yafarayi aka fara watsewa , har kowa suka tafi yayi saura ammu da fanan , Mr azaad se layla matar uncle asaad mikewa Mr azaad yayi ya ce " wifey muje mu kwanta dare yayi" ƙin motsawa tayi dan kunya takeji bazata iya binshi ba agabansu kuma dama ammu tace tare zasu kwana , duk da basa jin hausa amma sun fahimci abinda Mr azaad ya ke nufi , hararanshi ammu tayi cikin harshen larabci ta ce " katafi kabani wuri , gwara kaje kayi baccinka ita anan zata kwana" daure fuska yayi ya harari ammu shima cikin harshen larabci yabata amsa " ammu banason haka babu ruwanki dani da matata tunda ke na sakeki saki uku " dariya layla da fanan sukayi wato wasan kaka da jika ne ahakan kowa na hararan kowa musamman ma fanan jin Mr azaad yace yasaketa ne abin yasake bata dariya , haka suka dingayi tun sunayi kamar faɗa har yakoma lallashinta amma sam taƙi yarda tace fanan awajanta zata kwana haka yafita daga falon rai abace dan yasan ba lallai ne ya iya bacci batare da yaji fanan ajikinshi ba yariga da yasaba da ɗumin jikinta amma yau yanaji yana gani ammu tahana. Ita kanta fanan bataso haka ba amma koda ammu batace awajanta zata kwana ba , bazata bishi ba .

Dakyar Mr azaad ya iya bacci batare da yaji fanan akusa dashi ba , washe gari haka yafarka ranshi amatukar bace domin shi yafi ganin laifin fanan da ammu tace seta kwana awajanta aida setacewa ammu ni awajan mijina zan kwana amma tayi shuru daga baya ma se tadinga dariya ( iyeeeh lallai Mr azaad din nan wato kai bakasan kunya ba shisa kake fadar haka .)

Bayan sun gama breakfast ne aka yiwa fanan wanka da ruwan madara aka shiryata acikin alkyabbah domin za'a gudanar da al'adun da mutanen masarautar da akeyiwa surkanai , fitowa tayi a sarauniyarta sak dukda basusan itadin wacece ba amma sunyi matukar mamaki ganin yanda kayan ya amsheta ga wani irin kwarjinin da lokaci daya ta kara , manyan matan mutane masu muƙami a Dubai duk sunzo domin gabatar da al'adar saboda iya matane sukeyi . Zaunar da fanan akayi akan kujera me kyau da ado , addu'a aka farayi da gabatar musu da surkarsu Fatima kafin daga bisani aka fara gudanar da al'adun kasancewar ammu ce babba ita tafara gudanarwa, daukan sweet tayi ta bawa fanan a baki sannan ta fesa mata turare miƙa hannu ammu tayi wata kuyanga ta miko mata wani hadaddiyar box ta karba bude shi tayi , sarƙa da ɗan kunnen zinari ne me mugun tsada se daukan ido yake ta daurawa fanan akan cinya sannan ta manna mata kiss agoshi ta koma gefe , bayan ammu ta gama se matar uncle arash itama tazo tayi nata ta bata kyautan sarƙa ɗan kunne na zinari, haka akatayi har aka tashi fanan tasamu kyaututtuka sosai agajiye takoma part din ammu kuƴangu suka taimaka mata wajen cire kayan domin jinta takeyi kamar akan ƙaya aikuwa tana cire su tashiga bathroom tayi wanka hade da alwala tafito tasa abaya da hijab tayi sallah azhar ta kwanta dan tagaji sosai.

Yana fada shida sarki azaad suna hira da sauran kawunan shi , kiran sunanshi yaji anyi hakan yasa yaɗago saboda yayi tsammanin daya daga cikinsu ne ya kirashi din , kallon fuskokinsu yayi yaga hirama sukeyi babu wanda yakirashi daga cikinsu karajin kiran yayi ana fadin " azaaad kafito ina waje " mikewa yayi yace musu yana ɗan zuwa tafiya yakeyi bega ko alamun wanda ke kiran nashi ba acikin masarautar hakan yasa yanufi gate fadawan dasuke wajan suka bude mishi gate suna kokarin yi mishi rakiya ya ɗaga musu hannu alamar baya bukata yayi waje , titin masarautar shuru babu kowa tafiya yakeyi har lokacin bega kowa ba wani dattijo yagani yana zaune aƙasa kayan jikinshi duk ya koɗe yarufe jikinshi da yar bargo ga kwanon baranshi agabanshi wuce shi Mr azaad yayi, sekuma zuciyarshi ta raya mishi wani abu dawuwa yayi wajan wannan dattijon yazauna kusa dashi bedamu da ya jikinshi zeyi datti kokuma wani abu ba ya ce " kaine ka ƙirani ?" batare da dattijon yaɗago kai ya kalleshi ba yabashi amsa da " nine nayi ƙira agareka " kallonshi dakyau Mr azaad yayi kafin ya ce " shin ko zan iya sanin dalilin wannan kiran " gyara bargon da yarufe jikinshi dashi dattijon yayi yafara magana " nasan kanata tambayar kanka menene abinda yake shirin faruwa dakai abisa sabon al'amarin daka tsinci kanka a ciki na jiye_jiyen maganar mutane harta da wa'yanda ba mutane ba , abinda bakasani ba shine kaidin ɗan baiwane , kana dauke da baiwar jin magana duk nisar dakuwa akayi ta zaka iyaji . Awannan ƙarnin ku uku ne kaɗai masu irin wannan baiwa kune akewa laƙabi da ' majiya ' azaad kaiɗin majiyine yau na amsa maka wannan tambayar taka" cike da zallar mamaki Mr azaad yake kallon wannan dattijon dayake mishi wa'yannan bayanan domin tabbas wani sabon al'amarin daya tsinci kanshi aciki yana damunshi sannan kullum cikin tambayar kansa yake yi menene dalilin faruwar hakan, tambayar dattijon yayi ya ce " to kaiɗin wanene? " yaye bargon daya rufe jikinshi dashi dattijon yayi fuskanshi ya bayyana fara ni ƙal ga gashi ne ajikinshi kwantacce tako ina hatta fuskantar shi akwai suma kallon cikin idon Mr azaad yayi da idonshi da ya kasance kwayar idon jane da fari ba kalar na bil adama bane ya ce " sunana tsuntsu arnass me baku bayanai akan wasu lamuranku dasukeson sarƙe muku, yanzu babban abinda yakawoni wajan ka shine magana akan sarauniyar nasminaya, wato cikekkiyar yar baiwa me dauke da karfin ikon jaaazana atare da ita. ta kasance yar baiwa ce me bada abubuwa guda biyu a rayuwar dan adam , tana dauke da baiwar taimako dakuma baiwar yaɗa farin ciki a duk inda ta zauna wannan dalilin yasa setafi kowa iya sarrafa karfin ikon jaaazana ajikinta saboda shi jaaazana baya bayan mugunta hakan ne ya sanya ya zabeta a domin baiwar da Allah yayi mata atare da ita , sarauniya fadima inharde tana waje farin ciki yana bayyana awannan waje sannan tana taimako da iya iyawarta. Abu nagaba da baka sani ba shine kungiyar BAPHOMET sun shirya ganin bayanta adoron ƙasa domin cikar muradinsu hakan yasa suka nemo wanda yakasance dan baiwa domin suyi amfani dashi wajan tarwatsata sannan su mallaki jaaazana , daga zaran sun mallaki jaaazana kuwa komai ze dagule babu me iya ceton al'ummar duniya fa ce Allah SAW, shin kokasan dawa zasuyi amfani domin cikar muradinsu?" Ya wurgawa Mr azaad tambaya idonshi cikin nasa , jikin Mr azaad yayi sanyi sosai dakyar ya iya furta kalmar" ah ah bansaniba " Murmushi arnass yayi ya ce " kaine nan " arazane Mr azaad yake kallonshi ya nuna kanshi da yatsarshi ya ce " arnass nikuma ? Me dalilin hakan ? " Cigaba da magana arnass yayi " tabbas dakai zasuyi amfani ko kana so , ko bakaso dole dakai zasuyi amfani suna nan suna shirya yanda zasu jefa maka wutar kiyayyar sarauniya acikin zuciyarka wanda hakan ne zesa duk wani sirrin abinda yake wakanan zaka dinga sanar dasu , sukuma zasu shirya yanda zasubi su sameta harsu cire narƙekken jaaazana ajikinta wanda anacireshi ta karfin tsiya dole sarauniya zata mutu su kuma zasu samu abinda suke nema bayan bukatar su ta biya zasu kashe duk yan masarautar nasminaya kasan da sa hannun waye za'a kashe sarauniya? da sa hannunka za'a kashe ta . daga bayan bukatar su ta biya zasu tarwatsa kungiyar SATANIC sekuma abu nagaba zasu kashe ka domin ka gama musu amfani sesu dawo kan al'ummar duniya su fara yaɗa zalunci su . Wannan abun da nake fada maka du ka nanda yan watanni nan zasu faruwa kuma yanzu kaine sa ransu kaine makaminsu azaaad majiyi " idon Mr azaad ya rine yakoma jaa jin irin wannan tashin hankalin dake tunkarosu babban abinda yafi daga mishi hankali shine jin dasa hannunshi za'a tarwatsa sarauniya sannan akasheta shikuma yayi alƙawarin baze taba basu wannan dama hakan yasa riko dukka hannayen arnass dasuke kamar ƙankara tsabar sanyi ya ce" arnass shin babu wani hanya da zaabi domin ganin wannan mummunar ƙudirin nasu be faru ba ? Wallahi da inbada wannan gudunmawan ganin bayan wacce nake so gwara in rasa raina " jinjina kai arnass yayi yana kara girmama wannan girman soyayyar tasu domin sudin an haifesu ne saboda junansu hakan yasa daya ze iya bada ranshi ga dan uwanshi , shafa kan Mr azaad arnass yayi ya ce" akwai hanya daya dazaabi amma hakan ze iya sawa ka rasa naka baiwar jin , se bayan shekara hudu zedawo gareka " a gaggauce Mr azaad ya ce" na amince koma miye inhar hakan zesa bazasuyi amfani da ni ba" " hakan yayi kyau azaaad inkayi hakan shine Kacika babban masoyi, yanzu anan wajan zan zare maka baiwar jinka dakake dauke dashi zantafi dashi inje in ɓoye , zaka koma yanda kake ɗa , zaka dena jin wa'yannan maganganun , hakan ze ɓata musu nasu shirin zasu dena bibiyarka domin abinda kake dauke dashi din babu. Wannan kadai ze hana faruwar wannan lamarin, amma kasani nan da yan watanni za'a tabka babban zaluncin da ze farkar da jaaazana dake jikin sarauniya awannan ranar kuma zata tafi tafiya kuma kusan na har abada " tunda Mr azaad yake arayuwarshi betaba shiga irin wannan tashin hankalin ba seyau yanayin yanda kirjinshi yake bugawa kadai mutum yaji yasan akwai babban tashin hankalin dake damunshi wasu irin zafafan hawayene suke saukowa daga idonshi , tabbas abinda zesaka jajirtacce kuma jarumin namiji kamar azaad zubar da hawaye tabbas ba karamin abu bane . Dafa kafadarshi arnass yayi ya ce " kayi hakuri azaaad kasani koda ace tafiyarta bata rabaku ba to tabbas mutuwa dake kan kowa ze rabaku " yafada mishi yana sa hannunshi atafin hannun Mr azaad ya fara magana , wani irin kananun taurarine suke fitowa daga jikin Mr azaad suna shiga cikin kwanon baran arnass , har suka shige gabaki daya cikin kwanon sake mishi hannu yayi yarufe kwanon yamike tsaye , mikewa Mr azaad yayi shima arnass ya ce mishi " daga rana irin nayau bazaka sake jin wani magana dake nesa ba nafitar da majiyi ajikinka se nan da shekaru hudu zasu dawo gareka ni zan tafi ka isarmin da sakon gaisuwana awajan jaruma , sadaukiya sarauniya, duk sanda kakeson ganina kawai ka kira sunana da izinin Allah zan bayyana nabarka lafiya " kallonshi Mr azaad kawai yakeyi saboda baya cikin yanayi najin ze iyayin magana da kowa ba , murmushi arnass yayi mishi sannan yakoma wani irin tsuntsu me ban sha'awa yafire sama.

Shigowa cikin masarauta yayi duk wa'yanda suka haɗu dashi sesunyi mishi magana amma shi ina hankalinshi baya kan kowa babban burinshi shine yaje yaga fanan domin ji yakeyi kamar inyashiga zaace mishi bata nan annemeta an rasa, direct yanufi part din ammu mutane cike afalon kowa se magana sukeyi mishi amma babu wanda yakula yashiga dakin ammu akan makeken gadon ammu yasamu fanan kwance tana baccinta cikin kwanciyar hankali, hawa gadon yayi ya kwantar da kanshi akirjinta yasa hannu yarungumota tsam ajikinshi kamar za'a kwace mishi ita hawaye nazuba a idonshi , cikin baccinta datakeyi taji kamar tana jikin mutum farkawa tayi cin karo tayi da kamshin turaren shi hakan yasa tayi murmushi murya cike da bacci ta ce " habiby katashi kar ammu tazo ta ganmu ahaka" shuru yamata bece komai ba magana tasake yi mishi taga yasaketa yamike yazauna yabata baya ,tashi zaune tayi tana mutsutsuka idonunta saukowa tayi daga kan gadon tadawo gabanshi ta tsaya , tana mishi magana nan ma shuru ba amsa kanshi aƙasa, sa hannunta tayi tadago dakan nashi , bakaramin girgiza tayi ba ganin hawaye afuskanshi tallabo fuskanshi tayi hankali a tashe ta ce " habibyna menene yake faruwa dana ga hawaye akan fuskar jarumin mijina daya kasance gwarzo" nan ma shuru bece mata komai ba nan hankalinta yasake tashi nan take itama ta fara kuka tana tambayar shi abinda yake faruwa, jawota yayi yarungumeta gam kanshi akan shamulallen cikinta rungumeshi itama tayi tana kuka , dakyar Mr azaad ya iya bude bakinshi murya a kausashe ya ce " baby bazan iya rabuwa dake ba! zanshiga mugun hali inkika tafi kika barni bazan iya rayuwa batare dake aciki ba , duniyar zatamin kunci inbakya a cikin rayuwata , wifey kina tunanin zanci gaba da rayuwa mejin dadi ne idan bake ? narigada nasaba da komai naki kedin kece jigon rayuwata , duniya juyamin baya zatayi bayan tafiyarki " jin wa'yannan kalaman daga bakin Mr azaad ne yasake dagawa fanan hankali musamman idan ta tuna sun kusa rabuwa fashewa tayi da kuka na tausayin kansu , an rasa samun wanda ze lallashi wani acikinsu dago rinannun idonshi yayi yakalleta ya ce " wifey yau zamu koma Nigeria zanfi samun sauki acan kishirya yanzu zamu tafi bari inyi booking din ticket" takasa magana tsabar yanda kuka yaci karfinta se gyada mishi kai tayi raba jikinsu yayi yana kokarin barin dakin wani haske ya bayyana abdud Shakur ne da jakadiya abashiyya zubewa sukayi akan guiwowinsu suka gaida sarauniya sannan suka mike , abashiyya ce ta soma magana " kuyi mana afuwa abisa ganinmu dakukayi kai tsaye , sarauniya yakamata ayau din nan kikoma gida domin hana wani al'amari faruwa kuma bin jirgi da zakuyi ze ɓata mana lokaci kuyi musu sallama kawai mutafi " ta karishe magana kanta na kallon ƙasa, dama abinda Mr azaad yake jira kenan baya bukatar koda kara awa daya agarin yafito da waya yakira layin uncle arash yace mishi yabawa mutanen gida hakuri komawar gaggawa yakamasu suyi musu afuwa sun rigada sun tafi dukda hakan beyiwa uncle arash dadi ba amma haka yamusu addu'a Allah yatsare hanya . Bayan yakshene yake sanar da sarki azaad dakuma mutanen fada .

Abdud Shakur ne yace musu su rufe idanunsu , yanda yafada haka sukayi suka rufe idonsu bayan wasu mintunan dabasu fi minti uku ba suka bude idonsu atare ganinsu sukayi acikin tsakiyar bedroom din Mr azaad, basuyi wani mamaki ba toilet fanan tashiga tayi wanka tafito kallon Mr azaad tayi dake kwance kanshi na kallon celling kaya tasaka ajikinta taya fa gyale ta ce " habiby bari inje gun ummi " Kai kawai ya gyada mata ta tafi , duk suna falo suna zaune suna yar hira motsi sukaji upstairs yasa suka maida kallonsu wajan mamaki ne yakamasu ganin fanan ce take saukowa tambayar kansu suka farayi yaushe suka dawo harta shigo falon da kallo suke binta fadawa jikin ummi tayi ta rungumeta tana fadin " nayi missing dinki sosai ummina " ummi ta ce " my feena yaushe kuka dawo?" lalubo karyan dazatawa ummi tayarda tayi ta ce " ummi dazun mukadawo dama munce surprising dinku zamuyi " sunyi farin ciki da ganinsu dama sunyi kewarsu sosai musamman fanan, rungumeta zeenat tayi tana " highly welcome anty fanan dama wallahi jinayi gidan ba dadi dabake" murmushi fanan tayi ta ce " to yanzu gani nan nadawo ai" sukayi dariya gaishe dasu anty amina da dazun zuwanta gidan saboda maganar biki itada anty shayida anty zainab bata samu zuwa ba tace se gobe zatazo , suka amsa suna mata ya hanya daga nan ta juya tagaishe dasu areef da fawwaz maido mata da gaisuwarta sukayi taƙi amsawa , kamar daga sama taji wata bakuwar murya na fadin " inayini ya hanya ?" Kallon inda maganar yafito fanan tayi wata budurwa tagani rakube awaje daya bata saki jikinta ba tana sanye da kayan zeenat se sunnar dakai ƙasa takeyi , kafeta da ido sosai fanan tayi kafin ta amsa kallon zeenat tayi ta ce " zeee aina aka samo wannan baiwar Allah" taɓe baki zeenat tayi ta ce " dazun ne Abba ya kawota wai zata zauna tare damu yatsinceta ne wasu ne sukayi kidnapping dinta daga kauyensu yanzu de yace gobe ko jibi za'a maida ita kauyensu " jinjina kai kawai fanan tayi tana sake kallon yarinyar gaba daya hankalinta be kwanta da itaba tsigan jikinta ne taji yana tashi , tambayar ta tayi "meye sunanki ?" ta ce " sunana maryama" tunda ga nan fanan tasamu waje tazauna bata sake cewa komai ba amma hankalinta na akan maryam din domin tanajin wani abu dangane da ita . Anty shayida ce ta ce " mash Allah mutanen turai, feena gaskiya turai ya karbeki kinyi fresh sosai " dariya sukayi sannan suka fara hira , saukowa Mr azaad yayi yana zuwa ya rungume umminshi kawai bece mata komai ba tunda taganshi haka ummi tasan akwai wani abinda yake damunshi shafa kanshi ummi tayi yazagayo yazauna kusa da ita , gaisheshi sukayi babu wanda yacewa ƙala acikinsu suma ganin haka suka san yau he's not in a good mood gaisheshi Maryam tayi jin bakuwar murya yasa Mr azaad yakalleta nan take yaji hankalinshi be kwanta da itaba yadaka mata tsawa " ke daga gidan ubanwa " rawa jikin Maryam ya soma tafara hawaye ummi ce ta ce" haba son meyasa kake haka " kwantar da kanshi yayi akan kujera besake tanka musu ba .

Anty amina ce ta ce " yawwa anty shayida nunamin hotunan dake wayar naki na akwatunan " anty shayida ta ce " bari indauko wayar tana daki " tafada tana kokarin mikewa fanan ta ce " anty shayida zauna bari indauko miki " " to feena" harta kusa barin falon Mr azaad yaɗago ya kalleta ya ce " ina zakije?" langwabar da kai tayi ta ce " waya zandaukowa anty shayida" kamar zece mata tadawo tazauna zeje da kanshi sekuma ya gyada mata kai , bin bayanta Maryam tayi da kallo seda takusa hayewa stairs din karshe Maryam ta motsa bakinta yanda babu wanda yalura da ita, tsantsine yakwashe fanan ta sake karfen stairs din tafara gangarowa tundaga can stairs din farko ƙara tasaka wanda yajawo hankalinsu, tashi tsaye sukayi gabaki dayansu suka nufa wajanta ganin yanda take gangarowa daga bene da mugun gudu Mr azaad ya isa kan benen tana kokarin fadowa daga na karshe yasa hannu ya tallafota , hankalinsu yayi mugun tashi , kanta yafashe yana fitar da jini , rufewa idonta yake kokarin yi Mr azaad yasa hannu yana jijigata dakyar ta iya bude idonta ta ce " habiby zan mutu " tundaga wannan kalmar tadauke wuta cak tadena numfashi kuka zeenat tafashe dashi ta daura hannunta akai jawota fawwaz yayi yarungumeta da shima hawayene yake zuba a idonshi ummi kam ɗurƙusawa tayi agaban fanan takasa koda motsine anty amina da anty shayida duk kuka sukeyi harda areef kuka sukeyi yau sunshiga matsanancin tashin hankali, ummi ce ta ankara da jinin dake bin ƙafan fanan kamar wanda aka kunna famfo, da karfi ta ce " fawwaz dauko motar tana zubar da jini " duk kallon inda ummi take kallo sukayi jini ne bana wasa ba yakebin ƙafan fanan, daukanta cak Mr azaad yayi bedamu da jinin dake ɓata mishi jiki ba, be jira kowa ba yasata a back seat yatada motar, horn kawai yake dannawa da gudu baba me gadi yabude gate yafisgi motar kamar zasu fire sama , bin bayanshi su ummi sukayi , anty shayida da anty amina suna motar areef ,ummi da zeenat kuma suna motar fawwaz, gudu kawai Mr azaad yake yi akan titi motoci duk wa'yanda suka ganshi yanufo su hanya suke bashi , hakama fawwaz bin bayanshi sukeyi saboda karya ɓacewa ganinsu , horn yake dokawa abakin gate din medical center, ko kyawawan packing beyi ba yafito yadauketa , nurses naganinshi suka nufoshi da gadon daura mara lafiya kwantar da ita yayi , ya tayasu turawa manyan doctors ne suka rufa musu baya domin tun shigowar su suka ga Mr azaad ne shisa ba wasa suka shiga da ita emergency room yana kokarin shiga dakin suka bashi hakuri akan yajirasu awaje suka rufe kofar emergency room din suka rufu akan fanan domin bata taimakon gaggawa, jikinshi duk yabaci da jini amma bata shi yake ba ta matarshi yakeyi jirine yaji yana kokarin yada shi fawwaz da shigowarsu yanzu kenan yarikoshi suka zauna akan kujerun dake wajan , yau abubuwa sun hadu sunyiwa Mr azaad yawa ji yakeyi duniyar baya mishi dadi yanzu damuwarshi shine fanan tafito daga cikin hatsari. duk jugum_jugum sukayi kowa addu'a yakeyi aranshi zama ummi tayi kusa da Mr azaad, kwantar da kanshi yayi akan kafadarta murya na rawa ya ce" ummi duk wannan laifina ne daban barta taje ba da hakan be faru da itaba am at fault ! laifina ne" anty shayida dake kuka ta ce" azaad wannan ba laifinka bane ,laifin ne danaje nadauko wayata da kaina " shafa kanshi ummi takeyi takasa lallashin sa itakanta tana cikin tashin hankalin da zataso a lallasheta , kirane yashigo wayar zeenat tsabar tashin hankalin datake ciki up side down ta manna wayar akunnenta murya Abba taji yana tambayar ta suna ina dan yadawo gida ake sanar dashi abinda yafaru , goge hawayen da yazubo mata yayi ta ce " muna medical center" katse Kiran yayi .

Layin suhaima zeenat takira tasanar da ita abinda yake faruwa cikin tashin hankali suhaima takira ya ya usman tafada mishi , suhaima tayi kuka sosai babban takaicinta shine bata Gombe tana Bauchi.

Kusan atare Abba,baba,mama,anty firdausi,anty zainab,ya usman da hairah , yaseer , Amira da hajiyarsu suka shigo asibitin ko wannensu hankali atashe ko nutsuwar gaisawa basu samuyi ba duk zama sukayi kowa na jiran fitowar doctors.

Bude kofar doctors din sukayi suka fito suna goge gumin fuskansu tasowa sukayi sukayo kan doctors din suka fara tambayar su ya fanan din take, shuru sukayi , tunzura Mr azaad sukayi afusace yashake wuyan dayan doctor din da karfi ya ce " kafadamin meye yasamu matata ?" Ganin Mr azaad na kokarin yin kisan kai ne yasa duka mazan wajan suka fara kokarin raba Mr azaad da doctor din, dakyar suka ɓanɓare hannun Mr azaad awuyan doctor din , rike wuyarshi doctor yayi yana fitar da numfashi da kyar zillewa yayi yabar wajan dan yaga Mr azaad ze iya hallaka mutum .

Wani doctor ne ya ce " ku kwantar da hankalinku ! tafito daga cikin hatsari tana cikin koshin lafiya se abu nagaba babyn dake cikinta ma lafiyarshi klau babu abinda yasameshi.......

Comments and share fisabilillahi 🙏

Read more 10 to 11 is not easy 😢 inajiran comments dinku.

Se gobe inme duka yakaimu da rai da lafiya. https://chat.whatsapp.com/Jo87gS6QxQF58XSV10dYL8

🧑‍⚕️🧑‍⚕️ NIDA PATIENT DINA 🩺🩺

Story & written by ✍️ MRS 🌹 ISHAM 🌹 ( Yar lelen Jarumai)

🔔📚 JARUMAI WRITERS ASSOCIATION 📚📚

⚜️📚J. W. A 📚🖋️

Gargadi Ban amince wata ko wani yayi amfani da wani sashe daga cikin book din nan ba ta kowani siga ko a karanta minshi a youtube batare da an nemi izini awurina ba ko a hadamun document ko amin edit idan kunne yaji jiki ya tsira koda Allah nabar mutum ze sakamin yabimin hakkina.

Three paged in one PAGE 6️⃣1️⃣

Readers Also Read