Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 46
Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 46: Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 46. "To da ba ke kaɗai suka duka ba, kalli hancina ji…
3,333 words
"To da ba ke kaɗai suka duka ba, kalli hancina ji nake kamar jini ne yake zuba duk sun dauje mini, ga fuskata ma sai raɗaɗi take" Momi ta ɗan ɗago kai ta kalli fuskar Meenal wata dariya ta so wwace mata amma bata son ta yi saboda yadda bakinta yake zugi. Ganin Meenal ta yi kamar an yi murjin taliyar hausa a fuskar tata, ga wata ƙasa da ta yi buɗuɗu kamar wanda ta ziyarci yaƙin badar.
Sun jima a kwance a tsakiyar hanyar amma banu wani mahluƙi da ya biyo hanyar ma bare ya taimaka musu, haka suka ba kansu shawarar tashi su lallaɓa.
Momi ɗankwalinta sa yake can gefe ta ɗaukko ta ɗora a kanta ya kalli gabas maso kudu, amma bata damu ba burinta su samu su bar tsakiyar jejin. Haka ta ɗauki mayafinta ta yaɓa a kafaɗa tana riƙe da zaninta da ta tattare tamkar za ta yi tseran gudu. Meenal ma ta lallaɓa ta miƙe tana jin ƙugunta kamar ba a jikinta yake ba,ga shi duk haushi ya cika ta a haka ta ɗauki jakar da banu ko sisi a ciki takaicin ma da har da wayoyinsu aka ƙwace.
Haka suka tashi suna tafiya kamat masu tatata, Momi a gaba zanin nan a tattare a hannunta Meenal tana biye da ita, Meenal ta ce
"Wallahj Momi ina ga mutanen nan ƴan iska ne, ni fa ɗayan nan sai da ya jimƙe hannunsa ya dage ƙarfinsa ya kirɓa mini naushi a mazaunai" Wani gajeran tsaki Momi ta yi ta ce
"Kukan daɗu kike Meenal wallahi allon kafaɗar nan tawa kamar an buga mini filankin katako, wai hannu ne ya yi wannan aiki, ba gwara ma mazaunai wajen tsoka ba ne ni fa wajen ƙashi ne kin ga ai ni na ji abin da na ji, daga rakiya haka kawai an illa ta ni gani nan duk na fita hayyacina" Banza Meenal ta mata don ta ga kamar ma bata damu da abin da ta faɗa ba, haka suke ta tafiya amma sun kasa ganin ko mashin ne.
Suna cikin tafiya sai suka wani ƙaton mutum a amalanken shanu haka suka tare shi dama daga wata hanya ya ɓullo, suna ɗaga masa hannu da maaa magiya sannan ya tsaya, ganinsu a firgice sai ya ƙara ɓata rai, nan Momi ta dage tana sheƙa masa ƙarya cewa zumunci za su je waji kauye m nisa ziyara shi ne suka haɗu da haɗarin ƴan fashi suka musu duka duka musu ƙwace, shi dai bai ce komai ba sai cewa da ya yi su shiga tun da sun nema ya rage musu hanya. Dakyar yake tafiya su dai suna baya sun zazzaunai suna tafiyar dakyar ƙiƙar ƙiƙar.
Suna cikin tafiya tsabar wahala Momi tana jingina bayanta sai kawai gyangyaɗi ya kwashe ta, a cikin bacci ta yi mafarkin sun cim ma mummunar manufarsu, Meenal ta mallaki manyan gidaje da motoci suna mulkar Ibrahim yadda suka so. Meenal da ta kalli Momi tana gyangyaɗi har neman tuntsurawa take sai abin ya ɓata mata rai a nata ganin su da suke cikin wannan yanayin ina suka ga damar wani bacci in banda dai shi bacci ba ka sanin lokacin zuwansa.
Wasu ƴan mata ne suka ɓullo su biyu daga wata siririyar hanya, ya kasance suna gaban su Momi kamar an ce yanmatan su ɗago suka hangi amalanken shanun nan suna ganin mau tuƙawar sai suka kwasa a guje suka koma hanyar da suka fito suna faɗin
"Audu kwarto, Audu kwarto" Momi wannan ihun ne ya falkat da ita daga ɗan guntun gyangyaɗin ita kuma Meenal sai ta fara tunanin inda kwarton yake, kamar daba sama suka ji muryar mai amlanken ya ce
"Ƙarya suke mini"
Momi a zuciyarta ta ce
'In ba rami mai ya kawo rami?" ,Wato da shi suka tun da kaf dajin babu wani sai shi, kallon kallo aka shiga tsakanin Momi da Meenal don mutumin wani jibgege ne dukwanda ya sake ya damƙe shi to bai isa ya ƙwace ba. Shi kuma ya ji haushin bayyanar ƴanmatan don ya san da gaske suke tin da shi ne yake lalata ƴaƴan mutane.
Momi da ido ta yi wa Meenal signa duk da Meenal ta saba da banbaɗar da mutuncin ta ga maza sai ta ji wannan tana shayinsa shi kuma dama a nasa ƙudurin sai ya ƙarasa fa su gidansa da yake wata hanya zai tilasta musu shiga gidan don zai sanar da su zai ɗauki wani saƙo sai su wuce amma ba saƙo zai ɗauka ba, dama zai sheƙe ayarsa ne a tattare da uwa da ƴar gabaɗaya wato Momi da Meenal.
Momi ba ta yi wata-wata ba ta yi tsalle ta dira ita ma Meenal ta mara mata baya, Audu kwarto sai jin dirarsu ya yi da yake shi ya mayar da hankali gabansa, ai kuwa ya ji haushi domin ya gama sakawa a ransa cewa ya samu mata har biyu kasancewarsa hariji.
Momi suna dira suka yanke wata hanya a guje ko waiwaiye ba sa yi don ita Meenal hatta jakarta ta barta a cikin amalanken shanun, Momi da take ɗingishi lokacin tahowarsa amma yanzu ta ware ƙafa sai zabga gudu take, tsayar da shanun ya yi ya diro duk da girman jikinsa ba ya jin nauyinsa lokacin gudu a kan cikar burinsa don haka ya gwammace ya bi bayansu in ya so idan yana da rabo ko ɗaya ce a cikinsu ya kama a dokar dajin ya biya buƙatarsa.
Meenal ce a baya Momi har ta fi ta ware ƙafa su duka ko ciwon jikin da suka ce suna ji na dukan da ɓarayin kuɗi da wayar nan suka musu ba sa ji, ta ware murya ta ce
"Momi ga shi nan ya biyo mu"
Momi da sauri ta waiwayo sai ta ga ya dage tana sheƙa gudu, su duka ƙafa mai na ci ban baki ba, suka ƙara zage dantse wajen zabgar gudun famfalaƙi. gudu suke babu mai ko takalmi domin sun watsar da su. Ganin yana neman cim musu ya saka Momi ta sha wata kwatar cikin ciyayi ta durƙusa Meenal ma ta mara mata baya, suna durƙushe a wajen suna hakin gudun da suka yi, sai ga Audun ya zo sai dai ya ga hanya ta rabu biyu sannan ya rasa ina suka bi ya duba sawun su ya ga babu hakan ya sa ya ɗan tsaya yana dube dube. Yana tsaye a dab da su sai dai ya basu baya ne, jikinsa yana bashi suna wajen domin bai ga samun su na wucewa ba.
Momi bakinta har kumfa yake wajen karanto ƙulaƙuzai wa to falaƙi da nasi, sai dai a hankli take yi ba a fili ba gudun tonuwar asirinsu. Ita Meenal sai zare ido take tana kallon girmansa hatta mazaunansa kaɗai girmansu sai ya tsorata mutum.
Momi ba ta dakata da adsu,a ba don ba ta san iya mugun nufinsa a kansu ba. Ɗan ja da baya ya yi sai kuwa ya yi wa ƙatuwar ƙafarsa masauki a kan hannun Meenal, wani raɗaɗi ta ji don haka ta shiga zare ido tana ƙoƙarin rafka ihu sai dai Momi tana ta mata nuni da hannu a kan ta rufa musu asiri kar ta yi ihun. haka ta daure tana rausaya kai tamkar mai magogon naƙudar haihuwa. Idanun ya kaɗa ya yi ja sai dai a zuciyarta tana jin kamar ta hankaɗa shi ɗan gyara tsayuwa ya yi hakan ya sa Meenal jin tamkar wanda ya murtsuka ƙafar tasa wato tsananin azaba ya ƙara ratsa ta Momi kuma sai jan addu,a take duk wacce ta zo bakinta daga inda take iya hango gaban rigarsa ya ɗaga sosai daga saitin mararsa hakan ya sa ta yi mugun gani duk da cewa daga gafe ne take hange. Ajiyar da take mararsa tana ta harbin iska da alama a buƙace yake hakan ya tabbatarwa da Momi duk macen da ya damƙa sai ta gwammace kiɗa da karatu.
Meenal tana ta hawaye cikin ikon Allah kamar wanda aka ce ya tafi sai suka ji ya ce
"Ina jin gaba suka yi sai suka samu mafaka shi ya sa ban gan su ba, bari na bi bayansu wataƙika sun sauka daga tsakiyar hanya ne suna bin gefe inda da ciyayi shi ya sa na daina ganin sawunsu" Yana gama faɗar hakan sai ya zabga da gudu ya ci gaba da tafiya. Meenal ta ce
"Momi wayyo hannuna kalli yadda ya kumbura" Momi ta ce
"Meenal wa yake ta kumbuarar hannu, ki tashi mu kama hanya kar ya dawo ya iske mu a wajen nan, don wallahi wannan ya samu mace sai ya kumbura mata matantaka in ma bai ɓarɓarka ta ba" Babu yadda suka iya haka suka tashi cikin lallaɓawa suka kama hanyar da suka baro tun da ba zai yiwu su ci gaba da tafiya ba, gudun kar su yi arangama da shi!.
Gudu suka babu ƙaƙƙautawa har sai da suka ga sun zo bakin hanya" Sai haki suke suna da na sanin hawa amalanken Audu kwarto. Motoci suna wulgawa sai dai duk wacce suka tsayar sai su ƙo tsayawa don ana musu kallon kamar basu da cikakken hankali duba da kowacce babu takalmi sannan kuma kowacce ba ta da nutsuwa.
Dakyar suka samu wani mai mota ya ɗauke su da suka faɗa masa ziyara suka je ƙauyen ƴan uwansu a hanya ɓarayi suka tare su suka musu ƙwace tare da musu dukan tsiya, ya taimaka musu donnhat ƙofar gidan Momi ya kawo su, saboda ba motar haya ba c kuma shi kaɗai ne a motar. Godiya kamar za su ari baki. Sai da suka dawo gidan ƙofar gidan ma sai ɓalle ta aka yi don mukullin ma ba a san inda ya faɗi ba.
Bayan sun shiga gidan suka zauna suna mayar da yadda aka yi, a nan Momi tana nunawa Meenal kuskurenta na yin maganar kuɗi a gaban wasu tun da ta lura maganar kuɗin ce ta ankarar da su akwai kuɗin a atare da su, shi ya sa ake so mutum ya kama bakinsa idan ya je wajen da bai san mutane ba, tun da ba a goshin mutum za a rubuta waye shi ba, idan mugu ne ko akasin hakan.
Ruwan zafi Momi ta dafa suka yi wanka sannan suka ci abinci suna maganar za su koma wajen bokan don cim ma manufarsu domin ba su daddara da abin da ya faru ba, hakan ya san Meenal ta ce akwai wasu kuɗaɗe da za su shigo mata da zarat sun shigo za su koma, Momi ma da yakr zuciyar a bushe take ta goya mata baya.
Sai da Nasir ya dawo daga kasuwa ta biya suka ya ɗakko ta. Tana shigowa gidan ganin Sadiya tana shanya kafa ta aika mata saƙon mugun kallo, abin mamaki sai Sadiya ta ji Nasir ya yi sallama, amsawa ta yi ta juyo tana masa sannunda zuwa ya amsa da fuska a sake, yana tambayar ta Kalifa ta ce yana ɗaki yana wasa, maimakon ya shige ɗakin Meenal sai Meenal ta ga ya juya da ledojin hannunsa ya nufi ɗakin Sadiyar.
Gaban Meenal ne ya faɗi a take ta shigar zargin ko dai da saka hannun Sadiya a rugujwar shirin da suka yi yau, wani ɓangarr na zuciyarta yana zargin ko dai Sadiya ta je tanyi wani abu ne da har Nasir ya kula ta yau.
Abin da Meenal ba ta sani ba shi ne wani maƙocin Nasir ne a kasuwa suke tattaunawa a kan yana gobe zai kai matansa kasuwa za su yi sayayya kowacce ta zaɓi abin da ranta yake so, a nan maƙocin yake cewa
"Ina tsoron shanyewar rabin jikina a ranar
ƙiyama shi ya sa ba na nuna bambanci a cikin matana, ko da a ce ba zan iya daidaita matsayi da soyayarsu a zuciyata ba tun da dama Allah ba ya amfani da fifikon soyayyar a zuciya kawai adalci ne na zahiri shi ya sa nake ƙoƙarin kiyayewa" Wannan furucin ne ya sa Nasir ya tuna rashin adalcin da yake yi wa Sadiya hakan ya sa ya ɗan sakko domin ya mata adalcin ko da kaɗan ne ba da yawa ba, sai dai ita Sadiya ganin abin da Nasir ya yi bai ba ta mamaki ba domin ta san tana kai kukan ta wajen ubangiji don haka ta san addu,ar ta ce ta fara karɓuwa.
Tana gama shanyar ta nufi ɗakinta. Meenal tun da ta ga ya kama hanyar ɗakin Sadiya sai ranta ya hau suya, dakyar ta yi yaƙi da zuciyarta ta shiga ɗakinta, shi ma don kar Sadiya ta gane ainihin ta razana da alamarin duk da an ce labarin zuciya a tamabayi fuska!.
Tana shiga ɗakin ta yi jifa da mayafin Momi wanda ta sako don hatta kayan jikinta na Momin ne har takalmi. Da sauri ta shiga leƙo tsakar gidan don ganin abin da yake wakana, ganin Sadiya ta nufi ɗakinta da turtsetsen cikin ta sai ta ji zuciyarta tana zafi. Safa da marwa ta fara a tsakar ɗakin tana son kiransa a waya ta tamabaye shi wannan sabon salon fa, sai dai tunowa da crwa ɓarayi sun yi sama da faɗi da wayar sai ta rungumi na annabawa.
Ta kasa zaune da tsaye gabaɗaya ba ta da nutsuwa tana ganin wannan raini ne yake ao ya ja mata. A ɓangaren Sadiya ko da ta shiga ɗakin ɗauke da sallamaa bakinta, tana shiga ta ganshi zaune a kusa da Kalifa ya buɗe masa biskit ɗin da ya fito da shi daga leda wanda dama shi ya siyowa, yaron sai murna yake yana ta taɓa jikin Nasir ɗin ganin yau bai kyamace shi ba, kuma bai dakatar da shi ba daga taɓa shi sannan bai haɗe masa fuska ba, uwa uba har da biskit ya siyo masa, sannan yana ta biya shi suna magana duk da gwarancin maganar ta shi ba komai ne ake fahimta ba.
Ranta ta ji ya yi wani sanyi, tana kallon Kalifa da tausaywa shi ma ga shi yau ya samu ƴanci irin na sauran yara da suke samu a wajen mahaifinsu, shi ma yau yana ta dariya da farinciki sai ta ji gabaɗaya laifukan Nasir sun wanke daga idanunta duk da dama ba ta sakawa a zuciyarta amma dai ta san yana mata laifi. A rayuwa tana so a ce ko da ita ba ta samu komai ana kulawa ba to tana son ƴaƴanta su samu hakan zai rage raɗaɗi.
Kalifa ya kalle ta ya ce
"Momma kalli Abba ya siyo mini biskit" Ya faɗa yana ɗago mata biskit ɗin fuskarsa a washe, har ƙwalla idanunta suka tara ganinncewa yaro ma ya san kyautatawa bare kuma babba.
Murmushi ta yi masa, sai ya taho yana ɗakko guda ɗaya ya nufi bakinta hakan ya sa ta buɗe bakin ta gutsuwa, shi kuma Nasir sai yake kallonsu yana murmushi. Allah kaɗai ya san yadda Sadiya take ji a ranta abu ne da suka rasa a iya zamansu a gidan amma yau rana ɗaya ga shi sun samu wannan yake nuni da cewa mahaƙurci mawadaci!.
Sannu da zuwa ta ƙara masa ya amsa yana murmushi, leda ɗaya ya ɗakko ya miƙa mata ta karma da hannu biyu. Kallonsa ta yi ta ce
"Za ka yi wanka?"
Ya ce
"Akwai ruwa mai ɗumi?"
,Ta ce
"Eh akwai" Ta faɗa masa don ta cika filas ɗin shayin, ruwan wanka ta je ta haɗa masa ya tashi ya je ya yi wanka ya yi alwala ya fito.
Bayan ya shafa mai dama kayan jikinsa ya mayar kasancewar babu kayansa a ɗakin duk suna ɗakin Meenal shi turakar tasa ma dama ba zama yake a ciki ba kawai ɗakin Meenal ne yake zuwa. Bai ce mata komai ba sai ta ga ya fito falon ya ɗauki ɗaya ledar da ya ajiye a gefe ya juya zai fita sai Kalifa ya bi bayansa abin mamaki sai ta ga ya kama hannun Kalifan sun fita.
Gabaɗaya ta yi ɗiff tana ta mamakin abun kamar a mafarki. Ɗakin Meenal ya nufa yana shiga lokacin tana banɗaki, ledar ya ajiye a kan madubi, ya buɗe drower kayansa ya ɗakko kayansa lodi guda ya fito Kalifan yana biye da shi, kayansa gogaggu wajen kala goma ya shigo ɗakin da su, yana shigowa ta tashi ta karɓa, ta nufi bedroom don saka masa a drower. Yana bata ya ƙara komawa hannunsa riƙe da na Kalifa jallabiyarsa ya ɗakko guda uku, har lokacin Meenal ba ta fito ba, ita kuma ta ji shigowarsa domin ta ji motsi sai dai ta san shi ne ya shigo tana son sai ta gama abin da take ta fito ta zo ta sauke masa ruwan masifa.
Ba ta zaci kaya yake ɗauka ba, lokacin da yake shirin fita daga ɗakin yana riƙe da kayan da hannu ɗaya ɗaya hannun ya riƙe Kalifa sai kawai ta buɗe banɗakin ta fito, tana fitowa ta yi mugun gani da sauri har tana neman faɗuwa ta nufo shi ta ce
"Nasir mene ne nake gani haka?" Ta faɗa ranta a ɓace.
Yana ɗan murmushi ya ce
"A ina fa?"
A gadarance ta ce
"Oh ni kake tambaya? Baka ga ko da muka shigo gidan nan ban sake saka ka a idanuna ba, sai yanzu ka shigo kuma yanzun ma kana shirin fita,wannan kayan fa ko na bayarwa ne"
Ɗan jim ya yi sai ya ce
"Yau a ɗakin Sadiya na sauka" Duk da ta san hakan amma yadda ya furta sai abin ya mata ciwo, hakan ya sa ta ce
"Mai kake nufi? Ba dai rabon kwana za ka fara mana ni da ita ba?"
Ya ce
"A,a kawai dai ita ma zan kwana a ɗakinnta ne...
Ta katse masa hanzari da faɗin
"Kar ma ka fara wallahi"
Bai jira cewar ta ba ya juya ya bar ra a tsaye kamar ta rafka ihu tsabar takaici haka ta ji, wani tsaki ta duka tana juyawa ta yi ido huɗu da ledar kan mudubin ba ta yi wata-wata ba ta ɗauka ta yi wurgi da ita kayan ciki suka tarwatse.
Ko da ya koma ɗakin bedroom ya shiganya sauya kayan jikinsa ya fito da jallabiya a jikinsa ya ce mata zai je masallaci ta ce masa sai ya dawo, yana fita Meenal ta jiyo rufowar ƙofar gida hakan ya ba ta tabbacin ya fita da sauri ta fito har tana tuntuɓe a barandar ƙofar ɗakinta, ta ji yadda yatsanta na ƙafa ya bugu amma ba ta damu da zugin da yake mata ba, burinta ta shiga ɗakin Sadiya.
Sadiya tana bedroom tana linke kayan da ya cire a lokacin Meenal ta faɗo falon ko sallama babu ta, Kalifa yana ganin shigowarta ya tashi yana riƙe da alrwar tsinkensa ya kama hanyar bedroom a kiɗime don shi tsoronta yake. Sadiya tana ganinsa ta hau faɗin mene ne hankali tashe don ta yi zaton Nasir ɗin ne ya dawo ya zare masa ido tun da Nasir ɗin ma da ba ya sakar masa fuska tsoronsa yake. Kafin ya bata amsa ya riƙe ta sai ta jiyo muryar Meenal tana faɗin
"Kai ina uwar taka take?" Sadiya ta gane da ita take kuma ta fahimci ita Kalifa ya gani ya gudo amma sai ta ba falon ajiyarta, hakan yansa abin ya ƙonawa Meenal rai ganin ta ƙi fitowa. Murya ta ɗage ta ce
"To baƙar munafuka idan ma wani ƙulle-ƙule kika yj kika shiga tsakanina da shi ki sani na fi ƙarfin zama bora a gidan miji" Jin haka sai Sadiya ta fito tsabar ma ta ƙonawa Meenal rai sai ta fito hannunta riƙe da gajeran wandon Nasir da take linkewa wanda ya cire ta ce
"Shiga tsakani kuma? Kin taɓa gani an shiga tsakanin mace da miji? Kenan ni da ba ya zuwa ɗakina shiga tsakanina kika yi da shi?" Tambayar rainin wayon nan ta ƙara hasala Meenal har ta fara tunanin yaushe Sadiya ta yi baki? Ganin gajeran wandonsa a hannunta ya yi wa Meenal zafi a zuciya, tana ganjn kenan har Sadiya ta fara samun ƴancin taɓa gajeran wandon Nasir bayan tin daga lokacin da ta zo gidan hatta suturarsa ta bar ɗakin nata.
Cike da kashedi ta ce