Kenza eBookz

Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 10

Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 10

Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 10: Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 10. Bini-bini waya da Ibrahim da Jidda har dai ta kai ta…

3,346 words

Bini-bini waya da Ibrahim da Jidda har dai ta kai ta kawo yana zuwa hirar tsakanin magriba da isha, a hakan Aliya ta sha yanka masa magana wai laila ta ƙiya an koma caca. Ranar da ya zo ma kayan gwanjon ya sako abinsa, bayan Jidda ta koma gida Aliya take cewa wai wannan mai zuwa wajen nata matsiyaci ne.

*BAYAN SATI GUDA*

Ana ƙoƙarin kawo kayan saka ranar Aliya sai gobe, sai Ibrahim ya sanar da Jidda cewa zai aiko in ta amince duk da basu daɗe da haɗuwa ba, ita kuma ta yarda da shi ta yaba da halayyarsa don haka ta amince cewa ya aika a samu Abban nasu, lokacin da ya sanar da su Mummy cewa ya samu wacce yake so sun yi matuƙar mamaki sun yi murna ƙwarai . Daga haka ne ma ya samu damar saka kayan gwanjonnsa babu ɓoye-ɓoye ya ce saboda yana son ya auri mai sonsa da gaskiya ne ba wai don dukiya ba, basu san cewa yana amfani da kayan va ne saboda ita wacce yake so ɗin kuɗin basa gabanta.

Ya fahimci Jidda tana son ss duk sa ya san nasa son ya linka nata. Bai san dalilin da ya kore mata ƙuduri da burin auren kyakkyawa ba.

Tun da yake zuwa ko biyar bai taɓa bata ba, ko da Ibrahim ya sanar da ita za a je gaisuwar iyaye ta faɗawa Umma a kan ta sanar da Abba saboda tana jin kunya Umma ta ce

"Shi ma dai wannan zai kwasawa kansa jangwam, ko don talaka ne ai dama talaka ya saba da wahala" Jidda bata ji daɗin maganar ba amma babu yadda za ta yi.

MAMAN AFRAH

09025576222

[10/18, 9:27 AM] MOM MASHKR & AFRAH: https://chat.whatsapp.com/C12RFYqXnWf36AhjVZWDw4?mode=ems_copy_t

*RUWA CIKIN COKALI*

(Ya ishi mai hankali wanka)

NA

MAMAN AFRAH

. *Daga marubuciyar*

*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*

*09025576222*

BOOK 1

PAGE 8️⃣

*SADIYA*

Tana yin sallar asuba ta fita ta hura gawayi ya kama ta ɗora ruwan zafi, tuwon masara ta tuƙa wanda Nasir ya bata garin ta yi miya ta gama ta ɗora ruwan ɗumi ta dawo ta fara gyaran falon, lokacin ƙarfe bakwai da arba'in. Bayan ta kammala lokacin Nasir ya taso ya shiga wanka ya shiga bedroom ɗin zai shirya lokacin tana gyaran gado yana kawo kai ya ce

"Sadiya warin mene ne a ɗakin nan? Yanzu da girmanki kike sakarwa mutane tusa a ɗaki gabaɗaya ɗaki ya ɗumi da wari?" Ya faɗa yana saka hannu ya toshe hanci yana mata wani kallo. Ɗagowa ta yi daga sunkuyen da ta yi tana totsa zanin gadon sai lokacin ita ma ta ji ɗakin ya haɗe da wari cike da ladabi ta ce

"Haba Abban Kalifa tun da nake a gidan nan ka taɓa jin warin tusata?" Bata bashi damar magana ba ta ɗora da faɗin

"Wannan ba halayyata ba ce gaskiya sai dai ko Kalifa ne ya yi" Bai amsa mata ba ya ɗauki kayansa a drower ya ɗauki man shafawa ya fita falo a daidai nan Kalifa da ya yi juyi ya tashi zaune sai ta ji warin ya tsananta hakan ya sa ta fara tunanin ko kashi ya yi, net ɗin ta cire tana dubawa kuwa sai ta ga kashi ya yi gabaɗaya kashin har ya ɓata shimfiɗar, Kalifa ya ce

"Momma ruwa" Ta ce

"To Kalifa kalli kashin da ka yi duk ka mata shimfiɗa wannan kashin haƙorin naka da yake baka wahala ne ya dawo maka" Ta faɗa tana ɗago shi ta fito da shi, suna zuwa falo tana dab da fita a zuciye Nasir ya ce

"Sadiya mene ne wanann wai? Mai ya sa kike son shiga rayuwata kike hanani sukuni, kin cika ɗaki da wari na fito falo sannan kin kawo min wari falo" Ranta ne ya sosu da furucin sa tana riƙe da yaron ta ce

"Shin ni na yi kashin?" Tambayar da ta masa sai ya ga ta raina masa hankali hakan ya sa ya ƙara ƙufula, ganin bai ce komai ba sai ta juya ta saka silifas ɗinta ta kai Kalifan waje ta tsayar da shi, dawowa ta yi ta kwashe shimfiɗar ganin kashin bai taɓa katifar ba sai ta fito da kayan waje, wankewa Kalifan ta yi ta juye ruwan zafin da ta ɗora ta masa wanka tas. Kayan ta wanke ta shanya kafin ta ɗakko Kalifan suka dawo ɗaki turaren tsinke ta kunna duk da zuwa lokacin ma warin ya fita dama saboda kashin haƙori yana da wari ne, kaya ta sakawa Kalifan sai kuwa ya fito falon wajen uban yana ƴar dariyarsu ta yara ya je gaban Nasir da yake danna waya ya ce

"Abba" Nasir bai amsa ba fitowar Sadiya sai ta ga Kalifan yana tsaye a gaban Nasir ɗin ne ya ɗora hannunsa a kan gwiwar Nasir ɗin.

Kalifa ya sake cewa

"Abba" Maimakon ya amsa sai ya ɗago daga dannar wayar da yake ya ce

"Sadiya ni kika cewa wai ke kika yi kashin?" Sadiya da take tsaye ta zauna a kujera ta ce

"Wannan maganar da ta wuce mene ne na dawo da ita?"

Nasir ya ce

"Ban da shashanci da rashin sanin ciwon kai a ce yaro yake kashi a kwance wannan ai sangarta ce, ke ce baki koya masa ba amma sauran mata da suke da tarbiya ai suna koyawa ƴaƴansu abubuwa" Baki sake take kallonsa kamar ba za ta ce komai ba sai kuma ta ce

"Yanzu yaro ɗan shekara biyu ne za a ce wai ba a koya masa tarbiyar kashi a kwance ba, shin kana ganin yana kashi a kwance idan ba na jinya ba, wanna fa kashin haƙori ne, kuma ko da a ce akwai famfas a jikinsa kashin zai iya fitowa saboda wani lokacin ko famfas ba ya riƙe shi, wai don Allah Nasir mai na maka a rayuwa? Mai ya sa koyaushe cikin neman laifukana kake don ka hukuntani, komai na yi ban iya ba, mai ya sa ban taɓa birgeka a rayuwa ba duk abin da zan yi kuwa... Wani dogon tsaki da ya ja ne ya sa ta maƙale sauran kalamanta, ga haushin bai yi wa Kalifa magana ba sai ta ce

"Kalifa zo nan" Juyowa Kalifan ya yi ya kalle ta amma bai je ba ya sake buga gwiwar uban ya ce

"Abba" Ajiye wayar Nasir ya yi ya kama hannun Kalifan duka biyu ya ce

"Na'am Kalifa" Wani irin washe baki Kalifan ya yi da alama ya ji daɗin hakan. Sadiya kuwa sai ta ji sanyi a ranta ganin walwala a fuskar yaron ta.

Nasir ya ce

"Kalifa kai da jiya ka tafi ka barni, ka tafi gidan kakanka wuni kuma ya koro ku" Ya faɗa yana dariya, sosai Kalifan yake dariya da alama ya ɗauka wata kalma mau daɗi ce abinka da yaro, Sadiya kuma sai yanzu ta gane cewa ya yi haka ne don ya baƙanta mata zuciya, kuma cin fuska ne yake mata kai ta sunkuyar sai Nasir ɗin ya ce

"Maza je a zuba maka tuwo" Yana ta dariya ya juya zuwa wajen Sadiya, ɗago kai ta yi ta kalli Nasir ya sakar mata wani murmushin gefen baki tare da ɗaukan wayarsa ya cigaba da dannawa, ta rasa mai ya sa Nasir in dai zai ga walwala a fuskarta sai ya san yadda ya yi ya daƙusar da ita, ya fi so ko yaushe ta kasance cikin ƙunci.

Fita ta yi ta zubo musu tuwo ta ajiyewa Nasir, shi ma Kalifan ta ajiye masa har zai zauna ta ce

"Baka cewa Abbanka ina kwana ba"

Da sauri ya masa yana washe baki ya ce

"Abba nawana(Ina kwana)" Amsa masa ya yi ya koma ya fara cin tuwon bayan ta sa ya yi bismilla da bata fita a bakin ba.Bayan ya gama ci ta wanke masa hannu suna shirin juyowa zuwa ɗaki sai kawai ta ji ƙaran kashi sai ganinsa ta yi kamar ruwa yana biyowa ta ƙasan wandon sai Kalifa ya ce

"Momma foo" Haka ta cire masa ta wanke masa ta ɗora shi, wandon ta wanke ta wanke masa ta ɗauke foo ɗin tana taɓa jikinsa ta ji zafi sosai zazzaɓi ya rufe shi, haka ta ɗakko shi ta dawo da shi ta saka masa wandon ta kwantar da shi.

Nasir da ya gama zai fita kasuwa ta kalle shi ta ce

"Ina son zan kai Kalifa asibi... Tun bata ƙarasa ba ya ce

"Sadiya baki san wahalar da maza suke sha ba a wajen neman kuɗi ko? Wato daga yaro ya yi kashi sai ki ce wai za ki kai shi asibiti to ni bani da kuɗi idan kuma har kinnga sai kun kai shi ga hanya nan ba zan hana ki ba, amma naira biyar tawa ba za ta yi kuka ba"

Kamar za ta yi kuka ta ce

"Wallahi yanzu ma jikinsa zafi kuma kashin fa ya sake yi kar ya ci ƙarfinsa don All... Bata ƙarasa ba ta ji ƙaran aman Kalifan dama haka yake jinyar haƙori kashi da amai ga zazzaɓi kansa zafi.

Bedroom ɗin ta nufa, tana zuwa duk ya kelaya amai haka ta ɗane kayan shimfiɗar ta goge masa bakin gabaɗaya har jikinsa ya yi sanyi alamar abin ya fara ci ƙarfinsa.

Tana fitowa falon ta ga Nasir ya kara waya a kunne, Nasir kuwa mahaifiyarsa yake kira. A can gidan su Nasir mahaifiyarsa ce Hajiya Mariya wacce suke kira da Hajiya suna zaune ita da yaranta ƙannen Nasir ɗin guda biyu Husna da Hibba karyawa suke dankalin turawa ne da wainar ƙwai sai shayi mai kauri da kuma farfesun kifi suna ci suna hira wayar Hajiya ta yi ƙara ɗagawa ta yi ta ce

"Hello Nasir" Nasir ya ce

"Hajiya ina kwana" Amsa masa ta yi tana faɗin ga abincinsa ya amsa mata da gashi nan zuwa sai ya ce

"Kalifa ne yake kashin haƙori da amai da zazzaɓi shi ne Sadiya ta ce za ta kai shi asibiti"

A harzuƙe Hajiya ta fara faɗa tana cewa

"Wai Nasir sau nawa zan faɗa maka cewa wasu matan munfukai ne, suna faɗar jinyar ƴaƴansu ne kawai don su tatsi kuɗin miji, wato ta ɗauka kai sokon namiji ne to ahir ɗinta wallahi wani kashin haƙori ne za a kaiwa likita to likita ya bashi mai, sau nawa zan faɗa maka laulayin haƙori ba ya jin magani, shi ne za a wahalar da kai a yaudare ka ai wallahi ɗana ya fi ƙarfin mace ta ci kuɗinsa rabu da ita naira ɗari ta isa ta biya buƙata zan bada maganin a kai mata" Sosai ya ji wani daɗi a ransa yana son yadda mahaifiyarsa take taya shi tattalin kuɗinsa, ya gama wayar lokacin ta dawo falon ya kalle ta a wani wulaƙance ya ce

"Hajiya ta ce za ta bada maganin a kawo" Sai da ta kai zuciyarta nesa sannan ta ce

"To"

Store ya je ya ɗakko shinkafa da wake daidai wanda yake bayarwa a dafa ya kawo ya bata ya juya ko sallama bai mata ba ya fice ya banko ƙofar gidan. Shiru ta yi tana ta tunanin rayuwarta a ce kai baka da wata kima ko daraja a wajen miji bare ƴan uwansa ɗanka bashi da wata daraja yanzu a ce ɗansa bashi da lafiya amma ya hana a kai shi asibiti sai mahaifiyarsa ce za ta ce masa za ta bada maganin, kwanciya ta yi a kusa da Kalifa tana ta tunani.

Zuwa can ta tashi ta fita ta fara wankin banɗaki tana cikin yi ta fara jin ƙaran wayarta, kafin ta zo har kiran ya katse wani ya shigo, tana ta tunanin ko lafiya sai ta ga sunan Babanta gabanta ne ya faɗi ta fara tunanin Allah sa alkairi ne.

Jiki sanyi ƙalau ta ɗaga wayar ta gaishe shi ya amsa tana jin muryarsa raɗau babu alamun damuwa hakan ne ya bata tabbacin babu wata damuwa ko matsala.

Baba Ya ce

"Sadiya kiranki na yi in ce ki tayani godiya wajen mijinki kai Allah sakawa Nasir da alheri" Shiru Sadiya ta yi sai dai bata bayyanawa Baba mamakinta ba ta ce

"Godiyar mai Baba?"

Baba ya ce

"Ka ji yaron arziƙi ashe ma bai faɗa miki ba, shi ya sa fa ake so in mutum zai yi alheri ya yi tsakani da Allah ba sai wani ya sani ba, shi ya sa aka ce hannun hagu kar ya san na dama ya miƙa" Sadiya ta ce

"Haka ne Baba"

Baba ya ce

"Wallahi Sadiya wayata na ji tana ta ƙara ina dubawa na ga mijinki ne bawan Allahn nan na gaishe shi" Wani ƙululun baƙin ciki ne ya tsayawa Sadiya jin Baba ya ce wai shi ya gaishe shi ba ma Nasir ɗin ne ya gaishe da Baban ba.

Baba ya ci gaba da faɗin

"Kawai bayan ya amsa gaisuwata sai ya ce Baba ka tuwo akawun lamba, bai jira na ƙara magana ba ya yanke kiran, ni kuwa ban yi bori da sanyin jiki ba na kwashe lambobin akawun ɗina na tura masa, ina turawa na kira shi ban san lokacin da na ce ranka ya daɗe na tura ba" A take hawaye suka fara sartu a fuskarta wai Baban ne ya cewa sirikinsa ransa ya daɗe saboda kawai ya ji maganar kuɗi wannan wace irin zubar da kima ce.

Baba ya ce

"Da to ya amsa min ya kashe ana jimawa sai ka dubu ɗai-ɗari dubu na dukan dubu har dubu goma ya ce in ɗauki dubu biyar in ba tsohuwarki dubu biyar, na rinƙa masa godiya, yanzu dai na bata dubu uku ni na ɗauki bakwai shi ne na kira ki kema ki tayani gode masa, yaron arziƙi ai ke da shi sai mutuwa ce za ta raba"

Sadiya a zuciyarta ta ce

',In sha Allah ba zan mutu a gidan Nasir ba ina saka ran wataran zan fita daga wanna rayuwar marar ƴanci rayuwa marar galihu, rayuwa marar daraja' A fili kuma ta ce

"Amma na ji daɗi Allah saka masa da alkairi kuma in ya dawo zan yi ta gode masa tare da yaba masa" Haka Baba ya mata sallama cike da jin daɗi. Tana ajiye wayar za ta juya wani kiran ya shigo, ta ɗauka Baban ne amma tana dubawa sai ta ga Mama ɗauka ta yi bayan sun gaisa ta ɗauka Mamar za ta tambaye ta yaya aka ƙare jiya da ta dawo ko dai wani abu makamancin haka, ko ma dai ta tambaye ta damuwarta kamar yadda ta je mata da ƙorafin jiya ko ba komai sai ta lallashe ta ta tausasa mata yadda za ta rage mata raɗaɗi a matsayinta na uwa amma sai ta shiga faɗa mata alkairin da Nasir ɗin ya musu tana ta msta godiya da musu fatan haɗin kawunansu, haka dai Sadiyar take bata amsa cikin ƙarfin hali daga ƙarshe suka yi sallama.

Tana kashe wayar ta koma ta zauna daɓas tana tunanin kenan dai Nasir ya ƙara ƙirƙirar wata hanyar toshe duk wata ɓaraka, ita tana gidan yana musguna mata ko kuɗin kai ɗanta asibiti bai bata ba gashi a can kuma yana bajinta wato zai wanke laifinsa ko da ta je musu da magana ba za suke amincewa ba, tun da suna masa kallon mutumin kirki wannan alama ce ta sun zaɓi farincikin ɗan wani a kan farin cikin nasu ƴar!.

*JIDDA*

Ranar da aka kawo kayan saka ranar Aliya da yamma, guɗa ƙawayen Umma suka cika gida da shi Umma tamkar za ta zuba ruwa a ƙasa ta sha, saboda ganin kowacce a wajen ana kawo mata kayan saka rana sallayoyi dabino, kuɗi, wasu ma kuɗin ake kai musu amma sai gashi Aliya har da ƙaramar akwati wannan dalilin ya sa maƙota suke ta zuzuta abin har kan Mama da Aliya ya fashe. Da dare bayan an watse Aliya sai gwada takalman take tana wani bada faɗi a tsakar gida lokacin Abba baya nan yana waje tare da baƙi sai murna Aliya take tana cewa

"Umma na wuce raini a unguwa, na kere sa'a wallahi Kasim yana matuƙar sona, ya kankaro min mutunci a wajen ƙawaye irin wannan takalma kala goma atamfofi kala biyu da turaruka ina ga in aka ga lefe ai ina jin ƴan baƙin ciki sai sun zauce" Ta faɗa tana ɗaga murya.

Umma ta ce

"Aliya kin yi sa'ar miji, mijin nunawa sa'a mijin bugar ƙirji ki nuna a ko jna saboda duk namijin da aka ce miki zai iya bugun ƙirji ya faranta miki to tabbas yana da kyakkyawan buri idan ya samu maƙudan kuɗi ina ga sai kyautar miliyoyi" Suka kwashe da dariya duk abin da suke Jidda tana ji don ita tun da aka kawo kayan da aka buɗe a gaban mutane ta gani bata sake gani ba, don ko bayan mutane sun watse da ta je ta fara ɗaga takalman Umma ta ce

"Jidda kar ki ƙara ɗaga kayan nan, wato kina ɗagawa zuciyarki tana ƙuna ko? Abu ne da ba za ki taɓa samu ba, wataƙila ma mijin naki ya ƙoƙarta ko dubu talatin ne kuɗin lefen da na saka ranar har ma sadaki tabbas aurenki bashi da maraba da sadaka Jidda" Lokacin d Umma ta mata wannan furucin ta ji ciwo amma kuma tuno yadda take jin Ibrahim a ranta da zuciyarta sai take gani ko babu ko kwabo za ta aure shi ta zauna da shi tsakani da Allah, kuma za ta masa matuƙar biyayya har ƙarshen numfashinta!.

A fili kuma sai ta tashi siyam-siyam ta nufi ɗaki tana jin babu daɗi a lan abin da Ummar ta mata ko don ba ita ta haife ta ba, amma ita Jidda a zuciyarta daɗi da farinciki take na kayan da aka kawowa Aliya kuma bata jin ƙyashi ko baƙinciki kuma bata wani tunani a kan cewa tana jin tana son wani abu makamancin abin da aka kawowa Aliyar bare ma ita kamar yadda Ummar ta faɗa ta san ma hakan ne tun da a yadda take kallon Ibrahim bata taɓa zaton zai ce da aure yake son ta ba, tunaninta bai shirya auren ba duk da baka san tanadin mutum ba amma ita bata da buri a haka take son kayanta.

Abba yana wajen yake ganin matan jefi-jefi suna zuwa suna gani tare da yin Allah sanya alkairi. Abba bayan baƙin sun tafi ya jima zaune yana ta jimami da mamaki sai dai ya san ba a mamaki da jimami da lamarin ubangiji hakan ya sa ya rasa ma wa zai tunkara da wannan magana, jin wai ashe ɗan gidan Alhaji Sule ne ya zai auri Jidda, mutumin da babu inda za a ambaci sunansa a kasa gane shi babban mutum mai dukiya da ya yi shura, lallai Allah, Allah ne yana yin yadda ya so a lokacin da ya so, yana ba wanda ya so sanda ya so Wayo ko dabara ba ya ba mutum abu Allah kaɗai yake bayarwa, Allah shi yake bayarwa a gode masa ya ƙara!.

Abba ya nisa tare da sakin wata ajiyar zuciya yana duba naira miliyan uku a gabansa wanda 500k guda shida kowanne nannaɗe da kyaure, yana tunano yadda suka gabatar masa da kansu a matsayin baƙinsa da suka yi waya cewa za su zo bayan sallar isha'i bai taɓa saka ran zai gansu ba shi ya sa da ya ga zuƙeƙiyar mota ma bai kawo cewa baƙin nasa ba ne.

Yadda suka karrama shi duk da yana da labarin Alhaji Sule bashi da wulaƙanta ɗan adam ya san mutuncin mutane amma sai ya ga abin ya fi yadda ake faɗa, tabbas zai yi alfahri a ko ina da mijin da Jidda za ta aura saboda ko da ya zo ya gaishe shi haƙiƙa ya yaba da hankali da tunaninsa, kuma a yadda ya ganshi bai taɓa tunanin masu hannu da shuni ne har haka ba, amma ya zo gidan talakawa neman aure haƙiƙa duk wanda ya auri Jidda ya dace da mace kamila kuma ta gari, duk da ba shi ya haifi Jidda ba amma yana alfahri da ita, kuma ya yi wa su Alhajin bayanin wace ce Jidda kuma sun ji sun gani.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull