Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 47
Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 47: Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 47. "Ki sani wannan abin da kika yi tamkar shuka ne a…
3,345 words
"Ki sani wannan abin da kika yi tamkar shuka ne a idon makwarwa, kuma ina sanar da ke ni da Nasir nan gani nan bari farar tumfafiya, da sannu zai dawo gareni yadda zai zamana sama ta yi wa yaro nisa sai dai ya tada kai ua yi kallo"
Baki Sadiya ta taɓe ta ce
"Kanki ake ji wai mahaukaci ya faɗa rijiya" Tana faɗar hakan ta juya ta shige ɗaki, dana a can ta bar Kalifa don bai biyo ta ba, Meenal ganin Sadiya ta barta a faɗo wato ta mayat da ita kamar mahaukaciya, hakan ya sa ta ji takaici wata zuciyar tana raya mata cewa kamar ita wannan marar galihun za ta faɗawa magana ta tafi ta barta a tsaye a wajen.
Jiki babu ƙwari ta juya fuuuu ta fita suka ci karo da Nasir da shigowarsa gidan kenan ya mata kallon mamakin ganin ta daga ɗakin Sadiya ya ce
"Lafiya dai kika fito daga ɗakinta a fusace ni fa ba na son gutsiri tsoma ki kama kankj" Da yatsa ta nuna kanta tana faɗin
"Ni kake faɗawa hakan Nasir tabbas na yarda ba a hayyacinka kake ba an fi ƙarfika" ,Bai ce mata uffan ba ya raɓa ta ya shige ɗakin ya barta shanye a wajen, baki ta dantse da haƙori idanunta suna cikowa da ruwan takaici, tana kissima sai ta turbuɗe tauraron Sadiya da ya farw haske a zuciyar Nasir sai ta san yadda ta yi ta ƙwace komai ya dawo hannun ta fiye da baya.
Ko da ta koma ɗakinta dakyar da iya yin sallah tana ta tunanin Alhajin da ya mata alƙawarin kuɗi idan ya tura mata ma ta ina za ta gani ita ba da waya gare ta ba, duk sai ta ji ta raina kanta yau ɗaya rana da Nasir zai kwana ba a ɗakinta ba tana ganin hakan kaɓar gazawarta ne a ce mijinta ya koma hannun matar da take ganin ba ta da aji fa kimar da za ta yi gogayya da ita wajen haɗa miji, duk kuwa da cewar ita Sadiyar ita ce ta fara auren Nasir ɗin.
Sadiya wainar fulawa ya ce mata yana son ya ci haka ta masa ta kawo masa ya ci ya sha shayi mai kauri wanda Sadiyar ta haɗa masa da kayan shayinta da take saya.
Ganin yau a ɗakinta yake kuma bata shirya hakan ba duk da ita dama ba ta tsark da ruwan sanyi tun da ta san tsarki da ruwan zafi yana haɗe mace sannan yana hana ciwon sanyi infection samun wurin zama a wajen macen da take amfani da ruwan zafin wajen tsarki. Hakan yana sa mace ta kasance koyaushe a haɗe, saɓanin ruwan sanyj da yake buɗa mace sanann sanyi ya samu wajen zama inda shi kansa sanyi yakan saka mace ta zama a buɗe sannan ko da ta yi amfani da maganin mata ba ta ganin alfanu saboda cutar sanyin.
Yana nan zaune a falon yana danna waya Kalifa yana zaune a wajensa, ta ɗauki pure water ta shiga ɗakin da kofi da cokali ta tsakure dakan ni,ima na maman afrah ta zuba ta haɗa da madara ta ɗaga kofin ta shanye, wata ƴar roba ta ɗauka ta buɗe ta fito da ƙwallon dabino ta ɗauki guda huɗu ta rufe robar ta mayar ta fito daga ɗakin tana riƙe da kofin, kaskon turaren wuta ta ɗauka ta ɗakko gwarwashi ta haɗa kanamfari da ƙwallon dabinon ta je banɗaki ta zuba su a garwashin ta tsugunna. Sosai ta ji ya mayar da ita kamar sabuwar budurwa duk da dama Sadiya mace ce wacce tamkar ba ta haihu ba.
Bayan ya dawo daga masallacin isha,i lokacin Kalifa ya yi bacci, ya tarar ta masa shimfiɗa a falo ta ɗaura masa net, ita kuma tana sanye da wata figigiyar rigar bacci da bai taɓa ganinta da ita ba gabaɗaya rigar ta bi ilahirin jikinta ta manne kallo ɗaya ya mata ya luka duniyar ƙaunar kasancewa da ita.
Sun ƙule a ɗakin yana mata hira ƙasa ƙasa duk sai ta ji abun banbarakwai wai namiji da suna Hajara. A wannan lokacin ne Meenal ta zo ƙofar ɗakin da suka ryfe take bugawa tamkar za ta ɓalla, haka ya taso ya fito sanye da gajeran wando ko singlet babu ransa a matuƙar ɓace domin da kawo masa tsaiko a lamarinsa da Sadiya da yake jin tamkar yau ne ranar farko da zai kasance tare da ita ko don an daɗe ba a haɗu ba.
Ta windown ya tambaye ta ba,asin zuwanta da kiransa, ta ce magana take so ta yi da shi, shi kuma ya ce ba zai samu dama ba sai gobe, haka ta koma ranta yana ƙuna, tana kissma mummunan ƙuduri a zuciyarta.
Sosai ya ji sauyi game da Sadiya don shi kansa ya sani Sadiya ta da ban ce a cikin mata ta fita da ban ko da kuwa mata dubu ya tara!.
Washe gari ko da su Hibba suka zo girkin safe, ranar sun gama tsara yadda za a ke yi su da Hajiya cewa yanzu su daina bari sai abin da Meenal ta ɗauka musu suna zuwa suna zama da yunwa kawai suke ɗaukan dankalin a ɓoye, soai suka ji daɗin shawarar nan tun da suna ganin ai ɗan uwansu ne yake siya ba ita ba, kuma har mahaifiyarsa za a ci.
Lokacin da suka zo sun yi mamakin ganin yayan nasu ya fito daga ɓangaren Sadiya, sannan sai suka ga Meenal tana cika tana batsewa, ko da ta ɗauka musu ɗanyen dankalin ɗaki ta koma hakan ya sa suka samu damar ƙara ɗanyen dankalin a ɓoye suka ƙara fiƙewa suka yayyanka suka shiga kicin. Soyawa suka yi tare da soya wainar ƙwan. Ledar da Hajiya ta bayar Hibba ta fito da ita daga aljihun rigarta suka kwashi dankalin da wainar mai yawa sai ƴar dariya suke a ɓoye suna jin daɗin yau za su ci dankali ya ishe su. Bayan sun gama Husna ta je ƙofar falon Meenal ta ce sun gama ta daɗe kafin ta fito a shelaƙe tana wani taɓe baki tana shan ƙamshi.
Kicin ɗin ta je ta ɗauka musu dankalin ko waina ba ta saka musu ba haka kuma ta ƙi tsakura musu kayan shayin. Fulas ɗin ta kinkima don yau ita kaɗai za ta ci ba ta niyyar ba Nasir tun da ya kwana a ɗakin Sadiya. Sun fito za su tafi lokacin tana dab da hawa barandar ɗakin ta, kamar wanda aka ce ta juya haka ta juya sai kuwa idanunta suka sauka a kan aljihun doguwar rigar Hibba da ya yi tudu, hakan ya sa ta kafa ayar tambaya don ta san ita dai lokacin da suka zo ba ta ga wata alama ba a jikin ta.
Sai dai ba ta taɓa kawowa cewa dankali ba ne ita ta fara tunanin ko a kayan kicin ɗin ta ne suka ɗauki wani abun za su fara mata zari ɗai-ɗai. Murya ta buɗe ta ce
"Ke Hibba ku dakata!".
Cak!. Suka tsaya suna jiran tsamani domin ita Hibba har ta fara ƴar karkarwa don dama ƴan magana sun ce marar gaskiya ko a ruwa gumi yake. Fulas ɗin hannunta ta ajiye ta tunkaro su, tana zuwa ta ce
"Mai kika ɗauka min a kicin?"
Husna ce ta yi ƙarfin halin yin magana domin ta ga Hibba tana neman bayyana lamarin ta yanayinta.
Husna ta ce
"Ɗaukan abu a kicin kuma sai ka ce wasu ɓarayi"
Meenal ta ce
"Ke Husna dakata!. Kar ki ƙara faɗa min magana garangatsai kamar wata sa,arki ni ba da ke zan yi ba, domin ni ba tsararki ba ce"
Ta faɗa ta miƙa hannu za ta taɓo aljihun Hibba ta matsa gefe tana zare ido.
Ƙiiii Meenal ta janyo rigar Hibba tana saka hannu ta ƙarfi suna kokawa ta taɓo dankali yadda ta ji shi da zafi tana leƙawa ta fito da shi ta buɗe leda sai ga dankali ba kaɗan ba da waina. Idanu ta zaro cike da mamaki ta buɗe murya ta ce
"Ihu ɓarayi, ihu ɓarayi jama,a a zo ga ɓarayi"
Nasir da yake wanka ya yi saurin ɗauro towel jikinsa duk kumfa domin ya ji wannan baƙon al,marin alama ce ta babu lafiya, Meenal ganin Hibba tana ƙoƙarin rufa tabarmar kunya da hauka ne Meenal ta ɗaga hannu ta kifa mata mari, da sauri ta dafe kunci cike da mamakin sa ya sa bakinta ya ƙi rufuwa, hatta Husna ta tsorata da matakin da Meenal ɗin ta ɗauka, a daidai lokacin ne Kusan tare Nasir suka zo da Sadiya don jin ba,asin abin da yake faruwa....
MAMAN AFRAH
09025576222
https://chat.whatsapp.com/CoSIFObGSJeG4TLAuJwo3J?mode=hqrt1
*RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)
NA
MAMAN AFRAH
. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*
BOOK 1
PAGE 2️⃣9️⃣
UMMA
Addu,a take amma kukan da take na hawaye, kuka ne marar sauti wanda ambaliyar ruwan hawayenta ne kaɗai suke nuni da cewar kuka take sai bakin ne kaɗai yake kai komo, kai komo na addu,a da kuma kai komo na kukan da na sanin abin da ta aikata tun da dai ga shi ba a kai ga samun biyan buƙata ba matsaloli maau tarin yawa sun baibaye ta matsala ta farko riƙe ta da gawar ta yi matsala ta biyu gabaɗaya maganin ma ya zuba kuma ba a yi aikin da ya dace a yi da shi ba, wato aiki dai bai kammalu ba.
Jin ta kakare a wajen karatun da take sai ra ji ta ƙi gana ta ƙi ba ya sai wani abu da take ambato wanda ita kanta ta kasa bambance cewa karatu ne ko kuwa waƙa.
Jin ta take kamar ba a duniya ba idanu ta rufe gam tana tunanin mafita, ji ta yi an ƙarawa hannu da ƙafarta kaimi wajen riƙo, hakan ya sa ji duniyar ta mata zafi tana jin ina ma tana da damar da za ta tashi jama,ar gidan wataƙila su su kawo mata ɗauki amma yanzu lamarin sai saɓ barka. Kafin ƙiftawar ido sai ganin Malam Kalla ta yi a hankali yana tashi zaune har ya kai ya zauna dangargar.
Salatin da ta warto a bakinta wanda ba ta sanya da aka yi ba har ya fito fili ya karaɗe ɗakin tamkar landan ya taƙarƙare yana kiran sallah. tun daga salatin nan bakin Umma bai samu damar warto wani furuci ba ko da kuwa waƙa ce ba karatu ko addu,a ba. Sai kuka da take yi kamar an buɗe famfo zuwa yanzu taimako take nema ba ta ankara ba sai kawai ta ga Malam Kalla ya ɗauke hannun sa daga riƙon da ya mata na ƙafa da hannu ya ya ɗauke ta ya ɗora a cinyarsa duk da ƙoƙatin fisge kanta da take yi daga gare shi, tashin hankali wanda ba a saka masa rana jinta zaune a cinyar gawa har gawa tana miƙa baki saitin kunnenta tana mata raɗa da ƙarfi ƙirjinta ya buga wata irin karkarwa da jikinta ya ɗauka ita ta saka ta buɗe idanunta sai lokacin ta gane ba gaske ba ne a idanun zuciyarta ne da sauri ta mayar da kallonta kan gawar ta ganta tana a yadda take hannun gawa riƙe a ƙafa da hannunta wata nannauyar ajiyar zuciya ta sauke a fili.
Sai lokacin ta fahimci cewa tsabar halin firgici da ruɗanin da take ciki ne ya sa ta kissima wannn abun na ganin gawar ta ɗora ta a cinya, wannan ya ƙara ruɓanya halin tsoron da take ciki hakan ya sa ta saka a ranta duk runtsi sai ta kuɓuta, jan ƙafarta ta fara tana daga tsugunnen amma sai ta ji gawar kamar ta fisge ta, hakan ya sa ta yi zaman ƴan bori a cikin ruwan fitsarin da ta yi ɗazu. bata damu da hakan ba ta shiga jan jikinta don ta gwammace ko da rarrafe ne ta bar gidan.
Gani ta yi yadda take jan jiki za ta gudu tare suke da gawar domin motsi kaɗan sai ta ga gawar ta biyo ta ma,ana daga Umma ta ja sai ta ga haɗe take ja da gawa, amma bata damu da hakan ba ta bari idan suka je bakin ƙofar gida ta san yadda za ta yi ta tsere in ya so ko da a ce a wajen ne ta bar gawar a ɗauke gawar daga baya a kan ta zauna cikin wannan balai,. In ban da ma son zuciya irin nata kuma saboda neman biyan buƙata a yadda take da masifar tsoron gawa ba ta taɓa.zaton har za ta zo wajen gawa ba.
Dakyar take jan jikinta saboda nauyin gawar Malam Kalla da take ja, a haka ta daure har ta fito tsakar gida inda su Abba duk suke yashe kamar matattu. Har lokacin gawar a ƙame take, sai dai kash! Umma tana shirin kama hanyar ƙofar gida sai ta ji gawar ta fara rimjayarta Umma a zuciyarta ta ce ko ana ha maza ha mata sai ta ƙwaci kanta. A haka tana ja har wajen ƙofar fita sai dai tana shirin yadda za ta yi ta ɓanɓare gawar sai kawai ta ji kamar wanda aka ɗaga su sama daga ida har gawar ta gansu suna tafiya luuuu ba au yi masauki ba sai a tsakiyar ɗakin inda suke a ɗazu wato gawa ta koma gurbinta inda aka ajiye ta gaka ma Umma ta koma mazauninta inda take a gaba gawa. Umma ganin hakan ya sa ta rushe da kuka mai sauti a fili tana faɗin
"Wayyo na ga ta kaina, Aliya kin haɗani da jaraba ke kina can ɗakin mijinki, ni yau bami da tabbas ma zan kwana a ɗakina, sannan igiyar aurena ma tana wala,ali" Ta faɗa jikinta duk yana karkarwa Allah ne kaɗai ya san halin tsoron da take. Kuka take wiwi tana rayawa a ranta shiknn asirinta ya gama tonuwa tun da gawa ba za ta ɓanɓaru daga jikimta ba, sannan wani babban tashin hankalin ma da ta tuna cewa matsawar gawar nan ba ta sake ta ba idan gari ya waye za a iya samun wasu jama,ar su zo sannan ya zama wajibi kowa ya ganta kenan asirinta ya tonu. Kamar ƙiftawar idanu sai ta ji an saki hannunta an kamo wuyan hijabinra da farko ma ta tsorata fiye da kima domin a tunaninta maƙogwaro za a shaƙe mata a kashe ta ita kuma ganin gawa muraran tana rike da ita ya ƙara saka mata tsoron mutuwa, nan suka shiga kiciniya iya da gawa har hijabin ya yage!.
Kamar daga sama ta ji wata murya ta ce
"Lubabatu!" Gaban Umma ya buga da ƙarfi har ba ta san lokacin da wata tusa mai balain ƙara ta kuɓuce mata ba sai ƙara ta ji bobott tana fitar da iskar. Jikinta kamar mazati haka yake rawa bata taɓa jin tsoro irin na yau ba gabaɗaya wani gumi ya wanke ta kamar an sheƙa mata ruwa, faɗuwar gabanta ta tsananta yanzu kam ta tabbatar sai yadda hali ya yi shiga motar mai taɓi, don ta ga gawa ba ta da niyyar sakinta wato babu niyya ango ya kwana da wando!.
Hankalinta ya kai ƙololuwar tashi, jin sunanta da aka kira kuma ba ta ga kowa ba sannan gawar dai ba ita ce take magana ba hakan ya sa Umma ta fara tunanin ko dai taɓin hankali ne ya samu ƙwaƙwalwar ta da za ta ji an kira sunanta.
Sunanta da aka kira a karo na biyu ta shiga amsawa a tsorace sai ta ji an ce
"A gobe da safe za a rufe ku a kabari tare da Malam Kalla, don haka kina da damar ƙarasa aikinki na zuba maganin, don wannan hannun ba zai taɓa.sakin jikinki ba sai dai a binne ku a tare"
Idanu Umma ta hau wurwurgawa jin wannan batun sai da hakan uanyi sanadiyyat ƙwacewar wata ƙaramar gudawa, ta sassauura murya a ranta tana faɗin to ko dai mala,ikan mutuwa ne ya zo mata a ɗakin Malam Kalla.
"Cikin faɗuwar gaba ta hau faɗin
"Yanzu zan tafi gida, dama don bai saka min ƙafa ba ne, wallahi tallahi ina da rai ban mutu ba shi ne ya mutu!" Wata irin dariya aka sheƙe da ita Umma sai kallon kowa na ɗakin take amma ta ga ba su ba ne.
Ta ji ana magana da murya kamar gargaɗi aka ce
"Ɗayan biyu ko dai a binneku tare ko dai a datse mki ƙafa da wuya sannan ne za ki kuɓuta" Umma tana hawaye ta kalli ƙafarta da take manne da gawa ta fara kwatanto yadda ba za ta yi kyan gani ba idan babu hannu da ƙafa, wato babu hannu ɗaya babu ƙafa ɗaya.
Kamar al,mara sai ta ga idon Malam Kalla guda ɗaya ya buɗe da sauri ra rufe nata idon tana son tuno wata addu,a da ta iya domin komai ya kwance mata, cikin ikon Allaj ta samu ta kamo sunan Allah Al,maliku ta shiga maimaitawa sai hawaye da suke zuba kamar an buɗe famfo. Tana cikin hakan kamar a mafarki sai kawai ta ji hannun gawa ya fara sakin wuyan hijabin da aka shake da alamar an fara sassauta riƙon, kaimi ta ƙara wajen ambaton sunan Allahn amma ko idanun ba ta buɗe ba, a haka sai da ta ji ƙafa da wuyan sun saki, sannan cikin faɗuwar gaba ta yi saurin jan mayafin ta rufe gawar, ba ta jira komai ba ta fara rarrafe saboda ta san a halin da take ciki yanzu ba za ta iya tashi tsaye ba haka ta rarrafo ta fito cike da tsoro da fargaba, tana fatan Allah sa haka ne bakin wahalarta, wato kar sai ta zo fita daga gidan a ƙara mayar da ita ɗakin.
Tana haki ta warci takalmanta a hannu ba don ma kar a ga baƙon takalmi ba, da babu abin da zai saka ta ɗaukan wani takalmi tashin hankalin da take ciki ma ya ishe ta. Haka ta taho gwiwarta tana zafi saboda yadda take cin karo da dutsi da kuma ƙananan itace suna cake mata gwiwoyin.
Sai da ta fita daga gidan ta sako bakinta a zauren gidan ta dage ƙarfinta ta ce
" Malam Kalla!."Ta na faɗa ta juya da rarrafe hannunta da takalmanta ta ci gaba da rarrafawa tana fatan Allah sa dai muyane gidan sun falka daga suman dolen da ta saka su wanda ga shi ita kanta ba ta samu biyan buƙata ba. Sai da ta ɗan yi tafiya sannan ta je kusa da wani bangon jikin wani gida ta dafa ta miƙe tsaye har lokacin gabanta yana dukan lugude tsabar faɗuwar da yake. Haka ta samu ta lallaɓa gida tana jin jikinta kamar an cire mata ƙarfi kwata -kwata, dakyar ta shiga ta yi wanka shi ma ruwa kawai ta kwara babu nutsuwar yi da sabulu kasancewar tana tsoron Abba ya dawo ya ganta da kaya a jiƙe ga shi har da ƴat guntuwar gudawarta da ta saki a cikin kayan. Alwala ta yi ta koma ta zauna hat lokacin gananta yana faɗuwa. Tana jin yadda wayarta take ta ruri amma ta kwanta lifet a kan tabarta tana jin yadda har lokacin ƙirjinta yake fat-fat. Ta san kuma ba kowa ne mai wannan kiran ba sai Aliya za ta dame ta ita kuma yanzu ita kanta ba ta da nutsuwar yawan surutu, don gabaɗaya a firgice take fatan ta Allah sa ta iya yaƙi da zuciyarta kar Abba ya gano a halin da take cjki.
Ta jima a kwance tana ta jan lahaula wala quwwata illah billahi aliyal azim. Don daga ta rufe idanunta sai ta ga Malam Kalla ta rasa yadda za a yi ta daina jin bugun zuciyarta yana tsananta tana tsoron kar wani ciwon ya kama ta sanadin yawan firgicin nan..
A can gidan Malam Kalla kuwa Umma tana ambaton sunansa sai kowa ya tashi daga gajeran suman da ya yi, haka aka ci gaba da koke-koke tamkar babu wanda ya suma to kowa ma ya manta abin da ya faru, su Abba ma haka suka jajanta wa iyalan nasa tare da masa addu,a suka fito suka nufi masallacin don yin sallar isha,i.