Kenza eBookz

Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 11

Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 11

Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 11: Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 11. Kuɗin ya fara tattarawa yana tunanin yadda zai yi da…

3,341 words

Kuɗin ya fara tattarawa yana tunanin yadda zai yi da wannan kuɗin, tun da shi kaɗai ya karɓi baƙin nasa, duk da naira miliyan goma suka bayar a matsayin kuɗin gaisuwar uwa da uba da kuma kuɗin kuɗin saka rana gabaɗaya suka kawo amma ya ce shi ba zai karɓi miliyan goma ba ya yi yawa dakyar ma ya ɗauki miliyan uku.

A fili ya furta

"Alhamdulillah, Allah na gode maka da ka bani iko zan sauke nauyin marainiyar nan, zan damƙa ta a hannu na gari Allah ka taya mijinta riƙo ka bashi ikon kulawa da ita!" Gabaɗaya ya kwashe kuɗin ya saka a babbar riga bayan ya ware dubu goma ba don komai ya yi hakan ba sai don kar ya saka Umma ko Aliya jin wani abu marar daɗi a ransu saboda shi kansa bai zaci haka ba kuma ya ga suna farinciki da abin da Kasim ya mata, kar su fara raina abin da ya yi.

Gidan ya shigo ya same su suna zazzaune, suna cin abinci ɗaki ya shiga ya ɓoye gabaɗaya kuɗin yana sakawa a ransa cewa bayan bikin zai samu kadara ya sayawa Jidda da kuɗin wannan don bai yarda ya ba kowa kuɗinta ba.

Bayan ya fito ya zauna ana hira yana cin abinci sai da ya kammala ya yi gyaran murya ya ce

"Ummar yara" Umma ana washe baki aka ce

"Na'am" Ya ɗan nisa kaɗan tare da zaro dubu goman aljihunsa ya ajiye ya ce

"Ga kuɗin gaisuwa da saka ranar ƴarki Jidda!." Gaban Jidda ne ya bada wani rasss a inda Umma da sauri kafin ta furta komai ta miƙa hannu ta ɗauki kuɗin a fili ta fara irgawa tana cewa

"Dubu ɗaya, dubu biyu, dubu uku, dubu huɗu, dubu, biyar" Da ta zo kan dubu biyar sai da ta ɗago kai ta kalli Jidda wacce kanta yake sunkuye saboda kunya ita kuma Aliya bakinta washe tana kallon hannun Umma saboda tana ganin kuɗin hannun Ummar da take irgawa ya kusa ƙarewa. Umma ta ci gaba da irgawa tana murmusawa cike da ƙeta a ranta ganin dai kuɗin bashi da maraba da sadaka, da ta zo dubun ƙarshe sai da ta ƙara sautin ta ta ce

"Dubu goma cass" Ta faɗa tana kallon Abba da yake murmushi kafin ya furta wani abu Jidda ta tashi da sauri saboda kunya ta nufi ɗaki. Umma a zuciyarta ta ce

'Shegiya aniyarki ta biki wato ba za ki iya kukan baƙin ciki a gaban mutane ba sai kin shige ɗaki taɓɗi lallai iska tana yawo da mai kayan kara in banda matsiyaci kika kwaso har yaushe zai kawo dubu goma' Maganar da Abba ya mata ne ya dawo da ita daga maganar zucin da take ya ce

"Kin gama irgawa" Tana dariya mai sauti ta ce

"Wallahi na gani abin arziƙi yarinya ta yi goshi" Aliya ta ce

"Umma dubu goman ne goshi" Ta faɗa tana ƴar dariyar yadda Jidda za ta ji, Abba ya ce

"Ke ba na son shashanci tashi ki tafi ki ba mutane waje" Da sauri ta tashi ta shige ɗaki tana shiga ta rungume Jidda ta ce

"Amarya ta ango ya kawo mata dubu goma" Jidda duk sai ta ji kamar ta nutse ita kuma Aliya murna take ganin ta fi Jidda komai dama ta san babu yadda za a yi ita kyakkyawa mummuna ta fi ta komai na aure!.

Tun da aka saka rana wata guda sai soyayya da shaƙuwa suka ƙara tsananta a tsakanin masoyan biyu wato Jidda da Ibrahim, kowa ƙoƙarinsa ya ba ɗan uwansa kulawa tamkar ƴan biyu haka suke rayuwarsu kamar dai ƴan uwa ba wai wanda soyayya ce ta haɗa ba!.

Abba ya yi ƙoƙari ya saya musu kayan ɗaki iri ɗaya daidai ƙarfinsa, a inda ya saya kayan kicin ma komai babu bambanci. Sai dai Umma tana ta sayan kayan kicin tana turawa ƙasan gado don bata yarda a ce da Jidda marainiya da kuma Aliya mai uwa a raye an musu komai da komai iri ɗaya ba.

Jidda sosai suke murna ita da ƙawarta Salama Jidda za ta yi aure!.

Mummy yau saura kwana biyu su dira a Nigeri'a za su dawo daga Dubai inda suka tafi sayyayar kayan lefe.

Yau saura kwana biyu a kawo lefe don ranar ta kama gabaɗaya tare za a kawo domin Abba ya sanar da kowanne ɓangare na maza cewa rana ɗaya za a kawo. Aliya da Amatallahi suna ta rawar kai sanadin wasu hotuna da Kasim ya turawa Aliya na wasu lesuna ya ce kaɗan daga cikib kayan da aka saka a lefe ne sauran sai an kawo ta kashe ƙwarƙwatar idanunta. Wannan dalilin ya sanya Amatullahi da Aliya cewa ranar kawo kayan lefen a ɗakin Umma za su ɓuya babu inda za su tafi domin a kawo a kan idanunsu saboda Aliya ta sanar da Kasim cewa a samo motar da za ta kawo masu kawo kaya, hakan ya sa ya ce ai dole ma ya samo motoci, kanta ya fashe suna ta yadawa Jidda magana wacce ita bata wani damu da abubuwan da suke faɗa ba. Har yau bata san waye Ibrahim ba shi kuma yana jin daɗin mu'amala da ita a hakan rayuwar duniya bata dame ta ba kuma har yau ko ɗankwali bai bata kyauta ba bare naira biyar sai dai yana mata wani tanadi na musamman a cikin gidanta wanda farinciki ne da kwanciyar hankali in sha Allah.

Yau ya kama alhamis ranar da za a kawo lefen Jidda tun da rana ta shirya ta cewa Umma ta tafi gidan su Salama, suna can suna ta murna da kuma sakawa a ransu cewa duk abin da aka kawo za su karɓa su yi farinciki!.

A zaure Abba da ɗan uwansa da kuma amininsa da maƙota guda biyu. Umma ita da ƙawarta sun kasa zaune sun kasa tsaye suna ta tunanin yadda za a kawo kayan nan sun da Umma tana ganin kayan saka rana ma an yi musu bajinta bare kuma lefe mai kankat.

Kuɗi ma sai da aka ɗora dubu ashirin.

A can gidan Daddy zuƙa zuƙan motoci kuma galla galla sabbi dal, sai sheƙi suke na sabunta da kuma gani ka san sun ci kuɗi. Guda uku aka ware inda ma'aikatan gidan suke fito da wasu kyawawan kwatuna suna lodawa a motocin sai da suka gama saka wa tas, maza biyar ne wanda za su tafi kai kayan inda kowacce mota da direba. Wata baƙar mota sabuwa wacce ita ma gabaɗaya kujerunta ledojin sabunta ne za an buɗe get motocin za su fita Daddy ya zaro mukullin daga aljihu ya miƙawa wani direban da yake a tsaye karɓa ya yi ya shiga motar suka jera suna tafiya a laye sabuwar baƙar motar ce a tsakiya suna fita aka rufe get ɗin suka lula a saman titin da tamkar domin su aka yi shi, suka tasamma gidan su Jidda.

Ibrahim da yake kallonsu ta saman windown a bene ganin fitarsu ya ɗaga hanni yana godewa Allah tare da fatan Jidda ta ci gaba da amincewa da shi don ya san yau kayan lefensa za su tabbatar mata da waye shi, tun da ta faɗa masa an kawo dubu goma kuma bai ga alamar rainuwa a tare da ita ba, tabbas ya san Jidda tana masa wani ɓoyayyan so duk da tana bayyanawa amma ya san baki ba zai iya furta yawan son da take masa ba. Duk da ya san wanda take masa ba zai kai wanda yake mata ba.

A can gidan su Kasim, Kasim ne tsaye a ɗakinsa ya rasa yadda zai yi saboda ya faɗawa mahaifinsa cewa ga abokansa nan za su zo su kai su a motoci shi ne yake ta masa faɗa yana mene ne wani abin motoci kar wani mai motar da ya zo masa ƙofar gida, a ƙafafunsu za su je suna tafiya suna hira, haka yana ji yana gani Baban nasa ya kirawo wani mai ruwa ya ce ya zo da zai yi hayar baro, haka ya ɗakko baron aka ɗora akwatuna biyu sai ƙaramin kit guda ɗaya suka nufi gidan su Aliya.

Mai baron yana gaba maza guda uku suna binsa a baya shi kuma Baban Kasim ɗin ya koma cikin gidan.

MAMAN AFRAH

09025576222

https://chat.whatsapp.com/CoSIFObGSJeG4TLAuJwo3J?mode=ems_copy_t

*RUWA CIKIN COKALI*

(Ya ishi mai hankali wanka)

NA

MAMAN AFRAH

. *Daga marubuciyar*

*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*

*09025576222*

BOOK 1

PAGE 9️⃣

*SADIYA*

Ta daɗe tana nazarin rayuwa kafin daga bisani ta tashi ta haɗa kayan wanke-wanke ta wanke. Kalifa da ya ƙi kwanciya saboda zafin jikinsa ta ɗauke shi ta goya shi zuwa can ta ji yana mimmiƙewa alamar tana son sauka ga wani ƙananan kuka da yake tana sakko shi ta ga har ya fara kashin kamar ta yi kuka haka ta je ta gyara shi ta dawo dasho ta kwantar ganin ya kwanta ta je ta yi wanka ta fito ta shirya. Sai neman magani take amma babu na zazzaɓi babu na gudawa gashi bata da kuɗin da za ta saya masa maganin hakan ya sa take ta takaicin rashin sana'a domin sana'a makami ce kuma jigo a rayuwa in har kana yi ko yaya za ka fi ƙarfin abubuwa.

Nasir tun da ya fito ya turawa Baba wannan kuɗin bayan sun yi waya, gidan Hajiya ya nufa ana sauke shi a mashin ya shiga da sallama. Bayan ya zauna ya gaishe da Hajiya Husna da Hibba suka gaishe da shi, ya amsa suna ta raha abinsu.

Hajiya ta kalle shi yana cin abincin ta ce

"Gaskiya wannan matar taka an yi makirar mata wallahi, ita kullum bata da aikin sai son ta ɓanɓari kuɗi a jikin ka, ai wallahi an kusa dai yin ta ta ƙare daga ka auri Meenal ka huta yarinya mai hankali da sanin ya kamata kuma ka ga ita ko nawa ka kashe mata baka yi asara ba amma wannan ita ƴar gidan faƙirai ba wani saba kama kuɗi ta yi ba sai shegen munafurci" Ta faɗa tana yatsina fuska. Karaf Husna ta ce

"Hajiya ai daga matar nan ta Yaya sai baya wallahi sumi-sumi kamar munafuka ko kaɗan bata da hali" Hibba ta ce

"Ai gwara ya auri Meenal ƴar ƙwalisa ta zo gidansa ya huta ita ma ta huta"

Hajiya ta ce

"Wallahi kuwa abinsu tuwona maina"

Sai da ya kurɓi shayinsa ya ce

"Ai ni in ban da ƙaddara babu abin da zai saka na auri Sadiya, kuma yanzu ma tun da har ubanta ya nuna zaman auren yake so ta yi to za ta rayu a wahala kuwa"

Hajiya ta ce

"Ai karka saurara mata, dama mashinshi ne ta rasa ya yaɓa maka da yake kai ne mai tsautsayin"

Suna ta faɗin maganganu a kan Sadiyar har ya gama cin abincin yana faɗar ya yi daɗi sosai, Hajiya tana faɗin ai shi ya sa ta ce ake yin abincin da shi yake ci yana murmurewa tun da bakinsa ya saba da cin mai daɗi da mai maiƙo saɓanin Sadiya da dama ta saba da cin tuwo, dubu ashirin ya fiddo ya ba Hajiya dubu goma su kuma kowa dubu biyar sai wata tsohuwar ɗari biyi da Hajiyar ta ce ya bada za a siyowa Kalifan magani, daga haka ya musu sallama ya ce ya tafi kasuwa. Almajiri aka ba ya je maƙota ya siyo maganin rana da maganin kashi na gargajiya Hajiya ta ce su je su kai mata ta haɗa musu da fanadol ta ce su kai a jiƙa a ɗura masa maganin zazzaɓin, bayan ta san maganin yara ya kamata a bashi ba na manya ba.

Basu tashi tafiya ba sai da suka gama ɓata lokaci, lokacin da suka zo ƙofar gidan da ƙafa Husna ta tura ƙofar gidan har sai da ƙofar ta bugu da jikin bango da ƙarfi wanda hakan ya falkar da Kalifa daga baccin da yake a tsorace yana kuka, ko ba a faɗa ba ta san mai mata wannan ɗabi'ar don haka kawai sai ta shiga jiran zuwan su don ta san ƙannen mijinta ne.

Hibba ta ce

"Gafaranmu dai" Ta faɗa a gadarance, amsa musu ta yi domin ta san rainin hankali ne maimakon su yo sallama shi ne suka yi hakan, tana kallonsu ta window tana jijjiga Kalifa suna ƙarewa gidan kallo labule suka bankaɗo suka shigo ɗakih suna wani yatsina suka zauna.

Babu wacce ta yi magana cikinsu Sadiya ta ce

"Su Husna ne yau a gidan namu"

Hibba ta ce

"Gidanku ai yana can gidanku sai ko ki ce yau mu ne a gidan yayanmu, kuma zuwa gidan nan ai ya zama farillah saboda gidan ɗan uwanmu ne sannan kuma ki sa a ranki nan ba da jimawa ba za ku zama ku biyu don yayanmu dole a gallo sabuwar amarya irin matan da ake yayi wayyayu" Ta ji ciwon maganar amma sai ta basar ta ce

"Gidansa ne kam, to Allah ya kawo ta" Daga haka babu wacce ta tambaye ta ya maia jiki Husna ta dangwarar mata da maganin a tsakar ɗakin ta ce

"Saƙo daga Hajiya ta ce gashi nan in dai magani ne da na kashin da na rana har da na zazzaɓi ki jiƙa amma batun wai kike cewa Yaya za a kai shi asibiti bai taso ba" Ɗago idanu ta yi ta kalle su kowacce ta tamke fuska a gadarance amma Sadiya bata ce komai ba sai Husna ta ce

"Wato a faɗa miki saƙon uwar tamu amma ki wofintar saboda ba saƙon taki uwar ba ne" Sadiya ta ce

"Karki zageni Husna, kuma ai na ji saƙon ta ko kin ga na yi musu" Basu bata amsa ba suka ce uhm a tare suna masu tashi suka fita, tana ji suka fice daga gidan babu wacce ta yi ƙoƙari rufe mata ƙofar gidan!.

Ledar ta ɗauka ta duba abubuwan da suke ciki tana jin babu daɗi a zuciyarta tabbas duk macen da bata yi dacen miji ba kuma vata dace da uwar miji ba, sannan dangin miji basa ƙaunarta lallai ba za take jin daɗin zaman gidan aurenta ba.

Nasir soyayya suke shi da Meenal kamar su haɗiye juna, sai dai yanayin yadda take zuwar masa da buƙatar kuɗi abin yana damunsa sai dai da ya faɗawa Hajiya sai ta ce wuyarta a yi auren za ta daina wataƙila da yarinta duk da yarinyar tana da tunani da hangen nesa in ji Hajiya.

Yau ya kama talata inda Hajiya ta sanar da ƙawarta mahaifiyar Meenal za ta kai musu ziyara. Da yammacin ne Meemal da mahaifiyarta suna zaune a falo suna hirar bikin da ake son saka rana Meenal ta ce

"Ni wallahi Momi ba don dai saboda ke ba da babu yadda zan yi in aure wannan Nasir ɗin" Ta faɗa tana jan dogon tsaki, baki Momi ta taɓe ta ce

"To ya za a yi tun da ya nuna yana son ki kuma mahaifiyarsa ma ta nuna tana ƙaunar wannan haɗin, ai sai a yi tuwona maina" Ta faɗa tana wata ƴar bazawarar dariya.

Ƙwafa Meenal ta yi ta ce

"Hummm!. Yaro bai san wuta ba sai ya taka, ni wallahi ba zan ɗauki raini da cin kashin da suke yi wa wannan Sadiyar ba, tsaf za mu raba raini don wallahi ko ita Hajiyar ba saurara mata zan yi ba bare wannan riƙaƙun ƴanmatan ƙannen nasa duk sai na gasa musu ƙasa a hannu, shi kuma Nasir hummm sai ya zama mijin ta ce"

Momi ta dara har da ƴar shewa ta ce

"To Meenal idan baki yi wannan abubuwan da kika zayyano ba kenan ma baki cika ƴar halak ba, ai ba baiwa na kai musu ba ki ƙwatawa kanki ƴanci a gidan miji karki yarda da rainin kowane shege" A daidai nan kiran wayar Nasir ya shigo a inda hakan ya yi daidai da tsayawar napep ɗin da ya ɗakko Hajiya a ƙofar gidan su Meenal ɗin. Da sallama ta shigo gidan Momi ta amsa tana mata maraba tare da cewa ta shiga, ita kuma Meenal da sauri ta tashi ta shige bedroom tana kashe murya suka fara magana da Nasiri.

Nasir ya ce

"My love na matsu mu yi aure ko ma zama tsintsiya maɗauri ɗaya, ke ce taurauwa a gidana ke za kike murza kambunki wancan ta cikin gidan ma karki ba kanki wahala wajen sakata a layin kishiyarki don daga kin zo gidan komai ya dawo hannunki" Ya faɗa yana jin tamkar ya janyo ranar auren nasu da ba a saka ba duk da ana dab da sakawa. Wannan dariyar tata mai ƙaramib sauti wacce take nuni da tana jin kunya ita ta sakar masa tare da cewa

"Ni ka sa ina rufe fuska kunya nake ji Allah" Wani daɗi ne ya lulluɓe shi ya ji tamkar ya yi ihun daɗi don yana mugun son mace mai kunya duk da ya san Sadiya tana da kunya da kawaici amma dai shi yanzu hankalinsa yana kan Meenal ɗinsa wacce yake ji ɗaya tamkar goma, wacce kuma yake riritawa kamar ƙwai.

Hira suka ci gaba da yi tana ta nuna masa tana jin nauyinsa a inda shi kuma yake ji babu ya shi don yadda Meenal take bashi girma sai yake jin ladabin Sadiya kamar dai ma ba wata biyayya ce take masa ba, sun jima suna hirar daga bisani suka yi sallama ya kashe wayar yana sauke nannuyar ajiyar zuciya a inda a wani ɓangaren na zuciyarsa yana jin daɗi yau har sun yi waya sun gama bata buƙaci wani kuɗi daga gare shi ba, saboda ya lura ita bata san yawan tambayar abu kima yake zubarwa da mace!.Don roƙo yana taka muhimmiyar rawa wajen daƙile mutucin wanda yake roƙon, shi ya sa ma wani ya tambayi manzo S.A.W shin mai zai yi Allah ya so shi sannan mai zai yi mutane ma su so shi. Manzon Allah S.A.W ya cewa mutumin ka guji duniya Allah zai so ka, sannan ka guji abin hannun mutane mutane ma za su so ka, kenan duk wanda kake son abin hannunsa yau da gobe kimarka raguwa take a wajensa.

Suna yin sallama ta saki wani gajeran ɓoyayyan tsaki ta ture wayar gefe tare da kwantawa male-male a kan gadon a fili ta ce

"Wahalalle kawai, mutum kai baka son ka ɓamɓaru wato ka ji yau ban roƙi kuɗinka ba shi ne gudun kar na roƙa har wani saurin yi min sallama kake, ai zan shigo cikin gidan" Ta faɗa tana janyo wayat ta shiga wtsapp take ta chart ɗinta.

A falo cike da fara'a Momi ta tarɓi Hajiya a inda suka gaisa daga nan hirarsu ta ƙawaye ta ɓarke e tsakaninsu, Hajiyar tana faɗin cewa ƴan uwan mahaifin Nasir za su ji dangin mahaifin Meenal su kai kuɗin gaisuwa, saboda daga Baban Nasir har na Meenal basa raye.

Suna ta tattaunawa zuwa can sai gashi Meenal ta fito falo tana taku cike da nutsuwa, gaban kujerar da Hajiya take zaune ta je ta tsugunna tana mai sunkuyar da kai ƙasa ta ce

"Hajiya ina wuni" ,Hajiya cike da farinciki ta ɗora hannu a kan Meenal tana amsa gaisuwar tare da yaba hankalin Meenal ɗin, tana ganin idan suka samu Meenal a family nasu sun warke.

Cike da ladabi ta tashi ta fita, Hajiya ta kalli Momi tana murmushi ta ce

"Ƙawata wallahi kin iya haihuwa sannan kin iya tarbiya, haka kawai ya je ya kwaso masa jangwam ai wallahi Nasir da Meenal ya fara aura babu dalilin da zai sa ya auri wata Sadiya kuma wallahi yanzu ma ruwanta ne bai ƙare ba daga zama ya ƙare dole ta fita ta bata waje saboda gidan Nasir na Meenal ne ita kaɗai" Dariya Momi ta yi ta ce

"Ai ƴarki ce komai kika yi daidai ne!." Dariya suke suna ci gaba da tattaunawa, a inda Meenal ta dawo ɗauke da ruwa da lemo a faranta sai kofi ta zo ta durƙusa cike da ladabi da zubawa Hajiya ruwan ta tashi ta bar wajen Hajiya tana ta yabawa Meenal ɗin bata san cewa lumbu-lumbu ce wutar ƙaiƙayi ba.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull