Rayuwa da gibi na batul mamman - Chapter 4
Rayuwa da gibi na batul mamman Chapter 4: Rayuwa da gibi na batul mamman Chapter 4. Ƙuttt ya haɗiyi yawu sannan kamar mai taka iska ya bi su ciki. Ƙofar na…
3,336 words
Ƙuttt ya haɗiyi yawu sannan kamar mai taka iska ya bi su ciki. Ƙofar na rufewa gabansa ya sake faɗuwa. Sai dai duk wannan tsoron ya kau lokaci guda da ya ƙarewa kitchen ɗin kallo na kurkusa. Aiki kowa yake yi da sauri-sauri ga magana ana yi wadda ya fahimci karanto odar masu jiran abince ce ko bada umarni. A gefe guda kana iya ganin wasu suna ta jere plates ɗin da aka gama haɗawa a wani abin turawa za a fita da shi. Ga masu girki sun duƙufa suna yi. Wuta da mai da cokula sai chuu...chauuu su ke. Ganinsa ya ƙare akan masu yanke yanke kamar inji. Wasu su na yanka albasa, caras, da ma nau'ikan kayan lambun da bai taɓa gani ba. Wani haɗaɗɗen murmushi ya saki sai ga ƙaton mutumin ya dawo da tray shaƙare da kwanukan abinci.
"Eat."
Mutumin tsoro yake bashi amma duk da haka ya faɗa masa gaskiya "Am not hungry."
"Taste our food and we talk, okay?"
Juyawa ya yi yaga dattijon farko ne ya yi magana. Musu ma wuri yake samu. Karɓar tray ɗin ya yi babu shiri ya zauna a inda aka nuna masa. Ƙamshin abincin ya tafi da tunaninsa. Shinkafa ce da kaza. Ga kuma wani haɗin albasa, cucumber da tumatir da wani ganye mai tsami tsami da daɗi kamar kunne zai fita. Wani ɗan kwano mai zurfi a gefe kuma miyar naman sa ne wanda ya dahu ya yi luguf. Sai wani abu kamar bread ko gurasa mai faɗi. Abu ɗaya ya kula shi ne babu cokali. Ya ɗaga kai ya tambaya dattijon nan shi kuwa ya ce masa.
"We eat with our hands here."
Taj ya gyaɗa kai ya miƙe yace zai wanke hannu. Sink ya nuna masa ya wanko ya dawo. Yana zama ya yi Bismillah ya fara ci. Miyar ya ɗauka zai zuba a shinkafar da wani ɓangaren nata ya yi jaja-jaja, wani fari-fari, wani kuma yellow. Mutumin ya nuna masa ai gurasar nan ake ci da miyar. Shinkafar kuma ya zuba salad ya dinga haɗawa da nama. Ya tambayi sunan abincin aka ce masa chicken biryani ce da kuma chappati da beef curry (miyar).
Tunda ya saka hannu bai cire ba sai da abincin ya rage ɗan kaɗan. Yana ture plate kawai yaji mutanen kitchen ɗin suna ihu harda masu rungume juna. Ashe duk sun ankara da tsayuwarsa tun farko. Shi ne ogansu mai wurin ya shigo da shi. Farincikin fuskarsa a matsayinsa na wanda su ke da yaƙinin ranar ya fara cin abincinsu ne yasa su murna.
Sai da kowa ya nutsu aka cigaba da aiki sannan mutumin ya tambaye shi sunansa da dalilinsa na leƙensu.
"Kenan kana son girki" ya tambaye shi da turanci bayan ya yi masa bayani a taƙaice.
"Sosai."
"Ka taɓa yin makarantar girki ko ka koya daga wani professional?"
"A'a."
"Muna da makarantu a nan inda za ka iya yin degree."
Taj ya yi murmushi da ya hango fuskar Alhaji idan ya je gida da kwalin degree a fannin girke girke. Sanar dashi ya yi cewa karatu zai fara kuma banu damar canjawa.
"Idan ka tabbata kana da ra'ayi ni zan iya koya maka a nan. Ka je ka duba tsarin karatunka. Ranakun da baka da aji ka zo nan kayi aiki."
Baki ya buɗe da tsananin mamaki.
"Aiki?"
"Baka so ne?"
Da sauri ya ce yana so. Ya dai yi mamakin samu ne kafin ya nema.
Ƙaton mutumin nan ya sakar masa fuska ya ce.
"Dukkaninmu a haka yake ɗaukar mu aiki. Ra'ayin yi kawai zai gani daga gareka sai ya ɗauke ka yaronsa. Wurin nan nasa ne. Idan ka bada himma tabbas za ka ji daɗi. In kuma yaga baka da ƙwazo a wata ɗayan farko zai sallame ka."
Kamar wasa daga wannan rana Taj ya fara karatu kuma yana zuwa koyon aiki a ROYAL CUISINE. Abin farinciki shi ne kasancewar dattijon da ake kira Paaji (ɗan uwa ko yaya) musulmi. Yawancin ma'aikansa musulmai sun fi yawa ma. Komai na wurin halal ne. Sai da ya yi wata guda cur babu abin da ake koya masa a kwana ukun da yake zuwa duk sati sai sanin sunaye da amfanin kayayyakin abinci da kayan ƙamshi (spices). Hancinsa ya aikatu don ko abu na kama da ɗan uwansa idan bai tantance ba maimaici za ayi ta yi. Wasu abubuwan kuma a ido su na kama amma a zahiri ɗaya nada amfani ɗayan kuma guba ne. Dole suma sai ya gane bambancinsu don kada a bashi a kasuwa ya cutar da masu sayen abinci.
Bayan nasararsa a wannin fanin kuma aka koma koyon ɓare tafarnuwa da yankanta ƙanana. Kan kace meye wannan hannunsa ya cika da plaster. Irin wannan yankan na mugun sauri ake so ya iya. Da ƙwararre a wurin aka haɗa shi. Daga nan aka koma albasa. A haka, a haka ya ƙware a yankan kayan lambu da kayan marmari. Yankan nama ma zaman kansa yake. Sai da ya koyi haɗa mince meat ko babu na'ura da wuƙa kawai da ƴar muciya. Shekara guda ko mai ba a taɓa bari ya soya ba sai da ya zama zakara a fannin ƙananan ayyukan da su ne ƙashin bayan kowane girki.
Bayan an dawo hutu wanda yaje gida ya yi da kyakkyawan sakamakon ƙarshen shekara ta farko aka kai shi gaban wuta. Zo ka ga farincikinsa da na abokan aikin. Mutane ne ƴan asalin garin Punjab masoyan duk wani abu na farincikin al'umma. Su dai ayi nishaɗi a zauna lafiya. Shi yasa Taj ya saje cikinsu. Happy Taj su ke kiransa tun ranar da ya yi skype da Kamal su ka ji yana kiransa Happy. Da yake anfi samun ƴan ƙabilarsu mabiya addinin musulunci a Pakistan, shi yasa Paaji duk inda ya sami ƴan uwansa musulmi yake basu aiki. Taj da wani Uygur Chinese (wata ƙabilar musulmai a China) Aynur kaɗai ne baƙi.
A cikin shekara ukun farko Taj ya ƙware a girke girke da dama na yankin Asia. Banda na Indiyawa an koya musu na Larabawa da duk wani yankin Asia da su ka yi fice ta fannin abinci. Duk kuma wannan badaƙala ko sau ɗaya Ahmad bai taɓa sani ba har ya gama ya koma gida. Taj ya ci karensa babu babbaka ya haɗa riba uku a zaman nasa. Bai manta da ƙudurinsu na bitar hadda ba shi da Kamal shi yasa ya shiga wata makarantar ƙarshen mako da ake yi a masallaci. Kamal ne kaɗai ya san me yake ciki kuma ya bashi goyon baya tare da nanata masa mahimmanci barin abin a matsayin sirri.
A kwana a tashi ba wuya a wajen Allah. Taj da Kamal sun ƙarƙare karatunsu a cikin shekara uku da ƴan watanni. Kowanne akwai taron convocation da za ayi a makarantarsu. Kamar yadda aka fara kai Kamal, ranar nasu taron ta zo sati uku kafin na su Taj. Alhaji sai ya ɗauki Hajiya da Umma su ka tafi Dubai. Satinsu biyu a can su ka koma gida tare da Kamal ɗin. Bayan kwana huɗu ya juya da Ahmad, Mama da Inna zuwa India.
***
Gagarumar gasar girki ce Culinary Academy of India ta saka domin samun zakarun da za ta bawa tallafin yin karatun degree na tsahon shekara uku a fannin Catering Technology and Culinary Arts. Makarantar reshe ce ta Jami'ar da ya kammala wato Osmania University. Kuma ɗalibanta ta buɗewa gasar masu ra'ayin girki waɗanda ba ƴan asalin ƙasar ba. Paaji na samun labari ya saka shi a gaba a gaban kwamfutar restaurant ɗin nasu ya cike komai online. Abokan aikinsu su ka yi ta murna domin da fari har ya soma yi musu sallamar komawa gida da zarar an yi convocation.
A kwana biyar za ayi komai a gama. Taj bai san da tahowar su Alhaji ba kamar yadda Kamal bai san ya shiga gasa ba. So ya yi ya yi surprising ɗan uwan nasa. Wanda kuma da ya faɗa masa zai gargaɗe shi da tahowar tasu. Duk wayarsu da gida ana ta ɓoye masa don an san ba ƙaramin farinciki zai yi ba idan su ka zo. Tahowar Ahmad kawai ya sani saboda zai zo registration na masters tunda ya gama bautar ƙasa.
Sun iso ƙasar awa guda kafin a shiga gasar a rana ta huɗu wadda ta kasance alhamis. Zuwa yanzu team ɗin Taj da aka haɗa da wani banufe ɗan Nigeria mai suna Wakili su ne su ke jan ragamar muƙami na biyu. Wasu wa da ƙani ƴan Indonesia kuma a sahun farko. Wayarsa Ahmad ya kira ya faɗa masa sunan hotel ɗin da su ka sauka.
"Yaya ka daure ka ƙaraso Uma Nagar cikin Culinary Academy." Ya ce da farincikin isowar ɗan uwansa.
Don dai yau ɗaya yana ganin ba komai bane idan an sani. A tunaninsa nasararsa ta karatun da Alhaji yake so za ta sa ya bashi damar cika nasa burin.
"Me ake yi?"
"Gasar girki na shiga."
Gefe Ahmad ya matsa hankali a tashe.
"Ashe ba ka da hankali Taj? Tun yaushe Alhaji ya soke maganar nan?"
Da yanayi na ban tausayi Taj ya ce "Yaya ina so wallahi. Domin neman amincewarsa na dage sosai a makaranta. Kana ganin yanzu ba zai sauko ba tunda nayi karatun da yake so?"
"Baka da hankali." Ahmad ya sake faɗi yana jin zufa na karyo masa.
Duk abin da yake yi hankalin Alhaji dake magana da su Inna yana gare shi. Sauke wayar daga kunnuwansa ke da wuya yaji ya ce masa,
"Me ku ke ɓoyewa da har za ka tashi ka dawo nan?"
"Babu komai Alhaji. Ya ce min baya hostel ne."
Rashin gaskiya ya gani ƙarara a fuskar ɗan nasa shi yasa ya ce, "Kai ni inda yake!" RAYUWA DA GIƁI 5
Batul Mamman💖
"Alhaji..."
"Zan saɓa maka."
Ba yadda ya iya. Cikin minti shabiyar ya sama musu tasi su huɗu suka kama hanya. Mama da Inna ba su san me ake ciki ba. Shi kuwa Alhaji tunda yaga sunan makarantar a bakin gate jikinsa ya soma tsuma. Ahmad dai jikinsa duk ya mutu. Ya yi kiran Taj ɗin da su ka shiga bai ɗauka ba. Da tambaya su ka ƙarasa wurin da ake gasar inda mutane su ka yi dafifi kamar ƙudaje. Basu wani sha wahala ba su ka hango tebura huɗu na ƙasashen da su ka rage a gasar. A yau za a fitar da wani team ɗin sai ya rage uku. Washegari idan an yi na ƙarshe a fitar da na ɗaya, na biyu da na uku.
Cikin wata irin nutsuwa da tsantsar ƙwarewa Taj yake aiki. Shi da Wakili girkinsu cikin tsari yake kamar sun manta da lokacinsu na tafiya. Wannan nutsuwar ita tafi burge alƙalan gasar. Masu sauri saurin cimma lokaci kuwa daga kwano ya faɗi ya fashe sai ka ji su na washhh, mai ko ruwa mai zafi ya fallatso mu su saboda garaje.
Tunda Alhaji ya yi tozali da ɗan nasa wani abu mai masifar ɗaci ya sami wurin zama a maƙogaronsa. Taj yake gani sanyi da dogon wando baƙi da riga yellow mai tambarin makarantar sai apron fari tas ɗaure a ƙugunsa. APRON!?
Inna kuwa tamkar wadda aka watsawa ruwan zafi. Tunda ta nunawa Mama shi bata sake iya cewa komai ba. Maman ce ma ta iya yin magana da ƙyar.
"Ahmad me idona yake gani?"
"Gasar girki ce" ya bata amsa a sanyaye.
"Ku zo mu koma." Alhaji ya ce da matansa "Kai kuma ka jira ya gama ka taho min da shi."
Ahmad ya so raka su amma ya nuna masa yawo a ƙasar da ba tasu ba, ba baƙon abu bane gare shi. Haka su ka tafi babu mai cewa komai. Da isarsu Alhaji ya ɗauko magungunansa na hawan jini ya watsa sannan ya ce kada wanda ya tashe shi sai Taj ya iso. Dama ɗaki uku ya kama musu. Sai su ka koma ɗayan.
Ido cike da ƙwalla Inna ta ce "Yaron nan so yake ya jaza mana tashin hankali ko me?"
Kallonta Mama tayi ta girgiza kai.
"Matsi da takura yaro bai fiye haifar da ɗa mai ido ba. Taj ya yi masa biyayya an sami abin da ake so. Mene ne aibu don ya ɗan waiwayi burinsa? Don fa mun haife su ba yana nufin dole su rayu kwatankwacin tamu rayuwar ko ra'ayi ba."
"Kayya dai Mama. Rayuwar yara sai da nuna hanya daga iyaye."
"Nima ban musa ba. Amma babu inda addini ya bawa iyaye damar tauye ƴaƴansu akan abin da bai saɓawa addinin ba. Baki ji malamai suna faɗin ko sakin aure indai ba bisa adalci ba, iyaye basu da hurumin tilasta shi ba? Girkin nan kuma maza nawa ke yi? Mene ne aibu a ciki tunda ba daudu yake ba?"
Inna dai duk a tsorace take ta ce "tunda mahaifinsa ba ya so sai ya haƙura ko don neman albarka."
Mama gani tayi cigaba da nunawa Inna illar takura tayi yawa ga ɗa mai biyayya bata da amfani ba sai taga Innar ta kasa fahimta. Idan ta matsa kada abin ya yi kama da tana son sanya shi yin bore. Zaman jiran tsammani su ka yi har bayan Isha.
* Sakamakon gasa yau dai da su Taj ya tashi. Cikin nasara da taimakon Allah su ne su ka yi na ɗaya. Yawan makinsu idan an haɗa da na kwanakin baya ya basu damar iya yin na ɗaya gobe in sun dage. Banda ihun murnar ƴan Nigeria da su ke makarantar ba ka jin komai. Yanzu ya rage teams uku. Gobe za a fitar da na ɗaya, biyu da uku. Da su ka fito za su tafi Wakili ya tare shi da godiya.
"Ban san a ina ka koyi girki wanda yasa talent ɗinka ya zarce na kowa a nan ba. Your are truly amazing."
Taj ya yi murmushi "ai ban kai ka ba."
"Magana ta gaskiya ake yi. Idan muka yi nasara na san albarkacinka na ci. Saboda haka ina roƙonka don Allah gobe ka dage fiye da kullum. Samun karatun ya fiye min akan kuɗin da za a bawa na biyu ko na uku."
Murmushi Taj ya sake yi da alƙawarin in sha Allahu gobe zai yi bakin ƙoƙarinsa.
Da tallafin gwamnati Wakili ya sami tahowa karatu. Ya gama degree kamar Taj amma yana tsoron komawa gida yanzu. A ƙauye su ke. Gashi samun aiki yanzu ya koma wa ka sani, wa ya san ka. Tunda yana aiki a wani gidan abinci a nan yana samun abin turawa mamansa da ƙanne ba zai so ƙarewar visa yasa shi komawa gida a sake naɗe hannuwa ba.
*
Murnarsa ta koma ciki da Ahmad ya faɗa masa tare da su Alhaji su ka zo akan hanyarsu ta zuwa hotel ɗin.
"Yaya don Allah kada ka sanar dashi zancen competition ɗin nan."
Cije leɓe Ahmad ya yi wanda yasa Taj tambayarsa ko ya faɗa hankali a tashe.
"Tare mu ka shiga inda ku ke girkin. Ya riga ya gan ka."
Bayan karanto duk wata addu'a da ya sani ta neman sauƙi, bai sake cewa komai ba har su ka isa hotel ɗin. Kai tsaye ɗakin Alhaji su ka je su ka tarar da Inna da Mama a zaune jigum. Jikin Alhaji har ya soma tsananta saboda damuwar da ya sanya a ransa.
Wuri ya samu kusa da Mama ya zauna jikinsa a matuƙar sanyaye. Shiru yana jira a fara yi masa faɗa amma babu wanda ya yi magana. Cike da fargaba ya rarrafa gaban Alhaji kai a ƙasa.
"Don Allah..."
Tassss. Alhaji ya tsinke shi da marin da ya gigita shi. Inna tsam ta miƙe ta fice daga ɗakin don ba za ta juri gani ba. Ko da ta koma ɗaya ɗakin fashewa tayi da kukan da bata san na mene ne ba. Tana tausayin ɗanta. Tana kuma son ya sami damar cikar buri sannan kuma tana so ya yiwa mahaifinsa biyayya.
Sake ɗaga hannu Alhaji ya yi zai kuma marinsa cikin zafin nama Mama ta riƙe hannun da sauri.
"Ka dubi Girman Allah kayi haƙuri."
"Ki sakar min hannu" ya miƙe tsaye da fushin da yafi na farko yana mai fincike hannunsa.
"Haba Alhaji. Mene ne aibun girki a wurin namiji da har za ka kasa bawa yaron nan damar cikar burinsa."
"Buri? Buri fa ki ka ce A'i?" Ya nuna ƙirjinsa "ɗan cikina ki ke so na bari ya yi daudu?"
A hasale ta bashi amsa saboda har ga Allah tana ganin da gangan kawai yaƙi fahimta balle ya sassautawa ɗan.
"Mece ce alaƙar girki da daudanci? Maza nawa ka gani da wannan sana'ar kuma ba su lalace ba? Ka kyautata masa zato mana ka bi shi da addu'a."
"Ni ki ke ɗagawa murya?"
Ko ɗar bata ji ba ta ce "Gorin haihuwar namijin za ka sake yi min?"
Ahmad ya fice kiran Inna. Taj kuma jin yadda rigima take son tasowa tuni ya dawo daga duniyar raɗaɗin marin da aka yi masa.
"Mama bashi haƙuri mu fita." Ya durƙusa a ƙasa "in sha Allahu nima ba zan sake tada maganar nan ba."
Hannun Mama ya ja su ka haɗu da Inna tana dawowa ɗakin da jan ido. Ganin sun fito ita ma ta bi bayansu ita da Ahmad.
Kamar wancan lokacin yanzu ma nasiha game da mahimmancin yiwa iyaye biyayya su ka yi masa. Ya kuma karɓa hannu bibbiyu da zuciya ɗaya.
Ƙarfe goma da rabi na dare saƙon Wakili ya shigo wayarsa. Tuni akan fitowa da wuri ya soma yi masa. A ƙarshe kuma ya yi rubutu kamar haka.
"...My mum said we should keep reciting this Du'a tonight being friday night and tomorrow when the competition begins. RABBI INNI LIMA ANZALTA ILAYYA MIN KHAIRIN FAQIR. I will continue to thank Allah for bringing you my way no matter the outcome. Working with a pro like you is truly an honour. Thank you Happy Taj."
Duk iya sata ta bacci daidai da sakan guda Taj bai runtsa ba. Shaf ya manta ba shi kaɗai bane a gasar har ya yiwa su Inna alƙawarin haƙura. Gashi daga cikin dokokin gasar duk wanda abokin girkinsa bai zo ba har aka fara da minti goma sha biyar sun zama disqualified. Anya zai iya samun kwanciyar hankali idan ya zama sanadiyar rugujewar rayuwar wani?
Kafin asuba babu irin tunanin mafitar da bai yi ba. Yana idar da sallah ya fice daga hostel zuwa hotel ɗin su Alhaji. Bai tsaya neman abin hawa ba saboda ƙarancinsu a wannan lokacin. Sannan babu wata tazarar azo a gani ma. Da gudu gudu ya isa yana faman haki. Kai tsaye ɗakin Ahmad ya fara zuwa. Da ba a buɗe ba ya durƙusa a bakin ƙofar yana mayar da numfashi.
Zaman kimanin minti shabiyar ya yi sannan Ahmad ya dawo.
"Lafiya me ya fito da kai da asussuba haka?"
"Alhaji yana ɗakinsa? Ya tashi?" Taj ya tashi ya ma manta da gajiyar jikinsa.
Yanayinsa na rashin nutsuwa Ahmad ya fara dubawa kafin ya shige masa gaba zuwa ɗakin Alhajin. Shi kaɗai ne a ɗakin don matan nasa sun yi yaji saboda abin da ya faru jiya. Sanye yake da farar jallabiya yana fitar da daddaɗan ƙamshin turaren larabawa. Gemunsa mai sirkin fari-fari da baƙi ya ƙarawa fuskarsa kwarjini. Kamanninsa da samarin ƴaƴan nasa ta sake bayyana.
Gaishe shi Taj ya yi ya faɗi buƙatarsa kai tsaye. Ahmad na ji ya fita da sauri ya kira su Inna don su dakatar dashi kafin maganar ta lalace. Sun shigo daidai lokacin da Taj yake cewa,
"Ba don kaina nake son zuwa ba. Nayi maka alƙawarin ko na nawa mu ka yi ba zan karɓi komai daga gare su ba. Izini kawai nake nema kada rashin zuwana ya zama silar rushewar ...."
"Tajuddin!"
Durƙusawa ya yi duk da kiran sunan nasa ya kiɗima shi cikin ƙanƙan da kai ya shiga magiya kafin ma ya ji me Alhajin zai ce. Wannan ya ƙara tunzura mahaifin nasa sosai.
"Indai ni zan yi maka izini to ka sani har abada ba zan taɓa yarje maka ka sake tsayuwa gaban murhu ba. Allah Ya yi min rufin asirin da ko mata cikin tsatsona ba za su nemi kuɗi da girkawa wasu abinci ba balle kuma namiji."