Kenza eBookz

Nida patient dina book two by mrs isham - Chapter 19

Nida patient dina book two by mrs isham - Chapter 19

Nida patient dina book two by mrs isham Chapter 19: Nida patient dina book two by mrs isham Chapter 19. Tana zaune akan gadon ta sanya doguwar rigar atamfa…

4,495 words

Tana zaune akan gadon ta sanya doguwar rigar atamfa kanta ba dankwali saboda bandejin dake kanta ummi ce tahaɗe mata gashin tadaure mata da ribbon zama yayi akusa da ita yasa hannu yana ɗan taba kan nata kaɗan gaisheshi tayi shida yaseer, amsawa yaseer yayi sannan yamata yajiki , Mr azaad be amsa mata gaisuwar da ta mishi ba ya ce " wifey ya jikin naki " kallon ummi tayi taga hankalinta ba'a kansu yake ba tana magana ne da yaseer, ta ce " jiki alhamdulillah" tashi sukayi da niyyar tafiya rike hannunta yayi ya mikar da ita tsaye sannan yadau gyalen da ya gani akan gadon ya rufe mata ajikinta, gaba su ummi sukayi shikuma yana rike da ita suna baya , duk inda suka wuce se jama'ar asibitin sun mishi godiya tare da sa mishi albarka haka suka shiga motoci suka dau hanyar gida , bayan sun isa ne , duk afalo suka samu su zeenat suna zaune suna zaman jiransu tashi sunayiwa fanan ya jiki ta amsa musu fuska asake wucewa da ita Mr azaad yayi zuwa part dinshi basu tsaya a ko ina ba se a bedroom dinshi zaunar da ita yayi akan gadon ya zauna akusa da kwantar da kanta tayi akan kirjinshi tana shaƙar kamshin turarensa , " habiby inasanka sosai" kallonta yayi da sexy eyes dinshi yace " wifey! inasanki bantaba tunanin aduniyar nan akwai macen da zanso har inyi rayuwar aure da ita ba se akanki Allah yadoramin sanki banajin zan iya rayuwa batare dake ba, inasonki sosai da ke dakuma unborn baby mu " dagowa tayi dasauri ta kalleshi da alamar tambaya ta ce" habiby bangane abin kake son fadamin ba ! what do you mean by our unborn baby?" daura hannunshi yayi akan shamulallen cikinta da babu alamun akwai ɗa aciki ya ce" yes up course baby kina dauke da ciki , kinadauke da jinina acikin ki munkusa zama parents, bazan iya misalta irin farin ciki da nake ciki ba " hawaye ne yafara wanke mata fuska da mamaki yake kallonta ganin daga fada mata tana dauke da ciki tafara hawaye gabanshi ne yafadi tsoronshi daya kar fanan ta ce batason cikin dake jikinta, riko hannayen ta yayi suna fuskantar juna ya ce" baby why are you crying?" rungumeshi tayi gam cikin muryan kuka ta ce" habiby kukan farin ciki nakeyi , nima yau ina dauke da baby acikina alhamdulillah zanji abinda iyaye sukeji insuna da juna biyu. habiby babban farin cikina shine zantafi in bar muku abinda zaku kalla kuji sanyi aranku , ko bayan raina nasan nabar iri aɗoron ƙasa " shi yanzu babu abinda ya tsana sama da yadinga jin maganar tafiyanta hakan daga mishi hankali yakeyi se yaji kamar shima yabita kome ze faru ya faru shafa bayanta yakeyi ya ce" kidena fadar haka ko so kike kidinga dagamin hankaline , yanzu lokacin farin ciki ne ba lokacin bakin ciki ba Please ki bari " raba jikinta da nashi tayi ta aro murmushi ta yaɓa wa fuskanta ta ce" am sorry my love bazan sake ba , yanzu fadamin wata nawa ne babyn ?" fito da result din da doctor yabashi yayi ya bude duk sun nutsu shida ita suna karantawa sosai sukayi mamaki ganin cikin wata hudu ne dede, su duk tunanin su karamin cikine da be wuce one month ba ganin yanda cikin nata yake a shamule babu alamar akwai ɗa acikinsa " laah habiby cikin wai wata hudu amma kalli cikina " tafada tana daukan hannunshi ta daura cikinta shafa cikin yayi yaduƙo da kanshi dede cikin ya mannawa cikin nata kiss shafa kanshi tayi tana murmushi ta ce " father to be " yar dariya yayi ya ce " yes yakamata ko da yaushe mahaifi yadinga jin lafiyar ɗan sa " cike da so da kaunar juna suke ta hira .

Bayan kwana biyar da sallamota anty amina ta kawo me gyaran amaren part din mommy da ba kowa aciki aka gyara aka fitar da kayan tsafinta aka konasu, aka bar musu part din anan zasuyi komai dinsu aciki zeenat ce ta fara dawuwa aka fara mata ta , anty amina tace fanan ma itama amaryace harda ita tare aka fara musu ita da zeenat.

Suhaima tadawo gombe saboda baba ne ze aurar da ita , anty amina ce tazo har gidan ta roƙi alfarma awajen mama akan ta bata aron suhaima da hairah tadauko me gyaran da zata yiwa du ka amaren gyara , dakyar mama tayarda ita gani takeyi za'a daura musu dawainiya ahaka anty amina ta lallabata ta ɗauki suhaima da hairah daga nan bayan sun fito tashiga gidansu Amira ta taroki hajiyar Amira itama duka direct part din mommy tashiga dasu . Suna ganin juna sukasa ihu suna murna harda tsalle girgiza kai anty amina tayi ta ce " yaran nan Allah yashiryeku , my feena dan Allah kidena biye musu kinga ke bake kadai bace" " tom anty amina" cewar fanan. gyara akeyi musu na gani na fada lokaci daya suka canza acikin sati biyu sunyi kyau sosai fatar su ta kara glowing se sheƙi yayi luwai_luwai, fatar su kamar ataba jini ya fito bugu da kari ga shi ba shiga rana sukeyi basa fita ko nan da kofar falo duk abinsu acikin part din sukeyi ga kamshin da jikinsu yakeyi duk inda suka zauna sesun bar kamshin su awajan . ga tsumin da ake basu suke sha , burin zeenat de yashika abin nema yasamu ci da kaza da take magana akai ,yanzu itama lokacinta yazo tanaci.

Abun duniya ya dami Mr azaad shi gani yakeyi baayi mishi adalci ba ace sati biyu cur ahanashi ganin matarshi dakuma jin ɗuminta dana ɗanshi. Duk laifin anty amina yafi gani taya zata daukar mishi mata bayan tasan yana bukatar matarshi akusa dashi, rabon da yasata a ido tun ranar da tazo tadauketa da sunan za'a musu gyaran jiki , haka yayi hakuri ya kyalesu amma kullum suna manne awaya arana zasuyi waya sau uku sau hudu harda video call.

Haka bangaren sauran angwayen ma suma basu sake saka amaren a idonsu ba sede suyita waya.

Ana daurin aure saura kwana uku , Yan beauty saloon's sukazo domin yi ma amare lallai da wankin kai , lalle da dayis akayi musu me rai da lafiya ja da baƙi hannu da ƙafa sannan aka yi musu saloon duk kansu kitso akayi musu amma banda fanan da ta ce ita kawai a gyara mata kan . sun sha gyara kam na fitan hankali .

Washe gari ana jibi daurin aure Hajiya ta turo da motar yadau Amira da suhaima dakuma hairah . Masha Allah abangaren gidajen amare da angwayen komai yayi ready ranar daurin aure kawai ake jira domin abba da baba sunce bazaayi wata bidi'a ba saboda albarkan aure ake nema . Yan uwa na nesa da na kusa duk sun samu hallara yan Dubai sun iso haka su umma rahina da uncle kabir duk sunzo .

gidan da komai seda aka canza mishi komai sabo , babu abinda ba'a canza yazama sabo ba anyi ƙayitatciyar decorations, part din Mr azaad anzuba sabbin furniture haka part din fawwaz da areef ma anzuba furniture da duk wani abinda ake bukata, areef da Hafiz kuma sundawo part din downstairs na karban ba ki . Shirye shiryen biki akeyi ba kama hannun yaro duk sun shiga busy , anty amina da anty shayida da anty zainab sune gaba akan komai .

Safiyar jumma'at ranar daurin aure, da safe anty amina tashigo da masu aiki rike da kayayyakin da zeenat da fanan zasu saka.

misalin ƙarfe sha biyu , wanka aka sasu sukayi da ruwan madara dake dauke da sinadaren kamshi, sannan aka sake hada musu ruwan wanka da ruwan turare sukayi bayan sun fito ne aka basu kayan atamfa riga da zani rigar ɗinkin bubu ba'a musu kwalliya ba babu abinda aka shafa musu dangi nata shigowa cikin part din suna kallon amare ana jiran lokacin daurin aure , haka aka ta daukansu hotuna , ga fans din NIDA PATIENT DINA duk sun samu hallara se daukan hoto da fanan sukeyi saboda kowannesu yasamu nayin posting a status , karfe daya kuma aka sake sasu sukayi sabon wanka aka shirya su cikin hadaddun dogayen riguna na amare ,na fanan milk color na zeenat kuma white color aka musu make up sannan aka daura musu dankwali , sunyi masifar kyau .

Bangaren amare suhaima da hairah kuwa suma misalin ƙarfe sha biyu atamfa suka saka akayi ta musu hotona karfe daya aka sasu sukayi sabon wanka aka shirya su cikin breathing taking gown masu masifar kyau ga shi sun sha make up kyau kam ba'a magana kusan amare babu wanda yake kaisu kyau.

Manyan mutane daga ƙasa daban daban sunzo domin halartar daurin auren jikokin sarkin gombe da kuma Sarkin Dubai sannan ya'ya ga shahararren dan kasuwan nan, ga kuma azaad babban dan kasuwan da ake tunkaho dashi , sarakuna, gomnoni, manya masu faɗa aji aƙasar Nijeriya da kuma ketare duk sunzo , haka manyan abokan baba da uncle kabir da dangi ga abokan nan angwaye duk a masallacin sarkin gombe za'a daura auren nasu . Bayan an sauko daga salar jumma'at aka daura auren. (Usman Muhammad umar & Hairah Aminu ) da ( yaseer Yakubu sani & zeenat Muhammad mainasara) da ( Fawwaz Muhammad mainasara & Suhaima Kabir Umar ) da ( Umar Kabir Umar & Aysha Abubakar Wada ) akan sadaki naira dubu dari da hamsin hamsin lakadan ba ajalan ba , bayan angama daura aure suka tashi suna taya junansu murna , sosai aka taya angwaye murna da se washe baƙi sukeyi suma yanzu sunzama mazajen aure , duk sunsha manyan dakakkun shadda farare sunsha aiki , rungume juna yaseer da Mr azaad sukayi , Mr azaad ya ce " congratulations dude " yaseer ya ce " thank you dude" haka Fawwaz suka rungume babban yaya sukayi wato Mr azaad, taya fawwaz murna Mr azaad yayi sannan ya rungumi ya al ameen da ya usman yau suna cikin farin ciki sosai wanda baƙi baze iya faɗa ba haka baba da Abba da uncle kabir sukayi musabaha. Fadawa se kirari sukeyiwa angwayen anata bushe_bushen sarewa haka suka tafi akayi reception sannan suka wuce gida. suna shigowa gidan mata suka fara guɗa ana cigaba da busa sarewa murmushi ummi tayi tana hamdala yaranta sunyi aure .

Duk yanda zeenat takeson yaseer amma ana fadan an daura aure taji gabanta ya fadi . Mr azaad, yaseer fawwaz areef da sauran abokansu sun je part din ummi sun gaisheta da kuma sauran yan uwa sannan suka biyo anty amina zuwa part din mommy dan ganin matansu , zama sukayi a falo anty amina da anty zainab suka shiga ciki , anty amina tariko fanan anty zainab kuma tariko zeenat tafito dasu. Karan hills din takalman sune yajawo hankalinsu zuwa upstairs, suman zaune Mr azaad yayi ganin irin kyau da canzawan da fanan tayi tun kafin su iso Mr azaad yakarasa wajan nasu sannan ya mikawa fanan hannunshi satan kallon anty amina tayi , saketa anty amina tayi takoma gefe tazauna, daura hannunta fanan tayi akan nashi , shafa hannun yakeyi yakafeshi da ido yana kallon zanen lallen da aka mata kissing din hannun yayi ya jawota jikinshi yarungumeta fanan duk kunya yarufeta ganin duk mutane dake wajan su suke kallo sunayi musu video da hotuna. Ga zeenat zaune agefen yaseer se kallon kauna suke jefawa juna fawwaz ne ya ce " wallahi bazan yarda ba " maida kallonsu kanshi sukayi jamal ne ya ce " hey bro what happened?" dan shi bayajin hausa Fawwaz ya ce " babban yaya kuzo mutafi dan Allah " dariya sukayi harda Mr azaad shima seda ya murmusa dan yasan dalilin dayasa yayi maganar.

Duk fitowa sukayi zasu tafi gidan surkansu wato gidan su fanan tundazun suke jiran Mr azaad yafito yana can shida fanan afalo , kallonta yakeyi babu ko kyaftawa ji yakeyi kamar kar yamatsa daga inda take, sa hannunshi yayi ya zame daurin dankwalin da aka mata , ribbon din da akayi packing gashin yacire , daura kanshi yayi akan wuyanta yana shaƙar daddadar kamshin dake tashi ajikinta shafa cikinta yayi ya ce " baby kwanakin nan danayisu batare da ke ba , it has been very difficult for me! kinyi kyau sosai jinakeyi yanzu kamar induba ɗanmu anan " shafa jikinta dayakeyi ne yasa tafarajin wani irin yamm tsigan jikinta natashi jin wai zeduba babynsu anan ne yasa tafara kokarin raba jikinta da nashi ɗan tasan halinshi tsaf ze aikata abinda yafada. yana kokarin sa bakinshi cikin nata kira yashigo wayarshi tsaki yayi yadaga ganin yaseer ne abangaren yaseer ya ce " dude wannan wani irin iskanci ne ,muna jiranka kaƙi fitowa ka mannewa yarinya mudin anfada maka mudin ba mata bane damu " tsaki Mr azaad yaja yakashe wayarshi kiss ya mata a libs din ta sannan ya ce bari muje gida " ta ce " to habiby adawo lafiya " ya amsa da ameen yafice bin bayanshi tayi da kallo tana murmushi sannan tahaura upstairs tashiga daki tasamu zeenat zaune.

Tunda yafito yake watsawa yaseer harara yaseer ya ce " oho de tunda kafito " dariya sauran sukayi kafin kowa yashiga motar shi suka nufi gidan su fanan.

A canma ana nan anata daukar hotuna da sauran hidimomin biki ya usman se washe baƙi akeyi shigowa gidan tawagar su Mr azaad sukayi nan take aka sa musu guɗa anata tayasu murna , falo suka shiga suka zazzauna suna gaishe da iyaye kafin anty firdausi tafito da suhaima fawwaz ji yayi kamar yatashi yaje ya rungumeta yana jin dadi yanzu shikenan baby tazama mallakinshi. Gaishesu hairah da suhaima sukayi kafin suka fito waje aka fara dauka amare da ango hotuna da dangi , suna gamawa suka ɗuƙunzuma zuwa gidansu Amira nanma hotuna sukayi sukayi gaisuwa sannan suka watse suka koma hotel saboda kaf abokanayensu a hotel din suka sauka saboda abokansu a international hotel suka sauka .

Bayan sallar mangrib an shirya du ka amaren ɗan kaisu gidajensu , aciki kuwa harda fanan , duk shiryasu akayi cikin liffaya aka rufe musu fuska aka kaisu part din Abba yamusu faɗa sosai sannan aka kaisu part din ummi ita tayi musu fada dasauran yan uwa , dangin yaseer sunzo daukan amarya nan fa zeenat ta tuɓure tace bata san zancen ba tana rungume da ummi tana kuka , ummi kanta dauriya kawai tayi dakyar aka raba zeenat ajikin ummi har anfara tafiya da ita tafisge tazo da gudu ta rungume fanan tana kuka, itama fanan seda tayi hawaye da ta tuna itama lokacin da za'a kawota seda tayi kukan rabuwa da mama, haka aka tafi da zeenat su anty shayida da anty zainab sukayi musu rakiya har gidansu yaseer sun samu kyakkyawar tarba a gidan suka miƙa amanar zeenat awajan hajiyarsu nan suka koma gida danzuwa dauko amarya suhaima.

Bayan sundawo ne aka kai fanan part din Mr azaad, sannan suka wuce dauko suhaima .

Yan uwa su mama ne da anty firdausi suka kai hairah ɗanƙararriyar gidan da baba ya ginawa ya usman komai anyiwa hairah irin na yan gata an ƙawata mata gidan ta gwanin kyau komai an mata shi itama seda tayi kuka da akazo tafiya da ita ta rungume mama tana kuka autama na kuka ,sosai sukayi musu godiya sosai ita da Hafiz , hardashi aka kaita gidanta amatsayinshi na yayanta kamar uba ya ke , seda yazubar da hawaye dayaga aljannar duniyar da aka kawo kanwarshi sosai shima yamata nasiha akan wanda mama da baba suka mata duk da bashida wani shekaru , basu jima ba aka barta ita daya agidan tana kuka haka suka tafi suka barta .

Zuwa su anty amina sukayi dan tafiya da suhaima itama tasha kukanta sosai dakyar aka raba ta da mama da umma rahina aka tafi da ita harda auta , duka amaren seda aka kai kowacce gidan ta, Amira kuma ita se bayan kwana biyu zasu wuce bauchi gida aka kawota , aka kaita dakin fanan.

Duk adaren angwayen suka angwance banda ya al ameen , zeenat ansha azaba angane shayi ruwane babu sunan wanda bata kira ba musamman ummi tasha kira kamar ba gobe , haka suhaima ma seda ta gommace kiɗa da karatu roko babu irin wanda batayiwa Fawwaz ba tun tana kiranshi da habiby har takoma kiranshi da sunanshi tana dukanshi shikam ko jinta beyi ba. Ya Usman ma ya angwance amma sanin hairah karamace shisa yabita ahankali sosai , duk da haka seda hairah tasha azaba tayi kuka harseda ta gaji ɗan kanta .

LOVE BIRDS

Seda yaraka yaseer tukun nan yadawo, fanan na part dinta tasha wanka tasa wasu arnayen kayan bacci ta watsa gashinta a tsakiyar bayanta yasauko har kugunta ga fatarta ta dake daukan ido jikinta na fitar da kamshi ga zanen lallen da aka musu tagama duk abinda zatayi tana zaune agaban mirror tana jiran dawuwar Mr azaad taƙagu yadawo domin tayi kewarsa sosai , toilet yashiga yayi wanka yafito daure da towel a kugunshi shafa lotion yayi ya fesa perfumes jin har lokacin fanan bata shigo ba yasa yanufi bedroom dinta yamurda handle din dakin dago kai tayi jin an bude kofar sauke idonsu sukayi acikin na juna atare suka sakarwa kansu tsadadden murmushi, shigowa yayi yaje gabanta yadagota tsaye yanabin kayan jikinta da kallo hadiye yawu yayi domin tashin farko yaji hankalinshi yatashi ga fitinannen kamshin turarenta dake dukanshi , zuba mishi oily eyes dinta tayi tana kallon murdeden jikinshi da ke tafiya da hankalinta ,ganin irin kallon da take mishi ne da sexy voice dinshi ya ce " what are you looking at ?" Matsowa tayi kusa dashi tadaura hannunta akan kirjinshi tana shafawa ta ce " am looking at this " tafada tana daga mishi gira kamar yanda yake yi mata , killer smile yayi ya ce " yau zaki biya bashin sati ukun da kika dauka tunda guduna kikayi " murmushi kawai tayi batace mishi komai ba,ɗurgusawa kasa yayi yasa hannunshi du ka biyu ya riƙo kugunta yadaura kanshi akan shamulallen cikinta sannan ya manna mata kiss, mikewa yayi yajuyar da ita yarungumeta ta baya suna kallon kansu amadubi maida gashinta gefe daya yayi , ya manna mata kiss agefen wuyan lumshe ido fanan tayi saboda wani irin shocking din datakeji , haka yadinga manna mata kiss ajiki kafin ya dauketa cak suka koma kan gado ya kashe wutar dakin yau tsabar za'a sa ke sabon angwancewa ma ko bedside lamp din be bari ba dan kar indauko muku bayani nima araina nace to dama so nakeyi in ganku ne nafito waje abuna.

Asuba ta gari

Yaseer dakyar ya iya shawo kan zeenat tayi shuru yakaita toilet ya gasa mata jiki yanaɗota a towel yasa mata kaya da hijab sukayi sallah , turo musu da breakfast hajiyarsu tayi , yayi feeding dinta sannan yabata pain relief , samu yayi ya rarrasheta tayi bacci shima yaja musu bargo suka koma bacci yana jin farin ciki mara misiltuwa.

Ya Usman ma yasha rarrashi kam awajan hairah dakyar ta bari yasata acikin ruwan zafi ya gasata se zuba mishi shagwaba takeyi , bayan sunyi Sallah naji ana yin knocking fita yayi yaduba yaga driver anty firdausi ne, turo musu breakfast anty firdausi tayi , sukayi breakfast yabata magani sannan yajata suka koma bacci .

Abangaren suhaima kuwa lallashin duniyar nan fawwaz babu irin wanda beyiwa suhaima ba amma har lokacin kuka takeyi ta na " hubby ashe dama ba sona kakeyi ba ? Jiya banyi tunanin zaka barni da raina ba rabani gida biyu fa kayi ko tausayina bakaji ba! yanzu nasan irin zaman da zanyi dakai " kokarin riketa yakeyi yakaita toilet yamata wanka amma fir taƙi ya tabata ganin takeyi kamar sakeyi zeyi , daga zaran yanufeta zata zabga mishi uwar harara , haka tamike tana dafa bango takai kanta toilet tahada ruwan zafi a jacuzzi tashiga ciki, ruwan na ratsata ta runtse ido hade da cize libs dinta tana kuka, seda tafarajin dama_dama tukun tacanza ruwa tasake komawa sau uku tana sa ke ruwa kafin tayi wanka tsarki tadaura towel tafito tana ɗingisa ƙafa, shide fawwaz yama rasa yazeyi da suhaima gashi yanason yataimaka mata amma ta tsayar mishi da rigima nufarta yayi ze dauketa ta ce " Allah hubby karka sake ka tabani" haɗe fuska yayi ya koma kamar bashi ba, nan ne tsananin kamar dasukeyi da Mr azaad yafito nan take tashiga rigar nutsuwa ya ce" in kika sakeyi mini musu sena sake round two " tundaga nan yasamu lafiya da suhaima tadena mishi gardama shiryata yayi yadauketa yadaura akan gado kamar karamar yarinya , sukayi sallah asuba , ji sukayi ana knocking yaje yabude abu me aiki yagani gaisheta yayi ta amsa tana mishi yagajiyar biki mika mishi basket din breakfast dinsu tayi ta nufi part din su Mr azaad, koma ciki fawwaz yayi ya serving dinsu sukayi breakfast suka koma bacci .

Suna kwance manne da junansu suna bacci hankali kwance dan tun bayan su idar da sallah suka koma bacci jin knocking yasa suka farka Mr azaad ya ce bari yaje yaduba , abu me aiki ce ta gaisheshi sannan tabashi basket din breakfast dinsu. Ajiyewa yayi a dinning yakoma suka ci gaba da baccin su.

Haka suka yini a shashin suna soyewa se bayan isha ne suka shirya cikin wankan atamfa suka tafi part din ummi saboda an shirya cin abinci dare , anaci abinci anata shan hira ummi se nan_nan takeyi da suirkan nata fanan da suhaima saboda sonsu takeyi sosai auta na gidan tun daren jiya da aka kawo suhaima sunzo tafiya ummi ta ce abarta anan aikuwa sukayi ta wasansu itada aslam da islam saboda dukkansu shekarunsu daya ne kansu daya , areef ne yazo yajasu zuwa part dinsu sukaje suka dinga biye musu shida hafiz dare yayi suka koma part din su kowa yaje ya kwanta.

Washe gari kuwa baki suka watse kowa yakoma garinsu, haka ya rage iya sune kadai agidan su anty amina duk sun koma gidajensu, haka su umma rahina ma sun koma Bauchi tare da suhaima bayan sun isa sun huta gajiya ya al ameen yadauki matarshi zuwa part dinshi dake cikin gidan komai akwai aciki na more rayuwa, shima aranar ya angwance.

Rayuwa me dadi sukeyi hankalinsu kwance agidan mazajensu , suhaima da fanan suna samun kulawa sosai awajen ummi musamman ma fanan dake da ciki haka suma kullum suna part dinta tayata hira dakuma yi mata girki , ga kulawar da suke samu agun mazajensu, cikin fanan yafara girma yanzu yakai wata shida Mr sosai yamaida attention dinshi wajan kula da fanan da abinda ke cikinta sosai take samun kulawa agidan .

Hairah anzama manyan mata soyayya suke sha ita da yaya usman dinta kamar bazaa mutu ba , abubuwa haka sukata faruwa lokaci nata tafiya , laulayin ciki hairah da zeenat suka fara aikuwa gwajin farko aka gano ciki ne dasu na wata daya Hajiya sosai take kulawa da zeenat, haka mama tasa ya Usman ya dawo da hairah gida saboda cikin na bata wahala tana laulayi sosai duk abinda tace takeso mama nayi mata shi .

Yanzu cikin fanan watanshi bakwai da sati biyu ayan kwanakin nan ciwon mara da ciwon baya yasata agaba amma haka take daurewa bata nunawa .

Adamawa Yola

Nusaiba ce da wata kawarta me suna ruma sa'u data kawo mata ziyara suna cikin hira ruma sa'u ta ce " ƙawata dama tun bayau ba nakeson infada miki wata magana amma bansan ya za ki dauki maganar ba " nusaiba ta ce " karki damu ƙawata faɗa kawai inajinki" Ruma ta ce " ƙawata yanzu Yakamata ace kin kwantar da wuya ki karbi aurenki , wallahi karki tsaya kallon ruwa gwaɗo yamiki ƙafa, kindega yanda duniyar nan yake yanzu kisamu wanda ze soka ya yi hakuri daduk wani halinka shima kyau ne daga Ubangiji , ya lukman wallahi namijine da ko wace ya mace zatayi fatan samu amatsayin miji , yana da hakuri sosai ga ka war da kai bashida matsala ko kadan amma ke kinsame shi se ranshi kunya da wulakanci kike mishi amma duk da haka yaci gaba da hakuri dake . Kina tunanin da wani na mijin ne zeyi toleranting wannan abinda kikeyi ne ? In za ki farka daga wannan rashin hankalin dakikeyi gwara ki farka , wallahi yana samun wata matar ze ƙyaleki yayi aurenshi kinga daga nan kuma kinyi biyu babu ke baƙi samu ya sakekin ba kuma ke awannan lokacin zaki rasa hankalinshi, wannan shawara ce nake baƙi tun kafin lokaci yakure miki " maganganun Ruma yayi matukar ratsa nusaiba lokaci daya taji danasani ya kamata se yanzu take ganin wautarta dukda wani lokacin tanayi mishi wasu abubuwan ne bawai da son ranta ba sosai tayiwa Ruma godiya domin ta nusar da ita inbadan itaba da yanzu bata gane gaskiya ba , bayan tafiyan Ruma nusaiba ta tashi ta gyara gidan tas tashiga dakinshi ta gyarashi sosai ,ta shiga kitchen tayi girki me rai da lafiya bayan tagama tajera a dinning ta kunna turaren wuta dama me aikinta ta tafi saboda ta ce bazata iya da halinta ba.

Wanka tayi taci kwalliya tasa lace ɗinkin riga da skirt ya kamata sosai tasha dauri tazauna afalo tana zaman jiranshi , tunda lukman ya tunkaro falon yaji kamshi na tashi shiga ciki yayi yaga ko ina tsaff tana , sauke idonshi yayi akanta tana zaune akan kujera, mikewa tayi ta nufeshi tana sakar mishi murmushi tasa hannu ta karbi brief case din hannunshi ta ce " sannu da dawuwa ya lukman" shide kallonta kawai yakeyi ɗan gani yakeyi kamar amarfaki ganin yana binta da kallon mamaki ne yasa tariko hannunshi zuwa bedroom dinshi shide binta yakeyi kamar raƙumi da akala taimaka mishi tayi yarage kayan jikinshi yashiga toilet yayi wanka yafito har lokacin mamakin nusaiba ya hana shi bude baki yayi magana , fito mishi da kayan shan iska tayi yasaka taja hannunshi zuwa dinning table tayi serving dinshi girkin da tayi mishi , dakyar lukman ya ce " nusaiba yau wani irin mafarki nakeyi haka " murmushi tayi ta ce " yayana ba mafarki kakeyi ba, kayi hakuri nasan nayi maka abubuwa da dama na bacin rai nasan na kuntata maka amma baka taba daga min murya ba Kaci gaba da hakuri dani tabbas kaiɗin mutum ne na gari ,kuma miji nagari da ya cancanci soyayya daga gun matarshi ,sannan kuma uba nagari dan Allah kayi hakuri kayafemin natuba " tafada tana ɗurgusawa agabanshi tana hade hannayenta waje daya, yasan maganar datayi dakuma tuban datayi na tsakani da Allah ne domin nusaiba bata da fuska biyu kuma bata iya karya ba dan ta farantawa mutum komi munin magana inde yazo bakinta zata fada maka shi kuma har cikin ranta amma yau jin wa'yannan kalaman nata yasa yagane gaskiyar ta kenan dagota yayi yadaurata akan cinyarsa ya ce" alhamdulillah my nusee nagodewa Allah dayasa kika gane gaskiya, Allah yabamu ikon farantawa junanmu " yafada yana manna mata kiss a kumatu rungume juna sukayi kowanne yanajin farin ciki aranshi.

Readers Also Read